Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

goma sun shude da fara gyaran Negestati padima Amma Sam hankalinta a hargitse take takai yanxu ko rintsawa Bata iyayi tun abin na wasa tadawo ko abinci Bata iyaci take tafara wata irin rama da duhun tashin hankali daganan sai kukan dare Wanda yayi masifar daga hankalin NURU da duk duniya taqi jinin ganin damuwa akan fuskar iyayenta da 'yan uwanta ta tashi cikin tsakiyar dare tareda lalubar qaramar fitila ta kunna taga padima zaune hannunta riqeda wuqa tana faman wani irin kuka da sauri ta qaraso ta fixge wuqar cikin tashin hankali da tsoro jikinta yadau rawa sbd ita qaramin abu ke firgitata tace"

Padima me Zakiyi da wannan tafada ta wurgi da wuqar cikin tsananin tsoro.

Sabon kuka padima tasake tana qwacewa tace"

Mutuwa zanyi tunda ko ban kashe kaina yanxuba naje delah mutuwa zanyi.
#MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–

_SAFIYYAH HUGUMA_
_BILLYN ABDULL_
_MISS XOXO_
_HAFSAT RANO_
_MAMUH GEE_

_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN K xxAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._

ฦŠaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huษ—u____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0903 234 5899*_UBAYD MALEEK_*
_(Royalty versus love)_

*_Mamuhgee_*



*4*
Cikin tsoro da rawar murya NURU tace"
Padima kidena cewa mutuwa kina bani tsoro sosai kidaina kuka menene Dan Allah ki dena kina bani tsoro.

Ganin yanda NURU duk ta firgice cikin tsananin tsoro yasa tadan sassauta tayi tunanin amfani da tsoron NURU sbd dama can ita abu kadan yake Bata tsoro saita sake marairaice fuska tana faso wani kukan tace"

NURU idan Banga amed mukai magana ba akwai babbar matsala wlh komai zai lalace zamu rasa komai da iyayenmu duk mutuwa zamuyi.

Zaro manyan fararen idanuwanta NURU tayi jikinta na daukar rawa tana sake padiman takasa magana tana neman yin baya ta fita a rude padima ta riqota da qarfi tana cewa"

NURU wlh dagaske nake idan bangansa munyi magana ba komai zaifaru Dan Allah kimin hanya naganshi idan nadawo zan fada Miki komai Amma wlh rayuwata na cikin hadari danasu abal ma..

Kasa fahimtarta NURU tayi sbd firgici sai rawa da jikinta keyi ganin hakan yasa padiman taja wani qaramin tsakin takaici tareda girgizata da qarfi ta jawota ta direta zaune tafara shafa bayanta tana hura Mata iska tana kiranta ahankali ahankali hartafara nutsuwa tana dawowa hayyacinta saidata rarrasheta tadawo hankalinta tsaf tukuna ta janyota ta kwantarda kanta kan cinyarta tafara Sabin hawayen samun yaddar NURUn tasake fada Mata abinda tafada Mata da farko NURUn daketa ajiyar zuciyar ta qanqame padima cikin tausaya Mata murya amatuqar sanyaye tace"

Padima idan kikaga amed din shine zesa bazaki kashe kanki ba ko?

Eh NURU bazan kashe kainaba Ni sbd ma kune nakeson ganinsa na nema mafita.

Haka ta lallaba NURU taringa marairaice Mata da kuka hartayi nasarar cika tunanin NURU da tausayinta akan alamarin shiyasa washe gari da za'aje wankan ruwan Madara saita lullube fuskarta taje amaimakon padima bayan tayi Mata hanya sunyi sauyin kaya ta fitar da ita gidan masu wankan dasuka ganta saisuka tambaya tace ai yanzu ita za'a ringawa ba padima ba dayake bayin qasane gabaki daya saisuka yarda sbd manyan bayi basa fitowa delah bare akawo musu irin wannan.

Dama Shima NURU taje ta sanar dashi padima zata fito tanason ganinsa shiyasa yaje inda suke haduwa Yana jiranta danshima a mugun qage yake da ganinta Dan wlh Shima be shirya mutuwaba tunda yasamu labarin ita aka bayar yasan qaryarsa taqare kashesa zaayi duk ranarda akaji shine yafara kwanciya da ita.

Kamar munafuka haka take tafiya tana waiwaye tana boye fuska harta iso Yana ganinta da gudu ya qaraso yakama hannunta suka nufi can nesa da gidajensu cikin wani lambu bayan bishiyar ayaba ya rungumeta Yana cewa"

_Ya Allah Padima nafekushi_
(Ya Allah padima Nayi kewarki sosai)

Kuka tafashe dashi tana turesa daga jikinta tace"

Amed duk mutuwa zamuyi
Banason mutuwa guduwa zanyi da qasarnan zanshiga duniya bazan tsaya akasheni ba...

Riqota yayi da sauri Shima cikin firgicin yake yace"

Padima ki nutsu musamo mafita Nima angaya Miki na shirya karban wannan hukuncin ne?
Bazan iyaba nikaina mafitar nake nema.

Zamewa tayi qasa tayi zaman dirshan tana cewa"

Amed kayi gaggawar samo mafita kokuma kawai mu gudu.

Mu gudu muje Ina padima?
Idan muka gudu burirrikanmu fa damuka Dade muna....

Cikin masifar tashin hankali ta katsesa da cewa"

Burin banza tunda Saida rayuwa zamu cika burin,
Ni kaga kawai musan abinyi wlh na cikin masifa wannan wane irin balai ne nasaka kaina aciki amed ka cuceni...

Kinga yi hakuri kidaina kukan yanxu mafitarmu dayace ajanye badake abada NURU.

Wani kallon takaici da baqin ciki tai Masa tana cewa"

Sun San da NURUn suka badani sbd tunanin ita wawuyace batada wayo Ni bansan inda zansaka kainaba zuciyata fashewa zatayi....

Da sauri ya durqusa gabanta cikin Dan samun sa'ida yace"

Muyi amfani da sanyin halinta kiyi Mata wayo ki gurbata Mata tunani da tsananin tausayinki ki Bata tsoro da rayuwar iyayenku da kanta zata bada kanta.

Dakatawa tayi da kukan datake ta dago idanuwanta dasuka gama kunbura sukai jajir ta kallesa tana qoqarin karban abinda yafada din cikin nazarin maganar tace"

Kumafa hakane..
Batada wayo zan iya sata ta bada kanta da kanta.

Zabura tayi ta miqe tsaye tana share hawayenta cikin farin ciki tace"

Meyasa banyi tunanin hakanba tun farko?
Meyasa na tsaya Bata lokacina cikin tsoro da tunanin zan mutu bayan inada NURU.

Riqosa tayi da sauri cikin tsananin farin ciki tace"

Amed kashirya komai zai tafi yanda mukeso zanji da NURU sauran aikin idan mukazo tareda ita saikayi naka.

Rungumeta yayi Yana cewa"

Karki damu tunda munada wadda zata shiga tarkon mukuma mu fita kuka yaqare sai Dadi da rayuwar delah gizah dake jiranmu.

Shafarta yashiga yi Yana lallashinta da qara Bata shawarwarin yanda zasuyi hardai suka samu suka sake biyan buqatarsu agurin Saida duhu yadan yi yarakota har bayan gidansu ta zagaya tashige yakoma cikin farin ciki.

Itama cikin farin cikin tadawo gidan ta tararda NURU a daki tana jiranta cikin firgici da tsoron rashin ganin dawowarta kan lokaci tana ganinta ta taso da sauri cikin tsoro ta rungumeta tana sauke ajiyar zuciyar ganinta tace"

Padima kinbani tsoron rashin dawowarki kan lokaci.

Murmushin jin Dadi padiman tasaki tana rungume NURUn tace"

Wallahi Bet'ami afek'irihalewi NURU.
(Wallahi Ina tsananin sonki NURU)

Ajiyar zuciya kawai NURU ta sauke suka qarasa komawa ciki suka zauna ta marairaice fuska tana Shirin fara hawaye NURU ta katseta da cewa"

Padima karkiyi kuka Dan Allah tunda kingansa kinsamo mafitar matsalarki ko?

Girgiza Mata Kai padima tayi tana tsoyayo hawaye tace"

NURU banason mutuwa,
Banason abal da ammi suma su tafi su barku dagake se meryam qilama duka tafiya zamuyi mubar DUNIYAR bansan yazanyiba duk nice na janyo shiyasa nakeson na kashe kaina nahuta kowama ya huta.

Da sauri NURU ta girgiza Mata Kai tana cewa"

Padima bazan iya Bari ki kashe kankiba gwara mu mutu gabaki dayan koma menene yafi Mana sauqi bazamu iya juran rashin 'daya daga cikin ahalinmu ba kidaina fadar hakan muna tsananin sonki bazaki mutuba yanzu inshallah.

Jan numfashin kuka tayi murya na fita daqyar tace"

NURU kinsan menene yake faruwa ga duk negestati dinda aka Kai aka tararda batada budurci tabawa wani??

Ras Ras qirjin NURUn yayi wani mummunan bugawa harsaida jikinta ya nuna hakan sbd rawar daya Dan dauka ta kalli padima da fararen idanuwanta cikin rashin fahimta tace"

Meya kawo wannan tambayar padima?

Sunkuyar dakai tayi tana tsoyayo hawaye tace"

NURU nida amed mun.....

Wani mummunan tarine ya qware NURU idanuwanta suka firfito tafara tarin cikin azaba da tashin hankali tun tana shafa Mata baya hardai dole suka fito daidai fitowar amminsu Nan sukai kanta akaita Bata ruwa Ana fesa amata Amma sosai ta sarqu idanuwanta sunyi jajir sbd azaba cikin fada ammi tace"

Menene ya sarketa padima?

Ammi kawai zaune take saita fara tari shikenan ne kawai.

Fitowa abal yayi daukeda sabuwar madarar raqumi yabata yakuma fesa Mata take abin yafada Mata tafara fidda numfashi daqyar tana rufe idanuwanta cikin galabaituwa.

Padima ta tayata ta watsa ruwa takaita daki itama tadawo tayi wankan tazo tayi sallah saikuma takejin kunyar NURU din Amma Kuma tunda dai amfani takeson yi da ita dole zata fada Mata hakan.

Kwanciya dukkaninsu sukayi babu ko me dogon motsi sbd tunanin da kowa keyi musamman NURU dake cikin tashin hankalin jin masifar dazata samu ahalinsu.
Washe gari ma NURU ce taje wankan ruwan madaran haka zalika takasa sake tankawa padima maganar dasukai din sbd har lokacin shock din maganar Bata saketaba.

Padima ganin ankwana biyu NURU taki cewa komai gashi zuwa lokacin kowa ya shaida NURUn Bata cikin hayyacinta tana cikin tsananin tsoro da tashin hankali saidai anyi tambayar duniya taqi fada sai kuka.

Hankalin iyayensu yatashi sosai musamman da itama padima suka lura duk a firgice take ta bangare daya wankan haryanxu basuda masaniyar idan anzo NURU akewa sai gidan yakoma Kamar gidan da akai muguwar mutuwa sbd gabaki daya kowa baya cikin nutsuwa anyi anyi NURU tafada abindake damunta taqi fada sbd gabaki daya tsoro da firgicin abinda zaisamesu yasa ta kasa dawowa hayyacinta tsoron fadama takeji.

Yau dai padima da takaici da baqin ciki ya isheta sbd saura kwana goma sha biyu cikar wa'adin cikin tsakar dare ta tashi ta sake dauko wuqa yauma tadawo ta zauna tsakar dakin tareda fashewa da kuka yanda NURU zataji Dan dama tasan ba bacci takeba saigashi tana bude ido taga padiman ta daga wuqa zata sokawa kanta da gudu ta zaburo ta riqeta cikin tashin hankali tace"

Padima.

Qwace wuqar ta hau Yi padiman ta riqe cikin tsananin kuka take cewa"

Kibarni NURU gwara na mutu sai kowa ya huta matsalarmu da tsoronmu zai qare idan na kashe kaina shikenan Babu Wanda zaisan abinda nayi bare rayuwar abal da ammi tashiga hadari duk laifinane Dana Bari harnazo yanxu ban Kai qarshen matsalarba gashinan kema nasaki a damuwa bazan iya ganinki cikin damuwa da qunciba NURU sbd Ina tsananin sonki 'yar uwata.

Cikin hawaye NURU tace"

Bazaki iya ganinaba cikin qunci kike tunanin Ni zan iya ganin kin kashe kanki.

Zamewa tayi ta zube qasa tana rusa wani sabon kuka tace"

NURU komai ya lalace a rayuwata
Mutuwata itace salama agareku sbd matsalar ta wuce yanda kike tunani NURU cikine Dani yanxu haka...

Neman zubewa NURU keyi padiman tayi saurin riqota tana cewa"

Kingani ko gashinan kina neman sumewa sbd jin wannan muguwar masifa gwara na mutu kowa ya huta NURU kibarni kawai....

Kokuwa suka hau Yi akan saita dauki wuqar NURU na riqeta cikin tashin hankali take gabaki daya hankalinta yakasa dauka wai padima harta San bawa wani kanta,mutuncin,qimarta hadda ciki.

Zubewa tayi qasa tareda rushewa da wani irin kuka Wanda yasa padiman itama zubewa tana sakin nata kukan.

Kwana sukayi kuka Koda gari ya waye kowacce fuskarta da idanuwanta sunyi suntum ai Nan hankalin abal da ammi yatashi musamman dasukai tambayar duniya kowacce tayi shiru har Saida abal din ya harzuka yace aqyalesu koma menene idan sunji uwar Bari sunzo dakansu sufada itadai ammi hankalinta bai kwantaba taringa lallabarsu Amma ba wata mgn saima Kamar zurfafa da NURU keyi da tunani.

Jan padima NURU keyi Kamar wata qaramar yarinya harsuka isa inda tacewa amed su hadu suna zuwa kuwa Yana gurin NURU ta jefesa da kallon qyanqyami da baqin ciki take zuciyarta ta gaurayu da tsanarsa saidai Babu yanda ta iya tunda dole cikin biyu daya za'ayi dole shine zataji idan zai auri 'yar uwarta daya lalatawa rayuwa.

Wani abu ta hadiye me Kama da dutsi ta zuba Masa manyan fararen idanuwanta dasuka kusa gigitashi ya dauke Kai da sauri sbd wlh kallon cikin qwayar idanuwanta kawai na iya sumar dashi da duk wani ma'abocin begenta.

Ka yadda da Kaine kawai kasan padima amatsayin 'ya mace?

Da sauri ya gyada Kai Yana satar kallon padiman dake Masa wani kallo.

Sake jeho Masa qata tambayar tayi da cewa"

Kasan cewa tanada juna biyu yanzu haka a jikinta Wanda yake nakane?

Nasani Kuma ashirye nake da aurenta kafinma kowa yasan da akwai cikin Amma Kuma sbd zata zama negestati wannan al'amari yazama mafi hadari ga rayuwarmu mu duka hadda ta iyayenmu,
Wlh inason padima sosai itama tana Sona NURU Amma yanzu tsautsayi daya gitta mukai wannan abin yasa yazama Kamar wata mummunar qaddararmu da iyayenmu da basujib Basu ganiba..

Rintse ido NURU tayi wani nauyi na ziyartar zuciyarta idanuwanta sukai jajir tace"

Idan harka aminta zaka aureta shikenan kaje kashirya kawai.
Juyawa tayi tabar gurin idanuwanta na sake rinewa da tashin hankali ta nufi gida ko gabanta Bata gani sosai ta fada dakinsu ammi dake zaune tsakar gida tana gyarawa meryam gashi tabita da kallo zata miqe tabita saiga padima tashigo itama tafada dakin.

Rungume NURU tayi cikin tsananin farin ciki ba kunya tahau yimata kukan godiya NURU da baqin cikin al'amarin ya danne Mata zuciya tace"

Padima menene ribar wannan masifar dakika saka kanki damu aciki?
Shin bakiyi tunanin abinda zai faru da iyayenmu ba lokacinda Zaki bawa wani kanki?
Shin bakiyi tunanin wace rayuwace makomar nida meryam ba idan hukunci yahau kanki keda iyayenmu?
Menene laifin su abal dabasujiba Basu ganiba idan anhukuntasu akan laifin da Kika aikata bayan dawainiyar dasukai akanmu suka bamu tarbiya.

Riqota padima tayi cikin marairaicewa tace"

NURU nayi nadama nayi Dana Dani Kuma tunda kin amince da rufa min asiri ki sauyeni ai matsalar ta wuce......

Ta wuce?
Ta wuce fa kikace padima?
Cikine fa ajikinki na namijinda ba mijinki kike cewa shikenan yawuce.....

Qarar sakin kofin silba sukaje daga bakin qofa take suka juya da sauri cikin firgici ganin ammi hadda abal tsaye yasa padima fara rawar jiki cikin tsananin tashin hankali NURU kuwa zamewa tayi ta zaune al'amarin na isarta Sam kanta baya iya daukan doguwar pressure.





*************
_Jericho new York_


Setin akwatinanta guda biyar cif aka jera Mata cikin mota guda qirar Mercedes Benz beymach 10/2607 2021 ta fito daga bedroom dinta sanye cikin wata doguwar turkian royalle satin gown red me kyau wadda ta fidda kyanta da kyan jikinta hannunta riqeda handbag din arkins irin qamshin datake fitarwa me yawa zaisa kasake tabbatarda ta aje auren tun daga cikin dakinta Dan Vail din rigarma rolling dinsa tayi iya wuyanta tafara saukowa cikin yanayinta na yanga da aji kamar ko yaushe.

AFIA dake zaune Palo riqeda hannun farhat daketa kuka kamar ranta zai futa tana ganin fitowar mum din tasu ta miqe tsaye itama idanuwanta na fara tsiyayar hawaye tafara girgizawa mum din tasu Kai tana cewa"

Please no mum,
Mum please please no.

Itama lailar tanason 'yayanta tanason kasancewa dasu saidai tasan ko zatayi mushe ubayd maleek bazai barmata 'yayansaba Dan haka tunda tasan zasu samu kyakkyawar rayuwa tareda dad dinsu bazata wani damuba ta qaraso ta rungumesu suka qanqameta suna kuka sosai suna roqonta sai Basu hkr takeyi tana cewa"

Zakuyi alfahari da mum dinki idan kukaga tazama cikin top 20s Inshallah.

Zamewa tayi zata wuce farhat ta maqalqaleta tana sakin sabon kuka cikin firgici tana Kiran sunanta.

Ganin haka hankalin afia yatashi taga mum din dagaske tafiya zatayi batasan yazatayi ta hanata tafiya ba batada zabin daya wuce takira _NEGES MUHAMMAD KALEEB DELAH_ asalin kakan dad dinta, tsohon NEGES(sarki) Wanda shine mafi soyuwa da shaquwa agurin dad dinsu sbd shine ya riqesa tun yarinyarsa sbd mahaifinsa dashine yakama yazama sarkin yanxu ya rasu sai qaninsa ya hau bayan an aura Masa mahaifiyarsa Wanda haryanxu shine asalin sarkin delah gizah na yanxu mahaifiyarsa Kuma sarauniyar delah gizah hakan yasa kakansa shine mafi kusanci dashi arayuwarsa danma shine ya tsaya Masa aka taka dokar mulki yabari ya auri LAILAH OMAR masoyiyarsa dasukai karatu tare 'yar asalin ghana dasuka hadu a San Francisco.
Duk da ba wani yabawa KALEEB yayi da LAILAH ba Amma sbd farin cikin ubayd yasashi amincewa yakuma rufe idonsa ya taka doka Dan haka yakeda burin qarawa ubayd maleek Mata Amma ubayd Yana qaidojin rayuwarsa Dan haka abin be yiyuba.

Akwai lokutan da ba'a Kiran KALEEB kaman dad dinta dashima akwai lokacinda ba'a kiransa Amma yau dole zata kirasa sbd shikadaine zai Hana wannan rabuwar sbd iyayen nata Babu Wanda ya tsaya ya saurareta.
Cikin sa'a Kira biyu a na uku aka daga cikin sauri tayi bayanin ita wacece tanason mgn da KALEEB sanin matsayin UBAYD da iyalansa agurin KALEEB yasa aka Kai Masa wayar cikin girmamawa aka miqa Masa ya karba sbd sanin ba'a kawo Masa waya sai me mahimmanci idan bashi yace akawoba.

Tanajin nutsatsiyar muryar Kaleb ta nutsu jikinta na rawa zata fara Masa bayani taji durin motar dad dinta yadawo Wanda yasa gabanta faduwa.

A nutse ya zuro dogayen qafafuwansa dake sanye cikin black brian Atwood brand loafers kafin yafito gabaki dayansa cikin Ralph Lauren brown suit data fiddo da dukkanin hasken fatarsa ta asalin amhara ethopiano.
Kallo daya zakai Masa kasan shine ya haifi AFIA sbd Kamar dasukeyi tayi yawa duk da Kamar yanda bazakace LAILAH ce ta haifi budurwa kamar afia ba haka Kai tsaye Shima bazakace shine ya aje budurwar 'ya ba sbd kyawun jikinsa da dukda yafara girma bai rabu da geamin ba ma'ana motsa jiki uwa uba ajinsa da asalin kyawunsa tareda izzarsa datake cikin jininsa da har gobe fresh take zamar masa Dan ko ita lailar har gobe duk gayunta da kyanta da Jan ajinta Rena kanta take agabansa shiyasa har gobe take kishin tazama wadda zata tsayu da kanta duniya tasanta da sunanta bada sunan waniba.

Ciki ya nufo qanshinsa na sauya atmosphere din gidan afia na ganin hakan tafara fadawa Kaleb abinda yake faruwa cikin nutsuwa da sauri....

Daidai shigowarsa farhat tasaki Laila tayo kansa da gudu ta fada jikinsa tana sakin sabon kuka Wanda yasashi sake tsuke fuskarsa tsaf wadda tasa Laila dauke Kai daga kallonsa ta nufi qofa zata fita baice Mata qala ba hakama AFIA qafafun lailan dasuka fita ta qurawa ido daidai Kaleb yagama jin komai zaiyi mgn sukaji daddadar muryar dad dinta data ratsa har cikin wayar zuwa kunnen Kaleb yace"

Na datse igiyan aurena dake kanki na sake ki you're free to go MSS LAILAH OMAR.

Dif afia ta dauke wuta cikin tsananin tashin hankalin jin abinda dad dinta yafada Kamar daga sama taji muryar Kaleb cikin ikonsa na tsohon sarki yace"

Ki dakatar da ita injini.

Muryarta na rawa idanuwanta na dishi dishi tace"

Mum Kaleb yace ki tsaya karki tafi Injishi.

Qin juyowa tayi bayan Sarai taji me afia tace saidai bazata iyaba ta daga qafafunta ta isa bakin mota aka bude Mata tashige suna kallo ta tafiyarta idanuwanta na cikowa da hawaye ta maida tana qoqarin kawarda abinda yake taso Mata saidai takasa Saida ta fashe da qaramin kuka tana rufe fuskarta da hannuwanta har suka fice daga qatuwar harabar gidan.

Murya na rawa cikeda firgici afia tace"
Kaleb Ta fita,ta tafi tabarmu.

Wani numfashi Kaleb ya sauke akaro na farko a tarihin rayuwarsa da wani ya bijire Masa Kai tsaye Kamar agaban idonsa Wanda shikansa ubayd hakan yasa dukkanin wata sauran kaunar Laila yaqarasa fice Masa daga zuciya har abada.

Cikin wata irin murya me babban sauti Kaleb yace"

Ki sanarwa da mahaifinki Ina buqatar ganinsa cikin gaggawa zuwa delah.
#MAMUH#



_ZAFAFA BIYAR_๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–

_SAFIYYAH HUGUMA_
_BILLYN ABDULL_
_MISS XOXO_
_HAFSAT RANO_
_MAMUH GEE_


_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._


ฦŠaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huษ—u____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0903 234 5899*_UBAYD MALEEK_*
_(Royalty versus love)_


*_Mamuhgee_*



*5*
Zubewa AFIA tayi kan kujera tana sake wani irin kuka tana cusa kanta cikin tafukan hannayenta dasuke rawa.
Kamar zai wuce saikuma yaji afian na buqatarsa ayanxun sbd yasan tana cikin radadi.
Cikin takunsa na zallar nutsuwa ta asalin jinin sarauta yatako ya iso gabanta tareda miqa mata hannu batareda yayi mgna ba ta dago jajayen idanuwanta dake tsiyayar hawaye ba kakkautawa ta damqe hannunsa tana Kiran sunansa ahankali cikin kuka mara sauti.

Janta yayi farhat na jikinsa ya haye sama dasu zuwa ainihin babban bangarensa dake daukeda qaton palon farko Dana biyu Wanda baiyi girman na farko ba acikin palon na biyu Nan qofar qaton master bedroom dinsa yake ita Kuma lailah qofar bedroom dinta na tun a palon farko sukuma su afia din sukeda manyan bedrooms dinsu guda biya ata cikin Palo na biyu dake qasa ita daya farhat daya Amma a dakin AFIA din take kwana da farhat sbd tazama tamkar itace uwar farhat din duk da akwai tarin Nanny's da masu aikin dake kula dasu duk su duka din sbd Sam tun tashinta kafinma haihuwar farhat mum dinsu tabarwa masu renonsu dawainiyarsu Sam batada lokacin kantama bare na 'yayanta shi koyaushe tana gurin aikinda zata Gina sunanta duniya tasan da ita shiyasa acikin kadaici afia ta taso harsai bayan uwan farhat duniya tasamu sauqi sbd duk da akwai masu kula da farhat itakam Bata barmusu ragamar farhat din dukaba musamman da watanta goma cif aduniya lailah ta yayeta daga Bata nono tun afia Bata iya dawainiyar farhat ba harta iya shiyasa farhat din duk duniya tafi shaquwa da afia da dad dinta duk da tanason mum dinta Amma tafison dad dinta da afia itama afian sbd sanin mum ba lokacinsu takedashiba yasa girman dole yahau kanta duk da qananun shekarunta tazama itace madam din gidan dole masu aikin gidan kaf umarninta kawai suke jira sbd ita suka gani Matar gidan ko lokacin jininta tayi baresu masu aikin shiyasa basa Sonta bakuma su tsanetaba tunda batai lokacinsu bama bare musgunawa ko wulaqantawa da tozartawa 'yayanta dai Kam suna tsananin sonsu da qaunarsu tareda tausayinsu duk sbd mahaifinsu UBAYD MALEEK Wanda suke tsananin jin dadin aiki a qarqashinsa duk da tsananin miskilancinsa da ikonsa mulki dake jininsa Amma baida tsanani ko tsauri ko kadan.

Table din lunch aka gama gyarawa yaja 'yayansa suka isa dining room din farhat Kam harta sakewarta ganin ga dad dinta ga afia to itakam batada damuwa tunda dama haka suke rayuwa mum batanan koyaushe.
AFIA ce dai Saida qyar ta iya tuttura abincin Shima yacine kawai saidai Babu Wanda ya isa yace ya karanto kokuma ya fahimci halinda zuciyarsa da tunaninsa suke ciki cikin nutsuwarsa kaman koyaushe yaci abincinsa.

Ranar baisake fita ba yini yayi da yaransa cikin tsananin kulawa da qauna har dare sukai dinner sukaje sukai sallah da wanka suka kwanta AFIA na rungume farhat cikin jikinta sabbin hawaye masu zafi suna gangaro Mata.
Washe gari ma tare sukai breakfast da dad dinsu su suka fara wuce school da driver dinsu kafin shi daga baya ya fice.


Ahankali kwanakin suka fara tafiya damuwa tashigi afia sosai sbd yanda ta Sanya rabuwar iyayenta cikin ranta har abin ya tabata yafara taba karatunta komai Bata ganewa a makaranta tun Ana Mata mgn har Saida school din suka nema dad dinta sukai Masa bayanin kwata kwata Bata gane komai na karatu ko exams dinta gabaki daya Babu Wanda taci hakan yasa ya ragewa kansa aiki sosai sbd samun lokacin zama da yaransa Dan afia idan akai wasa zata iya samun matsalar qwaqwalwama.
Kullum takan Kira mum dinta Amma Bata wani Bata lokacin mgn she's always busy with aiki aiki aiki hakan yafara Sanya afian jin haushi musamman da ita mum din Bata taba kiraba saidai ita takira ta bangare daya ga dad dinsu Yana iya kokarinsa duk kasancewarsa me tarin abubuwan Yi Amma duk ya taqaita sbd su 'yayansa sai hakan yasa tafara dawowa hankalinta taji inama dad zaisamu farin ciki Kamar kowane mijin aure.
Ahankali ahankali trauma din rabuwar iyayenta yasaketa sbd watanni da aka 'diba tuni ta sakewarta yanzu suna rayuwarsu cikin walwala musamman Mum Sarah dake kulawa dasu sosai yanzu kamar itace ta haifesu matarda tun haihuwar AFIA Amman UBAYD ta Aiko musu da ita daga delah gizah gashinan haryanxu tana taredasu tana musu aiki danma ta zama Kamar kakarsu Amma Mum Sarah suke ce da ita sbd tun afia na qarama da farko ma ta dauka itace ta haifeta saidatai wayo tasan lailah ce ta haifeta Amma duk da haka qaunar kamr uwa da 'yace tsakanin afia din da mum Sarah,
Yanzu gidan rayuwarsu suke Kamar dama haka suke Basu taba rashin waniba agidan hakan yasaka hankalin dad dinsu kwantawa ya maida hankali kan harkokinsa musamman idan Yana dubin shekarun sauka mulkin NEGES ABDUL-SAMAD MUH'D KALEEB wato sarki na yanzu qanin mahaifinsa Kuma mijin mahaifiyarsa Wanda sbd Yana yarone mahaifinsa yarasu shiyasa akabada mulkin wa qaninsa kafin shi dansa ubayd ya girma Wanda Sam shi yanzu ba wani mulki dayakeso ko yake gabansa shiyasa bai taba sha'awar zama kusada mulkin ba yayi nesa dasu sbd ma kada son abin yasamu damar shigarsa Amma gashi lokaci na son qaratowa.

Ana cikin hakan kaleeb yaga lokaci nata ja zaman maleek guda baiyi Masa ba Babu mace ataredashi ma'ana Babu gurin sauke buqatarsa Sam Sam ubayd shine jika mafi soyuwa a rayuwarsa Kuma Wanda yakeji cikin ransa fiyeda 'yayan daya Haifa Dan haka bazaiso wata mishkila ta bangarensaba ko kadan zai Masa shirin

Please Login or Register in order to submit comment