Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dawo da mahaifinta Aliyu Bukar cikin garin Kano yana aiki a babbar makaranta wato jami'ar Bayero University dake Kano wato BUK inda yake zaune a gidansa mallakin kansa dake Rijiyar Zaki shida matarsa 'daya wato Hauwa'u da suke da yaransu shida AbdurRafi shine babba sai Rufaida mai bi masa sai AbdurRashid,Rumaisa,Rafi'a,Ra'is shine karaminsu.

Samiha Hashim Sarki 'kawar Rufaida ce tun daga primary har zuwa Secondary da suke tafiya tare aji 'daya benci 'daya dalili mai karfi da ya jawo amintarsu harta zama sun zama kamar 'yan uwa hatta iyayensu wasu 'yan makarantar tasu ma 'daukarsu 'yan uwa ne Samiha hafaffiyar garin Sokoto ce aiki ya maido mahaifinsu Kano Unguwar Nasarawa GRA da mahaifin nasu yake kwararran likita a asibitin Nasarawa matarsa 'daya Hajiya Maryam da yaranta Samira,Samina da sukayi aure,Samir,Saudat,Samiha,Samin,Samima.da a yanzu haka Hajiya Maryam ta aurar da 'ya'ya biyu Samira da Samina kowacce da 'danta 'daya,Sai Samir da yake aboki ga AbdurRafi da suke babbar makaranta Jami' a Yusuf Maitama Sule Northwest dake nan Kano wannan kenan

Samiha da take kokarin sa'ba Jakarta a baya ta dubi Rufaida tace "malama ba kyaji antashi kuma kinsan yau juma'a a gidanku zanyi hutun karshen mako" Rufaida da murna batasan sanda tazari jakarta ba saboda murna Aminiyarta zatayi hutun karshen mako a gidansu mikewa tayi tana cewa"Nifa bansan dagaske kike ba"Samiha ta harareta tace"aikema kinsan bana miki karya irin wannan"da haka suka fito ajin da suka hadu da sauran 'yan class dinsu suna firar yadda Sir AbdurRahman ya iya koyarwa suna gane lesson dinshi da shine malaminsu na karshen period yau da wannan firar suka fito zuwa kofar makarantar inda suka hangi motar Abbansu Rufaida dasu yake jira suka karasa sunayiwa abokan tafiyartasu sallama"sauran 'kannen Rufaida har sun shige bayan mota su Rufaida gaban mota suka shige Abba da yake kokarin tada motarsa ya kalli Samiha da take gaishesa ya amsa yacigaba da cewa"wato Samiha mungane saboda kawarki kike zuwa gidanmu duk hutun karshen mako kike yi mana acan?"murmushi Samiha tayi kawai dan tagane Abba ya gano saboda Rufaida take zuwa gidan Abban hutun karshen makon dan ita tana matukar son kawarta da a yanzu take jin Rufaida kamar 'yar uwarta ta jini dan ko Saudat da Samihar ke binta bata saba da ita kamar Rufaida ba ,Samiha ta canza maganar tace "Abba ya maganar Jamb 'din namu" Abba da ya maida hankalinsa ga tuki yace "oh Samiha anfara ne"Rufaida anan tasa baki tace" Wallahi Abba ba'afara ba Samihan ce batada hakuri kofa yau saida ta tanbayi wani malaminmu" Samiha tace" eh mana dole kice banda hakuri tunda ke bakyasan cigaba da karatun yanzu idan bama tunawa Abba har a gama bamuyi ba"Rufaida tace"ba wani nan wallahi ai kinsan Abba baya mantuwa a harkar karatu barema harda Yaya Saudat za'ayi kinsan tunda tayi candy bazai manta ba,ke dai azalzalar kice,"Abba murmushi kawai yake yana jin firar tasu yadda sukeyi wanima sai ya rantse ya da kanwa ne ko 'yan biyu saboda halayyoyinsu da sukazo daya a fisgema har yanayi suke da juna yanason wannan abotar yaran nasa da ta zama yan uwantaka bama gasu ba harga su iyayensu sun hada aminci tsakaninsu kai kace 'yan uwa ne a yanzu haka idan ba har an baka labari ba,Abba yana saukesu d ,yace zaije gurin abokinshi yaje ya dawo su fa'dawa Umminsu a dawo lafiya suka yi masa ya amsa da amin yasakan motarsa yabar gidan su kuma suka shige cikin gidan a fall suka sami Ummi suka yi mata sannu da gida Ra'is mai shekaru biyu yana ganin Samiha yayi gunta da yasaba da ita saboda yadda take masa wasa daukar Ra'is 'din tayi ta haye dashi sama tana mass wasa yana dariya Samiha kaya kawai ta canza ana Rufaida dan girmansu daya hakama kayan sawarsu iri daya ne yawanci saboda yadda iyayensu suke aminta sosai kaya ma kusan tare suke dinka musu Rufaida data fito daga bandaki da towel jikinta ta watso ruwa ta kalli Samiha tace "ya haka ba zakiyi wanka bane" Samiha ta dafe cikinta tace"yunwa nakeji nayi anjima "Rufaida tace" ba wani anjima ,bakyasan yin wanka sai dole kike 'daya badan kinso ba haka Ahmad 'din zai aureki ki bakyason yin wanka wallahi ya daukeki kazama"da Rufaida da tasan sunan Ahmad saboda labarinshi da Samiha take basu nashi kullum indai sun ha'du a makaranta to indai kana ajinsu sai Kasan labarin Ahmad saurayin Samiha a bakin Samihar "Samiha tace to"yi maza ki fadamasa"Samiha ta fice tana jiyo dariyar Rufaida

Samihan kai tsaye kitchen ta nufa ta samo abincin rana da miya taliya kawai tagama sai miya da take kan wuta da shigowarsu Ummi ta zuba markadan kayan miyan gurin datasan ana aje ragowar miya ta bude ta diba ta fito kai tsaye babban falo ta karasa bayan fitowarta kitchen din da ta samu AbdurRafi shi ka'dai ta masa sallama AbdurRafi ya amsa mata ya maida dubensa ga kallon ball din daya kori kannensa a falon yanayi ganin ancanza masa tasha ya juyo ya 'dan kalleta da ta zauna a kujerar dake gefen tasa ta tankwashe kafafunta akan kujerar ga remote tana dannawa tana lalubo tashar da takesan kallo yace cikin ha'de rai " waike Samiha ina kallo ya zaki canzamin tasha"Samiha tace"ai kaine Yaya AbdurRafi ko gaishe da nayi kaki amsawa kana can hankalinka yana kan kallon ball"AvdurRafi yace"ke Samiha banafa son karya a ina kika gaishe ni sallama kawai naji kinyi,ke dai kawai kinzo ki takurawa mutane indai kikazo gidan mutum bashida kata'bus"Samiha tace"kai Yaya AbdurRafi gaskiya bakayimin shaida maikyau ba amma bakomai nakusa daina zuwa ai"tsaki AbdurRafi yayi yace"yaushe ai sai dai in anyiwa wadda kike zuwa gunta aure ko an yimiki"Samiha tace"kai nifa Yaya AbdurRafi kadaina maganar idan munyi aure zamu rabu da Rufaida ga gida ga gida zamu zauna"AbdurRafi yace"Ku auri miji 'daya kawai zaifi"Samiha tace"kai Yaya"AbdurRafi yace"eh mana zaifi ai"Samiha ta canza firar da cewa "wai niko Yaya Rufaida ta baka labarin wani saban malaminmu da kuke kama yazo TP da ake turo masu Degree?" Tsaki AbdurRafi yayi yace "ke nifa kinga banasan shirme wallahi ni ka'dai Ummi ta haifa kuma ni ni ka'dai ne bada wanda nake kama a duniyar nan ma gaba 'daya kawai kuje Ku jajubo wani bakusan shi waye ba kuce ina kama dashi?" Samiha tace"haba Yaya AbdurRafi wannan dogon turanci haka daga nace kana kama da wani Allah ya baka hakuri,kuma ka masan shi waye 'dan Khalid Bashar ne" AbdurRafi yace"ke nifa Samiha ki dainamin maganar shi banaso,dama dan haka kikashemin kallon ball din danake"Samiha tace"Allah ya baka hakuri,amma nidai Allah naga kamarku"AbdurRafi ya mike yace"sai kiyi tayi ni kinga tafiya tama yayi gaba ya fara tafiya"Samiha da taga yana kokarin ficewa a falon da taga bayaso ace yana kama da kowa ta tsokanesa tana cewa "Yaya AbdurRafi Allah kuna matukar kama" murmushin mugunta yayi yana tuna abinda zai mata ya karasa ficewa daga falon gaba daya"Samiha ta bishi da dariya Ummi data shigo falon tana lallashin Ra'is da yake kuka taji Samiha na dariya tace"dariyar me kuma kike kuma kike kinje kin bawa yara yaro na sun yarmin dashi shine kike dariya ko?"Samiha tace"Ayya Ummi wallahi Rumaisa ce ta anshe shi da muka hau sama"Ummi Hauwa'u tace"to gashinan dai kin basu yarona sunyi fa'da da Rafi'a sunyarmin dashi,na 'daukama dariyar kike masa"Samiha ta anshi Ra'uf a hannun Ummi Hauwa'u tana lallashinsa tace"Haba Ummi ya kinsan nida Ra'is da amana,Yaya AbdurRafi nakewa dariya saboda nace yana kama da wani malaminmu yake jin haushi bayaso ace yana kama da wani"Ummi Hauwa'u tace"au wai saboda ance yana kama da wani yaji haushin Allah ya kyauta"Samiha tace"Amin dai Ummi" Samihan ta fara lomar abincinta data zubo tana bawa Ra'is Ummi ta wuce kitchen ta cigaba da aikin abincin da take Abba Aliyu ne yashigo gidan da motarsa ganin AbdurRafi ya budemasa gate "yace ya shigo ya shirya su tafi masallaci kasancewar yau Juma'ah yana shigowa falon yayi sallama,Samiha ta amsa masa takuma ce "Abba sannu da zuwa yace" yawwa Samiha ina sauran mutanan gidan" Samiha tace"Suna ciki Ummi kuma na kitchen"Ra'is da yaga Abbansu ya sauka daga hannu Samiha ya tafi gurin Abban nasu,Abba Aliyu ya daukesa yana cewa"nifa Ra'is shirin masallaci zanyi amma bari na tafi dakai na bawa ko Rufaida kai ne ko Rumaisa tunda kunfara batawa da yayartaka" murmushi Samiha tayi kawai ta harari Ra'is da haka Abba Aliyu yayi saman bene dashi 'dakinsu AvdurRashid kai tsaye Abba ya shiga yace ma AbdurRashid yayi shirin masallaci ya bawa Rumaisa Ra'is daya sameta a falon saman AbdurRashid yana fitowa daga dakinsu saboda tafiya masallaci yaga Samiha a falo da kwanon abinci a kan teburin tsakiyar falo tagama ci tana lashe hannu yace" uwar ci 'yanci kawai"Samiha tace"naji dai da ulcer ta kama nifa"AbdurRashid yace"ba wani aike cinki yayi yawa kuma ci babu kuf kullu jiya i......"jin karar takalmi yasa AbdurRashid kin karasa maganr yamayi had ficewa daga falon kar wani ya shigo yaji yana yiwa Samiha rashin kunya Samiha tace zaka dawo kasame nine mara kunya ganin AbdurRafi ne ya shigo falon ya wuce ko Samiha baikula ba tana kunshe dariyarta ganin wai shi ala dole yayi fushi da ita Rufaida tana zura kaya barci ta haye gado barci ya 'dauketa kasancewar basa taya Ummi abinci da rana saboda makaranta.


SADIYA KHALIY✍🏽*JININMU 'DAYA*♦️
By Sadiya Ibrahim Khaliy💞

Page 12

Sallamar Samir shi ya dawo dasu Rufaida daga cin abincin ranar da suke tare suka amsa gaba 'dayansu Samir ya gaisheda dasu Ummi Hauwa'u da Abba ALIYU sauran yaran suka gaishesa ya amsa yana murmushi Rufaida da bayan gaisuwar tace "lah yaya Samir yau Kaine a tafe a gidanmu hala makuwa kayi" AbdurRashid yace"Nima "yaya Rufaida na dauka makuwa yayi" Samir ya harari AbdurRashid yacewa Rufaida "ke dai bari Rufaida wannan yarinyar ce tasa saurayinta yazo gidanmu kuma tasan ba'anan take weekend" Abba Aliyu da Ummi Hauwa'u suka ce ai dama munsan ba'a aikin banza a kano banda haka yaushe rabon duniya da ayyaraye"Samir yace "wallahi bahaka bane Abba bahaka bane mutumin nawane AbdurRafi shima baya zuwa inda nake tunda aka samu hutu"AbdurRafi yace" kai Samir kaji tsoron Allah zuwa na nawa nayi gidanku"Ummi Hauwa'u tace kanku dai akeji"ta dora da cewa"AbdurRashid jama yayan naka kujera mana ya zauna yaci abinci shima Samir ya zauna yana cewa" Yawwa AbdurRashid"ya dora da cewa Ummi kamar kinsan banci abinci ba Ahmad yazo Momy tace nataso na rakosa gurin Samiha kinganni ma Ummi bako waya bare key din mota a hannu na sai dai idan mutumin nawa zai kaini gida ya fada yana kallon AbdurRafi da yagama yiwa karya"ganin baice komaiba yafara lomar abincinsa da Ummi ta zuba masa,Abba Aliyu yace "Hauwa'u baki tanbayesa ya budema bakon falon baki"Samir yace "Eh Abba na budemasa" Abba Aliyu yace "yawwa Samir ,Hauwa'u azuba ruwa da lemo akaimasa" Ummi Hauwa'u tace to, da haka Abba Aliyu ya cigaba dacin abincinsa"Samiha da take zaune tana ji duk abinda suke fada bata sa baki ba da tunda aka ce mata Ahmad yazo take cin abinci hankalinta raba da rabi ta qagara Abba ya mike taje taga sahibin ran nata,Jin maganar Ummi yasata tsaida tunanin nata da Ummin ke cewa
"Ya haka Samiha ko bakyacine kin koshi kiyi maza ki gama kinga yaron ke yake jira"AbdurRashid yace" Ummi ai dole ma ta koshi ta ci fa 'dazu bandana Yaya Samiha ci gare ta"Ummi tace"AbdurRashid bafa nasan raini kaike kawo abincinne" ya girgiza kai AbdrRafi jin haka yasa sh tuno abinda tayi masa dazu yasa shi cewa"wallahi Ummi Ba Karya AbdurRashid yake ba kifadawa Abba ya karo buhun shinkafa"Ummi ta gallawa AbdurRafi harara,Samiha jin hakan yasata hade rai ta mike ta fara barin falon ta haye sama"Yara ne sukayi dariya Rufaida tace"wa yaran dama kofar guduwa take nema Abba Aliyu da ya gama cin abincinsa ya mike ya bar falon a ransa yana kara jin san iyalensa,da kuma matarsa Hauwa'u ha'ki'ka yayi dacen samun mace tagari, Ummi ta shige kitchen ta shirya kayan da za'a kaiwa Ahmad falon baki ta kira AbdurRashid ya mikamasa Rufaida upstairs saman bene tabi Samiha dakinsu ta tura ta shiga da sallamarta inda ta sami Samiha tanata cacca'ba kwalliya kai kace gidan biki zata"Rufaida tace "Samiha wannan kwalliyar fa harkinyi wankane kinsan dazu fa baki yi ba"
Hararar Rufaida tayi tace"waike Rufaida ni kwado ce kamarki zantayin wanka ina laifi nayi daya tunda nayi da zan tafi makaranta ai ya isa"
Murmushi Rufaida tayi daga bisani tace mata"ai wanka jindadin jiki ne,kuma ai kinsan fa munshawo rana a makaranta,kyaeje gabansa kita warin rana"
Tace"ke ni banshawo wata rana ba,inma nasha haka zan fita,tunda turare yana magani ai"
Rufaida tace "nufinki turare na zan baki ki fesa kin da'de wallahi"
Samiha tace"kwantar da hankalinki nima inada turaren ai"jakar makarantarta dake kan lokar gado Samiha ta zage ta de'bi turare ta feshe jikinta dashi ta bude Sib ta samo mayafi mai girma kalar kayan jikinta ta yafa"
Rufaida da take tsaye tana kallonta Samiha ta kalleta tana bu'de kofa ta kashe mata ido tace"aini ba'ayimin gatse"Rufaida tace" naji kimaza ki tafi kinsan ajan aji ake barin arha,kuma wannan kashe idon ai Yaya Ahmad zaki yiwa"Samiha tace "kuma fa hakane,bari na wuce na tafi said kinzo gaisheshi ko?" Rufaida tace"bafa zanzo ba kigama fa'damin magana"Samiha ta dawo ta dafa Rufaida tace"haba kawata Yar uwata ki taimaka kizo"ganin Samiha zata cigaba da 'batawa kanta lokaci tace"zata zo su gaisa"da haka Samiha ta fice ganin Abba a cikin falon suna hira dasu Samir yasata dan jin kunya ta koma da baya ta tabi ta kitchen zata fita tanan ta wuce Abba Aliyu da idonsa na gun Samihan yayi dariya inda ya tuno halayyar matarsa Hauwa'u tana kama data Samihan amma azamanin baya tunkafin aurensu can yake tunowa sai gashi Rufaida gudan jininta bata biyo cakwakkwayyar Hauwa'unba sai Samiha da babu dangataka ta kusa kota nesa tsakaninsu,Dariyar da Samir keyi ita tadawo da Abba Aliyu daga wancen tunanin nasa"Abba Aliyu ya dubi Samir yace "lafiyarka kuwa Samir" yace "Abba lafiya ta kalau,Samiha ce data ganmu a falo taki wucewa tabi ta kitchen zata wuce tayi arangama da Ummi " murmushi Abba Aliyu yayi yace"kasan yaran suna da kunya duk cakwaikwaiwar Samiha tana da kunya diyartawa"Samir da baice komaiba Dan ya fahimci Abba baisan rashin kunyar da Samiha keyi a gidansu ba akan Ahmad"Abba Aliyu ya tsaida shirun nasa da cewa"Muna magana da Abbanku da muka hadu shekaran jiya yace min yaron ya turo magabantasa to bamu gama maganar ba aka kirani a waya....."Samir yace"Eh wallahi Abba yazo tsaida rana za'ayi Abba yayi bincike akansa baida Matsala babansa shine sabon Commissioner of police a Zariya Road suke da zama"Abba Aliyu da yaji dadin Labarin kamar akan 'diyarsa ya faru ,danshi dama yadda yakeson Rufaida haka yakejin Samiha har aransa baiji bakin ciki ko kyashin wannan labarinba,yace cikin murmushi mai yalwa a fuskarsa"To Masha Allah,ai kaga idan AbdurRafi zai ya tashi tafiya police (Dan sanda)ai bazamusha wuya ba muna da hanya"AbdurRafi da sai yanzu yasa baki yace"Abba yanzu kaima har dakai a tonan nawa" Samir ya kunshe dariyarsa"Abba Aliyu yace"ai kaine Rafi abu ka'dan kace bakaso har kannenka sun ganoka tsokanarka suke da abunda bakaso,kana girma kana kara rashiin wayau"AbdurRafi yace "ni dai Abba Dan Allah a bar maganar ,kai kuma da kake kunshe dariya ka tafi mana kai ga hanya nan" yacewa Samir,Samir,yace"Allah ya huci zuciyar manya musu tsoron training din 'yan sanda"daganan Samir ya gudu ya bar falon yana dariya dan yasan halin abokinsa sarai indai kan ace ya tafi police ne zaku iya yin baran baran,can majalissar unguwa Samir ya shige kasancewar yasan 'yan unguwar wasu saboda akwai abokan karatunsu acan nan ya zauna suna taba fira"AbdurRafi shima binsa yayi yana tunano rashin mutunci da zaiwa Samir saboda yadda ya rainasa dan kawai yace bayason dan sanda saboda training dinsu yanada wuya shiko riqe wannan bindigar aka barshi da shi ai anbarsa da aiki,Abba Aliyu yayi murmushi AbdurRafi da Samir fadansu sai su ba'a shiga koma ka shiga sabaka kunya ya cigaba da kallon da yake a TV
Rufaida ko Samiha bata jima da fita ba tasa hijabi mai girma tabi Samiha su gaisa da Ahmad a falon ba'ki ta samesu ta gabatar da sallama suka amsa mata ta shiga" ta zauna kusa da 'kawartata Samiha da take a kujera mai biyu shikuma yana zaune a kujera mai 'daya an ajemasa lemuka a plat da ruwa datasan duk aikin Umminsu ne inda Samiha ta tsiyaya ruwa a kofi Rufaida tace"Yaya Ahmad ina yini"ya 'danyi murmushi yace"lafiya kalau Hussaina,ya juma'ar?"
Tace masa" Alhamdulillah Yaya,wato bazaka daina cemin Hussaina ba"wanda tun farkon gaisawarsu da Rufaida da taje gidansu Samiha yace ita Hussainar Samiha ce saboda yadda take basa Labarin Rufaida kona Yaya Saudat bata basa haka,dan shi 'daukarsa suna da ala'ka ma,danshi har kama yaga sunayi,"yace mata "Eh mana ai Ku 'yan biyu ne idan akaga wata za'aga Zahra gashima kuna kama ma inda za'a kara tabbatarwama" ya fadi hakan da sigar zolaya"Rufaida tayi murmushi tace"Samiha kinji fa yaya Ahmad da wani zance"Samiha tace"kema dai kya fa'da nibanga wata kamarmu ba ko 'daya"Ahmad da har yanzu bai fahimci alakarsu ba yace"dama haka zakuce"Rufaida tayi murmushi tace" Ai hakane ma"da haka suka sake ta'ba hira ka'dan sannan Rufaida ta fice daga falon ta basu guri suyi firarsu.*JININMU DA'YA♦️*

Sadiya Khaliy💞

Page 13
Samiha ta shigo 'dakin ko sallama babu ta fada gado tareda cire mayafin kanta Rufaida tace" ke lafiya kuwa"Samiha tace"bansaniba wallahi Rufaida Ahmad ya cuceni"Rufaida ta jinjina kai tace mai kuma yayi miki bawan Allah"Samiha ta ta'be baki tace"kinsan tun kwanaki da yacemin zai turo a tsaida magana asa rana"nace masa ya bari keda Yaya Saudat kuma Ku samu miji tukun"ita da Rufaida abinda dariya ya bata ma,Samiha tace"au dariya ma kike ko"Rufaida tace"Ai abin nakine abin dariya banda abinki mainene dan ankawo kudinki muba'a kawo mana ba,kinsan komaifa lokaci ne,kafin ayi naki bikin sai kiga munsamu namu mazajenmu,"da haka dai Samiha tasamu kan Samiha dan ita Samiha dagaske bata yarda ba sai sun samu nasamu mazajen Ahmad ya jira saboda ayi bikin nasu tare

Ranar da Weekend ya kare Monday litinin su Rufaida suka shirya Abbansu da zai shiga Makaranta suna wani taro a BUK din ya tsaya ya saukesu a Al'AZHAR har bakin gate din makarantar ya kaisu inda hankalin Samiha ya tafi a motar da aka sauke Sir AbdurRahman motace maikyau da tsada drivernsa ya tsaya ya fito Samiha tace"Abba kalli malaminmu maikama da yaya AbdurRafi"Abba Aliyu da ya 'karasa parking ya dubi AbdurRahman kasancewar ya 'dan juyar da fuska bai ganshi sosai ba ya daiga bayansa saida ya sake kallonsa yaga fuskarsa shidai baiga wata kamarsu ba sai dai a fisge"Samiha tace "yawwa Abba ka ganshi ko?yace mata " Eh a ina yaron yake kunsan shine"Samiha ta cemasa"Khalid Bashar way yake kusa da gidanmu wasu ma cewa suke 'dan sane,TP yazo makarantarmu inda kake lecturing yace yake karatu BUK" Abba Aliyu yace"ok,Allah sarki ba lallai nasan yaron ba akwai daliba da yawa kinsan kuma department department ne "tace " eh hakane"da haka suka fice daga motar sauran yaran suna cewa sumafa basu ga kama ba,Abba Aliyu da shima baiga kamaba yaja motarsa ya bar harabar makarantar,a kofar Gate 'din suka ci karo da Sir Samir suka gaishesa suka shige tare da ya shaida fuskokinsu yaran ne ma baigane ba,saboda baya daukar 'yan ajujuwansu,yace"Health prefect da Labour ne ashe"Rufaida tayi murmushi"
Samiha tace"Sir yanzu Abbanmu ya saukemu a mota da har zan kwala ma kira ku gaisa"Rufaida da take zungurar Samiha tayi shiru taki banda shiga ukun Samiha meye na fa'dar hakan bandama koyarwa daganin wannan matashin AbdurRahman zaiyi ji dakai,kuma ga iron motar da aka saukesa da gani dan masu dashine sosai,amma Samiha sai zaqalewa take,tana nema ta wuce gona da iri"AbdurRahman yace"Aiya wani lokacin zamu gaisane"Samiha tace "hakane " tabar maganar daga haka kar dalibai su hangosu a yimata wata fassarar,dan tasan halin 'yan makaranta"
Ana gama a assembly malamin biology AbdurRahman ya shigo yafara koyarwa nan aka aiko wata daliba ta kira Rufaida da sallama 'dalibar ta shigo ajin inda AbdurRahman ya tsaya da koyarwar ya amsa 'dalibar tace"Sir ,Sir Nura yace Rufaida Aliyu Bukar tazo"AbdurRahman yace"to kice tana zuwa"ya dawo ya kalli 'daliban yace"wacece Rufaida Aliyu Bukar"Rufaida ta mike tace"Sir gani"AbdurRahman yace "au Health prefect dama kece Rufaida?" Tace masa" Eh"yace "ok,kije Sir Nura ke kiranki kiyi maza kidawo kinga lesson muke"da haka Rufaida ta fito daga bencin tana cewa"to"shi ko AbdurRahman zama yayi akan kujera ya huta kafin Rufaida ta dawo ya cigaba shi sai yanzuma ya tuno Rufaida itace su Nasiba sukace yana kama da wani yayanta,shi kasancewarma baidamu da sabgar ba yama manta gaba 'daya tundaga ranar baisake tunowa ba ,saida ya dawo ya cigaba da lesson 'din harya gama ya fita ya kira Nasiba"ya bata wani class work daya basu ta rubuta a allo period ta gaba da malamin period din baizo makarantarba zaizo ya duba"daliban da sai zagin Sir AbdurRahman suke don ya fiye takura daga fita abada wani aikin aji suna mita suka rubuta suka fara duba test Book 'din biology ita Rufaida key point kawai ta duba tayi taba Samiha tayi ita kanta Nasiba zagin AbdurRahman tafarayi duk shirin da suke da AbdurRahman din don kusan a ajin sunanta yafi riqewa
Periof nashiga yana shigowa ajin ya fara da duba litattafan daliban benci benci matanma sunfi mazan kokartawa bencin su Rufaida ya karasa da shine ya bari na karshe duk sunfi sauran kokartawa dan da marking zaiyi sune suka cinye duka tundagan suke 'dan shiri dan shi AbdurRahman yanaso yara masu kwazo Samiha har number dinshi gareta da Ahmad ya kawo mata wayarta mai tsada ba laifi infinix ce da a yanzu haka ansa rana da sunyi candy za'ayi bikin dukda yadda Samiha taso a hada bikin koda na Yaya Saudat ne da yanzu haka tasamu saurayinta mai sonta cousin dinsu a sokoto Mujahid dan tuni ta hakura da wancen da suka hadu a biki dan akarshema wayoyinsa daina shiga sukayi,hakanan Yaya Saudat ta hakura da jiran gawon shanun da take ta amince da Mujaheed Abba Hashim mahaifi ga su Samihan shima kansa ya amince da hadin auren kuma abin yayi masa dadi sosai itako Momy Maryam mahaifiyarsu Samihan da Mujahid din yakasance 'dan yayanta tamafi kowa murna da wannan hadin
AbdurRahman ranar da zai gama TP dinsa haka 'yan ajin duk suka ji ba da'di kasancewar sunsan ba lallai su sake cinkaro da Shiba koda a hanya ne don su dai sunsan haduwa da iyalan Khalid Bashar da kamar wuya dan Nasiba Shehu da Hauwa Umar sunada ya kinin gaskiya suka fada musu dukda yawanci yan makarantar 'ya'yan masu da shine amma wasu sunfika kaima kafi wasu sunfika haka rayuwar ke tafiya.
AbdurRahman ya kalli su Nasiba gaba 'daya su shida group 'dinsu harda su Rufaida da yake ji a ransa duk ba dadi saboda yadda ya fara sabawa da yaran da yake jinsu har a ransa gasu masu kwazon karatu donshi ko 'yan ajin basu taba masa rashin kunya ba ko zaginsa sai dai ko a bayan idansa shiyasa yake ji babu dadi bayan ya fito daga ajin nasu inda yake tsaye birandar ajin nasu sukuma sun tsugunna a gefe yace"Nasiba Shehu ya maganar karatun naki ne"tace masa"Sir Jamb zamuyi nidasu Zainab Farouk,da Hauwa"AbdurRahman yace"banji kince su Rufaida da Samiha ba"Nasiba tace "lah sir dama banfa'dama su Samiha aure zasuyi ba" ita da Rufaida"Samiha tace"Sir karya fa suke"AbdurRahman yace"to inma shine aiba wani abu bane"Hauwa'u tace"wallahi Sir bama karya muke ba itafa Samiha bayan candynmu da sati biyu za'ayi bikinta,itace dai Rufaida bamu sani ba"AbdurRahman yace "hala wannan yayan Rufaidan da kuke cewa muna kama zasuyi auren zumunci dashi da Samihan,gashima har zan tafi bamu haduba" ya fada da murmushi kan fuskarsa Dan shi ma tunaninsa sunada dangantaka"Aisha Mudassir tace "Eh Sir laifi su Samiha ne basu hadaku kun gaisa ba amma yarone fa koni nakusa girmarsa"Rufaida ta harari Aisha"tace kinma girmesa kawai zakice"AbdurRahman yace"To masu 'dan uwa,don tace ta kusa girmarsa shine harda bakar magana" Rufaida tace"Sir koni fa shekara kusan biyar ya bani inji Umminmu shine zatace ta kusa girmarsa "murmushi AbdurRahman yayi kawai yacanza maganar da cewa"saura kuma kumanta dani lokacin bikin kuki fadamin"duka suka amsa da Insha Allah zasu fadamasa tunda suna da number

Please Login or Register in order to submit comment