Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE



You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kara domin kuwa an zo dayawa, 'yan uwan Lukman ta ɓangaren mahaifiyar sa duk sun zo, ga 'yan uwan su Najeeb da su ma su ka cika wajen.

Tsakanin ma'auratan su ka yanke shawaran sunan da za a sawa yarinyar. Farida kam ba ƙaramin mamaki ta yi ba da Najeeb ya kira ta daga masallaci yana faɗin sai ta kawo kuɗin suna domin an samu *little Aisha Farida*

Bayan sun gama waya ta je ta ɗauki 'yar tana ma ta addu'a. Sabreen da ke kwance sai murmushi ta ke yi...


..........................


Rayuwa na cigaba da tafiya shekaru sun fara ja domin kuwa an samu haɓaka na arziƙi da iyali.
Najdah da Anas sun sake haifan mace inda su ka sawa 'yar su sunan *Aisha Amira* aka yiwa marigayiya Aisha takwara.

Farida ta sake haihuwan namiji bayan Zafreen ta cika shekara biyu su ka yiwa Daddy takwara *Adam * suna kiran sa da *Aasim*

Sabreen ma ta sake haihuwa bayan Little Farida, shima ɗin CS aka ma ta dan ance da wuya ta iya haihuwa da kan ta. Sun samu *Muhammad Mubarak*

Baffa Musa da iyalen sa na zaune lafiya kowacce ƙoƙarin faranta ran ɗan tsoho ta ke. Amma alamu sun nuna Amina ta ci galabar sace zuciyar wannan tsoho, ilimi da wayewa sun sa duk abubuwanta sun banbanta da na sauran matan. Ba ta ganin tsufan sa kwata-kwata, duk ranan girkin ta haka ta ke birkitashi da salon ta na matan zamani wanda ya ke sa ya ji ina matan sa su ka shiga lokacin da sauran mata ke koyan dabarun sarrafa miji. Abubuwan da ya ke yi yanzu da wanda Ummi ke ma sa ko lokacin yana matashi bai samu wannan gatan ba.

Yakubu ma shekara ɗaya bayan haihuwar Zafreen ya angonce da amaryar sa Halima.

A ɓangaren Aneesa da Majiddah ma sun haɗe kan su suna zaune lafiya. Duk da Aneesa na zuwa aiki hakan bai hanata samun lokacin miji da 'ya'yanta ba. Bayan Mujahida haihuwa ta tsaya ma ta amma Maijiddah ta samu Yusuf bayan Al'amin ga kuma tsohon ciki da ta ke da shi yanzu. Shi kam AbdulWahab sai dai yai ta hamdala kawai domin kuwa kwanciyar hankali da nitsuwa sun samu gindin zama a gidan shi...

............

Zama aure sai haƙuri, akwai soyayya, akwai faɗa, akwai matsaloli amma idan kuka san yadda za ku dinga tafiyar da lamuran ku sai ya zamana duk inda matsala ta kunno kai za ku samu mafita cikin ƙanƙanin lokaci.

Najeeb da Farida su na nan su na soyayyar su, su na abubuwan su ma su sanya farin ciki da jin daɗi. Idan ana aiki a office jiki ya buƙaci abubuwa, sai a kashe wuta a rufe ƙofa a cigaba da abubuwa kawai 😂
It wasnt a perfect life, they werent perfect. Su na faɗa suna samun saɓani kuma suna soyayya. Ba abinda su ka maida hankali akai kamar tarbiyyan yaran su da kuma tsare gidan su da yawan addu'o'i da yawan sadaka da kuma taimakon mabuƙata. Shiyasa lokacin da Sabreen ta buɗe Foundation ɗin ta, duk wata su na zuba maƙudan kuɗi a ciki saboda a samu a tallafi mabuƙata...


Mrs Comfort ta mutu kafin Naomi ta samu lafiya, ta samu lafiyan ne bayan Boka Ifagbemi ya mutu. Chan wani ƙauye a Owerri Naomi ta tsinci kanta lokacin da hankalinta ya dawo jikinta. Mutanen ƙauyen su ka ce ai tafi shekara biyu tana hauka. Su su ka haɗa ma ta kuɗi su ka bata kaya ta shiga mota sai Kano. Da ƙyar ta samu ƙaninta Abel saboda ya riga ya tashi a gidan su na da. Bayan ta samu masauki a gidan Pastor kafin aka sanar da ita mutuwar mahaifiyarta ta yi kuka kuma ta yi baƙin ciki sosai. Daga ƙarshe dai da ita da Pastor su ka je gidan su Najeeb inda ta ba wa Najeeb da Farida haƙuri. Sun riga sun yafe ma ta tuntuni, haka ta tafi tana kuka. Neman Maureen ƙawarta ta shiga yi inda ta gano ta bi wani chief ne hotel aka neme ta aka rasa har yau. Zance dai da ya fi tabbata shi ne an tsafe Maureen ne. Naomi ta yiwa kan ta karatun ta nitsu ta koma zama a gidan Pastor tana yiwa church ɗin su hidima alƙawari ma ta yi za ta zama Nun saboda ma kar ta yi aure. Pastor dai ya ba ta shawaran ta ƙara tunani a kai....


Rayyan kam ya rasa Farida har abada. Matar sa Aisha tana ƙoƙarin kyautata ma sa, sai dai har yau akwai ƙaramin gurbin Aisha Farida a zuciyar sa. Suna zaune da matar sa da 'ya'yan su uku Kamal, Abdullahi da Zainab

.......... .......... ........


Gaba ɗayan su su ke airport ɗin. Ƙarshen shekara ne inda iyalen uku su ka shirya zuwa Maldives da kuma London dan yin hutun ƙarshen shekara.
Lukman da Sabreen suna tare da Little Farida 'yar shekara uku sai Mubarak ɗan shekara ɗaya.
Najdah da Anas ma na tareda Najeeb Bobo da kuma Amira 'yar shekara biyu.

Sai zugan FARNAJ
Yaman ɗan shekara biyar
Zafreen huɗu
Aasim biyu da kuma babyn da ke cikin Farida ɗan wata biyar...


..............

...Maldives 2017...



Wajen beach ɗin ya cika da mutane kala-kala. Kowa ka gani yana sha'aninsa ne a wajen.

Wani mutum ne ya hango Zafreen da Little Farida su na wasa a wajen yashi yaran sun burgeshi. Shima tareda ɗan sa Nasir su ka zo beach ɗin tunda mai ɗakin sa shekararta ɗaya kenan da rasuwa.

Jin suna ingautsan Hausa Larabci da turanci ya sa su ka ƙara burgeshi. Ya ƙarasa wajen su riƙe da hannun ɗan na sa ɗan shekara bakwai.

"Hey pretty" ya faɗa yana kallon Little.

"Ya sunan ki" little ta kalleshi daga sama har ƙasa kafin ta ce " Aisha Farida Lukman Magaji"

"Wow what a cute name"

Kafin ya tambayi Zafreen ta yi caraf ta ce " my name is more cute than hers"

Ya ce " Oh really and whats your name?"

"Nabeelah Zafreen Najeeb Adam Jibo, see i have the most cutest name in the world and i'm also a princess" ta faɗa tana cuno baki

Yai ƙaramar dariya ya ce "where are your parents?"

Dukkan su biyu su ka ma sa nuni da inda iyayen na su su ke.

Mutumin yai murmushi tareda nufo su Najeeb saboda kodan yaran da su ka burgeshi yana son ƙulla ƙawance da iyayen su tunda shima ɗan Nigeria ne...

Bilal yana magana da su Najeeb inda ya introducing kan sa a matsayin Engineer Bilal Bello Bukar sai ga Bobo ya zo da gudu yana kuka.

Wajen Anas ya nufa yana kuka sosai. Sai ga sauran yaran suma sun iso wajen da gudu.
Anas ya tambayi ɗan na sa ko mi ya faru sai Bobo ya nuna Zafreen.

Farida ta kalli Zafreen wanda ta yi tsaye ƙyam da ita ba ko tsoro a idon ta.

Farida ta ce " mi ki ka ma sa?"

Zafreen ta sa hannu a ƙugunta tana faɗin " ce min yai 'yar lukuta, and mommy i'm not fat"

Farida ta harareta ta ce " bakin ki ne i'm not fat ai, zo nan na cire bakin rashin kunyar na ki"

Najeeb ya ce "princess zo nan" Zafreen ta je wajen Najeeb da gudu tana dariya.
Little Farida ne ta faɗi abinda Zafreen ta yiwa Bobo. Marin sa ta yi sannan ta watsa ma sa yashi a fiska.

Kowa ya juyo yana kallon Zafreen wanda ko'ina ta je sai ta nuna halinta na rigima, ƙiriniya da masifa.

Farida ta ce "wannan 'ya wannan 'ya"

Najeeb ya harareta ya ce " Thank God princess gado ta yi"

Gaba ɗaya wajen aka sa dariya. Farida kuma ta haɗe rai, ƙarshe ita ɗin ma ta joining na su aka cigaba da dariyan ana yi ana tuna baya..



*Anan jirgin sakatariya ta ya sauka*

*Alhamdulillah*

*The end*

*Anan na kawo ƙarshen labarin Romantic Comedy mai taken SAKATARIYA TA, da fatan kun ji daɗin karanta shi. Kura-kuren da na yi Allah ya gafarta min. Duk da ya kasance RomCom hakan bai hana shi zuwa da darussa na rayuwa ba. Rayuwar gaba ɗaya cike ta ke da ƙalu bale. Labarin Najeeb da Farida was not perfect and soyayyar su ma ba perfect ba ce, dukkan su suna da flaws na su. Amma su kan yi ƙoƙari wajen saita tsakanin su cikin ƙanƙanin lokaci. Yayinda Najeeb ke da sanyi ita Farida 'yar zafi-zafi ce*

* labarin sakatariya ta labari ne akan yadda wata sakatariya ta sace zuciyar Ogan ta. Note that, in reality mafi yawanci secretaries mata za ka ga suna ƙoƙarin shiga rayuwar Ogan su, idan Ogan bai kai zuciya nesa ba su zo su fara yin abubuwa tsakanin su and mafiyawanci za ka ga Ogan magidanci ne. Akwai wassu secretaries kuma wanda su ke munafukai ma su haɗa guri, akwai wanda su ne ke hana ruwa gudu a kamfani ko wajen aiki. Akwai wanda kafin ka ga Oga ko file ɗin ka ya je wajen Oga to sai ka bada cin hanci. Ga su nan dai birjik. Da sakatare namiji da sakatariya mace akwai na banza akwai kuma na ƙwarai. Whether namiji ne ko mace mu ji tsoron Allah a duk inda mu ke aiki sai ka ga an samu cigaba mai amfani*


*ban yarda wani ko wata ya sayar min da labarin nan ba, ko kuma a karanta shi a youtube channels. Ko a yaɗa shi ta ko wanni fanni. Akwai wanda sun fara haɗa documents na labarin nan, su ma su sani ba da yarda na bane. Akwai wanda su ka yi ta sharing labarin nan bayan sun san na kuɗi ne. Har wassu idan an mu su magana su ke maida martani da furuci mai muni. Gaskiya ba ku kyauta ba.*

*Alhamdulillah na samu alkhairi dayawa dalilin rubuta labarin nan, wanda su ka biya jazakumullahu khairan, wanda bayan sun biya sun haɗa da wani ihsanin kuma ina godiya Allah ya saka muku da mafificin alkhairin sa.*

*zan cigaba da labarin Tsohuwar soyayya daga gobe Insha Allah. Wanda ba su samu daman biyan sa ba, akwai free story da zan yi immediately bayan Tsohuwar soyayya za su iya jiran wannan idan har Allah ya sa muna cikin ma su rai da lafiya*


*Suna na Azizat Hamza ina yiwa dukkan masoyana fatan alkhairi. Ma'assalam*





































































































































An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment