Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fara yi miki sannu da zuwa,ina Ra'is din ya jikin nasa"
"Hmm,akwai abinda ke damunka nake tunani gashi baka walwala,yana hannun Abdul yanzu zasu shigo a rubuto masa magunguna ,anyi masa allurai,sai dai kudin daka bayar busu isa an siyosu duka ba,ni kuma babu kudi a gu...
Bata karasa maganar ba sallamar su Abdul ta katse ta da ya shigo,sabe da Ra'is a kafada da Ra'is din ke shan alawa,daya hannunsa kuma rike da ledar maganin,sallamar suka amsa masa dukansu,kannensa suka masa sannu da zuwa ya amsa ya zauna akan kujera ya sauke Ra'is shima kan kujerar yaran suna yima Ra'is ya jiki
Abba Aliyu yayi gyaran murya ,ya kalli Hauwa'u yanasan sanar musu lokacin ranar Rufaida da Abba Bukar yasa,dan boyewar batada anfani tunda Allah ya gani ba shida laifi shi,magana ya soma
"Jiya da nayi waya da Yaya Bukar ya shaidamin sun saka ranar Rufaida wancen satin yau saura sati uku nan gaba"
Abdul da yaji maganar kamar dirar aradu
"What Abba mai kake fada Rufaidan za'ayiwa wannan auran biki wata guda kamar wata bazawara aiko masu kudi da suke tada kai dasu basa irin wannan auran sai....
Abba cikin bacin rai ya soma magana bai bari Abdul ya gama tasa maganar ba don batun yau ba ya fahimci Abdul wata rashim kunya yake ji dashi ma yi masan zaiyi.
" Sai Ubanka kome zaka ce ,dan uwarka yarinyar ta samu miji yana santa sai aki aura mata shi,so kake atasa ta a dunga kallo,kota dinga yi mana jajibe jajiben samari wawaye da busu san darajar dan adam ba"
Ummi Hauwa'u da take jin maganarsu saidai ta kasa tsaidasu saboda yadda ita ma ranta yake bace a wannan lokacin,ita da 'yarta a dauke mata ita kan kuskuren da ita bata ma gansa ba,dan zuwa yanzu ta fara gajiya da halin Aliyu komai za'ayi baza'a shawarce taba saboda son kai irin nasa
Abdul ya dan sassauta murya ganin mahaifin nasa kalaman da yayi masa sun bata ransa har yana zaginsa da kafin kaji Abban nasu yayi zagi to tabbbas zaka dade
"Amma Abba ai karatu zata cigaba dayi da mun kyaleta,aure lokaci ne ai koda ma ba karatun zatayi ba, mu ba zamu gaji da ganinta ba dadai auran Yaya Wahid da zatayi gwara ta shekara goma ba aure, kota auri wancen saurayin nata dukda ba'a sansa nake ba,haba Abba maiyasa kake kokarin manta kiyayyyar da Umma Jamila ke gwada ma..."
Cikin zafin nama Ummi Hauwa'u ta taso daga Inda take ta rufe bakin Abdul ta wankesa da mari,dan idan tabarsa dukda ita ma ranta a bace yake da Abba Aliyu amma tasan Abba Aliyu uba yake ga Abdul bazata bari ya cigaba da sa'insa da Ubansa ba,dan bats yimasa irin wannan tarbiyyarba ita bata tana sa'insa da Abbansu a gabansa ba,dan yau kenan ka haifesa ne amma baka haifi halinsa ba,gashi a gaban kannensa,hannunsa taja da karfi zuwa upstairs tana magana cikin fada
"Abdul baka da hankali mahaifinnaka kake fadawa haka,kamanta duk karkashinsa muke yanada ikon zartar da hukunci akanmu...."
Da wannan maganar suka karasa hayewa Upstairs din da Abba Aliyu ya bisu da kallo da ransa ke masa tukuki yanzu ace Abdul shike fadamasa bakaken maganganu har haka gaban sauran kannensa dukda yasan ya musu laifi amma dai abinda Abdul yayi masa ya bata ransa matsayin Abdul na dan cikinsa koshi sa'ansa ne sai haka ,baya tunanin Hauwa'u tanada laifi wajen lalacewar yaran da yake nema yayi yanzu,saidai zai yiwa tufkar hanci,kofa yayiya mike ya duba magunan Ra'is da suke leda ya dauki kati yaje ya ciko masa ragowar magunan da aka rubuta masa
Yaran da babu wanda ya shiga maganar da tsoro fal ransu ,dansu basu taba cin karo da wannan matsalar ba bare su saba da ita tunda suka taso a gidansu ba akwai girmama juna atsakaninsu amma lokaci guda gashi ana musayar magana tsakanin Abbansu da Yayansu busu san meke shirin faruwa da suba Ra'is da kowa yaki kulasa kuma yaji hayaniya da baisa ba da jiba ya rushe da kuka Rumaisa ta daukesa tahau lallashi dan ko kusa bata yi gigin kaisa gurin Umminsu ba dan a yadda taga bacin rai a ranta ta iya dukanta ma"

Team of Rufaida ,team of AbdulWahid,team of AbdulRa'uf

Team of Ra'uf
Anya ba za'a yiwa AbdulRa'uf sakiyar da ba ruwa ba koda yake dama dai anmasa saidai ya rungumi sorry
Team of Wahid
Ya kuke tunanin zata kasance idan Hajiya Jamila taji labarin.wannan bikin anya zata yarda kuwa?kai akwaifa gwarama a gaba nake tunani. Nidai na fece bani na fada baπŸ˜‚πŸ˜‚πŸšΆπŸ½β€β™€οΈπŸšΆπŸ½β€β™€οΈπŸšΆπŸ½β€β™€οΈπŸšΆπŸ½β€β™€οΈ
A suburbudo ruwan comments aga typing nagama sa ayauπŸ˜‚πŸ˜‚ basai gobe baFJininmu 'daya

By Sadiya Khalil
Page 39


"ZARIYA"
"Wasila mikomin wayata naga tana kara an kirani"
Hajiya Jamila tayi maganar da suke zaune da sauran matan gidan a babban falo suna fira wasila da itace ta rage a gidan bata zuwa makaranta ta dauki wayar tana game
Wasilar ta danne wayar silent
"Umma bafa kira a kaiba sakone ke shigowa"
Aunty Amarya da take kusa da Wasila ta le'ka wayar
"Kai Wasila kema kin iya karya ko ga kirannan yana shigowa kin danne wayar a silent"
"Hajiya Jamila jin maganar Aunty Amarya yasata mikewa ta anso wayarta da har wani kiran ya shigo wancen ya katse,tsaki tayi ganin mai kiran Gwaggo Lariya ce kanwar surikarsu ,tasan tunda taga kiranta roko zatayi saida takoma ta zauna ta daga wayar da sallamarta saida suka gaisa Gwaggo Lariyar da labari ke cinta ta fara da cewa

" Gaskiya Jamila kin bani mamaki duk aminci na dake ace za'akai kayan lefen AbdulWahid saidai naji labari gurin Bukar"
Tsaki Hajiya Jamila tayi ka'dan ba tareda Lariyar ta jiba,ita to ta ina zata zama kawar Gwaggo Lariya bare suyi aminci bayan kanwar surikinsu ce itace Autar a gidan su surukin nasu ,shiyasa bata Gwaggo Lariyar bata girmeta ba,kuma Gwaggo lariyar takeso suyi aminci,saidai ita taki jinin mutum mai shishshigin da karya,da son abin hannun mutane, da Gwaggo Lariya dukta kware ta wannan fannin shiyasa yanzu ta kasa gasgata maganar Gwaggo lariyar ta dai daure tace
"Wacce irin magana kike ne,wanne irin laife kuma ni bansan wannan zancen ba"
Da mamaki sosai jin maganar da Hajiya Jamila tayi Gwaggo Lariya ta cigaba
"Kamar ya kina nufin ba kisan auren da Wahid zaiyi ba zai auri Rufaida ta wajen Aliyu"
Cikin firgici Hajiya Jamila ta ce
"Haba Gwaggo Lariya wacce irin magana ki kene"
"Abinda kika ji nace,Wahid zai auri Rufaida yauma su Hauwa'u zasu taho zariya gurin biki nufinki basu fadamiki ba..."
Ba tare da Hajiya Jamila takarasa jin zantukan Gwaggo Lariya ba ta kashe wayar ta mike zunbir
Mai yafaru ne Maman AbdulMalik ,lefen wa za'a kai"
Aunty Amarya tayi maganar cikin rashin sani ,dan itama ko kadan batada masaniya da saka ranar bikin"
Wani kallo Hajiya Jamila tayi mata da haka ta shige daki ta dauko hijabi da dan makullin motarta ta dawo falon tana kokarin fita Hajiya Kubra tayi kokarin riketa
"Haba Hajiya Jamila komai yayi zafi maganinsa Allah,mai Gwaggo Lariyar tace miki ko mutuwa akayi ne, ki fadamana"
Fisge hannun Hajiya Kubra ,Hajiya Jamila tayi daga rikon da ta mata cikin zafin zuciya ta fara magana
"Munafuka cikani,kunje an hada baki daku an munafurceni, wallahi yau sai na kashe waccen yarinyar da take kokarin shiga rayuwar dana,saidai nima yau akasheni ,dan dana hada zuriya dasu gwara na hada da kare"
Tana kaiwa nan ta fice daga falon gurin motarta ta karasa ta mata key ta bata wuta tavar gidan da wani irin gudu
Cikin sanyi jiki Hajiya Kubra ta dawo cikin falon Aunty Amarya ta kalleta bayan ta zauna ta soma magana
"Niko Maman Hussaini mu kira Gwaggo Lariyar muji maike faruwa,sai mukira Abban Wahid mu fadamasa,dan a yadda Maman Abdulmalik ta fita kinsan komai zai iya faruwa"
"Eh hakane kinyi tunani nima zullimin da nike kenan ,tunda gashi har tana kiranmu da munafukai"
Hajiya Kubra ta karasa maganar tana daukar wayarta ta lalubi numbar Gwaggo lariya
Wadda Gwaggo Lariyar tana can cikin zullumi dan sai yanzu tayi danasanin katobarar da tayi na fadawa Hajiya Jamilar dan tana tsoron hukuncin da zata dauka kan wannan maganar,tana wannan tunanin haka taji karar wayarta ta bugu daya ta dauka ta kara kunnenta,
Hajiya Kubra ta maida wayar a handsfree jin ta saga
Magana Gwaggo Lariyar ta fara
"Assalamu Alaikum ,Kubra lafiya kuwa,ina Jamilar ,muna waya naji ta katse ,dama batun auren Wahid fa Rufaida muke da za'akai lefe yau...."
Hajiya Kubra da bata bari Gwaggo Lariyar ta gama maganar ba tayi hantsarin katse wayar ta sake danna lambar Abba Bukar a kidime tana gudun mai zaije yazo,dan tana da yakinin gidan Gwaggo Zainabu Hajiya Kubra ta nufa
shima ringing daya ya dauka da sallamarsa
Ba ta jira sallamarsa ba tace masa
"Abban Wahid yanzu Gwaggo zainabu ta kiramu,tace ka aje duk abinda kake kaje tana san ganinka" da haka ta katse kiran dan bataso ta fadamasa gaskiyar lamarin saboda gudun kada hankalinsa ya tashi,lamarin suke tattaunawa akai bayan gama wayar tasu dan ko ita Hajiya Kubra ba tasan maike faruwa ba itada take 'yar uwarsa ,a ranta tana fadin amma Gwaggo Lariyar bata kyauta ba ,a matsayinta na kanwar mahaifiyarta shiyasa bata fito ta fadawa Aunty Amaryar ba don kowacce matsayinta daban ne agurinta
Tunanin kiran Gwaggo yake da yaga ita bata kirasa ba ta shaidamasa ba,kuma bata Saba yi masa kiranba ma,to mai yake faruwa ganin tunanin ba zai anfanesa ba ya sashi mikewa ya dauki makulle ya fito daga office dinsa ya rufe,massinjansa da ya tare sa,Abba bukar yace
"Ba tashi nayi ba,zanje wani guri na dawo,idan anzo ne mana kace ba nisa nayi ba su jira ni"
"To Allah ya kiyaye hanya masinjan ya fa da ya koma inda yake zaune"
"Amin kawai Abba Bukar ya iya anbata yabar wajen gurin aje motoci ya karasa ya shiga tasa ya tayar ya fito daga cikin makarantar ABU Zaria da a ciki yake aiki da tunani a ransa


****
RUFAIDA

Rufaida ta kalli himmin fulawar da Gwaggo take so ta kwaba tayin doughnut da cin-cin,da ta tasata saita kwaba zata bar gidan zuwa gidan Gwaggo Hajiya mahaifiyar Hajiya Kubra
" Gwaggo Allah na gaji ace aikin nan duk tare za muyi,maimakon ki bari su Aunty Samina su zo tunda yau zasu zo"
Rufaida ta karasa maganar tana kunbura baki
Gwaggo ta 'dago dakanta daga kwabin alkakin da take ta dubeta taga ta kunboro baki ta ta tabe baki tare da cewa
"Yarinya koda ma kuka zaki ba ba kunboro baki ba saidai kiyi,dan sai kin kwaba zaki bar gidan nan"
Rufaida ta dan lankwasa murya
"To Gwaggona naji zanyi yadda kikace amma dan Allah kiyarda na kira Harira ta tayani,muyi mugama da wuri"
Gwaggo ta zaro ido
"Wacce Harirar yarinyar da ko uwarta bata mora mata bare ke ta mora miki daga kawancen unguwa kinajin artabun da suke da Mamarsu ta katanga akan aiki,idan Mamarta tace tayi mata"
Kasancewar su Harirar makoftansu ne da suke shiri da Harirar a Unguwa itada Rufaida
"Eh dukda haka Gwaggo nasan ni zata tayani kinsan muna shiri sosai"
Rufaida tayi hanzarin cewa Gwaggo hakan dan karta kuma fadar wani abun
"To inanan dai zan jiyo ku ta katanga,dan indai Harira ce kinsan ba shiri ba kome kuke idan vatasa kanta ba saita iya watsa miki kasa a ido"
Da haka Rufaida ta mike daga tabarmar da suka shimfida a tsakar gidan ta zura takalmi ta janyo hijabinta jikin igiya tasa tana cewa
"Gwaggo saina dawo"
"To adawo lafiya'"Gwaggo tayi maganar tana maida kai ga abinda take,a ranta tana tunanin halin Rufaida batasan auren yaron kowa ya sani badan komaiba saidan halin mahaifiyarsa amma ko a fuska vazaka gane ba

A bakin kofar zaure Rufaida tayi kicibus Hajiya Jamila da take kokarin shiga ciki hartayi kokarin bangaje Rufaida Rufaida tayi saurin matsamata hanya ta kalli Hajiya Jamilar da kallon daya tayi mata taji gabanta ya fadi ganin yanayin annurin fuskarta babu shi anbaton Allah tayi kafin tayi saurin cewa
" Umma sannu da zuwa"
Hajiya Jamilar ta kalli mai mata sallamar tayi ido biyu da Rufaida da da idonta ya rufe bata san da mutum a zauren ba dan tunaninta yayi cikin gidan gaba 'daya wata irin fisga Hajiya Jamilar tayi mata zuwa cikin tsakar gidan tana cewa
"Wallahi yau sai na kashe ki,dan muddin ina raye dana bazai hada iri da kuba"
Jin maganar Hajiya Jamilar ya ankarar da Gwaggo inda a lokacin take kokarin wanke Rufaida da mari gurin Gwaggo ta karaso da niyyar kwace Rufaida Hajiya Jamilar tayi kukan kura ta angije Gwaggo tana cewa cikin 'daga murya" matsanan Munafuka angungunma ca kike yadda kika munafunci 'yan uwanki nima zaki munafunce nine,wallahi sai dai yau na kashe ta inyaso nima akashe ni dan bazan hada zuriya da wannan mazinaciyar uwarta taba ,",ta karasa maganar tana sake kwada wa Rufaida mari daga visa ni ta shake wuyan Rufaida"
Ganin haka yasa Gwaggo saka kuru ruwa tana ihu makwabta neman taimako
Lokacin yayi dai-dai da karasowar Abba Bukar kofar gidan ganin motar Hajiya Jamilar kofar gidan yasashi saurin kashe motarsa ya rufe ya isa cikin gidan harda gudunsa dan yasan,tunda yaga motar Hajiya Jamilar yasan akwai matsala
A lokacin da ya iso Gwaggo ta sake kukan kura ta nufesu tana kokarin cire hannnun Hajiya Jamilar daga wuyan Rufaida amma ta kasa Rufaidan sai zaro ido take
"Jamila wallahi idan biki saki wuyan 'yar mutane ba to wallahi a bakin aurenki"
Abba Bukar yayi maganar yana karasa shigowa ciki,da babu wanda yaji shigowarsa
Badan Hajiya Jamilar taso ba ta saketa
Ta kuma cigaba da dukanta,da alokacin makwabta sun fara shigowa jin kururuwar Gwaggon da suke,da kowacce take tsaye tana kallon ikon Allah,mai kuma Rufaidan tayi wake dukanta dan busu shaida fuskar Hajiya Jamila ba saboda ta juya bayanta
Gurin da suke Abba Bukar ya karaso ya kwace Rufaida daga hannun Hajiya Jamila da Harira da har da ita a masu shigowar tayi kokarin karasowa gurin Rufaida ta janyeta gefe
shiko Abba Bukar Hajiya Jamilar ya nufa da zafin zuciya ya kwashe fuskar da wani gigitaccen mari yayi ball da ita,ya fara dukanta yana cewa
"Ke dabba ce 'yar mutanan zaki kashe"
ganin yana kokarin cigaba da dukanta yasa Gwaggo rikesa tana basa baki
"Kan wannan 'diyar mazinaciyar ka dokeni ko,wadda danginta suka juya mata baya,to wallahi indai kukai kokarin aura mata 'dana saina kashe ta inyaso nima a kasheni"
"Da ubanki tayi zinar ko,kuma dangin ubanki ne suka juya mata bayan ko,kuma wallahi aure sai anyi shi ,kuma karki sake ki koma min gida ,na tsaneki da zama dake ,fitinanniya babu abinda auranki ya tsinanamin face asara"Abba Bukar yayi maganar cikin zafin zuciya
" Saina koma ,koda saki na zakayi saina zauna nayi zaman 'ya'yana"
Cewar Hajiya Jamila tayi maganar tana kokarin tashi tsaye
"Abba Bukar yace
" Bismillah ki koma wallahi da sai kin yi danasanin da tunda uwarki ta kawoki duniya baki taba yi ba"
Rufaida Hajiya Jamila ta nuna da Harira ke bata ruwa tace
"Kan wannan,Yarinyar da ko acikin dabbobi tafi su iya dabbaci saboda 'yar mungada ce, ka wulakantani gaban jama'a ko,bismillah Ku daura auran wallahi saikunyi danasani fiye da tunaninku" tayi maganar tana dukawa ta dauki makullin motarta ta soma tafiya
"Duk barazanarki ba zata hanani aurawa Wahid Rufaida koda ace vayasonta idan harni inasan ya aureta sai ya aureta,saboda bake kadai keda iko da 'danba" cewar Abba Bukar
Kofa Hajiya Jamila tayi ta fice
Sai bayan ta fita Abba Bukar ya jiyo ya bawa Gwaggo hakuri shima ya fice yana sanar dasu zai dawo gidan idan ya tashi daga gurin aiki
Makwabtanma hakuri suka bawa su Gwaggo suka firfito suna jinjina lamarin masu tsinewa Hajiya Jamila nayi masu zaginta nayi,da kwashe mata albarka,dama mutane jiran suke ayi,dan danki zai auri 'yar uwarsa saitazo tana hauka maiye laifin Rufaidan yarinya mai hankali.*JININMU 'DAYA*

By Sadiya Khalil❀️

40.

Hajiya Jamila da tunda ta fito gidan Gwaggo take kuka a cikin motarta bawai kukan danasani ba akan abinda tayi kokarin aikatawa da kuma furucin mijinta akanta ba illa tunaninta 'daya ina zata da wannan abin.kunyar ace dan ta zaiyi aure bata sani ba sai ana saura kwana uku kuma aure ma ya rasa wadda zai jajubo sai 'yar Hauwa'u da kowa yasan kiyayyar da take ma Hauwa'un,ganin tunanin ba shine mafita ba yasata yiwa motarta key tayi gidan Gwaggo Lariya

Abba Bukar yana fitowa gidan yatarar da kurar motarta kai ya girgiza ya shiga motarsa da tunanin abinda ya yanke aransa kai tsaye gidan wan mahaifinsa ya wuce Baba Ashiru,Abinda ya faru kaf ya fadamasa da kuma hukuncin da ya yanke a daura auren Wahid da Rufaida saboda baiga alamun Hajiya Jamila zata hakura ayi auren ba
Baba Ashiru dubesa
"Gaskiya Bukar kayi tunani me kyau,abinda ya kamata ayi kenan,tunda ita Jamila har yau bazata yi hankali ba kamar wadda ake zugawa"
"Wallahi Baba babu wata zuga danni sai yanzu nake danasanin aurenta ma....
Baba Ashiru yayi saurin dakatar da Abba Bukar maganar da yake yace
"Kul Bukar koba komai ai uwar 'ya'yankace ba kuda wata makankara sai dai muyita yi mata addu'a"
Abba Bukar ya mike ya na cewa
"Haka ne Baba ni bari zan koma wajen aiki dan Allah ka kira Baba Amadu kasanar masa dan Gwaggo da mukai waya tace gaban kaina na fara yanzu tun busu mutu ba"
Baba Ashiru yace
"Ina ruwan Zainabu ,to zan sanar masa da dukkan abinda ya faru zan fadamasa hukuncin da ka yanke amma bazan ce kai yanke hukuncin ba karmu sake yin laifi"
Abba Bukar ya fito daga dakin Baba Ashirun yana dariya
*******
Gwaggo ce tayi kokarin karaso wa inda Rufaida take ganin kowa ya watse daga gidan da ga Rufaida sai Harira da Gwaggon dafata tayi ta soma maganar ba tare da ta damu da Harira dake gurin ba dan abu ne akayi sa ba a boye ba
"Haba Rufaida kukan ya isa haka kinemi sakayya gurin Allah kawai"
Rufaida ta dan goge hawayenta ta dubi Gwaggo tace
"Gwaggo nidai dan Allah a fasa auren nan"
Gwaggo ta zaro ido tace
"Baki da hankali Rufaida auren za'a fasa saboda wannan shashashar yarinyar tazo tayi haukanta,kenan a fasa taci galaba akanmu,to koda Wahid baya sanki sai anyi auren nan dan akuntata mata"
Kuka ta kuma rushewa da shi tare da cewa
"Ni dai dan Allah Gwaggo a fasa ,kina gani fa kashe ni Umma taso yi,ga maganganun da take fada akan Umminmu,Gwaggo dan Allah mai muka yi mata"
"Kinga bafa za'a fasa ba, ita bata isa ta kashe ki ba haukan banza take,maganganu kuma taje tayi tayi ita ce mara aikin yi,kuma sharrin ta saidai ya bita"
Da haka dai Gwaggo ta lalla'beta ta daina kukan suka koma inda suke aikinsu suka cigaba dayi
***
Sallamarsu Ummi Hauwa'u ta katse firarrakin da suke jefi jefi suna aiyukansu da gudu Rufaida ta karasa gunsu ta rungume Aunty Samina dukda ba wani kuzari jikinta
Gwaggo da Harira suka amsa musu sallamar
Ciki suka karaso da fara'arsu suka zauna a babbar tabarmar da aka shinfida
Saida suka gaggaisa ,Aunty Samira ta dubi Rufaida tace
"Yanaga ba kuzari jikinki kamar kinyi kuka ga idonki duk ya kumbura"
Gwaggo tayi saurin cewa
"A'a ba wani kuka sauro ne ya ciccijeta jiya bata sa net ba"
Aunty samira shiru tayi vadan ta yarda ba
Rufaida ta ja hannun su Kalim da Khalil yaransu Aunty Samina dakinsu dan surutun ma batasan shi ko daya
Ummi Hauwa'u ta bita da kallo aranta tana tunanin tabbas da abinda ke damun Rufaida zuwa dare zata sameta suyi magana
Su Rumaisa ne suke shishshigo da kayan da suka taho dasu da sauran yaran Abdul kuwa da shiya kawosu baima shigo gidanba ya tafi gidan Gwaggo Hajiya gurin abokansa

A'a marhavin lale da kanawa,Malam yake maganar da murmushi fuskarsa da shigowarsa gidan kenan ya cikaro dasu Aunty Samina suna aikin doghnut bayan sun huta sunci abinci
Da murmushi a kan fuskarsu suka gaishesa ya amsa yana cewa ina su Gwaggon suka ce masa suna daki
Dakin ya nufa ya tarar dasu a zazzaune suna nunawa Gwaggo kayayyankin da sukai wa Rufaida
Gaishe da Malam sukayi ya amsa yana musu sannu da zuwa
Zuwa can ya nisa yace
"Yau ne daurin auren fa yanzu Ashiru yake sanarmin ina kokarin shigowa nan gidan ya kirani a waya,shine nazo nasanar muku zance na shirya yanzu ,bayan daura auren zasu kawo lefe" da haka ya mike ya bar dakin dan baya san jin wani zancen su yanzu haka

"Wannan wanne irin aure ne Gwaggo daga zuwan mu yau ace yanzu za'a daura"Momy Maryam tayi maganar bayan Malam ya fice daga dakin
Gwaggo da ranta ya fara baci ita ma
"To ya za'ayi Maryam yadda suka tsara haka za'ayi"
"A'a Gwaggo kuma fa kuna da hakkin magana akan 'yar nan ai ba 'yarsu bace su ka'dai,ya daga zuwanmu za'ace yau daurin aure gaskiya babu alamun gaskiya a auren nan"
Momy maryam tayi maganar
"A'a maryam kar kice haka,mudai yi musu fatan zaman lafiya"
Cewar Gwaggo
Ummi Hauwa'u bata ce komai ba tana zaune tana saurarensu har suka gama firarsu
*******
"Rufaida Dan Allah karki nunama yayyenki ko a fuska akwai abinda ya faru dazu"Harira tayi maganar tana dafa Rufaida da suke daki zaune itada harirar tun da su Aunty Samina suka karbi aikin
" Harira ke ma kinsan halina a 'dan zaman da mukai kinsan bazan iya fada ba,abinda kuma Umma tayimin lokaci ne watarana sai labari"
Cewar Rufaida
"Harira ta nisa tace
" nifa matarnan ta bani mamaki kai kace mahaukaciya ce ,kikama 'yar mutane ki shage,shegiyar mata kodaddar banza ita banda farin tama wazai kwasheta mai bakin hali,ai wallahi dan sunga kece shiyasa zasu hadaki aure dashi da wata fitsararriyar suka samu ai bazata yarda ba a rabani da dan arziki a hadani da irin tsiya....
"Kai kai Harira wannan surutu haka kinata kwashe mata zunubi kina dorawa kanki ta hanyar zaginta"
"Ai matar ce na lura da cewa cikin dabbobi Kafin asamu irinta za'a yara"
Rufaida tayi dariya jin maganar Harira

Aunty Samira da take tsaye bakin kofar dakin dasu Rufaida ke ciki azo kiran Harira ta tayasu aikin da suke tayi niyyar shigowa taji suna wannan maganar bata shiga ba ta dawo inda suke aikin tana jinjina lamarin aranta ashe shiyasa suka ga alamun damuwa a gidan da suka zo har Rufaida bata wani nuna murnar zuwansu ba,lallai akwai matsala a wannan auren amma yaza suyi itada ko kusa bataso auren nan Rufaida ba koda ma ba wata matsala dan tana son Rufaida kamar Samiha.
Aunty Samina ta kalli Samira tace
Yadai Samira maike damunki
"Kedai bari kawai Yaya ashe 'dazu surikar Rufaida ce tazo tayi wa Rufaida duka ta shake wuyanta ta kusa kasheta"
Maganar suka cigaba da tattaunawa saida Harira ta karaso wajen sukayi shiru


*****
Sallamar Abba Bukar a falo yasa kowaccensu amsa masa da kokarin yi masa Sannu da zuwa ya amsawa matan nasa da ko wacce da maganar dake bakinta ga mijin nata ganin vaidawo yadda ya saba dawowa ba dan har hudu ta gota yanzun daya shigo,maganarsa ya dawo dashi daga tunaninsu
"Yadai kowacce tayimin kasake kamar nayi tafiyar shekara ba wadda ta iya koda mikewa ta kawon ruwa" yayi maganar da murmushi kan fuskarsa
Hajiya Kubra tayi hanzarin cewa
"Abban Wahid ka manta yauba girkin daya daga cikinmu na Maman Wahid ne kuma tunda ta fita har yau bata dawo ba"
"Kinga Ku share zancen ta"
Abinda ya faru ya sanar musu,ya kuma sanar dasu an daura auren Wahid da Rufaida da azahar a babban masallacin Zariya, kowacce ta jinjina lamarin,
Ya sake cewa
"Har yau babu mai kawan abincin da ruwan"
Hajiya Kubra ce ta mike ta kawo masa abincin da ruwan kadan yaci ya aje yakallesu yace
"Kayan lefe suna gidan ,Baba Ashiru kuje ku dauka akai musu,nayi wa Wahid magana asabar zaizo ya dauki matarsa kayan dakin kuma acan za'a siya ayi komai"
"To Allah ya sanya Alkhairi", suka fada badan sukansu sunji dadin wannan auren ba,da wadannan tunanukan suka shiga ciki su kara shiryawa busu jimaba suka fito suka yi ma Abba bukar sallama da har lokacin yana falo yana yiwa Ubaidullah wasa da shi baya bukatar a kara shiryasa Aunty Amarya ta daukesa suka fita a motar Hajiya Kubra suka fita taja su zuwa gidan Baba Ashiru

Kaya kam sunyi kyau da tsari kala arba'in ne akwati 6 su Momy Maryam busu kushe kayan ba sai dai auren ne basa so ko daya da su Aunty Samina suka fada musu abinda ya faru da Aunty Samira taji su Rufaida suna tattauna maganar da Harira, sun bawa masu kawo kayan tukwici mai yawa daganan masu kawo kayan suka tafi da tarin kayan soye soyen da aka hada su dashi da lemuka da Abdul ya siyo musu aka basu.*JININMU 'DAYA*

By Sadiya Khalil

41.

yanzu Gwaggo Lariya inaji ina gani 'dana ya zai auri irin tsiya"
Hajiya Jamila tayi maganar bayan cire hannunta daga abincin da Gwaggo Lariya ta kawo mata.
Gwaggo Lariya ta kalleta tare da cewa
"Eh to muddin ki ka zauna ba,amma da zaki tashi ki rabawa malamai kudi sai kiga aiki,tunda dai bakyason

Please Login or Register in order to submit comment