Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

a Nigeria yanzu shine a gabansa ba maganar aure ba yanzu abinda ya damesa ya bunkasa kasarsa ta hanyar cigaba ta kowanne fanni shi kuma aure yasa a ransa lokaci ne,yanaso daya kammala gininsa ya koma gida ya samu ya sami nitsatstsiyar mata a kasarsa ya aura don shi gaskiya baya kawo wa ransa zai auri Rufaida saboda tayi aurenta ita tuntuni harma yaga kyakkyawan Baby boy dinta a Dp din Samiha daya na gani yaga kamar yaron da Wahid da bai manta kamanninsa ba shekarun baya da suka wuce ,Husna ta koma Nigeria a can zatayi bautar kasarta,data gama kuma za'ayi bikinta zata auri cousin dinsu Bello,Hajiya tayi tayi Ra'uf yazo Nigeria yaki sam bayajin son zuwa kuma koda ma zashi don su Yakumbo da Mama suwaiba zashi ba dan itaba

***********
"Rufaida meyasa ne Umma take so ta matsamin akan auran nan,yanzu fisabillah hakan ya dace"
Rufaida jin maganar da Wahid keyi yasa ta aje wayarta gefen gado ta maida kallonta gare sa
"To mene ne ya faru kuma?"
Yace
"Sam ta kasa fahimtata tace min nine na fadawa Abba karya amince da auran nan vayan kuma ,ba mu taba maganar da ta shafi aurena da Ruqayya ba nida Abba,amma zancen da ni ke miki yanzu ya kafe kaida fata ba zan aureta ba,ita kuma Umma ta kafe sai nayi auren nan"
"To yanzu ya za'ayi" fadin Rufaida
"Ina so zanje gida gobe saboda inaso Umma ta fahimceni maganar waya bazata wadatar ba"fadin wahid
" amma Yaya gobe gobe banyi kusa ba"
"Wanne kusa kanwata kinsan dai wacece Umma idan banje ba kinsman abinda zaije ya dawo ba karami bane"
"Eh da kuma hakan,Allah ya kaimu lafiya" jin karar wayarsa yasa shi mikewa ya karasa inda yasa caji a falon ya dauko wayar ya dawo inda yake,ganin mai kiran ya sashi saurin dagawa ganin Ummansa ce
"Assalamu Alaikum Umma ina yini"
"Wa'alaikumus salam lafiya lau ya aiki"
Bai dama tsammaci za ta ce yasu Rufaida ba hakan yasa shi saurin ce mata
"Alhamdulillah ,Umma"
"Yawwa dama so nake na fadama inason ganinka gobe,saboda Ina so Bukar ya amince da auran nan kana sane indai ba amincewarsa babu abinda zai yiyu"
"Eh hakane,Umma dama yanzu make maganar zuwa na da Rufaida"
Jin ya anbaci Rufaida yasa ta jan dogon tsaki dan ita ko sunan Rufaida bata so ma a fadama ta shigar mata cikin rayuwar danta wato ma saboda zaizo gida sai yayi maganar da matarsa kila ma har shawara ya nema,tsaki taja a karo na biyu tace
"Ok"
Wahid dinne yace
"Yasu Wasila da karamar kanwata"
"Wacce kanwartaka kuma kana da kanwa da ya wuce Wasila ne"
"Eh mana Umma,akwai 'yar Aunty da Mama"
Tsaki tayi tace
"Naji"
"Yawwa,Ummi kema yaushe zaki min kani,ko kanwa"
"Kamar ya ai yanzu nabar muku kudai kuyi,yanzu idan ka auri Rukayya,ai shikenan zan fara tara jikoki,kaga ai gwara na bar muku tunda wuri"
"Eh hakane gama ,Umma amma ga Yasir nan ai yafara zuwa"
Hajiya Jamila jin an sako maganar Rufaida da batasan jinta sam yasa ta cewa
"Kaga sai anjima"daga haka sukayi sallama ya katse wayar
Ya dubi Rufaida yace
" Allah Rufaida banason zuwa Zariya akaran kaina dandai akwai muhimmanci a zuwan nawa,amma inajin kar naje Umma tace min na sake ki,jikina yana bani wani abu zai iya faruwa Indai nasanar da Umma abinda Dady yace"
Rufaida ta kallesa da hawaye ya taru a idonta tace
"Yaya Wahid,ka daina wannan tunanin ni dakai mutu ka raba,nasan Umma ba zata ce haka ba"
"Idan to batace hakan ba, idan kafin goben na mutu fa,Rufaida banaso na mutu na barku"
Rufaida da ta fara hawaye tace
"Yaya dan Allah ka daina maganar mutuwa,bazaka mutu ba,tare zamu mutu"
Murmushi Wahid yayi yace
"To zan daina amma kinsan da cewa mutuwa dole ce duk mai rai zai zama gawa,kuma na fiso na rigaki mutuwa saboda ke din yanzu kikasa kafa a cikin rayuwarki ni kuma nafara kwana biyu"
"Eh,a'a Yaya ni baka tsufa a guri na ba so nake mu rayu mu mutu tare"
Dariya yasa ya nuna ta
"Oh kinganki dama kina sona sosai haka"
Murmushi tayi tace
"Yaya idan banso mijina ba wazan so"
"Ra'uf mana ai ni duk a tunani na gangar jikinki na aura"
Harararsa tayi tace
"Kai Yaya,Wannan Ra'uf yaki fita a ranka shi yana can ya manta da shafin rayuwarmu kaiko kana tason sawo mana shi a cikin rayuwar mu,bayan ba muda alaka dashi"
"Rufaida kenan ba zaki fahimci yadda nake son Ra'uf a raina ba inajinsa har a jinin jikina"
"To fa saboda me" fadin Rufaida tana zaro ido
"Saboda inason abinda kikeso Rufaida nasan kin soshi koda a yanzu baya ranki,kinsan mene fata na"
Kai ta girgiza yace
"To bazan fada ba ma nafasa"
"Yaya Dan Allah ka fadamin"
Yayi dariya yace" badai shagwaba zaki ba to dama abinda zance shine koda bana raye ki zauna da mutumin da zai zama sanadiyyar haska rayuwarki"
"Oh Yaya kwanaki ma fa ka fadi haka,dan Allah kadaina fadar mutuwa duk sanda bana tare dakai zan zama banida ragowar farin ciki"
"Ai hakane Rufaida zaki samu haske da zai haskaka ki a rayuwarki,Rufaida mutuwa dole ce,amma tunda bakyaso na daina fada yanzu dai ina Yasir"
Rufaida da murmushinta tace
"Ya kwanta a falo,bari naje nadaukosa"
"Kyale kawai zanje na daukosa yau ni zan masa shirin barci ma"
"Yaushe rabon duniya da ayya raye yau wacce rana m
Yace " asabar" yana kokarin fita da dariyarsa
*JININMU D'AYA*
By Sadiya Khalil
48.
DAWOWA LABARI
*RUFAIDA POV*
Abdul Malik ne ya dubi Rufaida da suke zaune a harabar gidan suna fira kasancewar yau an tashi da zafi garin kuma ba wuta babu inji yara kuma duk sun tafi Islamiyya Tahfiz da yau lahadi babu boko harda Yasir suka tafi
Abdulmalik din ya soma magana
"Rufaida yau fa naga mai kama dake"
"Ni kuma yaya AbdulMalik" Rufaida tayi maganar da mamaki akan fuskarta
Ya sake kallonta yace
"Kwarai kuwa,da farko dana ganta tana tafiya tunani na bani yayi kece ma,harna fara tunanin maiya faru a kadunan kikazo saida ta juyo da fuskarta naga bake bace,tafiyarku ce sak daya amma a fuska bakwa kama sai dai a fisge"
"Oh kodai Samiha ce,ana cewa muna kama nida ita?"
Harararta yayi yace
"Samihan ce bansani ba"
"Aunty Amarya tasa vaki a firartasu tace
" oh maiyasa baka tsaya yi mata magana ba,kaga aida ko lambarta saika samowa Rufaidan"
AbdulMalik yace"wallahi kuwa Aunty kinga dana hada su kawance,amma zan rika bi ta hanyar kozan sake ganinta,kamar tayi yawa duk da babu a fuska amma akwai a siffar jikinsu"
Hajiya Jamila da take jin firarsu tasa baki gurin cewa
"ai babu mamaki ko a cikin yawon da akayi ana abun kunya aka sameta"
Jin maganar Hajiya Jamila da Rufaida ta jita kamar dirar mikiya yasata mikewa daga gurin gaba 'daya kanta a kasa
Ganin Rufaida ta mike daga gurin tayi shigewarta falon gidan kallon data tarar a kunne shi ta kashe tayi kwanciyarta da ita sai yanzu tasan andawo da nepar data san an dawo da wutar ita kam mai zai jama ta zama a can sam shiyasa batasan zama koda a fall ne indai Hajiya Jamila na gurin dan saita fadi bakar magana akanta
Ganin Rufaida tabar gurin yasa AbdulMalik kallon Hajiya Jamila ya soma magana
"Haba Umma hakan baida ce ba"
Hajiya Jamila ta hararesa
"To ubanka nace da baida dace ba a cikin maganar,don na fadi gaskiya"
AbdulMalik zai sake magana Hajiya Kubra da sai yanzu tasa baki tace
"Kaga AbdulMalik kyaleta karka sake yin wata magana"
Hajiya Jamila ta harari Hajiya Kubra tace
"Kinga nifa banason shishshigi 'dan kine ko nawa,ki barsa ya fadi abinda zai fadama na,a haka a nuna ana sonka sai an ware a fara gulmarka"
AbdulMalik ya dubi Hajiya Kubra yace
"Mama don Allah kar kice komai"
Ya maida dubensa ga Mahaifiyarsa yace
"Haba Umma daga ban hakuri"
Hajiya Jamila tace
"To ubana,hana ni na maida martani"
Ganin ba zata fasa maganar ba yasa shi mikewa ya bar gurin don yasan indai yana nan ba zata gaji da magana ba ya nufi falo
A falo ya sameta a kwancea a kujera kamar mai varci ammma da gani ba barci take ba zama yayi kujerar dake kusa da wadda take kwance yace
"Rufaida kiyi hakuri don Allah,nasan Umma ba ta kyauta ba"
Murmushi tayi ta bude idanunta wakeke waken da Rukayya ta fito daga kofar kitchen da Kofi a hannunta tanayi shi ya tsaida maganar da Rufaida
Rukayya ta kai kallonta ga Rufaida da take kwance da hankalinta vaikai ga ganin AbdulMalik ba Rukayya ta fara magana cikin bacin rai
"Malama ke wacce irin kidahuma ce ya zaki zo ki tarar na kunna kallo ki kashe min ki kuma kwanta wa mutane shame shame a kujera kamar ta gidan ubanki,sakarai kawai ana mata kora da hali kina nacewa mutane..."
Ganin Rukayya ba zata yi shiru ba yasa AbdulMalik gyaran murya da zuciyarsa take tukuki jin maganganun Rukayyan
Rukayya da sai yanzu ta san AbdulMalik na gurin tuni ta fara zaro ido ta soma magana
"Yaya AbdulMalik wa...."
cikin bacin rai AbdulMalik ya nuna nuna Ruqayya da ya tsa yace
"Ke daka ta munafukar banza ke waya kai kidahumanci,inba kida humanci ba mai zai kawo mace budurwa gidansu saurayin da taso don ya mutu kuma bama zuwa gaisuwa ba a'a zuwa a zauna kamar wadda tarasa mafadi,kuma kenan gidan ubanki ne? da kikazo kikayi shame shame kina cin arziki mai kika hada danan gidan,to ita din ta fiki matsayi da komai anan gidan,donke arzikin Umma kikeci,don koni Rufaida ta fiki matsayi a zuciya ta"
Cikin bacin rai da hawaye taf idon Ruqayya tace
"Naji ta fini matsayi anan gidan amma ita da ba'ada tabbaci akanta shine,zaka fadamin magana akanta"
"Tabbacin ubanki ne va'ada shi akanta,ke ba'ace ba'ada tabbaci akan Ku ba,saike zaki fadawa wata"fadin AbdulMalik
"Wallahi mu anada tabbaci akanmu,ita da uwarta take karuwa fa niko mai uwata tayi wallahi muna da banbanci nida ita fiye da tunanin mai tunani"
AbdulMalik jin maganar da Rufaida keyi yasa ran Abdulmalik ya kara baci ya mike ya nufi Rukayya zai doketa Rufaida da hawaye ya cika idanunta ganin haka yasa Rufaida mikewa tayi gurinta tace
"Yaya AbdulMalik karka doketa kaya hakuri"
Hannu AbdulMalik ya dagawa Rufaida ya shiga dukan Rukayya
Da kyar Ruqayyan ta kwaci kanta tayi gurinsu Hajiya Jamila tana kuka wiwi
Abdulmalik ya bita shima Rufaida ta biyo bayan sa tana kiransa ya dawo amma baya jin ma mai take cewa tana hango Rukayya tana maida lumfashi yayi kanta ya fara dukanta cikin zafin zuciya ba tare da ya bi ta takan mutanan dake rirriqesa ba
Tsawar da Abba Bukar ita tasa AbdulMalik sakinta yana maida lumfashi
Bai saurari kowa ba ya fara tafiya da niyyar barin gurin Abba Bukar yace
"Dawo nan"
Dawowa yayi ya sunkuyar da kansa
"Rukayya me ya hadaku"cewar Hajiya Jamila
Rukayya tana rusa kuka ta dago kanta ta nuna Rufaida wata hararar Rufaida Hajiya Jamila tayi Rufaida ganin haka yasa Rufaida kai kallonta kasa
Ganin ta nuna Rufaida Abba Bukar ya kalli Rufaida yace
" Rufaida mai ya hadaku da Ruqayya?"
Idon Rufaida ne ya ciko da hawaye Abba Bukar yace
"Kiyi min bayani ina sauraranki,banaso wani hawayen banza kiyi laifi kizo kina hawaye"
Jin maganar Abba Bukar yasa Rufaida goge hawayenta ta zayyana masa duk abinda ya faru
Abba Bukar yana gama ji ya dubi Ruqayya cikin bacin rai yace
"Yanzu Ruqayya dama baki da mutunci ina ganin kamar zaki fita daban a cikin 'yan uwanki,shiyasa ma ke na amince ki zauna na lokacin da Jamila tace min zaki yi wato ashe har kin fisu ma,dama zaman danki kuntatawa Rufaida kika ce zaki yi"
Rukayya tace
"Abba dan Allah kaya hakuri ba haka nake ba Aunty Jamila ce take cewa na rika yi mata"
Abba Bukar ya jinjina kai yace
"Wato ita ke baki labaran karya da karai rayi akan Rufaidan ma ko?"
Rukayya ta girgiza kai tana kallon Hajiya Jamila da take girgiza mata kai kar tace ita ce
"Ki fadamin gaskiya bana son karya ita ke baki ko kuwa kifadamin wake baki"
Abba Bukar yayi maganar yana kallon Hajiya Jamila yadda take girgiza wa Ruqayya kai
Rukayya da duk ta tsorata tace "Eh Abba ita ce,tuntuni take bamu wannan labarin"
Abba ya jinjina kai ya kalli Hajiya Jamila ya soma magana
"Jamila kin bani mamaki amma ba abun mamaki bane nasan fiye da haka ma zaki yi saboda bakya tunani kafin ki aiwatar da abu sannan zai wuya idan kinyi badaidai din ba kiyi danasani,amma nasan akan wannan maganar tabbas zaki yi dana sani koba yanzu ba,sannan babu wani matakin da zan dauka akanki amma tabbas ranar dana sani zata zo miki,sannan yau ba sai gobe ba inaso Rukayya ta barmin gida na dama mahaifinta yayi min waya yanaso Rukayya ta koma gida saboda maganar aurenta da zai aurawa dan abokinsa ita da kune kuke ziga yarinyar karta yarda da auren,batun Rufaida kuma baza ta bar gidan nan ba sai sanda na tsara zata bari"
Da wannan maganar Abba Bukar ya maida kallonsa ga Abdulmalik yace
"Malik nasha fadama kai ba mace bane ka daina shiga fadan mata,banason karajin irin haka ta faru"
Abdulmalik yace cikin ladabi
"To Abba zan kiyaye insha Allah" amma a ransa baya tunani zai hakura muddin yaga ana kwarar Rufaida don shi mutum ne da bayason zalinci
Da haka Abba Bukar ya bar gurin Abdulmalik da Rufaida suka take masa baya
Hajiya Jamila jikinta duk yayi sanyi ta kama hannun Ruqayya,Ruqayya tayi saurin fincikewa daga rikon da Hajiya Jamillar tayi mata ta bar gurin don gani take duk Hajiya Jamila ce ta jawo mata koma mene yanzu ba ta da wata daraja a idon kishiyoyin Hajiya Jamila dama Rufaida ga uwa uba Abba Bukar,da gatanta da komai bawai arziki za'a nunawa mahaifinta ba bakomai ba amma ta ja an yi mata wulakanci har haka kum AbdulMalik ne yayi mata suma sauran matan gidan sumi sumi suka bar wajen aka bar
Hajiya Jamila ita kadai ita mikewa tayi ta bar gurin.A daki ta samu Ruqayya tana hada kayanta Hajiya Jamila ta dafa Rukayya tayi saurin cire hannun Hajiya Jamila daga jikinta ta soma magana
"Kinga Aunty don Allah ki kyaleni,kinsa an cimin mutunci,nima kuma kina zuga ni na ciwa wata,dama nina gaji da zaman gidan nan koda ba'a koreni ba,tafiya zanyi,gwara naje nabi umarnin Abba da na cigaba da zama anan,ki riqa gulmata na tare a gidan ki bayan wanda nake so dinma baya duniyar,amma kinsa ni na zauna ina goga kishi da matarsa bayan ita bata damu da muba"
Hajiya Jamila da ranta ya fara 'baci ta kalli Rukayya tace
"Kinga Rukayya a haife dai kinada tabbacin nayi 'yata hudu ma dake,ba zai yiyu ki zauna kina jeramin magana ba nina jawo miki dukan?ince dai ke kika jawo wa kanki,sannan dama fa ba wanda ya rike miki kafa kuma karki min sharri ni bance ki zauna a gidana ba,dama a zagwaigwai dinki ne yasaki zama a gidan nan,amma sanin kanki ne na nuna miki banaso saboda nasan baki da hankalin iya zama da mutane,baki iya rufe sirri ba,kinzo ni kin hadani da miji na cikin kishiyoyi kin kwance min zani"
"Au haka zaki ce,kin mata harna hada kayana kila kika ce na zauna,ke ai abinda kika yi na fada nifa kinsa danki ya kwance min zani a kasuwa ya kuma yimin shegen duka kika zaunar dani"
"Karfa kimin rashin kunya Rukayya ni zan sa AbdulMalik ya doke ki bakin halinki dai yasa ya doke ki"
Dariya Rukayya tayi tace
"Su bakin hali manya rashin kunya manya,aishi dama gwano bayajin warin jikinshi,nifa bari kiji baki isa ba wallahi ki fadamin magana na kyaleki,idan kina yiwa Rufaida tana kyaleki,to ni baki samu wannan damar ba ba kuma zaki sameta ba"
Haka dai suka cigaba da musayar kalamai tsakanin Ruqayya da Hajiya Jamila saida Hajiya Kubra ta jiyo tazo ta yi musu magana ta kuma shiryawa Rukayya kayanta haka aka rabu da Ruqayya da Hajiya Jamila kaca kaca harda su gore gore (to dama ba dan Allah aka shirya zaman ba)
Da Ruqayya ta fito saida ta shiga dakin Rufaida ta shiga da sallamarta Rufaida ta dago da kanta daga kallon wayar da take ta yi murmushi ganin Rukayya ce ta amsa mata sallamar jikin Rukayya a sake ta karaso inda Rufaida take zaune a kujera itama ta zauna kusa da ita ta kalli Rufaidan ta soma magana
"Rufaida don Allah ki hakuri ki yafemin abubuwan dana rika yi miki Wallahi Umma ke zuga ni"
Murmushi Rufaida tayi tace
"Haba Rukayya karki bata bakinki nidama ban taba rikonki da komai ba"
"Yawwa Rufaida nagode"
"A'a ki daina yimin godiya,yanzu yaushe ne bikin naki ban taba jiba ko a firarku keda Umma"
"Hmm kedai bari nice dama banason auren da tuni ma anyi har ankawo kudi fa jin yaya Wahid zai yarda da auren my shine naki yarda asa ranar,to jiya Abba ya kirani yace na shirya na dawo gida,shi bazan bashi kunya ba yasa bikina nanda wata biyu masu zuwa"
"Allah sarki,a ina zaki yi auren?"
"Adamawa ne"
"Lah kinga inada kawa tana aure acan, zan hadaku insha Allah"
"OK 'yar inace?"
"Kano"
"OK,ki bani Lambarta"
Rufaida ta duba wayarta ta fado mata lambar Nasiba tasa a tata wayar tayi saving daganan Ruqayya ta amsa ta Rufaidan taayi saving da haka Rukayya ta mike tana cewa
"To Rufaida nizan tafi,sai kinzo biki na nasan sannan kin dade da fita takaba tunda yanzu ma baifi saura kwana goma ba ki fita"
"Eh hakane,amma kinsan indai na koma Kano ba lallai Abba ya yarda"
"Nasan zai yarda insha Allah,sai dai.idan kece bazaki zo ba zaki ce"
"A'a zanzo dama yardarshi nakewa kokwanto "
"Idan lokacin yayi zan kira ki ki hadani da Ummi kinga saita fadawa Abba"
"Murmushi Rufaida ta yi mata tace
" to shikenan"
"Kinga zan tafi va muyi sallama da yasir ba"
"Eh wallahi babu rabo hakanan suka jashi Tahfiz yau din"
"Babu komai Idan kunzo biki zan gaji da ganinsa ma indai da zan iya hakan"
Dariya Rufaida ta yi tace
"Oh saikace idan munzo din shekara za muyi"
Da haka Rukayya ta fito sukayi sallama da Rufaida Rukayya tana sake rokar Rufaida ta daure tazo bikinta
Bayan fitar Ruqayya Rufaida ta dan goge kwallar data taru a idanunta bata taba tunanin abubuwa zasu sauya lokaci kusa haka va,yanzu ko a mafarki idan aka ce mata Rukayya zata sota sai ta Musa saboda irin kiyayyar da Ruqayya ta rika nuna mata,lallai Allah shine mai juya al'amura tana da yakinin watara na komai zai zama tarihi,insha Allah kamar yadda kiyayyarta da Ruqayya ta zama labari.[9/25, 10:23 PM] Sadiya Ibrahim Khalil🤍: *JININMU 'DAYA*
By Sadiya Khalil
49.
RA'UF POV
"Ammi na yunwa nake ji" Ammi Asma'u ta juyo ta harari Ra'uf ta cigava da tafiyar da take
"Ammi magana fa nake,ina jin yunwa,ki samamin abinci na ci" Ra'uf ya sake maimaita maganar
Sai sannan tace
"Ni zan kawo ma abincin kenan,kana kwance sai dai ayi ma komai"
"Oh Ammi yanzu ba zaki kawon ba,shiyasa banso aka tafi da Safiyya ba da tuni ta kawomin"
"Ita ce zata jure dama"
"Au banda ke Ammi,shikenan bari na kira Dady a waya na fadamasa"
"Au Da Dadynku zaka hadani yaro ka dade baka hada muba".
Da ganan ta bar gurin
Ra'uf ya saki murmushi ya tashi zaune daga ki shingidar da yayi jikin kujera ,wayarsa ya jawo ya danna ya kara a kunne a ringing biyu aka dauka muryar Safiyya ta shiga kunnensa da ta soma magana da yaran indiyanci da kuma turanci
"Assalamu Alaikum,my Yaya"
"Wa'alaikumus salam,kanwata ya gida da kowa da kowa"
"Lafiya kalau"
"Ya Nigeria,ina daru Hajiya"
"Tana lafiya,amma Hajiya fa ta rage daru,muna zuwa ta fara korafi kai yaushe zaka zo"
"Kina nufin bata bata ranki ba"
"Eh tanbayarta taka ce kawai muna zuwa"
"Kai amma naji dadi"
"Yaya ysushe zaka zo,wallahi sun damu kazo Family 'dinka,gaskiya suna sonka sosai, dana ga yadda suka damu dakai nima sai nakeji ina ma ace watarana na hadu da nawa Family..."
Ra'uf da hawaye suka tarar masa jin maganar da Safiyya keyi yace
"Haba Sophie maiyasa kike da son dawo da abinda ya riga da ya wuce,mune familynki a yanzu haka,dan Allah ki cire komai a ranki"
"To shikenan Yaya insha Allah"
"Yawwa kanwata,yanzu kina ina ne"
"Ina gidan Aunty Malika a can na sauka"
"OK ina Auntyn"
"Ta shiga kitchen"
"Oh shine ba zaki je ki taya ta aiki ba"
"Oh yaya kasan nafi iya abincin nan,karna mata jagwalgwalo tace ba dadi"
Yayi dariya yace
"Oh Safiyya idan kinyi aure fa,kuma kinsan dai a gida za'ami ki aure gwara tin wuri ki sauke wa kanki iyayi"
"kai Yaya ba fa iyayi bane"
"To menene"
Canza maganar tayi tace
"Yaya jiya munje asibitin daka gina da Abba ,yayi kyau sosai ni ban dauka yayi kyau haka ba dana gansa a waya sai da naganshi a fili"
Dariya Ra'uf yayi yace
"Ya kikaga sunan asibitin yayi kyau kuwa"
"Sosai ma RJM DANBATTA"
Dariya Ra'uf yayi yace
"Yawwa kanwata idan zan sake gina wani,SJM DANBATTA zansa"
"Kai amma naji dadi Yaya"
"OK yaushe zaki tafi Kano"
"Abba yace tare zamu tafi,sai ranar Asabar ta sama zai kaini 'danbatta nayi kwana biyu"
"Ok Allah ya kaimu"
Sun jima suna waya daganan su kayi sallama
suna gama wayar kiran Ahmad ya shigo wayarsa ya daga
Ahmad yana jin Ra'uf ya daga yace
"Oh kodai da budurwa kake waya ne,ina ta kira ana suna nuna min user busy"
Ra'uf yayi Dariya yace
"Ni budurwa,Safiyya ce muke fira"
"Ok sun tafi Nigeria ko?"
"Eh mana,kai yaushe zaka koma ne,kaje garin mutane kayi zamanka"
"Wallahi sun hanani tafiya sun riqeni"
"Oh kai tafiyarka mana"
"Eh dama haka kawai za muyi shiryeye muke, Ni kaina nayi kewar gida over"
"To yanzu ya little Rufaida ban tanbayeta ba"
"Tana lafiya wato bazaka tanbayi little ba sai Rufaida"
"Eh mana,ai ita takwarar masoyiyar farko ce,ko zaku bani aurenta tunda na rasa waccen
Ahmad yayi dariya yace
"Tsohon zan bawa 'yata sai dai kaje kayi zawarci gurin Rufaidan"
"Ina ma za'a bani ita yanzu da sai naje wallahi"
"Lallai Yaya Ra'uf bazawarar zaka aura,sun hana ka aurenta tana budurwa yanzu kawai tana bazawara kaje ka nemi aurenta"
"Eh mana dama Allah yayi bani zan fara aurenta ba ne,kuma laifin fa su Abba Sule ne sune silar da aka hanani aurenta"
"Haka dai kake tunani,amma dai sunyi niyyar dama aura mata dan uwanta ne kawai"
"Karkayi wannan tunanin Ahmad,haka Allah ya tsara dama"
"Haka ne kam,wallahi Yaya Ra'uf Rufaida abar tausayi ce,gaba daya abinda 'yan uwanta ke mata basa kyauta mata gashi Umminta bata isa tayi magana ba,Samiha tana bani labarin komai,kwanaki ma har kudi Samiha tasa na turawa Rufaidan ni na rasa meye matsalar"
Ra'uf da jikinsa yayi sanyi yace
"Maike faruwa ne Ahmad kayi min bayani ba Rufaidan na kano ba"
"Ko d'aya tana Zaria"
"Amma su iyayenta sun manta da abubuwan da suka rika faruwa suka barta acan"
"Zumunci suke tunani shiyasa suke yin shiru nake tunani"
Cikin bacin rai Ra'uf yace
"An taba zumunci da zalinci,ni wallahi mutane mamaki suke bani don da bana ka bane idon yana tare dakai kaita zalintarshi"
Da haka suka cigaba da tattaunawa akan maganar

RUFAIDA
AbdulMalik da shigowarsa falon kenan ya idanunsa suka sauka ga Yasir yana zaune shi ka'dai a falon sallama yayi Yasir da yake game a waya ya dago kai yana murmushi yace
"Wa'alaikumus salam,oyoyo Dady Malik"
AbdulMalik yace
"Ina Mamarka AbdulMalik yayi maganar yana kokarin zama a kujerar falon
" taje kitchen ta zubo min abinci"
"Oh kaifa ina ka baro ci ina zaka ci ne"
Yana cikin maganar Rufaida ta dawo falon da plat da abinci a ciki idonta ya sauka ana AbdulMalik AbdulMalik ya sakar mata murmushi itama murmushi tayi masa ta mikewa Yasir abinci ta nemi guri a kasan carpet ta zauna tare da cewa
"Sannu da zuwa Yaya Malik,ba dai harka dawo ba?"
"Yawwa Rufaida,Eh nadawo yau kinsan friday"
"Au nama manta,bari na kawo ma ruwa,a'a bar abinki,na biya gidan Aunty Zainab daga can ma nake nayo Zaria"
"Ok"
"Baki tanbayeni labarin,mai kama dake ba,munfa sake haduwa yau nagansu ita da Auntyn ta a unguwarsu Aunty Zainab"
Murmushi Rufaida da mamaki tace
"Dan Allah fa"
"Yace
" serious har magana mu kayi"
"Please ka bani labarin ya akai kuka hadu"
Murmushi AbdulMalik yayi yace
"Bayan na fita daga gida naje gurin aiki shine nayi kokarin biyawa gidan Aunty Zainab,kafin na shiga Layin su Aunty Zainab na ganta tsaye kofar wani gida a bakin titi shine na tsaida mota ta a kusa da gidan na fito na karasa gurinta na mata sallama,bata yi min magana ba sai dai naga alamun amsawar a labbanta ina cewa Ranki ya dade wata mota ta karaso ta shiga shine na bi bayansu a mota ta har saban kawo" jin yayi shiru yasa Rufaida cewa
"Uhmm ina jin ka"
"Ke kinga kofar gidan da motarsu ta tayi parking kuwa,ina ganin kyau da tsarin gidan nasan dole yarinyar tayi jin kamshi indai gidan ya kasance gidansu ne,ina gani aka bude musu gate din suka shiga ya rufe ni kuma ina ganin haka na fito a mota ta na kwankwasa kofar gate din maigadin ya leko yace min was nake nema nace masa budurwar da suka shigo nan gidan yanzu a mota,maigadin ya kalleni sosai yace na shigo,gurin kallon gidan na 'bige Rufaida"
Rufaida tayi dariya tace
"Yanzu akwai gidan da zai rudaka Yaya Malik,bayan kuma gidanku mai kyau ne sosai"
"Ke ana miki maganar gaba fa da gabanta akace fa,kuma kinsan komai gareka akwai wanda ya fika haka rayuwa ke tafiya
"Eh hakane

Please Login or Register in order to submit comment