Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

korarin rufe laptop ta kwanta ta ajiye laptop din tana kallon kofa kafin ta taso sbd kada atada afia datai baccin gajiya.

Ganin jekadi cikin yanayin ba daidaiba yasata fitowa dakin gabaki daya tana rufewa tareda kallon jekadin cikin mamaki tace"

Lafiya kike jekadi?
Bakida lafiya ne?

Girgiza Kai tayi wani irin mummunan gumi dayafi kamada Ana sheka Mata ruwan zafi Dan har tsiyaya take ta bude Baki daqyar a Dan wahalce tace"

MALEEK....kije kidubo MALEEK....guba..gubar qona jini a tea.....

Arude NURU take kallon bakin jekadi kayan cikinta na juyawa tsabar kaduwa tace"

Guba...maleek kuma?....

Turata jekadi tayi tana cewa"

Kije da sauri kidubosa akwai matsala babba.

Juyawa tayi da gudu tana waiwayen jekadi akaro na farko tana hawa Daman MALEEK dukkanin jikinta na rawar tsoro da firgici itakuma jekadi Kai tsaye dakin padima ta Isa ta Sanya mukulli daga waje kafin tafada dakin mum Sarah tana fidda wani gurnani azaba da wahala.

Tana Shiga qaton palonsa na farko taga Kofa biyu daya ta palonsa na biyu daya ta dakin matarsa lailah Bata tsaya komaiba ta nufi wadda qafafunta suka jata zuwa ta bude da sauri ta fada nanma wani palon ne tana hango kofar Master bedroom dinsa ta nufa da gudu ta fada ko ganin gabanta sosai batayi.

Cak ta tsaya tsakiyar dakin sbd fitowarsa wanka kenan dagashi sai towel iya qugunsa dukkanin fatar jikinsa tayi jajir kamar anmasa duka da danqo
Hankalinta take yaqarasa hargitsewa tanabin jikinsa da kallon qafafuwanta na daukar rawar tashin hankalin ganin wannan mummunan al'amarin.

Sbd jininsa nada tsananin karfi yasa yake iya controlling tsananin azaba da radadin dayakeji na juyawa cikin jininsa ya dauke idonsa daga kallonta tareda juya Mata baya sbd rashin kayan jikinsa.

Ganin masifar tafi yawa abayansa yasa batasan lokacinda ta qaraso da guduba ta Dora duka tafin hannuwanta a tsakiyar bayansa Wanda yasa wata ajiyar zuciya me qarfi kufce Masa sbd wani sanyin saukin azabar dayaji
ya juyo gabaki daya Yana kallonta hannuwanta akan jikinsa ya lumshe fararen idanuwansa dasuka koma jajir yabudesu fes akanta.
Ba sha'awar mace yakejiba ko kadan sbd komaima bazai iyaba ayanxun sbd konuwa da tafasar dayakeji acikin jikinsa Amma haduwar jikinta da nasa ya raunana azaba da zafin dayake ji sosai
yasake ware idanuwansa akanta tareda matsowa cikin jikinta sosai tayi saurin kasa da ido zuciyarta na harbawa haryana iya gani ta saman kirjinta

Hannu 'daya yasa ya zagayota tareda matseta cikin jikinsa yasakejin wani sanyi yasake sauke ajiyar zuciya tareda Dan sassautawa yana kallon fuskarta daidai ta dago zuciyarta na harbawa da tsoro da firgici da komaima ta kallesa idanuwansa suka shiga cikin nata kusan atare suka sauke ajiyar zuciya
Ya dago hannunta ahankali Yana kallon fuskarta ya Dora kan botiran rigar baccinta
Ta maida idonuwanta ahankali ta rufe bugun zuciyarta na tsananin Tues tanaji Yana bude botiran rigar har qarshensu rigar ta zame a tsorace ta rungumesa sbd kirjinta dake bayyane qyam.

Atare suka sauke qaqqarfar ajiyar zuciya musamman shi dayaji sanyi na shigarsa ya rungumeta gabaki daya cikin jikinsa idanuwansa alumshe.
##MAMUH#




_ZAFAFA BIYAR_๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–

_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_


_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._


ฦŠaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huษ—u____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0903 234 5899
*_Mamuhgee 27_*
Wani irin 'dumi taji Yana yawo cikin jikinta sbd akaro na farko arayuwarta da jikinta ya hadu Dana wani ba kayan komai ajikinta ga jikinsa da zafi Sosai sai qara manne jikinsu yakeyi Yana sassauke ajiyar zuciya ajere batasan lokacinda ta rufe idanuwanta ba tana sake shigewa jikinsa sosai sbd ganin kaman hakan na rage Masa Abinda yakeji,
Ahankali tazagaya da hannuwanta zuwa bayansa ta rungumesa da kyau take wani wawan jiri ya debesu su dukan ba shiri ya xebe kan makeken round royal bed din dake make da tsakiyar dakin shine a qasa itace a samansa ya lumshe idanuwansa tareda budesu daqyar ya kalleta yaga yanda idanuwanta sukai lahu alamar batada zabi sai nasa ya juyar da ita gefe ta kwance tareda sake shigewa jikinta ahankali Yana fidda wani boyayyan wahalallen numfashin tsananin azaba.

Ganin haka yasa hankalinta yatashi tasake rudewa ta qanqamesa cikin jikinta tana shafa bayansa da tafin hannuwanta ahankali ahankali tana karanto addua sbd batasan takamaimai mezatayiba ga jikinsa har lokacin da wani irin zafi.

Zameyi da sauri ta sauko gadon idanuwansa na rufe har lokacin ya dungule guri daya sbd azaba ta Sanya hannu ta zare wandon rigar baccinta tareda pant dinta cikin tashin hankali da sauri ta nufi toilet dinsa ta fada daqyar ta iya gane kan toilet din ta sakarwa kanta ruwan sanyi masu tsananin sanyi harsaida numfashinta yakusa daukewa sbd sanyi haka ta daure ta fito da sauri ta nufo gurinsa
Ya bude idanuwansa daqyar yayi Mata wani irin kallo yanajin 'yarinyar qarasashi kawai zatayi daga kwance kafin ya lumshe ido tashige cikin jikinsa sanyin jikinta na shigarsa yasake qanqameta Yana cusa kansa cikin wuyanta dake zuba qamshin turaren _Byredo_ ya sake Kai fuskarsa kan tata suna shaqar numfashin juna sosai ta bude fararen idanuwanta itama dasukai taushi ta kallesa shima ita yake kalla da nasa jajayen idanuwan tanajin hannuwansa na yawo jikinta Amma Bata iya motsawa sbd har lokacin cikin azabar ciwon yake Saida duk sanyin jikinta yashige nasa jikin itama jikinta yadauki dumin nasa yafara sauke ajiyar zuciya yanajin sauki saukin tsananin zafin dayakeji.

Tsit dakin yayi bayan sanyin AC daketa yawo a dakin Babu me motsi acikinsu musamman ita dake cikin jikinsa a nade numfashi ma ahankali take fitarwa sbd tsananin hali na kunya datakejin kanta aciki yanzu sbd ayanda taji yayi tsit tabbas sauqi yafara zuwar masa.

Tsawon lokaci suna ahaka Babu me motsi ahankali ta zame Yana jinta Amma bai motsaba ta tashi zaune ta gyara Masa rufa ta sauka gadon ahankali ta dauki kayan baccinta ta maida tareda dauke towel dinsa aqasa ta maida toilet tafito tasake taba jikinsa har lokacin da zafi Sosai sauqin kawai shine Yana iya daure ciwon yanzu Dan haka ta juya ta nufi kofa Dan zuwa gurin jekadi Koda akwai maganin daza'a bashi sbd tsananin zafin jikin yayi yawa idan Babu zata Kira Mr Omar yanxu cikin Daren nan yazo anema likita.

Saukowa tayi tana duba qaton agogon dake Palo daya nuna qarfe biyu da mintuna hudu ta nufa dakin jekadi Kai tsaye ta bude tashiga Bata gantaba.
Da mamaki cikin tsoro ta Isa kofar toilet din dakin cikin rashin nutsuwa takira sunanta harso biyar taji shiru a rikice ta bude bayin tana jefa idanuwanta ko Ina Amma bata ciki ko rufe kofofin bataiba ta fito da gudu tayi dakin mum Sarah tana bude kofar tayi saurin zaro ido tareda qarasowa cikin firgici tayo kan jekadi da jikinta haryafi na maleek yin jajir da daukar zafi ta dago arikice tace"

Mum Sarah kikawo ruwan sanyi sosai da towel da sauri.

Hannuwanta har rawa sukeyi tafara ragewa jekadi kayan jikinta tabarta daga ita sai shimi
Ta karbi towel din da mum Sarah ke miqo Mata yadau sanyi sosai sbd ruwan kankarane aka saka Masa ta ya6a Mata ajiki take sanyin yafara shigarta tafara jero ajiyar zuciya a wahalce.
Ganin hakan yasa NURU ta miqe da sauri kafafunta har rawa sukeyi ta nufi dakinsu kota kan afia dake kwance a qasa batabi ba ta zari wayarta ta fito sauri ta nufi dakin mum Sarah tana Nemo numbern Mr Omar dayake shima acikin mansion din yake Yana ganin kiranta ya tashi zaune sbd koyaushe a shirye yake kullum dare Baya wani dogon bacci sbd tsaro.
Cikin girmamawa ya dauka da cewa"

Barka da.....a yamutse ta katsesa da cewa"

Mr Omar maleek da jekadi sunci ko guba kokuma wani Abu daban kaga kawai kazo yanzu yanzu matsalan babbane, maleek... maleek..jikinsa duka yayi wani...

Ko rufe Baki batayiba taji buga kofarsa
Ta dago a tsorace ta kalli kofar palon zuciyarta na bugawa da qarfi sbd tsananin tsoro
Ta cikin wayar dake kunnenta har lokacin taji yace"

Nine abude kofar da sauri.

Da gudu ta qarasa kofar ta bude Masa dukkanin jikinta rawa yakeyi Bai dago ya kalletaba yace"

Zanduba jekadi ta jikinta zamu gano ko menene.

Da sauri tayi gaba tana cewa'

Zo zo zo kaduba suna cikin tsananin azaba,
Maleek ya....shiru tayi tana kaucewa ya qarasa gurin jekadi da sauri
Kallo daya yayi Mata yasan menene
Da sauri ya daga hannunsa daya yakai bakinta saikuma ya kasa tabbatarwa ta hakan ya dakata cikin tsananin tashin hankali yace"

Idan na tabbatar garin asirin Kona jinine Wanda zai.....

Cikin tsawar dabatasan Tai Masa ba tace"

Mekake jira ka tabbatar Mana maleek na can cikin irin halin kayi sauri kafada mana abinda za'ayi kokuma Akira Dr Damien kaduba kaga halinda suke ciki...

Sake sauke Kai yayi cikin Dan Jin nauyin zancen yace"

Bakinsu za'a laso aji idan da daci sosai.

Wani irin kallo Tai Masa itama cikin tsananin Jin zancen wani iri daga sama.

Ganin kallonda mum Sarah Tai Mata ta sauke Kai haka shima Mr Omar din yasata Shan jinin jikinta sbd hakan na nufin itace Dole zataje ta dandano musu na maleek tunda dai Babu me iya Shan na jekadi hakama maleek Dole sai ita Dan dama irin wannan masifar idan ta samu mutum Miji ko Mata ke lasa bakin idan Kuma yarone iyayensu idan tsofine yayansu.

Juyawa tayi da sauri ta fita ta nufi hanyar sama zuciyarta na bugawa a qarfafe sbd tsoro haka ta qarasa dakin har lokacin Yana kwance lullube idanuwansa arufe ganin hakan yasa ta qarasa da sauri ta haye gadon Bata tsaya wata wataba takai fuskarta dap da tasa zuciyarta na harbawa tasa hannuwanta biyu ta tallafo fuskarsa ta rufe idanuwanta ta Dora qaramin bakinta kan nashi ta zura harshenta cikin bakinsa ahankali ta laso sai alokacin ta bude fararen idanuwanta ta kallesa ga mamakinta saitaga idanuwansa a bude hancinta yake kallo.

Da sauri ta zabura tareda zare bakinta tana saukowa gadon dukkanin jikinta na rawa tayi kasa da kanta zatai mgn can qasan maqoshinsa ya bude Baki a wahalce yace"

Idan jekadi ce ko mr Omar kice abinda suke zargine Mr Omar yasan password na inda maganinsa yake
Daga haka ya maida idanuwansa ya rufe sbd azabar abinda yakeji cikin jikinsa

Da sauri ta juya daga dakin ta fice zuwa qasan har tana hada bene uku uku gurin saukowa ta iso dakin da sauri ta kalli Mr Omar muryarta na rawa tace"

Yace shine duk abinda kuke zargi din kayi sauri ka dauko antidote din yace kasan komai please please please hurry Mr Omar...

Cikin sauri sauri shima yace"

Ok ok Amma Dole saimun tabbatarda bakin nasa akwai "daci sbd ta hakan zansan idan yagamabin jininsa..

Rikicewa tayi tana rawar murya tace"

Eh"kawai sbd ita Bata wani gane daci acikin bakinsaba gabaki daya ta rude da wani irin dumi da qamshin _Vedshakti lemon mouth freshner_ data debo abakin nasa Dan haka bazata iya tantance komaiba.

Tashi Mr Omar yayi ya fice daga dakin da sauri haryana tuntube tabarsu cirko cirko a tsaye kowa kayan cikinsa na juyawa sbd fargaba.

Jin shiru shiru yasa NURU fitowa takalli agogo lokacin har qarfe uku da arbain tayi tafito Palo yafiso goma tana komawa dakin mum Sarah Jin take Kamar tayi Ari hauka ta dauko wayarta zata Danna Masa Kira sai gashi yashigo da gudu gudu ya miqa Mata Yana cewa"

Hada da ruwan zafi kikai Masa yasha inshallah zafin zai sauka gabaki daya bayan asuba saina Kira Dr Damien.,
Idan yasha zaiyi amai sosai karki basa komai bayan wannan sai bayan 2 hours.

Karba tayi tayi kicin mum Sarah na bayanta jikinta na wata irin rawa take dafa maganin harsaida mum Sarah ta matso cikin tausayi da damuwa itama tace"

Ki nutsu Inshallah maleek da jekadi Babu abinda zaisamesu.

Gyada Kai tayi kawai tana dauko cup cikin cups din MALEEK dake gurinsu daban ta zuba Masa ko a tray Bata tsaya dorawaba ta dauka ta fice da sauri tana cewa"

Mum Sarah ki zuba kiyi gaggawar bawa jekadi.

Tana Isa dakin ta ajiye cup din saidata qara sanyin AC kafin ta qaraso gadon ta aje cup din kan bedside ta kallesa tanajin nauyin yanda zata bashi sbd tagama fahimtar Dan idanuwansa na rufe bashine ke nufin Yana bacci ba.

Kafin tayi wani yunquri taga ya motsa tareda bude idanuwansa Yana tashi zaune batareda ya kalletaba ya miqa hannu daqyar
Dasauri ta dauko cup din ta matso ta miqa Masa tareda tsayawa akansa Kamar zata fasa kuka sbd Jin yanayin take har cikin ranta.

Kurbi daya yayi ya dakata sbd abinda yakeji ta matsosa sosai cikin kulawa da damuwa tace"

Yace duka za'a shanye.

Ko kallonta Bata samu damar yayiba yasake daga cup din yasha Yana rufe ido tareda shanyewa ya miqa Mata cup din da sauri Yana saukowa gadon ya nufi toilet yafara kelaya wani irin aman azaba Wanda yasata kasa hkr tabisa ciki idanuwanta na cikowa da ruwa musamman ganin Aman hadda jini sosai aciki ta rude tana dafa bayansa da har lokacin yake bayyane ba Kaya ajikinsa Dan abin kamar daurin Rai da dai towel dinsa har lokacin be kunce ba koya kunce akwai qaramin gajeran wando ajikinsa.

Saidayayi mugun amai sosai kafin taji take zafin jikinsa ya sauka gabaki daya ta zuba Masa ruwa ya wanke fuskarsa da bakinsa ta fito tabarsa aciki ta sake gyara Masa gadon da duk suka cukuikuye sbd rudewa ta dauki cup din ta fice daga dakin tun kafin yafito sbd ta lura tun cikin toilet din yadawo MALEEK dinsa.

Gurinsu jekadi ta Isa da sauri itama cikin sa'a ta tararda ta amaye komai gabaki daya ta shigo suka kamata tareda goggge Mata jiki suka kwantar da ita take baccin wuya ya dauketa sai alokacin dukkaninsu suka saki ajiyar zuciya me qarfi abinda takeji tokare a zuciyarta ya fada Mata ta dafe goshinta tana sake sakin jerin ajiyar zuciya kafin ta dago dmta kalli mum Sarah tace"

Menene yafaru bayan shigewata da daddaren?

Ajiyar zuciya mum Sarah tasaki tareda sauke Kai qasa cikin rashin sanin takamaimai na komai tace"

Bansaniba
Kawai dai abinda nasani shine jekadi tashigo dakina acikin wannan halin
Abu daya tace shine na jininta na quna.

Wani sabon numfashin takuma saukewa me zafi kafin ta bude Baki tace"

Shikenan zuwa da safe idan duk sunji sauki zamuji abinda ya samesu
Ki lura da ita Mr Omar zai Kira Dr bayan asuba.
Juyawa tayi ta fice jikinta a matuqar mace sai yanxu takejin tsamin jikin guje gujen dataitayi daga sama zuwa qasa ta nufi dakinsu ta fada kan gado tareda lumshe idanu tana godewa Allah dayasa komai ya tsaya nan Amma Kuma zuciyarta na Bata wani irin yanayi Mara Dadi na afkuwar al'amarin sbd idan har ciwon maleek ne kaman yanda yasaba to ita jekadi fa?
Gabaki dayama wannan ciwon wani babban abune na daban sbd azabar dasuka Shiga sai me qarfin jini ne kawai zai iya dauka dan kuwa taga tsananin azabar dasuka shiga musamman MALEEK.

Bude ido tayi ahankali tasake lumshewa har lokacin tanajin dumin jikinsa daya Shiga jikinta sbd ba qaramin full body contact suka samu ba Dan ita yacire rigarta shikuma dama Babu anasa jikin.

Saurin rintse ido tayi da qarfi tana cire tunanin cikin ranta ta gyara kwanciya Dan tasamu bacci ya Dan dauketa kafin asuba.
##MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–

_Alkiblah--SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara--BILLYN ABDULL_
_Dalaal--MISS XOXO_
_Mabudin zuciya--HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek--MAMUH GEE_

_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._

ฦŠaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huษ—u____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0903 234 5899*_Mamuhgee 28_*
Da asuba Saida afia ta tada ita sbd nannauyan baccin daya dauketa ta bude ido daqyar ta kalli afia kanta na wani irin sarawa sbd nauyi dayayi mata sbd rashin bacci da damuwar abinda yafaru cikin daren.
Tashi tayi daqyar ta nufi toilet tashiga tayo alwala tafito ta tsaya gefen afia ta tada tata sallar.

Suna idarwa afia ta ringa satar kallonta a kaikaice sbd duk wani motsin NURUn qamshin turaren dad dinta takeji ajikinta yana tashi.
Shiru tayi sbd batamasan mezatace ba Amma mamakinta anan Ina NURU ta hadu da qamshin?
Ta Yaya?

Ganin idan tayi magana Kamar ta muzanta NURUn ne yasata yin shiru ta Adana kalamanta tukuna.
Gari nafarayin haske NURU ta fito ta nufi dakin mum Sarah ta dubo jekadi har lokacin bacci takeyi saita fito ta nufi dakin padima ta tura tajisa arufe taga key din ajiki ta waje saita bude dakin tareda shiga har lokacin bacci padiman keyi ta qarasa bakin gadonta ta taba bargonta ahankali zata tasheta
Padiman tasaki wani razanannan ihu tana zabura zaune gumi duk yagama jiqata idanuwanta duk a waje take kallon fuskar NURU jikinta na Dan rawa ta sharce gumi tana saukowa daga gadon.

Da mamaki da tsoro NURU ke kallonta tace"

Lafiya padima?
Mafarki kikayine kike wannan ihun kina hada gumi haka?

Kasa kallonta padima tayi sbd har lokacin gumi takeyi cikin tsananin firgicin mummunan mafarkin datayi batareda ta waiwayo ba ta nufa hanyar toilet tana cewa"

Mafarki nayi sbd banyi addua ba na kwanta.

Bayanta NURU tabi da kallo cikin mamaki sosai kafin ta juya ta fice daga dakin ta nufi kitchen tana Danna Kiran Mr Omar.

Saidata tabbatarda ita kadaice a kicin din tace"

Gud morning Mr Omar.

Barka da tashi ranki ya dade"yafada daga can bangaren cikin girmamawa.

Shiru tayi cikin nazarin abinda zata fada Masa...shikuma Jin hakan sai ya gyara murya cikin nutsuwa da Bata tabbaci yace"

Dr Damien yazo ya duba MALEEK tun six harya wuce ma inshallah komai ya wuce.

Sake yin shiru tayi tana wani nazari kafin ta sauke ajiyar zuciya me sauti tace"

Mr menene wannan ciwon?
Shin kodai wani abun sukaci kokuma ya taba skin dinsu?

Tsit Mr Omar yayi Jin tambayar tata saidai baija shirun da tsayiba Dan kada ya Bata hope na zai amsa tambayar ya Dan sake gyara murya cikin Bata girma yace"

Ranki ya dade Inshallah allergy ne kawai Amma bana saka ran da...
Qin qarasawa yayi tareda dauko zancen itama jekadi kowane lokaci duk zasu farka lafiya Inshallah.

Ajiyar zuciya ta sauke zuciyarta na wasi wasin abinda yace na cewan allergies ne,
Wane irin allergy ne wannan me tsananin azaba.

Daga sama tajisa Yana qara saita murya yace"

Ranki ya dade idan na hali Dan Allah basai 'yayan MALEEK sunsan meya faruba,kowama Dan Allah kada yasani sai maleek ya tashi anji daga garesa shida jekadin.

To" kawai tace tana kashe wayar cikin 'yan tunane tunanen dasuke shigarta.

Kasa yin komai na breakfast tayi tabarwa Fana aikin ta wuce daki tashiga wanka tafito lokacin har afia tagama shirinta itama tahau shiri suna gamawa ko breakfast NURU batayiba afia ce kawai tayi suka wuce makaranta.

Tunda suka Isa NURU batada sukuni tunanin halinda yake ciki ya hadu da karatun exams dinta ya hargitsa Mata Kai har wani jiri jirin ciwon Kai takeji sauqinta dayane daga yau tagama exams dinta hutun gaske zatayi kafin sudawo hutu inshallah sbd tana tsananin buqatar hakan.


****
Qarfe goma Sha 'daya da mintuna shida maleek ya sauko ahankali yake tafiya cikin nutsuwa da kamewa Yana sanyeda jallabiya milk sai daukan ido takeyi sbd maiqo da laushin yadin jallabiyan.

Mr Omar dayake tsaye tuntuni Yana jiransa a palo yayi saurin sake sauke kansa cikin tsananin biyayya ya sake ja baya maleek ya wuce yabi bayansa cikin tsananin girmamawa yace"

Barka da fitowa MALEEK.
Allah yaqara lafiya da Nisan kwana tareda tabbataccen tsari da kariya.

Fitowa sukai suka nufi gym dinsa har lokacin Mr Omar na bayansa suna shiga a Dan qaramin palon dake ciki maleek ya zauna tareda Dan lumshe idanuwansa dasuke Dan nuna yayi rashin lafiya sbd sunyi haske sosai sun 'dan fada sai hakan yayi kaman yaqara Masa kyan fuska.

Cikin nutsuwa Mr Omar ya matso daga bayansa yace"

MALEEK garin meriz ne jekadi ta farka tun dazu nayi magana da ita a dakin littafai ta tabbarminda.......shiru yayi tareda sauke Kai.

Dagowa maleek yayi batareda ya kallesaba yace"

Uhum...

Sake gyara tsayuwa mr Omar yayi Yana Dan gyaran murya a raunane yace"

Jinin mushrah ce tayi wannan aikin.

Alokacin ya dago manyan idanuwansa dasuka koma fararensu tas ya dorawa Mr Omar dayayi saurin yin qasa da Kai Yana cewa"

Afuwa MALEEK Amma tabbacen zancen kenan na duba shayin da jekadin ta gabatarmin tareda tabbacin zancenta na cewa tun a gizah taga abin zargi atattare da jinin mushrah din.

Shiru dakin ya dauka tsit na tsawon lokaci maleek baice komaiba
Mr Omar Kuma jiran damar dazai cigaba da koro bayanin sauran zancen.

Ko motsi maleek yayi Mr Omar yasan manufarsa Dan haka shirun maleek din ya tabbar Masa da abinda zaiyi ya juya a nutse ya fita tsawon mintuna uku saigashi tareda jekadi da itakam ta zurma sosai ba laifi saidai jikinta lafiya kalau takejinsa Mr Omar ya rufe kofar ya qaraso yace"

MALEEK ayanda jekadi tayi bayani Babu sanin mushrah ko wani daga cikin ahalinsu gameda wannan aiki na 'yar uwarta,
Akwai banbancin halaye da ra'ayoyi me girma a tsakaninsu Wanda Kai tsaye zamuce hassada kokuma rashin wayo yasa wani daga cikin gizah yake amfani da ita batareda tasaniba.

Kallon jekadi maleek yayi cikin nutsuwa da kamewar murya yace"

Inawa jekadi ya jiki tareda barka da arzikin samun lafiya.

Cikin girmamawa me girma tace"

Godiya nake maleek hakama jekadi nayi maka sannu da jiki.
Maleek kaman yanda kasani Babu inda wannan aiki yafito sai a gizah Kuma kamar koyaushe dai zarginmu Yana yawone akan mutane da yawa musamman idan mukai la'akari da bincikenmu damuketa fama a dunkule na rasuwar mahaifinka,
Tsawon shekarun Nan Danayi a delah naqi barowa nayi bin duk wani diddiqin sirri Babu wani alamar acan ko wanenen me wannan garin na meriz yake Amma yau bayan shekaru masu tsayi garin yasake bayyana Wanda hakan na nufin garin meriz a cikin delah gizah yake.

A Daren ranar dazamu zo cikin dare Naga abin zargi a sassan baquwar mushrah Amma sbd na tabbatar nashiga najata da wani zancen Kuma tabbas hancina ya shaqi kusan qamshin meriz Amma sbd tabbatarwa naqi magana sbd tasamu damar zuwa dashi anan mu tabbatar da hujja saidai banyi zaton zatayi tsaurin aikata abinda aka aikota dinba ayimin afuwa MALEEK.

Kuma kaman yanda Mr Omar yafada hassadace me qarfi a tsananin padime da mushrah wadda ta samo asali daga cigaban aure da mushrah tasamu na MALEEK Kuma haryanzu mushrah batasan da wannan halayen na 'yar uwartaba Dan kuwa ko wannan zuwan nata inada tabbacin Babu alkhairi acikinsa sbd iyayensu takanas kaleeb yayi magana dasu bayan nayi Masa bayanin komai na ranar danaga mutum yafita daga sassanta Dan haka Ina me roqo da neman afuwan maleek akan kada yayi fushi da mushrah akan laifi mafi Muni da jininta ta aikata.

Tsit suka kumayi gabaki dayansu na tsawon lokaci maleek na nazartar abubuwa da dama acikin kansa wainda ba komai bane sai mutuwar mahaifinsa dayayi wato mutuwar azaba yanaji Yana gani duk da Yana yaro qarami lokacin Amma Yana iya tuno azabar dayaga mahaifinsa aciki,

Tun daga lokacin Basu sake ji ko ganin wani Abu daya danganci garin meriz ba sai yau sama da shekaru arbain kenan.
Tabbas zarginsu ya tabbata cewar a gizah kowanene yake Dan haka yanxu Kam aikinsu na gaske zai fara.

Dagowa yayi ya kalli Mr Omar dake jiran umarni ya maida idonuwansa kan jekadi Kai tsaye cikin kamewa yace"

Baza'a bari kowa yasan da zancenba ciki kuwa harda ita datayi aikin ki maidaita gizah idan tanacan ne za'a San waye shugaban aikin nata sbd na tabbatarda ita kanta nasan wa takewa aikiba sbd al'amarin me girmane bazasuyi saurin bayyanarda kansuba,

Amfanin wannan aikin na meriz da aka sata shine komawata gizah neman magani sbd sunyi tunanin acan ne kawai za'a samu maganin warkar Dani dagacan ne zasu qarasa niyarsu wadda baasantaba.

Gyada Kai jekadi tayi tace"

Kabar komai ahannuna kafin ka iso gizah Inshallah aikin yayi nisa
Inshallah sai Allah yacika nufin kaleeb Dan kuwa alqawarine sai anciyar da dabbobin gizah Naman duk Wanda ko da ido yataba ganin garin meriz bare ya taba.

Mr Omar ne ya matso yace"

Jekadi sai magana ta gaba itace umarnin maleek ne kada mushrah tasan abinda yafaru sai lokaci yayi hakama iyayenta
Duk abinda tayi idan lokaci yayi zatafada musu dakanta aranar qarshe da Babu gyara.

Gyada Kai jekadi tayi tana sake yiwa MALEEK fatar samun lafiya ta miqe ta fice.

Mr Omar kuwa gyara tsayuwa yayi yana sauke Kai yace"

Maleek meye ainihin wannan hukuncin na jinin mushrah da aka sanarwa jekadi.

Jininta ta aikata kuskure babba na cutatar da 'yar uwarta hassadarta tasa tasaka kanta cikin masifarda tun kafin mahaifinta yazama saurayi bare yayi auren haihuwarta.

Wayar kaleeb ya karba da Mr Omar ya miqo Masa bayan yagama yimasa bayanin komai dasuke ciki suka fara magana kowanne cikin kalar nasa ikon da kamewa ta sarautar dake jininsu kafin ya ajiye

Please Login or Register in order to submit comment