Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Yana tunanin Dole akwai dalilin neges na bawa Lailah damar zuwa gizah ta zauna itakuma gata idanuwanta sun rufe gabaki daya batada tunanin komai yanxu saita yanda zata farfado da kanta ta jikinsa take ya yanke shawaran zuwa gizah ya bude Baki cikin nutsuwar murya yace"

Kayi Mana Shirin komai gizah din zamuje wannan karon Ina buqatan tunatarda wasu waye maleek Incase idan sun samu mantuwa.

Yes maleek"Mr Omar yafada Yana kashe wayar maleek din take yakira ya sanarda tafiyar maleek aka garzaya karban tickets da komai.
Yaso barinta anan gidan yaje yadawo tukuna Amma Kuma bazai iyaba sbd duk tsoron dazai Bata hankalinsa zaifi kwanciya idan tana cikin mutane shiyasa ya maidata can gida zibrian gaba daya kafin suka wuce.

A gizah kuwa sosai yakoob yagano akwai abinda jekadi ke boyewa musamman Dama sunsan Dole itakadaice tasan inda padima take sbd itace wadda tashigo gizah din da ita Dan Haka ya kasa ya tsare cikin taku sosai harya gano inda take zuwa acan bayan sassan maleek duk da Bai Isa cikin sassanba ya isa kofar yasan akwai babban abinda maleek yasakata take boye gurin dangane da padima Dan Haka yakoma yafadawa neges komai
Cikin wani irin yanayi neges ya murmusa Yana jinjina Kai yace"

Ayi aike gurin tsohuwar matar maleek lailah cewa nabata damar zuwa muyi mgn.

Allah yaqara ma girma da lafiya."yakoob din yafada Yana yin baya baya ya juya ya fice.

Ta bangaren lailah kuwa yau ta samu damar Isa gurin hutawar neges Dan maganar aurenta da maleek data kawota har cikin palon akai Mata iso ta qaraso gabansa ta gaidashi cikin girmamawa kafin ta zauna cikin tata isar ta zamtowarta Matar asalin me mulkin
Take aka fara shigo da kayan marmari dasu Zuma da kayayyakin tabawa aka cike gurin tsab ta dago ta kalli kayan tareda dauke Kai sbd hakan tamkar cin fuskane ga maleek ace macen dake matsayin matarsa tana zaune gaban wani Wanda ba maleek ba har akawo Mata abinsha Dana ci Ana nufin taci gabansa wannan rashin darajar yayi yawa tana matsayin Matar maleek guda.

Numfashi ta sauke tareda waiwayowa ta kallesa Kai tsaye cikin tausasa harshe tace"

Allah ya taimaki neges me gizah ta yanxu ina maka barka da hutawa tareda barka da ganin wannan lokacin.

Kallonta yayi daka zaman hakimcen dayake ya Dan saki fuska wani murmushin dattijantaka na sauka kan fuskarsa yace"

Neges ya amsa Kuma Yana biki barka da fitowa medakin maleek na gizah.

Lailah tunda tashigo cikin zuriarsu take tsaye a wuyansa sbd mace ce me tsananin son mulki da Isa tareda kwadayin komai yazama Yana qarqashinta da ikonta Dan kuwa Jin take kamarma itace maleek din sbd sosai ikonta da gadararta ke bayyanarda mijintane me kujerar sosai take shigar Masa hanci Yana dannewa sbd taku da zamanta sirikarsa amma zai Bata darasi daidai da ajinta sbd ita takawo kanta gurinsa yanzu neman mafitar matsalarta da maleek.

Cikin nutsuwa da kulawa ya Dan juyo da Kai a kame yace"

Abu dayane akan matsalar aurenku da maleek shine karkata da hankalinsa yayi ta wani bangaren
Ma'ana wani Abu daya rinjayi tunaninsa akan iyalinsa.

Dagowa tayi cikin mamaki tace"

Akwai abinda ya rinjayesa kuwa bayan wannan auren da yayine...

Wani murmushin yakuma saki Yana cewa"

Mace bazata juyarda maleek ba ko wacece kuwa nafi sakaran wani Abu daban Wanda Banda sani akai Amma Dole saikin Saka ido kin bincika kin gano kafin asan inda gyaran zai faro.

Shiru tayi tana nazarin zancensa sbd Bai wani shigetaba zancen Dan kuwa duk me lafiya ya kalli al'amarin dakyau zai fahimci cewan Babu wani dalilin sauyawar maleek zallar halinsane rashin daukan reni ko kadan sai aure daya qara take hasaso wani abun daban Amma tunda yafadi hakan zata bincika tagani Dan a shirye take da maganin dukkanin abinda zai shata Mata layi da zamowa Matar maleek.

Batareda ya kalleta ba yasake Dora Mata tunanin bibiyar daddaqin abinda maleek ke tunani ta hanyar bibiyar jekadi sbd itace mafi amintar maleek a duk gizah da rayuwarsu bayan kaleeb da Mr Omar ko mahaifiyarsa Anneti batasan sirrinsaba sai wainnan mutanen uku.

Da wannan tunanin sosai lailah tasakawa jekadi ayar tambaya Dama tajima da sanin jekadi maqiyiyarta ce ba kauna atsakaninsu munafukartace kodan yanda tasamu cikakken bayanin jekadi itace tsaye akan komai na NURU a rayuwar maleek Dan Haka ta kanta zata fara saita rusa yardar dake tsakaninsu da maleek bayan tasan menene matsalar tukuna.

Bayan tabaro can sassan Anneti ta nufa akaiwa Anneti shelar isowarta tashigo cikin shigar alfarmarta kamar koyaushe ta zauna ta gaida Annetin Kamar dai yanda suka Saba cikin yanayi na Ni Matar neges nikuma Matar MALEEK Babu wata qarin Hira akai sbd Lailah har cikin ranta duk tsanarsu da qiyayyarsu takeji sbd sune munafukanta dasuka tsayawa NURU akan auren MALEEK Dan Haka Bata wani tsayaba ta wuce tabar Anneti da bin bayanta da kallon mamakinda baigama sakintaba saidai bazatani takan zancen lailah ba zata jira maleek yazo tana buqatan bayanin dawowan lailan.
##MAMUH#*_Mamuhgee 41_*


Are you guys looking for where to buy ur skincare product @ mg's skincare is the best plug for you🤗
Do you wish to have that flawless skin that's free of all skin prblm
Do you wnt to achieve that milky skin that turn heads wherever you go😉
Try mg's product nd I assure you you'll never use any other product except mg's product✅
Mg's will gv you the best out of all
With mg's product ur skin is 💯 clear,fresh,smooth nd ur skin will absolutely glow all day💃
We have herbal whitening black soap now nd beauty set available
Nd both the soap nd the beauty set is for all skin type everyone can use it🤗
Just gv it a try now nd see wonders✅
Chat:08062991549
Call:08064532391
Soap price:3k
set:11k

Follow us on
Instagram@glow_with_mgs
Facebook:mg's skincare

Nd guess wht🦻
Duk Wanda zesiya Kaya daga yau Alhamis 30-9-21 zuwa Nanda 5days that is ranar talata there will be 20% off discount a soap nd the set😍so what are you guys waiting for hurry nd grab urs💃 now is the time to glow🧖♀️
Pamper ur skin🦵
Shine like a bride 👰
be part of the glow team karkubari abaku lbr
Just chat 08062991549 to plc ur orders😘
Do not forget to follow us👆
Like nd comment pls dearies😘
Patronize us🙏
mg's always serve you the best✅❤️



*****************
Tun dasukai magana da neges tasakawa jekadi ido sosai akan motsinta takai har bibiyarta tafarayi Amma sbd jekadin ta iya takunta fiyeda tunani lailan Bata taba samun damar sanin komai dangane da wani baqin yanayi ko sirri atareda jekadin ba harta fara sarewa daga bin daddaqin na jekadi sbd Sam ba dabiarta bace Dan ita ta dauki kanta tanada abinyi hakama ba girmanta bane tsayawa irin wainnan labe laben ga abun duniya yafara sakota gaba sbd yanzu rayuwarta ta wayi gari kowa baya tareda ita tun daga kan mijinta har yayanta su danginta ba'a magana sbd ta Jima da watsar dasu dama mahaifiyarta ta Dade da rasuwa mahaifintane kawai shima tsufa yacisa sosai har baya gane kowa sai anfada Masa wannan waye shiyasa batada lokacin kowa saina Gina rayuwarta sbd gidansu kaf kowa yazamo wani hamshaqan kansu duk da ita kadaice mace sai tana alaqanta kanta da matsayinsu suda suke maza bazata taba yadda itama ta zauna tana amfani da alfarmar wani ko sunansa so take ta Gina kanta da kanta ta yanda za'a fadeta da matsayin datake dashi badai da matsayin wani datake a qarqashinsaba shiyasa ta rufe ido ta watsar da 'yayanta da komai Amma yau ta wayi gari ko 'yan aiki batadasu sai guda biyu kacal da ganinsuma baqin ciki yake sanyata sbd Kamar Saida aka zabo wainda suka fi Muni da rashin kakkamtuwa aka Aiko matasu batada 'da, batada miji, batada gidan kanta bare matsayin kanta ko sunan Wanda zatace a qarqashin alfarmarsa take batada Dan Haka gabaki daya yanzu Jin take kamar ta rasa nustuwa da tunaninta Bata iya tunanin komai kanta ya toshe zuciyarta bayan kwashe kwashen tunane tunanen duniya dasuka kusa haukatata Babu abinda takeyi tarasa wazata zauna dashi ko masifa tayi ta rage abinda takeji bare.
Tunanin 'yarta afia ne yafado Mata Rai take taji idanuwanta na neman cikowa da hawaye ta hadiye tana miqewa zuwa bakin window ko zataji sanyi sanyi Amma takasa Saida hawayen suka tsinke Mata ta zauna bakin windon tana fashewa da wani irin kuka Mara sauti tana buqatan mutum atareda ita Wanda zai dubeta ya saurari damuwarta.
Afia take tsananin buqata ayau din sbd ta Dan duk duniya yanzu 'yartace kawai me iya rarrashinta ta rungumeta ta saurari duk haukar dazata iya fada da wadda zata iyayima kaf duniya yanzu 'yartace kawai me iya Mata wannan bayan ita ko maleek tasan bazai taba kallonta da idon sauki Kona mutunciba
Dan Haka hankalinta yaqara tashi tana jinta cikin mummunan yanayi na baqin cikin rayuwarta da Kamar tayi hasara.

Ta Jima Yana boyayyan kukan daya Gama kumbura idanuwanta da fuskar datake masifar ji da ita sunyi jajir sunyi suntum duk da hakan bataji wani sauki ko sassaucin komaiba ta miqe ta nufi toilet jiki amace ba kwari ta wanko fuskarta tareda yowar alwala Dan ko wankan batada karfin Yi tafito ta goge fuskarta ta tayarda sallar ishai da akai tun dazu bayan tagama akaro na farko bayan tsawon lokaci yau ta daga hannu tana rokon Allah sassauci da mafita sbd ada ganin tagama samun komai na rayuwa yasa sallah data zama Dole kawai takeyi Amma adhkar da sauran adduoi gurin ubangiji basa gabanta sbd duk abinda takeso tagama samu.

Agurin take zaune tana tsiyayar hawaye ta gefen fuskarta batareda ta iya tashiba takai hannu ahankali ta dauki wayarta ta Nemo sunan afia akaro na farko bayan tsawon lokaci taji qaunar 'yayanta na dawo Mata sbd haryanzu tasan kome zata zama arayuwa 'yayantane kawai bazasu taba iya guduntaba musamman afia datake kaunarta fiyeda komai saidai takasa duba kaunar da yarinyar ke Mata sai yanzu take ganewa Dan kuwa a yanda takeji yanzu ko 'yayanta abata ta zauna dasu zataji saukin duhu da kuncin da zuciyarta ke ciki.
Numbern afia takira tayita ringing No answer harso biyar take jikinta yasakeyin sanyi hannuwanta sukai sanyi ta juyar da kanta ahankali tana kallon qasa kafin ta daga wayar ahankali ta shiga gurin saqo ta rubuta mata" _Kiyi hakuri afia_
Tura Mata tayi tareda ajiye wayar tana rufe idanuwanta zuciyarta na wani irin nauyi da kunci.


Jekadi jin tsarin na barin padima tareda tattalata tasamu lafiya amaida gida yasata sauya nata tsarin itama nabin umarninsa tafara bawa padima magani tareda kulawa da goge Mata fatarta data Gama konewa tana shafa Mata magani akai akai Wanda take padiman tafara dawowa hayyacinta Dan hartana Dan iya bude Baki Kuma tana iya zaunawa sai hakan yasaka jekadi sake bada himma sosai cikin kwana biyu padima tafara dawowa mutum sosai a ranar da padiman tafara iya bude Baki sbd tsananin farin ciki jekadi ta fita ta kebe tasake Kiran Mr Omar ta sanar dashi komai alokacin suna hanyar tahowa gizah suna cikin jirgi Amma Basu riga sun tashiba Dan Haka baida damar ganin maleek sbd Yana first class Dan haka yabari harsu Isa tukuna.

Dayake da daddare ne sosai jekadi ta fito tayi wayar adaidai lokacin lailah Tana zaune taji motsi me girma ta window din dakinta Kuma Kamar harma da mutum tagan gilmawarsa saita tashi zaune dakyau tana kallon windon zuciyarta na Dan harbawa Amma takasa riqewa ta miqe tsaye ta nufi windon tana Dan daga manyan dogayen labulayen windon saitaga kaman sake gilmawar mutum Kuma idan idonta ya gani kamar da kyau jekadi tagani.

Kallon hanyar tayi tana dawowa cikin dakinta zuciyarta na gargadarta da bin jekadin saidai Kuma wata zuciyar tana ingizata ga zuwan ta rintse ido tana komawa ta zauna saidai Kuma takasa nutsuwa tanason bin jekadin
Ta miqe da sauri tareda daukan wayarta ta fito sanyeda slippers tabi hanyar baya ta fice daga sassanta tabi inda jekadin tabi tana tafe tana waige waige har tayi Dan nisa saitakasa gane inda jekadin tabi tafara waigawa koina tana dubawa saikuma tsoro yashigeta ta juya da sauri zata juya saiga jekadi ta fito ta wata hanya tabi hanyar Nayan sassan maleek tana tafiya cikin nutsuwa sbd kada tabar qarar sawu.

Da fargaba da mamaki me tsanani take kallon jekadin tareda rintse idanu tabude mamakinta na neman komawa tsoro sbd kayan dake jikin jekadin bashine kayan data ganiba ajikin jekadin data wurga ta windontaba Kuma tabbas Bata Isa ace yanzu yanxu ta sauya kayanba.
Kodai idanuwanta ne ke Mata gizo kokuma wanine ya wurga ta windon ba jekadiba?
To idan wanine waye?
Meyasa yayi irin shigar jekadin?

Girgiza Kai tayi da sauri cikin tsananin tsoro dason tabbatarwa tabi bayan jekadin cikin sanda tana Nemo camerar wayarta tareda kashe hasken flashlight sbd idan ba tabbarwa tayi da wacece jekadin acikinsu hauka zata iya kamata Dan haka a sidade sidade tabi bayan jekadin tana waiwaye cikin tsananin tashin hankali sbd Jin kamar Kuma Ana binta itama san'da san'da abayanta.

Wata boyayyar kofar dataga jekadi ta fita yasata zare idanuwa cikin mamaki da tabbatarda zancen neges kenan dai da akwai wani Abu da maleek ke boyewa¿Aikuwa yau saitaga ko menene to Amma Kuma ta Yaya tunda jekadi rufe gurin zatayi..

Tunani tafara ta yanda zata samu Isa cikin dakin Kota halin qaqa taga abinda kila zai dawo da aurenta da maleek Dan Haka bazata Bari wannan damar ta wucetaba.

Waige waige tahau Yi cikin sauri Idonta ya fada kan wani qaton katako Wanda batama tsaya mamakin ganinsa a guri irin wannan ba ta dauka da sauri ta lallaba taqarasa bayan jekadi dake kokarin rufe kofar da mukullin ta waje bata tsaya wata wataba ta daga katakon ta buga Mata akai bada karfi ba sbd Jin bazata iya da qarfinba sbd kadata illatata sai kawai ta tureta gefe ta Fadi ta qarasa dakin da gudu ta tura kofar ta fada ciki tana dubawa.

Faduwar da jekadi tayi ganin lailan ta nufi cikin da gudu yasata miqewa da sauri tana Kiran sunanta saidai kafin tayi wani yunkuri wani mummunan duka ya sauka akanta me tsananin azaba take ta sulale agurin ta zube a some jini na fita ta goshinta batareda taga Wanda yayi Mata dukan ba.

Lailah kuwa ganin mace a kwance cikin dakin cikin wani yanayi na Kamar majinyaci yasata takowa ahankali zuciyarta na harbawa cikin tsananin mamaki da tsoro ta iso har gabanta zata Kai hannu ta tabata padiman ta bude idanuwa ahankali baccin daya fara daukanta na sakinta ta zubawa lailah idanuwanta ahankali tana kallonta da mamaki Jin motsi abakin kofar shigowan yasa padima kallon bayan lailah mamakin ganinsa nasata kaikata Kai tana kallonsa dakyau ahankali ta bude Baki tace"

AMED????

Da sauri lailah ta juya zata waiwaya wani mugun duka ya sauka a tsakiyar kanta batareda ta waiwayo ba ta yanke jiki ta Fadi agurin sama sama tanajin padiman nasake maimaita amed har idanuwanta suka rufe numfashinta na daukewa.


******
Ruwan sanyin dake sauka kan fuskarta zuwa jikinta masu tsananin sanyi ya sanyata fara numfasawa tana motsa idanuwanta dasukai tsananin nauyi tafara budesu ahankali ahankali tana rufewa tana budewa sbd hasken dayayi Mata yawa harta budesu duka suka sauka kan mutanen dake zagaye da ita tafara Binsu da ido daya bayan daya kafin ta tsayar dasu akan fuskar maleek da yayi Mata kallo daya ya dauke Kai
Ta juyar da kanta gefe taga manyan jami'an tsaro tsatsaye agurin take ta zabura da sauri tana miqewa zaune tana sake kallon mutanen dake gurin ga qarin mamaki da firgicin ganin safiyace tas idanuwanta suka sauka kan mutum kwance miqe sambal anrufesa da farin kyalle har fuska Wanda ke nuni da gawar mutum ce,ta hadiye wani mugun yawu daga bakinta daya bushe kyam Nan take tana miqewa tsaye kanta na sarawa ta dafe kan tana Jin wani tashin hankali na shigarta sbd jekadi tasan tabari agurin jiyan da daddare bayan ta tureta, wani sabon tashin hankali da faduwar gaba me qarfi tashiga kardai wani Abu yasamu jekadi Dan dukan da turewar datai mata???
waiwaye waiwaye tafara tana neman rikicewa jikinta take yafara rawar tashin hankalinda Bata saka Masa ranaba ta nufi maleek da sauri tanajin ma ta wartsake daga ciwon da kanta keyi me tsanani ko gabanta Bata gani saidata Isa gaban maleek zatayi mgna idanuwanta suka sauka gefensa daya da jekadi ke tsaye sunkuye da Kai goshinta duk jini daga gani itama tana cikin tsananin tashin hankali
A haukace lailah ta waiwaya ta kalli gawar dake rufe agurin taji qafafunta na sagewa tayi baya zata Fadi macen dake sanye cikin uniform na hukumar qasar ta tareta tana riqeta dakyau da alamar dama ita ake jira.
Ta fizgo da qarfi tana kallon maleek bakinta na rawa cikin tsananin tashin hankali tace"

Wanene???
Me yake faruwa anan?

Kallo daya yayi Mata ya juya yana sauke siririn numfashi sbd gabaki daya al'amarin ya sauya acikin qanqanin lokacinda basuyi zatoba.

Kallon gawar padima yayi akaro na hudu Yana tunanin yanda 'yar uwarta zata iya handling wannan mummunan al'amarin Sam an shammacesa a guri mafi mufi Dan kuwa yanzu acikin jekadi da lailah baisan wazai fara wankewaba duk da dukkanin shedu lailah suka nuna ita tayi kisan sbd baro baro jakadi ta fada cewar lailah ce tazo ta bugeta ta Suma itama lailan ta nuna hakan ta Yaya za'a fitarda lailah daga wannan ta bangare daya ta Yaya NURU zataji wannan mummunan labarin?
##MAMUH#
*_Mamuhgee 42_*


*Assalamualaikum warahamatullah taala wabarakatuhu*
08121491609
*Aisha s bayero traditional medicine and herbal reaserch center*
08121491609

08121491609
1_maganin sanyi
2_maganin niima set
3_maganin nankarwa
4_maganin kiba babba 8kkkarami
5_maganin hips
6_maganin gyaran nono
7_maganin rage kiba
8_maganin saka feeling
9_maganin cida kwai
10_zuma yar asali
11_maganin basir kowanne iri
12_hodar niiama
13_maganin mallaka
14_gumbar nonon rakumi 10k boket😨
15_gumbar madara 10k boket😨
16_turaren farin jini
17_kaza Mara kwai
18-turaren mallaka 3step
19_hadin matar minister
20_ kaza me kwai



Step 2
1.Turaren mallaka me kwalba
2. Me kunama Dan matsi 3k
3.tuaren goshi
4.turaren girji
5.tauwadar Mata
6.memory
7.kahon mallaka 8.yajin maza tea din maza
9. Dambun matsi
10. Man ayu 11.man damo pure daga zuwa sama
12. Kwallin idonka idona
13 garin Sha daka me kyau
14. Kubewar Mata gasunan dai da yawa bazan iya lisaafawaba harda na kyakkayin cinyoyin da matse matsi kina shafawa zakiji wasai

08121491609
dadai sauransu serious buyer yabiyoni private
me shawara ta bari saita gama karki batamun lokaci plx
**08121491609




******************
Kasa hakuri lailah tayi cikin sabuwar qaramar haukar dake Shirin kamata agurin take tafara kwacewa tana kallon maleek da sauran mutanen dake gurin cikin tsananin ihun dukkanin jikinta na rawa take cewa"

Meyasa zaku tafi Dani?
Bani nakashetaba wlh,
Dan Allah ki tsaya nayi muku bayanin abinda yafaru wlh tallahi bani bace
Dan girman Allah maleek kace su barni kasan bazan taba iya aikata wannan mummunan abin ba
Ba halina bane,
Dan Allah ki sakeni wallahi bani bace ku tambayi jekadi Dan Allah maleek karka Bari su tafi Dani....


Tana ihun tashin hankali dukkanin jikinta Babu inda baya wani irin mazarin tashin hankali da ficewa hayyaci musamman data tabbatarda tabbas kisa akai Kuma itace ake nufin tayi kisar kenan kasheta za'ayi itama tabar duniya da 'yayanta
Tunanin hakan ke saka haukatarda kwanyarta tafara fizgewa tana kokarin zuwa gurin maleek dake tsaye batareda ya dago ya kalletaba sbd kunyar hakan da baqin cikin hakan dake cinsa koba komai ita din uwar 'yayansace matarsa ta farko wadda koman lalacewarta za'a kirata da matarsa ta farko har qarshen rayuwarsu.

Dayake har bakin kofar sassansa qatuwar baqar motar jami'an tsaron take suna Isa aka sanyata aka rufe tana wani irin kuka da neman ceto daga maleek tana rantsuwar ba ita din bace har muryarta tafara dishewa musamman daya zamto kallon karshene takewa koina Dan tasan hukun kisarta bazai dauki delay ba tunda komai a bayyane yake tasake sakin wani mahaukacin kuka tana buga kanta da tint windon motar da qarfi tana kuka tana Kiran sunan maleek cikin dukkanin bada imaninta ga shikadaine zai iya cetonta
Haka aka janyo jekadi itama aka saka cikin motar aka rufe Kafin
Ja motar suka wuce sai alokacin maleek ya dago ya kalli Mr Omar dake tsaye a gefe tsaye kansa sunkuye cikin yanayi na tsananin jimami idanuwansa suka kada sukai jajir ya dago Yana kallo 'yan motar asibitin dasuka Kira suka matso Dan daukar gawar su wuce da ita saiga shelar sanrwar tahowar NEGES da kansa zuwa sassan Dan tuni abinda yafaru ya karade gizah saidai Babu Wanda yasamu iko ko damar shigowa sassan hakama Babu Wanda yasamu masaniyar shin wanene aka kashen daga jami'an tsaron da Mr Omar yakira sai motar asibitin da jami'an tsaron sukazo dasu Dan daukan gawar sai Anneti data iso sassan cikin tsananin tashin hankali tana zubda hawayen ganin wannan mummunar qaddararriyar ranar ace kisa acikin gizah Kuma daga sassan maleek qari da Dadi tsohuwar matarsa da jekadinsace cikinsu daya ya aikata wannan mummunan Abu me duniya zatayiwa MALEEK kallo?
Gashi Anki bude gawar bare asan wanene aka kashen.

Neges na zuwa cikin tsananin jimami da tashin hankalin wannan mummunan al'amarin ya kalli MALEEK Yana bayyanarda damuwarsa da rashin Jin dadinsa akan al'amarin yace"

Ina me jajanta maka wannan al'amari
Saidai nayi maka alqawarin hukunta duk Wanda aka tabbatarda shine yayi kisan a tsakaninsu biyun Dan kuwa wannan al'amari babbane dazai iya tana darajarmu gabaki daya da ikonmu Dan Haka komai zai tafi abisaga adalci da doka wannan alqawarinane.

Sai alokacin maleek ya dago ya kallesa da idanuwansa dake bayyanarda zallar bacin Rai da wani irin zafi na iko da mulki dake yawo jininsa ahankali ya bude Baki cikin kamewa yace"

Godiya maleek yake Kuma Ina fatar zaka tuna wannan alqawarin naka Dan cikakkene jinin delas basa alwawarinda basa cikawa Ni nayi maka alqawarin tayaka cika wannan alqawarin za'a tafiyar da komai bisaga adalci da doka.

Jinjina Kai neges yayi Yana danne abinda yakeji gameda maleek din ya sassauta kallonsa zuwaga gawar da aka dauka za'a shigar ambulance ya waiwaya ya kalli yakoob Yana cewa"

A tabbatarda gawar kafin su tafi da ita.

Matsowa Mr Omar yayi Ya tarewa yakoob hanzari Yana sauke Kai cikin tsananin girmamawa ga neges Yana sassauta harshe da cewa"

Allah yaqarawa neges girma
Ina neman afuwar rashin barin abude gawa irin wannan agabanka sbd darajarka fifitacciyace dabazai yiyu irin wannan abudeta a gabanka sbd dukkanin suturarta a yage take Wanda ya nuna alamar Tasha dama da makashinta kafin samun nasararsa
Ni zanyi shedar tabbarda gawar aduk lokacinda buqatan hakan ta taso agurin Sharia.

Cikin jinjinawa yace"
Shikenan hakan yayi Allah ya kyauta Amma duk da hakan Ana buqatan tabbarwan.

Matsawa mr Omar yayi tareda bawa yakoob hanya ya wuce Dan ya tabbatar din saidai Yana Kai hannun zai bude jami'an tsaron dasuke jiran ambulance su tafi tare suka dakatar dashi cikin yanayi na dokar aikinsu da girmamawa ga neges shugaban yace"

Allah yaqarawa neges girma Babu Wanda zai sake taba gawar Nan ayanxu sbd Babu abinda mukai bincike akansa zamuje da gawar lab muduba komai ayi aune aune daga lokacin ne bayan angama komai zamu bayar da gawar ayi Mata janaixa daganan ne kowa zai iya tabawa Amma yanxu muna bawa neges matuqar hkr
Saidai idan hankalinka yafi kwanciya da kwakwariyar shedane zamu iya cewa tunda maleek yagani hakan zai gamsar da Kai.

Numfashi boyayye neges yasake Yana jinjina Kai tareda kallon maleek cikin yanayi na kulawa da damuwa yace"

Duk yanda za'a ayi kada abari media suji wannan mumman labarin ayi komai a sirrance tunda hukumarma a sirrance suka shigo suka fice.

Motar asibitin tafara wucewa daukeda gawar kafin akabar jamian tsaro uku da sauran securities din maleek a bakin sassan na maleek sbd shima Yana cikin wainda hukumar zata tsare sbd komai a qarqashin bangarensa yafaru Dan Haka an saka tsaro a sassansa babu inda zashi zai zauna aciki bame Shiga sai mr Omar kawai aka bawa dama shima abincin kawai zai ringa shiga dashi yafito sai zuwa headquarter aduk lokacinda aka buqaci ganinsa harsai antabbatarda cikin su biyun lailah ce ko jekadin ce tayi kisan.

Da hakan zancen yasake qamari hankalin jama'ar gizah yayi mumman tashi musamman Anneti tana tsananin buqatan ganinsa saidai ba dama Haka Takoma sashenta cikin tsananin tashin hankali da damuwa tana daga hankalinta da rokon Allah sassaucin wannan mummunan masifar har lailah take roqawa sassauci sbd ita uwace tasan wannan Abu wani babban al'amarine daga ubangiji kowa na neman doki daga garesa Dan Haka kowa zata rokar Masa.

Ta bangaren Mr Omar Yana fitowa gizah tareda maleek cikin sirrantacciyar mota sai motar jamian tsaro da securities dinsa fitowarsu gizah kenan ga tarin dibbin mamakinsu 'yan media ne birjik suka yo kansu tareda zagaye motocinsu suna jeho tambayoyin dasuka kusan hargitsa tunaninsu su dukan Dan kuwa bayani ne akan cewa"
Shin me maleek zai iya cewa akan tsohuwar matarsa da jekadinsa dasuka taru suka

Please Login or Register in order to submit comment