Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

shige bargo take bacci yayi gaba da ita me Dadi ko abinci Bata tsaya nemaba.

Saida yagama komai shima ciki hadda waya da Mr Omar kafin ya hawo gadon ya kwanta tana shigewa jikinsa
Shima baccin yayi me nutsuwa.

Sai qarfe bakwai na washe gari suka tashi har sunyi lattin sallah
Sukai sallar sai alokacin yunwa ta taso Mata
Yayi Mata odar abinci lafiyayye baa dauki mintuna da yawaba aka kawo ta tashi taje kan table tafara ci yazo ya zauna kusada ita suna ci tare duk da Bai saka hannuba da hannunta sukeci.

Bayan sungama wanka sukai suka sake komawa bacci sai Rana sosai suka tashi sukai sallah suka Kara cin abinci
Gabaki daya ranar dai a kwance suka yini sallah da cin abinci kawai ke tadasu ko washe gari ma Haka Saida sukai kwana biyu kafin suka fara fita da qafa yawon Shan iska cikin qananun Kaya Wanda ta mutu da mamakin duniyanci da iya zallar soyayyar da maleek din ya iya musamman dayake yazaba Nan dinne sbd Ana rayuwane anan ta couples sbd yawanci Yan honeymoon ne.

Kwanaki sukai suna fita wani irin shaquwa da sabuwar soyayya me qarfin gaske tasake shiga tsakaninsu musamman da yariga yagama busar Mata da idanu akan soyayyarsa ko Ina Babu ruwansu kissing juna sukeyi musamman shi ko magana take Masa wani lokacin Haka zaibi bakin Yana kissing sbd komai nata kashesa yakeyi.

Yau ba awani gajiye suka dawoba Dan Haka suna dawowa yaqarasa gajiyar dasu akan gadansu aikuwa taqarasa gajiyar gaske kafin sukai wanka suka kwanta bacci.

Wata irin sabuwar rayuwa suke a qasar ta zararrin masoyan da basa ganin kowa sai junansu
Dan kuwa yanzu ko irin kayan datake saka Masa cikin daki sun gama makantar da idanuwansa da ganin kowa bayan ita musamman da yanzu ya koya Mata batada gurin zama sai kan cinyoyinsa da jikinsa.

Tana waya dasu afia sosai saidai har lokacin takasa fada mata inda take tadai sanar da ita Bata tafi delah ba tana gida sbd cewa abata su abal su gaisa afian datai.

Su abal ma dadin duniya da farin ciki ya ishesu duk lokacinda sukai waya da 'yarsu
Itakuma padima kullum akai waya da NURU sai kaman ciwon ya tashi sbd ta ringa Kiran sunan NURU kenan yinin tana cewa ta yafe Mata.

Satinsu uku cif suka dawo gida har lokacin su afia Basu dawoba sbd afia data gane mahaifiyarta tana samun 'yar matsalar juyewar Kai wani lokaci shiyasa takira dad din tasake rokon yaqara Mata sati daya yakuma qara musu din.

Koda suka dawo kallo daya mum Sarah tayiwa NURUn ta dauke Kai tana yaba zallar kyau da cikar data Karo shi kansa oga kwata kwatan Mr Omar dinga satar kallonsa yayi Yana Masa barka barka akai akai har Saida maleek din ya kallesa yace"

Yaushe ka zama me saka ido Mr Omar?

Murmushi yayi Yana shafa Kai yace"

Allah dai yaqara maleek lafiya da kwanciyar hankali.

Dan guntun murmushi shima yasaki Yana share Mr Omar din sbd dama yasanshi da 'yar Karan saka Masa ido musamman daga baya bayan Nan.

Kwanansu biyu da dawowa yayi tafiya tareda Mr Omar bayan yagama aikin bada Baki sbd kedaicin dazata shiga basu afia babushi
A ranar kafin ya wuce yakira afia yace su biyo jirgin washe gari su dawo gida
Afia tace to.

Washe gari da yamma saigasu sun dawo cikin tsananin farin ciki da murna tarbesu ta rungume farhat kafin ta rungume afia din tana cewa"

Oh my God I missed you guys so much
Musamman wannan beautiful sabuwan likitan tamu" taqarasa fada tana kallon farhat data tsuke fuska zatai mgn ta tareda da Bata kiss a goshi tana cewa"

My sweetie kinsan kece farko a zuciyana basai kince komaiba kinji.

Har dakin afia din suke duk su dukansu suka zauna afia na sauke ajiyar zuciya tana lumshe ido tace"

Alhmdlh Ya Allah
Gida me Dadi.

Murmushi NURU tayi tana tayata janye akwatin ta gefe tace"

Keda Zakiyi aure wata Ran kitafi
Amma nidai har banason tuna ranar
I don't wnt you to leave us" taqarasa fada tana kallon afian cikin kwabe fuska.

Dariya Afia tayi tana miqewa ta dauko wayarta cikin Jakarta tadawo kusada NURUn ta zauna tana cewa"

Hmmm ki shirya to babe sbd nakusa tafiya idan kina maganar aure ne sbd....
Wani tsananin farin ciki NURU tace"

Yaushe kika fara soyayya Banda labari¿
Wane me sa'ar ne wannan?

Dan wani blushing afia tayi tana kallon NURUn kafin ta miqe ta nufi toilet tana cewa"
Zanfada Miki komai kinsani Amma saina hutu yau da daddare akwai fira.

Murmushi kawai tayi tana cewa"

To ahuta lafiya Bari naje na saka hannu a abincin yau abincin dakukafi so za'ayi.
##MAMUH#
*_Mamuhgee 51_*
Sai dare suka samu kansu a dakin afia din ma suka kwana bayan sun kwanta
Afia ta fuskanci NURUn ta sauke ajiyar zuciya da numfashi ahankali tafara cewa"

NURU mum Dina tasamu matsalar juyewar Rabin Kai dayake Dan tashi wasu lokutan idan tana tuno abinda daya faru na wannan al'amarin.
'dan shiru tayi tana sake juya al'amarin cikin ranta ta bude Baki tacigaba da cewa"

NURU mum ta rokeni alfarmar na amince na auri Imran sbd nuna sha'awarsa da yayi ga aure Dan samun cikakkiyar nutsuwar Bata kulawa shine ta nuna sha'awarta nason auren Hadi a tsakaninmu idan har dad Dina ya amince,
Na zauna nayi nazarin maganarta NURU Nima inason kasancewa tareda ita Dan samun lafiyarta Dan Haka na amince da maganar auren saidai bansaniba ko hakan danayi nayi daidai kokuwa?....

Ajiyar zuciya ahankali NURU tasaki tana kallon afian cikin tsananin tausayinta da qaunarta sbd a rayuwa tasamu gata da dukiya da kyakkyawan asali da ilimi da komaima na rayuwa Allah yabata Amma ta bangaren mahaifiyarta ta hadu da jarabawa me qarfi wadda gashi dai daga karshe tayi sacrificing rayuwarta kacokan akan auren Hadi sbd neman lafiya da kawo sauyi a rayuwar uwarta Wanda hakan yaqarawa NURUn ganin girman afian fiyeda koyaushe sbd tabbas tsakaninta da Allah takeso da kaunar mahaifiyarta komai halayenta kuwa.

Cikowa idanuwansu duk su biyun sukai da hawaye NURU tace"

Ina Miki fatan kyakkyawar nasara arayuwa fiyeda kowa afia,
Allah ya dasa Jin Dadi da kwanciyar hankali tareda soyayya me girma acikin wannan auren Kuma Inshallah dad dinku ma bazaiqi hakan ba sbd burinsa dama akanki karatunki ne Kuma kin kammala Dan Haka burinsa na gaba akanki bazai wuce aurenki ba.

Ahankali ta furta"

Thank you NURU.

Murmushi tasaki tana dafa hannunta ta girgiza Mata Kai.

Washe gari a washe suka tashi kowa da nasa farin cikin sbd takardunsu dasuka fito Kai tsaye tare data aikinsu
Murna da farin ciki a ranar ma Saida sukai partynsu cikin Palo wannan karon afia harda rawa Tasha
Farhat da itama farin cikin ganinsu cikin farin ciki duk ya lullubeta itama tasha rawarta duk da Bata iyaba
Saiga Imran yakira afia din vcall ta zauna sunayi tana gyara gashinta data sauyawa kala daga baqi zuwa dark brown suka fara fira sama sama wadda yawanci idone yake kafe dasu sbd wasu halayenta da kyakkyawar kamilalliyar fuskarta dasuka fara saka Masa Sonta.
Mum dinta yafita yakaiwa wayar suka hau murna mum dinta na cewa"

My baby I love Allah ya albarkaci rayuwarku duka.

Amin ta amsa tareda janyo NURU dake can gefe tana waya da Alama duk wanda take wayar dashi yanada mahimmanci a rayuwarta ta kara Mata wayar tana cewa"

Mum ki gaisa da NURU ki tayata murna itama.

Kallon kallo sukayiwa junansu tareda yin tsit na wasu sakanni kafin NURU ta Dan ago tana kakalo murmushi cikin nutsuwa tace"

Ina wuni?
Ya gida?

Ajiyar zuciya tareda numfashi lailah tasaki kafin ta kalli NURUn cikin nutsuwa tace"

Congrats to you.

Thank you.

Sake kallonta lailah tayi tace"

Kiyi hkr da duk abinda yafaru abaya Ina fatan Zaki yafemun komai ya wuce?

Murmushi NURU tasaki tana girgiza Kai a natse tace"

Yariga yawuce na Dade da yafe Miki sbd girma da darajarda afia take dashi a zuciyata.

Nagode sosai" lailan tafada tana sake murmushin daya qarawa kyakkyawar fuskarta kyau ta Dora da cewa"

Ina gaida farhat.

Jawo farhat NURUn tayi tana cewa"

Sweetie zo ga mum dinki ki gaisheta.

Zama farhat tayi tana karban wayan fuskarta daukeda farin ciki sbd yanzu tafara sakewa da mum din tasu sbd ta sauya sosai yanzu har cikin ranta takeson yayan nata ita Kuma farhat dama tsorone yasata take shakkar kusantar lailan.

Har Imran suka gaisa dashi kafin NURU ta miqe Takoma ga tata wayar datakeyi da Bata oga kwata kwatan Wanda duk wayar datayi da lailah da gaisawa datai da Imran duk yanaji Kuma shima hakan yasashi farin ciki ganin atlast dai afia tasamu soyayyar mahaifiyarta dataketa kwadayi tun tasowarta.

Da daddare sbd gajiya tunda suka kwanta Basu farka ba sai qarfe takwas na safe suka miqe cikin sauri sukai sallah kowa yafara Shirin fita aiki musamman afia datafi NURU buqatan fita da wuri sbd yanayin aikin nasu ba daya ba.

Cikin ikon Allah kowaccensu tafara aikinta cikin aminci da kwanciyar hankali har sun Dan fara sabawa cikin kwanaki kadan.

Yau NURU ce tajasu suka fita tare suka biya ta ajiye afia asibiti kafin ta wuce gurin aikinta tana sake trying numbern MALEEK dabata shiga tun safe rabonta dashi tun jiya cikin Daren dasukai vcall.

Tunanin rashin samunsa yasakar Mata ciwon Kai da damuwa qarshe Bata Bari yamma tayi sosaiba ta tattara ta baro office din harta Kama hanyar zuwa gida ta fasa ta nufi asibiti gurin afia sbd tayita kiranta tafada Mata zata wuce gida idan tagama takira zata Aiko Edward yazo ya dauketa Amma afian Kuma Bata dauki wayarba shiyasa Mata biyawa asibitin Dole tana sakin Dan qaramin tsaki sbd kanta dake tsananin sarawa
Tana yin parking cikin asibitin saidata dakata cikin motar ta sauke ajiyar zuciya da numfashi sbd yanzu Kam kaman hadda jiri tana gani Haka ta daure ta fito sanyeda shades sbd Rana ta nufi ciki.

Direct hanyar office din dazata samu afia wato office din Dr Damien ta nufa saidai kafin ta qarasa tana daf da Isa ta dakata sbd wani jiri daya dibeta tayi gefe zata Fadi afia data hangota zuwa ta taso tana kawowa ta tareta cikeda mamaki da 'yar damuwa tana kallonta tace"

Lafiyanki kuwa???

Gyara tsayuwa NURUn ke kokarin Yi tana Dan dafe goshinta ahankali tace"

Bansaniba kawai ciwon Kaine yake damuna yanzu Kuma Kamar karna baro office jiri yafara kamani Ina ganin stress ne da rashin bacci.

Kallonta afia keyi da kyau kafin ta gangaro da idanuwanta zuwa kirjin NURUn ta kalla tasake maida idanuwanta kan fatar hannuwan NURUn saitaga kaman Bata gani sosai ta kalli NURUn tana cewa"

Bana tunanin stress ne kadai muje nadubaki mugani sbd jiri matsala ne zai iya jefar dakai inda zaka halaka kanka.

Suna Shiga office din Dr Damien ta zaunar da NURUn tana juyawa ta dauko ruwa takawo Mata ta Bata Tasha ta durqusa gabanta tana cewa"

Muji pulse dinki.

Bata hannunta tayi ta riqe tana Jin pulse din NURUn tayi shiru zuciyarta na bugawa
Duk Bata yarda ba ta juya da ita kan gadon scanning din dake office din Dr Damien din NURU ta kwanta tana gyara Mata kafafunta.
Tana Dora Mata abin scanning din take cikin jikin NURUn ya bayyana baro baro ta ajiye abin tana kallon NURU da cikakken mamaki da tsoro harma da shakku da firgici duka
Bakinta na rawa Kai tsaye ta fuxgo kalmar cikin tsananin mamaki tace"

NURU you are 7weeks pregnant.

Da sauri NURU ta kalleta tana saukowa daga gadon tana goge jikinta da tissue ta Dora hannunta kan cikinta cikin son tabbatarwa tace"

Pregnant???
Ni¿

Wani irin Murmushin farin cikin da Bata taba tsammanin yiba ta sake dafe cikin tana dagowa ta kalli afia datai mutuwar tsaye tana kallonta cikin mugun mamakin da batasan lokacinda bakinta ya furta"

Dad ne???

Sai alokacin kunyar afia din takama NURU ta Dan takaita farin cikinta tana kallonta ta daga Mata Kai ahankali tana cewa"

Yes wannan qaninki ne afia.

Wani yawun sabon mamaki afia ta hadiye tana sake dulmiya cikin tunani da tsananin mamaki alokaci daya Kuma hadda kunya tana kamata
Daga ita har NURUn sai suka samu kansu da kunyar juna afian tayi saurin juyawa tana zaro takardar scanning din da batama Gama dubawa ta miqawa NURUn ba shiri bakinta na furta"

Congratulations.

Kallonta NURU tayi ahankali tace"
Thank you tana sakin murmushi.

Bakin afia mutuwa yayi murus da mamakin al'amarin dakuma kunyar dad dinta Haka ta raka NURUn har mota Dan Dole itace taja motar tabar gurin aikin ranar saidai Kuma gobe suka nufo gida tana satar kallon NURU wadda farin cikine fal cikin ranta Allah zai Bata 'da ko 'yar kanta.

Suna shigowa gidan tun daga motocin maleek dake harabar gidan taga alamun an sauya musu parking wanda hakan ke nuni da yadawo kenan
Cikeda murna ta fito motar tana mantawa da komai ta nufi hanyar office dinsa na cikin gidan dayake aikin office aciki sbd hango Mr Omar agurin tasan Yana can Dan Haka ta nufi gurin cikin tsananin farin ciki da murna.

Tsaye suke daga bakin kofa tareda baqinsu 'yan China dasukazo wani aiki harsun Gama magana sun fito kenan zasu wuce ya hangota tana tahowa
Sanin sabon daya koya Mata da yanayin yanda take tahowar ya tabbatarda abinda zai faru ya hadiye wani 'dan yawu ya waiwaya ya kalli Mr Omar Wanda take yagane kallon ya matso Yana washewa bakin Baki Yana nuna musu hanya da cewa"

chairman Zhou let me see off please?

Gyada Kai sukai suna sake bawa maleek hannu suka tareda Mr Omar zuwa gurin motocinsu da securities ke zagaye suna jiran fitowarsu.

Da gudu ta qarasa qarasowa ta fada jikinsa tana Dora bakinta kan nasa ta bashi wani lafiyayyan kiss daya sanyashi dagota ya kalli fuskarta kafin yasake maida fuskarsa yayi kissing din lips dinta Yana fidda wani lafiyayyan murmushin dayasa afia kusan suman tsaye sbd Bata taba ganinsa akan fuskar dad dintaba
Ita gabaki daya daburcewa tayi ganin abinda idanuwanta suka ganar Mata wato dai ba yanzu bane al'amarin ke faruwa sbd komai data gani ya nuna dad dinta ya dade da tsunduma wata sabuwar daddadar rayuwa hakama NURUn.
Wayyo Allahna" tace tana juyawa da sauri zata bar gurin sbd ita duk kunyar komaiba ya rufeta Jin take Kamar ta nutse a qasa
Tana juyowa saura kadan suyi Karo da Mr Omar da shima yake tsaye agurin Yana jiran sugama soyewar ya qarasa.

Kallon kallo sukai itada Mr Omar dake sakin murmushin Haka yakeson ganin megidansa ya sake kallon gefen su maleek din ya juyo ya kalleta da ido yayi Mata alamar tasake waiwayawa tagani
Ta juya ahankali daidai lokacin NURU ta Dan daga duga duganta takai bakinta kan kunnensa daya rankwafo yana riqeda qugunta cikin rada tace Masa"

_Nenyì Irìguzí_ (Am pregnant).

Wani irin Abu yashigesa ya dagota ahankali yana kallon cikin idanuwanta da ido yake tambayar" da gaske??

Kai ta gyada tana zagayo da hannuwanta qugunsa tana cewa"

And I missed you yau duka bani muryanka ba.

Dago fuskarta yayi ya hade bakinsu yabata wani irin lafiyayyan kiss daya sata kallonsa a kasale tace"

Are you this happy??

Kamar yaro haka ya daga Mata Kai Yana kamo hannunta suka nufo ciki
Afia da Mr Omar sukai saurin barin gurin har suna ture juna tayi saurin fadawa Palo ta nufi dakinta da gudu tana cewa"

Heyyyy
NURU kin wuce tunanina
Dad kuma bazan iya cewa komaiba sbd yau Naga asalin MALEEK da bakowa zai taba samun damar ganiba sai su Mr Omar 'yan kullum da kullum din MALEEK.

Suna shigowa dakinsa suka wuce Kai tsaye acan aka qarasa sauran murnar da farin cikin cikin Wanda yasata mamakinsa Dan Bata dauka yanada sauran son haihuwa har hakaba.

Sai dare gurin cin abinci Afia tasamu ganinsu lokacin ba kunya NURU tayi wanka tana sanye da wata lalatacciyar riga Mara tsayi Sosai gashinta daure tsakiyar Kai kaman baby shikuwa akai akai idanuwansa na kanta
Duk sai taji abin wani iri saidai Kuma farin cikin data gani taredasu din ya tabbatar Mata da ba qaramin so sukewa juna ba
Ta ajiye spoon dinta ahankali ta dago ta kallesu cikin farin ciki tana murmushi tace"

Congratulations dad you are having another child Allah yakawo manashi lafiya.

Murmushi yasake Ya kalli afian yace"

Thank you princess Afia.

Da ihu farhat tayi kan NURUn tana cewa"

My aunt zata haifamuna baby me kyau kamanta.

Murmushi NURU tasake tana kissing kumatun farhat din.

Tun daga dining din Babu Wanda yakuma ganin NURU sai washe gari da safe dasuka fito cin abinci sai alokacin afia tabada shawaran NURUn tafara ganin likita musamman akan jirin aikuwa ba Bata lokaci Mr Omar dakejin kaman ya taka kan jariri yakira Dr Damien yazo har gida ya duba NURUn daganan yafara zuwa dubata akai akai.

Lokacinda su abal dinta suka samu labarin cikin hadda sadaka ammynta tayi meryam kuwa tuni tafara takura tanason zuwa gurin NURUn saigashi kuwa maleek da kansa yasa jekadi taje har Delah ta daukota dama Kuma itama jekadin tana Shirin zuwa ne harsai NURUn ta haihu.

Zuwan jekadi da meryam da sati biyu maleek ya dauketa suka tafi _Maldives_ inda sukai zamansu acan suna hutawa Saida cikin yashiga wata na budu kafin suka dawo lokacin anfara maganar auren afia Imran Wanda tun kafin suyi tafiya dad din Imran din ya nemesa yayi magana da afia tace da amincewarta take yace ya Basu aka tsaida Rana.

Imran yadawo Paris gabaki daya da lailah sbd gidansa a Nan Paris yake bazai zauna gidan mahaifin matarsa ba ba girma bane Dan Haka murna kan murna agurinsu NURUn da afian sbd bazasuyi nesa da juna ba take aka hau Shirin biki gadan gadan musamman uwar amarya lailah da ba laifi yanzu ta warke harta fara komawa ayyukanta zata fara daga farko Dan ma a qarqashin kamfanin dad din Imran din take aiki.

Sosai akai shagali a gizah na auren afia din Wanda hatta iyayen NURU sun halarto tareda kaleeb sosai tayi farin cikin ganin iyayenta Suma sunyi farin cikin ganinta musamman cikinta daya fara tsufa a gizah kowa yasan MALEEK na gaf da samun magaji kila suke fata.

Padima dai ba laifi tananan sama sama wani lokacin kalau wani lokacin Kuma abin ya Dan juye ahaka aka gama bikin suka tattara suka dawo Paris afia ta tare a babban gidan mijinta Wanda mum dinta take sashe guda na musamman da Imran din ya ware Mata.

Ranarda afia tacika wata hudu cif da aure ranar nakuda ta tasowa NURU
Maleek ya tattara mulkin da sarautar ya ajiye suka dunguma zuwa asibiti sbd ganin gidan zata wahala bazai iya jure ganin hakan ba
Saigashi cikin ikon Allah suna Isa ta haifi qatoton jaririnta me Kama da farhat sak.

Koda maleek ya karbi Dan wata hamdala yasaki Yana godewa ubangiji yayi Masa huduba da sunan Mr Omar tareda yiwa Mr Omar wata gagarumar kyautar datasaka Mr Omar din rungumesa Yana hawayen godiya duk dai yatara tarin dukiya me yawa a qarqashin maleek din Amma sai bazai iya dainawa maleek din aiki ba sbd sunzama kaman jini.

Acikin motarsu ta dawowa gida duk yabita ya lashe da kisses itada baby Omar Wanda hotonsa tuni yafara yaduwa a duniya Matar UBAYD MALEEK me gizah ta haifar Masa baby boy.

Daqyar ya suka iya raba gurin kwanciya sbd jekadi data Dan sako NURUn agaba har aka samu sukai 50days daga Nan delah suka tafi tayi sati biyu gurin iyayenta daganan suka dawo gizah tayi kwana biyar kafin tadawo Paris su afia sukazo aka wuni gidan suna Yan kus kus dinsu na kayan datazo dasu suka raba
Washe garin ranar maleek ya dauketa suka tafiyarsu _Santorini_ sbd wata sabuwar duniyar da NURUn ta jefasa a Daren jiyan inda sukai wata daya kafin suka dawo
Saidai Koda ta dawo da sabon ciki ajikinta wanda yazo Mata da Dan laulayi da son jiki Haka shima duk ya shirirce gurin tattalinta da jinya sbd koyaushe tana lafe ajikinsa karshe dai Mr Omar Dole ya rungumi wasu ayyukan da kansa yakeyi a office.
##MAMUH#
*ALHAMDULILLAH YA ALLAH*

*MUNZO QARSHEN WANNAN LABARIN ME SUNA UBAYD MALEEK WANDA NAKE FATAN KURA KUREN CIKI DA ABUBUWAN DANAYI BA DAIDAIBA ACIKI ALLAH YA YAFEMABA GABAKI DAYA HAKAMA KURAKURAI IRIN NA MANTUWA DA TYPING ERROR DUK INA FATAN ZAKUMIN UZURI HAKAMA WAINDA ZASUGA BAI KAI MUSU INDA SUKESO BA SUYI HAKURI AMMA DAI KYAN L
LABARI AGAMASHI ANA MARMARINSA BASAI MUNKAI INDA ZAKUJI YA GUNDUREKU BA NIMA BASAI NAKAI INDA RUBUTASABA ZAI GUNDURENI DAN HAKA INA FATAN NUSHANDIN YAYI DAIDAI YANDA ZA'A DADE ANA TUNAWA*

*NAGODE SOSAI SOSAI DA KAUNA DA KUKA NUNAWA LABARIN KUMA INSHALLAH INA MANA FATAN HADEWA A GABA DA LABARIN DAZAIFI UBAYD DA NURU DADI* 😜😜
*NAGODE*
*_MAMUHGEE_* 💋

An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels


Please Login or Register in order to submit comment