Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

a Nigeria ta dalilin ki ne nake zuwa, haka kawai Ina Kan har kokina saikin aikata abinda zaisa dole sainazo qasar Nan, ke wacce irin mahaukaciya cene? Kwata kwata bakida aji bakida Hankali irinna yanmata, anturaki makaranta ashe soyaiya kike harda su kiss, nakafa doka a gidan Nan kina take wa yafi a qirga, saboda ga sa'anki, to yau idan jikinki yagaya miki, ko ance ki kalli samari ma bazaki kallesu ba, dangane da makaranta Kuma nasan matakin dazan dauka a kanki"

Yana kaiwa Nan ya tashi yafice daga Dakin, Waheeda tafashe da Kuka, cikin kuka tace "Nashiga uku na, ashe yaji, shikkenan Aryan yacuceni, Allah ya'isana" haka taci gaba da kneel down tana kuka, babu damar tatashi yazo yaga tatashi nanma taqara wani laifin, tun yanzu ma jitake gwiwowinta harsun fara zafi


Yana futowa daga Dakin yatarar da Dady da Ummah a zaune, gaida su yayi cikin ladabi sannan yakoma gefen Ummah ya zauna tareda Dora Kansa akan kafadarta yace "Ummah"

Murmushi tayi tace "Yayansu ya hanya, maza tashi muje Kaci abinci, gashi can na shirya ma" babu musu ya tashi, saboda yayi missed girkin umman tasa, saboda aturai koda yaushe baida abinci saina gwangwani, Daddy ya kallesu itada Yaron yace "idan kin gama bashi abincin inason magana dashi"

Ummah tace "to Alhaji"

Ita da kanta ta dinga bashi abinci abaki, kowa ya kallesu yasan akwai tsantsar soyaiyar uwa a tsakanin su, Sai shagwaba yake mata abu kadan yace Ummah, ita Kuma Sai lalla6ashi take

Saida ta tabbatar ya qoshi sannan suka koma falon, wajan Alhaji Umar, Babban Yaya ya Kalle shi yace "Daddy nagama, meyafaru?"

Kallan sa yayi yace "menene zai faru banda maganar Aurenka?ai tunda Naga kazo yau nasan kun daidai tane kaida ita Habiban ko? Yaya kukai da'ita?" ๐Ÿ˜‚

Sunkuyar da Kansa yayi yana Sosa girarsa, yama kasa dagowa ya kallesu

Ummah tayi ajiyar zuciya tace "wacce Habiba Kuma Alhaji? Yarinyar da harma munyi magana da mahaifiyar ta awaya sunce sun janye batun auren, nabawa mahaifiyar yarinyar hakuri Amma Sai tace ai habiba tace bazata iya zama da mutumin da bazai bata kulawa ba, to tunda naji haka, kawai saina bata hakuri tunda bansan me suka Tattauna ita dashi a wayar ba, shi yasan meya qulla "tana fadar haka takawar dakanta Gefe tana girgiza qafa

Alhaji Umar ya Kalleshi yace"Naufal"

Ahankali yace "Na'am Daddy"

"bakada lafiya ne irinta maza?"

Maganar tayi masa nauyi, saiya kasa dago Kansa ya kalli mahaifin nasa, Ahankali ya girgiza Kansa yace "A a Daddy"

Daddy yace "okay, iskanci ne yake damunka kenan?"

Nanma yakasa bashi amsa ya girgiza Kansa yayi shiru

Daddy ya ajiye Jaridar hannun sa yace "kaiba 6oyaiyan mutum bane dakake tunanin mutane bazasu saka Maka ido akan aure ba, muna zaune lafiya bazaka ja mana zagi agari ba, zamusa qafar wando daya dakai tunda haka kaza6awa rayuwar ka, Kuma neman aure yanzu muka fara nema Maka, idan ma wani abun daban kake fadawa yaran mutane har suke gudunka kaika Jiyo, mude bazamu fasa nema Maka aure ba, har a wajan Allah muna neman fita haqqin ka ne a matsayin mu na iyayenka akan kayi aure gudun aikata Zina, mutumin banza mutumin wofi, katashi kabamu waje Kuma aure dolen dole Sai kayi "

Runste idonsa yayi, maganganun Daddy sun shige shi sosai, yaji zafin maganar Daddy sosai, tayaya ne zai futo fili yafada musu yarinyar dayake so Bayan tarin matsaloli dakuma qalubalan dazai fuskanta ? Tayaya? Ahankali ya tashi daga gabansu yanufi dakinsa, zuwa yanzu magrib har tayi

Yana shiga dakinsa yaga Waheeda yanda yabarta, gaba daya cinyoyin ta sun sage, Saitayi kamar zata fadi qasa, saita dawo baya taci gaba da abinda take, bacin ran dayake ciki ne yasa yanemi belt yanufeta gadan gadan, tana ganin haka tatashi tsaye tanaja baya, kuka take wiwi tana bashi hakuri Amma idonsa sun rufe saida ya lafta mata belt dinnan ajikinta, qara tasaki tana fadin "Dan Allah kayi hakuri, wallahi tallahi nadena Babban Yaya, Dan Allah kayi hakuri"

Cikin 6acin rai yace "kifadamin waye wannan Yaron dayake neman lalata ki?, harkinashan bakin wani saboda bakida mutunci ko? "

Belt din tariqe idanunta cikeda hawaye tace "Dan Allah kayi hakuri, wallahi bazan sake ba, idan nasake Kamin komai ma nayarda"

Fizge belt dinsa yayi yasake zuba mata shi ajikinta, zafin dataji ne yasa batamasan lokacin data tashi ta rungume Shiba,yana jin yanda Albarkatun qirjinta suke tsikarinsa saboda bata saka bra ba, lokaci daya jijiyoyin jikinsa suka kar6i saqon, ๐Ÿ™ˆAmma tsananin 6acin ran dayake ciki yasa baza'a gane hakan ba
Fizgeta yayi daga jikinsa yasake Dora mata wani belt din, cikin kuka tace "Akofar fada yake, gidan Alhaji Hamza"

Tsaki yasaki tareda wullar da belt din qasa yace "Stupid"

Ummah tana Jiyo kukan Waheeda tata6e baki tace kanku akeji kunfi kusa, Daddy ne yake tambayar ta meta masa, anan ta fada masa komai ciki harda wayar Babban Yaya data daga batare data saniba

Futowa yayi daga Dakin yabarta anan, su Ummah suna zaune har lokacin, suna ganinsa yafuto fuskar sa a daure, yana shirin fita daga falon, anan yaci Karo da Yanbiyu harsun dawo daga islamiya kasancewar anfara Kiran sallar magrib, yanda sukaga fuskar sa sunsan ransa a6ace yake, cikin sauri suka bashi waje yafice daga falon

Suna qarasowa falo suka gaida Daddy, Shima ya tashi yayi shirin tafiya masallaci, Dakin Babban Yaya aka bude ahankali, kamar me koyon tafiya hake take takawa, idanunta sun kumbura sunyi jajir, Sai yarfe hannunta take, hawaye wani nabin Bayan wani, Ahaka tashige cikin dakinsu babu Wanda yace da'ita uffan daga Ummah har Yan biyu, tana zuwa daki wani irin zazza6i yafara kokarin rufeta, kawai zubewa tayi agadonsu taja Bargo tarufa.๐Ÿ˜‚

Da daddare duk suna zaune afalo gaba dayansu suna kallo, har wajan karfe takwas da rabi Waheeda bata futo falo ba
Babban Yaya yana zaune yana danne danne a wayarsa, Sa'eed da Sa'ad Kuma suna gefen sa suna bashi labarin 'yanmatan dasuka hadu dasu wasu yanbiyun suma, magana suke masa Amma hankalinsa yanakan wayar dake hannun sa, ahankali yake amsa musu, su yanbiyu suna zaune suma, suna Kallan film din da'akeyi, Ummah da Daddy suna can Gefe suna zance qasa qasa, Daddy ya kalli Babban Yaya yasake yin qasa da murya yace "ke baki lura da abinda nafada miki ba? Ki lura dashi sosai qarya yake mana bashida lafiya"๐Ÿคฃ

Itama Ummah Kallan sa tayi tace "Aina yarda Alhaji, kunyar fada mana kawai yake, Amma duba fa yanda 'yan' uwan suke bashi labarin yanmatan su Amma yayi mursisi, maza dason zancen yanmata Amma shi kaduba kagani fa suna masa magana kamar sunayi da dutsi"

Daddy ya girgiza Kansa yace "dole zan dauki mataki hajiya"

Shikuwa Babban Yaya baisan sunayi Bama ๐Ÿ˜‚Kallan intisar yayi yace "ke tashi ki kira wannan yarinyar tazo tayi kallo"

Intisar tasan da Waheeda yake, ita kadai ce bata futo falo ba, cikin sauri ta nufi dakinsu, tana shiga tahau kan gadon ta yaye bargon da Waheeda tarufa, bude idon ta tayi ta kalleta, duk yanda Waheeda take gane yanbiyu, take banbancesu dukda tsananin kamar dasuke, yau kasa ganesu tayi,๐Ÿคฃ intisar ce tazo kiranta Amma Waheeda tana qare mata kallo cikin wahala tace "Ihsan Dan Allah ki temaka ki taro ruwan zafi a toilet kizo ki gasa min cinyoyina, jikina yayi tsanani bazan iya tashi ba"

Dariya ta kama Intisar, saita danne gudun karsuzo suna fada, tace "Babban Yaya ne yace kifuto kiyi kallo kowa yana falo banda k....." kafin ta qarasa magana taga Waheeda ta duro daga kan gadon ๐Ÿ˜‚
Kokula sauran zancen batayi ba tafice daga Dakin, tana zuwa falon babu Wanda ta nufa Sai shi, har gefen qafarsa ta zauna, hawaye yazubo daga idanunta, a Hankali tace" Babban Yaya Dan Allah kayi hakuri kaji.... "

Babu Wanda yasan metake fada masa, saboda ahankali tayi masa maganar, Shikuwa banza yayi yarabu da'ita, hawayen tasake gogewa tace"kaji" memakon yabata amsa saiya tashi daga falon yashige dakinsa, haka ta zauna a wajan tana Kallan dole, saida takusa minti talatin tana kallo Amma bata fahimtar komai, Dan haka tatashi Takoma dakinsu tafara gabatar da sallah


Karfe bakwai daidai afalo tayi masa,yayi kyau sosai cikin manyan Kaya, yanda yaqara cika da kamala zakace yanada aure, agogon hannun sa ya kalla yadubi Ummah yace "kice musu Idan sun gama Ina waje Ummah"

Ummah tayi dakin yaran tace "kuyi sauri kufita yayanku fa kuyake jira"

Yanbiyu ne suka futo sun shirya cikin uniform dinsu, suna zuwa compound din suka hangeshi yana Dukan tayar motar da qafarsa yana Kallan agogo, suna ganin haka suka qara sauri suka shige motar, shida Kansa yayi driving din, Kai tsaye yanufi makarantar su

Suna zuwa kuwa Kai tsaye yanemi iso zuwa office din director, teachers dinsu maza Wanda suke harkar ball suna ganinsa suka fara zuwa suna gaisawa dashi, yana gaisawa da director yanemi afwa akan yanbiyu, babu bata lokaci sukace komai ya wuce Yara sukoma aji, Amma waccan dayar de kar akawota bazasu karbeta ba

Duk da haka saida yaqara basu hakuri sannan yayi musu ihsani yafuto daga makarantar, daga Nan ma ba gida yakoma ba, kofar fada ya nufa, yana tambayar gidan Alhaji Hamza aka nuna masa, futowa yayi ya jingina da motar yace ayi masa sallama dashi, Alhaji Hamza yana futowa yaga farin buzu a kofar gidansa, qarasa wa yayi yabashi hannu suka gaisa, Babban Yaya yace "Alhaji sunana Naufal, da Alhaji Hamza nake magana ko?"

Alhaji Hamza yace "nine samari, ba kaine yaranmu suke cewa Big Brother ba?"

"nine Alhaji, dama nazo ne akan maganar qanwata dakuma Yaron wajanka Aryan"

Alhaji Hamza yace "to menene yafaru?"

"Alhaji, Yaron wajanka yana soyaiya ne da qanwata, shine nazo muyi magana akan yaturo iyayensa idan aure zaiyi yanzu"

Alhaji Hamza yace "Wai Aryan wannan Dana Sani Dan wajena kake magana akansa?"

"shide Alhaji"

Murmushi Alhaji Hamza yayi yace "samari Aryan fa shekararsa goma shatara ne Idan nayi lissafi daidai, tayaya za'ayi masa maganar aure yanzu?"

Babban Yaya yace "hakane, to ita yarinyar dayake nema aurenta zamuyi, saboda haka Dan Allah Alhaji ajawa yaro kunne yadena bibiyarta, jiya matsala ce tafaru a makarantar su har hakan yasa suka Koreta daga makaranta, so aja masa kunne please"

Alhaji Hamza yace "Subhanallah, ashe yar'uwarka ce yaro, to kuyi hakuri Dan Allah, insha Allah zanyi wa tufkar hanci"

Babban Yaya baice dashi komai ba yajuya yashiga motarsa yatafi gida

Yana zuwa gida ya tarar da Hajiya Anty da Ummah afalo, can ya hangi Waheeda a dinning tana cin abinci
kwanciya yayi akan doguwar kujera ya Dora Kansa akan cinyar anty yasaki wani irin murmushi dimples dinsa suka lotsa duka biyun yace "Anty nah ta kaina"

Sumar Kansa ta shafa tace "yayansu nayi fishi, kazo Amma koka leqoni, yanzu ma sannu da zuwa nazo yima dakuma wani albishir"

Hannunta datake shafa sumarsa yariqe yayi kissing Bayan hannun sannan yace "Ina jinki Hajiya Anty"

Tace "wallahi wata yarinya ce take zuwa Asbiti Ina dubata lokaci zuwa lokaci, shine nayaba da Hankalinta, nace zan turo mata Dan yayata su daidai ta ko Allah zaisa ayi abun da'ita"

Cikin sauri ya tashi daga kan cinyarta yace "Anty me kikace?"

"abinda kaji nace"

Kansa ya shafa yace "Anty Kode neman Kai kuke Dani ne?"

Tace "mekake nufi yayansu?tayaya zamu nemi Kai dakai?"

Bata rai yayi cikin shagwaba yace "to Anty gashinan Kuma arasa da wadda za'a hadani Sai majinyaciya?"

Ummah ce tasa musu baki tace "tunda kaqi lafiyayyu ai sai kakoma kan majinyata" tajuya ta kalli hajiya Anty tace "ki fada masa komai, kidena wani Lalla bashi"

Hajiya tace "yayansu harna yiwa uncle dinka maganar yarinyar shida Dadynka, Amma Kai Yaya kagani?"

Ummah tace "Yaya zai Gani kuwa? Yama amince kawai"

Tashi yayi daga wajan su yace "to Anty idan nasamu lokaci zanje naganta"

Ummah tace "yaushe zakaje?"

Kansa yadafe da hannun sa ๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™‚๏ธyace " wayyo Allah Ummah, zanje wallahi, anjima zanje"

Anty tace "to idan katashi zuwa ga wannan kayan kwalliyar kakai mata"

Uwar ledar data turo masa gabansa ya kalla, cikin ransa yace Dama de sun shirya komai
Yace "to"

Bai dauki ledar ba ya wuce ta gaban Waheeda yayi dakinsa,yanaaji yana cewa "good morning Babban Yaya" Amma ya shareta
wani qullutun taqaici ya to kare mata maqoshi, tasan yanzu Babban Yaya ya tsaneta, gashi ya maida yanbiyu makaranta Amma banda ita.

Hajiya Anty tana tafiya gida Waheeda taje wajan Ummah ta zauna, Ummah ta kalleta tace "Lafiya Waheeda?"

Girgiza kanta tayi tace "Ummah, Babban Yaya baya sona yanzu, ya tsaneni"

Ummah ta kalleta tace "yayanki uwa daya uba daya tayaya zakice baya sonki Waheeda? Halinki ne baya so, Waheeda bakya jin magana, saikin masa laifi Kuma kizo abun ya dameki, yanzu ni me zanyi muku akan haka?"

Idanunta ne yayi qwalqwal hawaye yana shirin futowa tace "to Ummah kinajifa nagaidashi Amma ya share ni"

"bai gama hucewa bane, kibari zuwa anjima ai zai sauko"

Hawayen data riqe ne ya silalo daga idanunta, tasa hannu ta share, sannan tayi dakinsu domin ta watsa ruwa

Umma na ganin tafiyar ta ta nufi Dakin Babban Yaya, yana kwance agadon sa yayi mata shi da hannayensa, duniyar tunani yatafi ita wannan yarinyar ta wacce hanya zaibi yarabu da'ita?

Turo kofar tayi tashigo, yana ganin shigowarta ya tashi zaune, zama tayi akusa dashi tace "Yayansu, magana nakeso muyi"

Nutsuwa yayi yace "to Ummah"

Tace "akan Waheeda ne, yakamata kadinga Jan 'yan'uwanka ajiki, qannanka ne bakada kamar su, idan Bama Raye kaine zasu kalla a matsayin ubansu, yarinya qanqanuwa Waheeda har tana min magana akan rashin kula da'ita da bakayi, tacemin yanzu kadena sonta, hannunka fa baya ru6ewa ka yanke kayar, yakamata kadinga janta ajiki kanuna mata fari da baqi, tunda Dukan bazaisa ta sauya ba saika dinga yimata nasiha "

Kallan ta yayi yace"Ummah nasiha bazata shiga qwaqwalwar yarinyar nanba, batajin magana, kullum itace takemin sanadin zuwana Nigeria "

Ummah tatari numfashinsa tace" kaikuma gashi baka son zuwa Nigeria saboda kar muyi ma maganar aure ko? "
Qasa yayi da Kansa yace" Bahaka bane Ummah, insha Allah zan jasu ajikin kamar yanda kikace "

Tashi tayi tsaye tareda fadin" Allah yamaka Albarka "

Cikin jin dadi yace"Amin Ummah tah"

Dayamma suna kallo afalo, Amma dukansu su ukun suna saka kayan makarantar islamiya, jira suke kawai lokaci yayi sutafi, futowa yayi daga dakinsa yayi wankan qananun Kaya kamar ka saceshi kagudu, wandon Jeans yasaka baqi, Sai Riga me kama jiki ruwan toka, dakuma yar sama me ratsin baqi, yasaka kambos Shima baqi me ratsin brown, yayi kyau sosai sumar Nan tasa Sai sheqi take, Ummah ta Kalle shi tace "masha Allah, yayansu Sai ina?"

Kansa ya shafa yace "inda hajiya Anty tace naje"

Fara'ah ce ta wanzu a fuskar Ummah, tace "kace gidan surukar tawa zakaje, irin wannan wanka haka ai dole a dedeta, Bari in Dauko Maka kyautar Tata"

Baice komai ba, yanemi kujera ya zauna, tareda daukar remote ya maida tashar Kallan ball, Kallan Waheeda yayi, suna hada ido tayi qasa da kanta, yace "4 o'clock kuke tafiya islamiya ko?"

Atare suka amsa da "eh"

Yasake dubanta yace "tashi ki rakani"

Cikin murna tatashi tayi dakinsu, farinciki take yayan Nata da alama yahuce, uniform dinta tacire tasaka doguwar Riga, sannan ta dauki dogon hijab dinta tasaka, tana futowa Ummah ma tana futowa daga daki, ta bashi ledar kayan, ya nuna mata Waheeda ataqaice yace "bata"

Ummah tace "yanaga kincire uniform din ko tare zakuje zancen?"

Waheeda tasaki wani murmushin jindadi, tace "eh Ummah"

Kallan ta yayi sosai, sautari idan yarinyar tayi wani abu saiya ga Takoma photocopy dinsa sak, musanman idan tayi dariya ko murmushi duk dimples dinta suka bayyana kamar de nashi, kauda tunanin yayi daga ransa yafita daga falon ita Kuma ta Mara masa baya, saida tajuyo tayiwa yanbiyu gwalo ๐ŸคชSannan tafita

Ummah ta girgiza kanta cikin ranta tace gaskiyar sane daya ce bazata sauya ba

Motar dasuka shiga glass din motar tint ne, ba zakaga naciki ba, mafi yawan lokaci irinta yake Hawa saboda shi mutum ne na mutane, ko Yaya yafuto awaje dole ne kasamu Wanda yasan shi
Suna cikin tafiya ya kalleta yace "Bani labari"

Kallan sa tayi tace "Babban Yaya wanne labari gashinan muna shirin zuwa Naga Anty"

"wacece Anty?"

"Babban Yaya wadda zamuje wajan ta, budurwarka, harna matsu naganta wallahi"

Haushi ne yakama shi, yace "to naji Dan Allah, ni labari nace kibani bawani shirme ba"

Kallan sa tayi, cikin ranta tace zancen budurwar tasa yake cewa shirme to in hakane komai ma ta fada bazai birgeshi ba, duk da haka saita Juyo tana fuskantar sa tace "Babban Yaya inaso Naga kana Ball, ka'iya ball sosai, wani lokacin idan ka saka qwallo araga Sai inji jikina yana tsuma kamar nice nasaka"

Dariya tabashi, saida yayi dariyar sa sannan yace "ke meyasa bazaki Koya ba?"

"Bayan wacce kake Koya mana agida?"

"yes, idan kinaso saina sake Koya muku"

"muna so wallahi Babban Yaya,nafiso nafi yanbiyu iya Ball"

Kallan ta yayi kawai yayi shiru, saboda qarasowa dasukai gidan yarinyar da Hajiya Anty tabashi address, a kofar gida suka tsaya yakira Hajiya Anty ya tambayeta sunan yarinyar tace masa naja'atu, daga Nan yakashe wayar yatura wani yaro Akira masa ita

Yaron ya dawo yace ance su shigo, har falo suka shiga suka zauna, babu laifi gidan sunada rufin asiri, kusan minti biyar da zamansu Sai gata tafuto tana Sanye cikin atamfa Riga da siket, Sai wani Dan qaramin mayafi data saka, da farko tsorata tayi data ganshi, saboda lokaci daya yadaki zuciyarta, gayen yahadu dayawa, fatanta daya Allah yasa Shima ta masa
Zama tayi tareda gaidashi, ya amsa cikin kulawa, acan Qasan ransa yaji dadi dabata ganeshi ba da alama bata ganin ball, Waheeda ce itama ta gaidata fuskar ta d'aukeda murmushi, ta amsa mata

Shiru Waheeda tayi tana jira taji irin kalaman soyayyar da Babban Yaya zai tsara mata kamar yanda Didat yake mata idan sun hadu a school, saitaji yace "Naja'atu Anty nace taturo ni wajanki, basai nayi Miki dogon bayani ba nasan kinsan dalilin zuwana wajanki"

Murmushi tayi tace "Hakane, nide daga wajena babu wata matsala, Ina fatan kaima haka?"

Babban Yaya yace "a a, banda wata matsala Nima, saide inaso namiki tambaya guda daya"

Kafadunta ta daga๐Ÿคท๐Ÿปโ€โ™€๏ธtace "babu damuwa Ina jinka fadi duk maganar dakake so"

Yace "Kina school ne yanzu?"

Tace "a a, tunda nayi candy bankoma makaranta ba"

Yace "masha Allah, Nima banda burin yarinya tayi dogon karatu batare da aure ba, but meyasa ke kinyi candy Amma bakiyi aure ba har kika dade agida kina neman tsufa?

Waheeda ta zaro ido ๐Ÿ˜ณta Kalle shi da sauri

Itama naja'atu ta Kalle shi tace"me?, nice na tsufa babu aure? "

Batareda damuwa ba yace"idan bakiyi shekara ar'ba'in ba tokin kusa, tunda Naga idanunki na tabbatar kedin Nan sa'ata ce, bazan girmeki ba, nikuma gaskiya nafison na auri yarinya qarama, wadda zan Koya mata komai"

Haushi yakama naja'atu, ta jinjina kanta tace "ni Dama nasan babu wani namijin Arziqi daza'a dinga neman Kai dashi haka kawai, na tabbatar kaima kyan Dan maciji ne dakai tunda har ake neman Kai dakai duk wannan kyan Naka, tunda kana tareda P.A dinka ai shikkenan saikaje ka aure ta"taqarasa maganar tana Kallan Waheeda

Cikin sauri Waheeda tace "kaiiii Yaya nane fa"

Naja'atu ta miqe tsaye tace "Au...to Allah yasa gware kukai kuka futo" ๐Ÿ˜‚
Waheeda ta kalli Babban Yaya ko zai dakatar da naja'atu daga tafiyar datake shirin yi, taji yayi shiru, ahankali tace "Haba Babban Yaya"

Kallan ta yayi ya daga murya yace "Naja'atu"

Cikin fishi naja'atu tajuyo tace "kutashi kubar mana gida tun kafin nakira Yara su tule ku da qasa"๐Ÿ˜‚

Dafe Kansa yayi ๐Ÿคฆ๐Ÿปโ€โ™‚๏ธ?, sannan yadago yace "Dama wannan ledar ce kika manta bakidauka ba, Inji Anty tace akawo miki"

Tsaki naja tasaki tace "kuje da tsiyarku" daga Nan tashige tabar su afalo, ita kanta Waheeda taji babu dadi, tayi tunanin haquri zai bata Wai ashe leda zai bata, wannan rashin mutuncin ko ita akayiwa Allah ne kadai zai rabata da saurayin ranar ๐Ÿ˜–

Haka suka futo daga gidan Waheeda jiki a sanyaye, shi kuwa ransa fes

Amota kasa magana Waheeda tayi, Shima bece da'ita uffan ba, cikin ranta tana so ta tambayeshi meyasa yake gudun aure? Amma tarasa ta'ina zata fara? Duk cikin iyayensu babu Wanda yataba zama dashi yaji menene dalilin sa naqin matan da'ake hadashi dasu, kawai sude iyayen burisu suga yayi aure kawai, tana so taji menene matsalar sa, meyake so? Amma tana tsoron abinda zai biyo baya, saboda zai iya cewa ta raina shi

Tunanin tane ya tsaya lokacin dataga sun tsaya awani super market, p-cap dinsa ya dauka yasaka me d'aukeda sunansa ajiki, sannan yashiga wajan, itade Waheeda tana binsa Abaya taga Sai provision yake yi, itama yace tayaya shi haka suka dauki , su suger, cornflakes, madara, Maggi, kayan zaqi dangin su biscuit da chocolate, saida yagama hada komai tsaf, har tana mamakin Ina zaikai wannan uban kayan,? Wasu yanmata ne suka ganshi su kazo sunaso yayi photo dasu, babu musu ya tsaya sukayi sannan suka nufi wajan biyan kudin, a lokacin wani saurayi Shima yana wajan zai biya nasa kudin, ganin Babban Yaya yasa farinciki yarufe shi, Yama Rasa inda zai Dora ransa, Sai magana yake masa, Babban yaya yayi murmushi Shima yasake da saurayin kamar ya sanshi, shida Kansa ya biya kudin saurayin danasu kayan sannan yamasa sallama suka tafi gida

Suna zuwa gida taga yabawa Sa'eed wannan kayan dasuka zo dashi, sannan suka wuce Dakin Ummah, tare suka gansu itada hajiya Anty Sai hira suke da shewa kamar ba facaloli ba๐Ÿ˜ƒ
a lokacin biyar da rabi har tayi, Ummah ta kallesu cikin farinciki tace "harkun dawo? Jinake ai sai dare"

Hajiya Anty tace "yayansu nasan de Najaatu tayi hundred percent"

Zama sukai gaba dayansu babu Wanda yayi magana, Ummah ta kalli ledar kayan kwalliyar dasuka tafi dashi tace "yanaga kunyi shiru, meyafaru ko bakuje bane?"

Waheeda ta janye hannunta daga tagumin da tayi tace "hmm Ummah cewa tayi mutashi mutafi tun kafin tasa atule mu da qasa, gashi mayafi take sakawa, shikuma Babban Yaya baya son mayafi, shine ya tambayeta meyasa ta tsufa batayi aure ba, ranta ya6aci tace masa yaje ya aureni tunda ni p.a dinsa ce, Wai ai Dama neman Kai kuke dash.... "
Hajiya Anty ce ta katse Waheeda cikin tsawa" ke dallah can rufe mana baki shashasha kawai. Yen yen yen Sai magana kike Babban Yaya baya son kaza, Babban Yaya baya son kaza, kunhada Kai kunje kunci mata mutunci kun dawo toshknn Hankalinku saiya kwanta, ita yar'iskace dabaza tace yaje ya aureki ba? Ina aka taba tafiya zance , ganin farko adiba atafi da qanwa? Saikune zaku nuna mata ku yan'uwan jini ne, banji dadi ba dabatasa anmuku wanka da qasa ba, tashi kibawa mutane waje manya suna magana kin tsomo baki kamar maganar aurenki ake "
Sum sum Waheeda tatashi tabar Dakin, shi kuwa Babban Yaya kasa hada ido yayi dasu

Ummah tace"ashe abinda kake fadawa yaran mutane kenan shiyasa kowacce Sai tace bata sonka, Toda kake cewa ta tsufa batayi aure ba kaidin shekarar ka nawa?" ๐Ÿค”

Shiru yayi yakasa Bawa Ummah amsa, Ummah tace" dakai nake, nace Kai shekararka nawa bakayi aure ba? "

Kansa aqasa yace" Ummah kuyi hakuri, Nima ba laifi na bane "

daga Nan ya tashi yafuto daga Dakin Shima

Yana fita hajiya Anty tace" Yaya kinji me yace kuwa? Ba laifin sa bane Anya kuwa Yaron Nan kalau yake ba Sanyi da basir ne sukai masa mugun kamu ba? "๐Ÿคฃ

Ummah tace" to Hajiya Anty tayaya zan Sani? Kuma yaqi yayi auren balle mugani kalau yake koba kalau yake ba "๐Ÿ˜‚

Hajiya Anty tace" kaiii ninama Rasa mezance wallahi, tunani na ya tsaya Hajiya, Bari inje gida, idan nasake wani tunanin saina dawo "

Washe gari da sassafe ya shirya cikin qananun Kaya, so yake yabar qasar saboda jibi sunada match a Qatar, sannan muddin yaci gaba da zama to bazasu daina hadashi da yanmata ba, suna gama bresk fast, ya kalli Ummah da Daddy yace" Ummah, Daddy, zan wuce England yanzu, jibi munada match a Qatar, kuyimin addu'ah "

Atare sukace" Allah yabada sa'a "

Ya Juya ya kalli Waheeda, yabata 10k yace" gashinan, kiyi amfani da wannan idan kinje makaranta, anjima su Sa'ad zasu kaiki Boarding school, nariga nayi magana da principal din ta waya, Shopping din da muka iyo jiya nasan komai yamiki tunda ke kika za6o da kanki, Tunda bakya jin magana Dan Allah kisake aikata wani laifin Wanda zakisa nasake dawowa Nigeria saboda ke kinji..... "

Spoon din hannunta ne yafadi qasa tace" nashiga uku Babban Yaya Boarding Kuma? "

Kallan qwayar idonta yayi yace"yes, nafiso a kaiki inda zasu kasheki su kawo mana gawarki"





Duk me buqatar Babban Yaya yakirani kokuma yamin magana ta whtsapp 08033300034


Share please ๐Ÿ™๐Ÿป





Amnah El Yaqoub โœ๐Ÿ?
1/28/22, 20:49 - Ummi Tandama๐Ÿ˜‡: BABBAN YAYA


Writing By Amnah El Yaqoub


Like my Page On Facebook
https://www.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493/


5&6


Tanajin abinda yace tayi dakinsu da gudu tana kuka, Shima yajuya yafita daga falon, wannan Karon driver ne yakai shi Airport, Bai dade da zuwa ba jirginsu ya tashi

A wannan safiya Waheeda breakfast din da batayi ba kenan, tana daki
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment