Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

AUREN MU Complete Hausa Novel Document by AUREN MU


AUREN MU

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 88832



AUREN MU

Reading Time: 7 Hours

Added On: 13, Aug 2024

Author: Asma Baffa ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : +234 8061929616, 08033933642, 09032409668, +227 90795939

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 446.51 kb

File Type: txt

Views: 840+

Download: 1315+

Last download: 15 hours ago

Description/Story: [4/1, 5:47 AM] Sis Asma: 🛢️AUREN MU🛢️

COPY BY ZAINAB BUTALAWA

1-5


Official

By
AsmaBaffa



Page naki ne
UMMU LATEEPHA






Biye yake da ita a baya tana gaba Yana fada itama tana Masifa tare da furta bar maka gidanka zanyi,ya furta ki bar gidan Mana sai me nima haka nake so ki tafi dama kin isheni,ae naji tafiya zanyi suka shiga bedroom suna masifa,cikin akwatinanta ta dakko daya ta bude sannan ta bude ma'adanar kayanta ta Fara fito da kayanta,Hannu yasa tare da fisge wani leshi yace wannan ai ba kayanki bane Rannan na siya Miki da kika zo gidan nan dama ba a kawoki da kayan kirki ba,au haka kace yes wannan tsohuwar atamfar taki ce ya furta tare da fito Mata da ita,ta sake dakko wata shadda yace ajiyeta maidata ai baki zo da ita ba idan kin tuna last year na dinka Miki ita,ajiyewa tayi ta zabo Wanda tazo dasu kala biyu, fannin takalma tazo ta dauki wani white flat yace maza ajiye shi ni na siya Miki,tace na manta au Kaine fa ka siya,na tuna Miki yau to yace, amma Farooq baka da kirki amma ba komai,Farooq yace ae naji,cikin fushi ta jawo akwatinta ta fito Yana cewa itama akwatin mutunci na miki amma wlh da sai dai ki zuba kayanki a Leda,Aisha tace ni ka daina matsowa kusa dani bana bukatar taimakonka,yace wayyo yarinya Allah ya kiyaye na taimakeki rakaki zanyi Sabo da na kulle gidana Kuma karki sake kice Zaki dawo gidana daga yau,Aisha tace me Zan dawo nayi a wannan banzan gidan naka.

A Palo ta tsaya tana karewa palon kallo tana son gidan bata son barin gidan yace malama ki tafi ke nake jira tana kallon gidan tace karka taba min jaka karma kace zaka taimakeni kace zaka daukar min jaka bana so karka soma bana so,cikin masifa shima yace Allah ya kiyaye na daukar miki jaka ki daina kallar min gida ki Kara gaba,Ina kaga gidan wannan gidan nasan komai yayanka ne ya siya maka Ina kaga kudin gina gida,ae naji jeki bana son ganinki,Aisha sabo da maita sai kallon gidan takeyi karshe cikin fushi da azama ta fisgi akwatinta zata fita sai suka ji ana Kwankwasa palonsu,juna suka kalla sai Suka ji muryar Babar Farooq tana cewa ko ba kowa ne? Farooq da sauri yace gani nan Muna nan,da sauri ya dauki akwatin Aisha yace maza koma ciki Umma ce,da gudu ta dauki akwatinta ta koma bedroom,Shi Kuma kofar ya bude Mata cike da ladabi ya furta Sannu da zuwa Umma,da fara'a tace yawwa Farooq Ina matar taka ne naji gidan shuru? Farooq yace tana nan aiki ma ta gama yanzu ai Yar Albarka ce akwaita da kwazo,Umma tace Kai Kam kayi dace ba irin Dan uwanka ba gashi Kuna zamanku lfy, Aisha ya kwalawa Kira ta fito harda saka katon Hijab har kasa ta gaida da Umma tace bari na kawo Miki ruwa,a'a barshi ma tafiya zanyi dan Allah ku zauna lafiya duk da nasan Kuna kokari ba a Jin kanku Kuna zamanku lafiya kowa ya sheda,Farooq yace to Mene amfanin mace da miji su dinga fada ai babu amfani,Aisha ma tace shi yasa Muka fahimci juna mu ko fada bama yi bama cacar baki,

Shima Farooq yace yanzu Umma ai ba a yayin fada mu bamu San ma ma'aurata suna fada ba sai dai muji labari a makwafta,Umma tace ai ni haka nake so Allah ya Kara zaunar daku lfy ta mike suna cewa ameen ta tafi,tana tafiya Suka gallawa juna harara,Farooq yace dalla daina kallona mutuniyar banza marar tarbiyya,Aisha tace tafiya zanyi gidan Ubana dama,Farooq yace ba inda Zaki je baki Isa ba na fasa barinki ki tafi kudi na biya na aureki,gidanku son abin duniyarku ya baci,tunda na fara neman aurenki ake rokata kudi,sannan Sadakin da akace na biya wajen aurenki iyayenki ai da tsada Suka sa min, ko ke lokacin da na fada Miki sai da kika tsorata,sannan ai caka min akayi cewa Kika yi ke virgin ce da nazo na shige ki wuuufff na wuce ciki ba abinda ya tareni sai kace rijiya haka na fada cikin ki,harda cewa virgin ce amma a haka na hakura na zauna dake sabo da haka ba inda Zaki je kina nan gidan,Aisha kuka ta saki tace wlh Farooq Allah sai ya saka min sharrin daka min ni zaka cewa ba virgin ba Allah Yana ganinka ta fashe da kuka me tsuma zuciya,Tsaki yaja ya koma Palo yace ba inda Zaki je Ina gidan Nan banza shashasha.

kwan....gwan...gwan taji ana uban buga Mata kofa,lemo ne a hannun na ina Sha uban kida na tashi,kofa na bude kyakyawan Matashin ne ya dauki wanka cikin kana Nan kaya farin Jean da riga sky cike da bala'i yace dalla malama kin cika Mana gida da kida ko ke kadai ce a gidan nan, da masifa nima kyakyawar budurwa dani nace ai kudin haya na biya Kai fa nasan sirrin komai baka biya kudin haya ba sai uban daukan wanka baka da sisi,Jin na fara tona Masa asiri yasan bai biya sisi ba yayi mukus ya juya gwiwarsa tayi sanyi ihu na Masa wooo yaji kunya ba uwar da ya sani Sai wanka shi a dole gaye na ja tsaki tare da komawa ciki,shi kuwa dakinsa ya koma ya Fara shiri Yana kallon Kansa a mudubi yace gaskiya na hadu zanyi cizo,ya dauki lokaci me tsawon gaske Yana kallon Kansa kafin ya fito Yana taku dai dai.

Lokacin nazo fita a motata ja me kyau ko kallona baiyi ba ya tako ya wuceni a bakin gate Yana Shirin barin gidan,glass na sauke a hankali cikin nutsuwa na furta dan Allah Affan taimaka ka bude min gate,kallona yayi shekeke da bala'i yace kin ga nifa ba sa'anki bane,Kawai Dan kin mallaki wannan banzar motar kina tunanin ke wata ishashiya ce me kike da shi wannan har mota ce Yana magana Yana dukan motar da hannunsa,stop insulting my car,mota hadaddiya zaka dinga zagi,Tsaki yaja yace kinci sa'a Ina da appointment fita zanyi da kin gane kurenki ya juya yaci gaba da tafiya da gadara,haka ka iya kullum kace kana da Appointment kuma har Yanzu bama gani a kasa kullum jiya iyau na furta ina Jan tsaki na Bude motata na fito tare da bude gate na fita Office

Affan gidan Abokinsa ya wuce Direct Mustapha Yana aiki a ministry of Environment,Shi kuwa Affan baya aikin komai sai dai buga buga idan ya samu ya siyi kayan daukan wanka kudin gidan haya ma a Estate din ya kasa biya duk lokaci in yazo sai anyi fada da shi,suna Palon Mustapha me kyau a zaune Mustapha yace me ya kawoka gidana ne nasan sai da dalili,Yace zuwa nayi ka ranta min dubu biyar bani da kudin abinci komai na kayan abinci na ya Kare, Mustapha yace dama na sani to gaskiya bani da kudi, Affan yace please ka taimaka min Kai fa abokina ne na gaske common 5k nasan baza ka rasa ba, Mustapha ba a son ransa ba yace ya zanyi da Kai kazo a abokina bai kamata nayi baboki irinka ba amma ya zanyi Zan baka 3k Amma ka tattabar ka biyani na gaji bashin da nake binka yayi yawa,Affan Yana murna yace karka damu muna tare fa sai lokacin Mustapha ya saki ransa suka ci gaba da labarin duniya.

Affan gida yazo da Niyyar shiga sai ga wani Mallam yasha babbar riga da rawani ya tsaida Affan yace Saurayi Innalillahi wa Innailayhirraju'un, masifa ta tunkaro ka,Mallam yaga Affan Kalar Naira ya dau wanka Kalar me kudi yace kana da makiya Alhaji wasu suna nan zasu sace maka mota,Affan ya bude baki yasan karya yake shi da baida mota,yace sannan makiyanka Yan uwanka ne sun Kai sunanka za a maka asiri kwana nan zaka rasa milliyoyin kudi a cikin dukiyarka,Affan ya sheke da dariya a ransa Shi da bai da ko sisi yanzu ma bashin dubu uku ya samo da kyar,a fili gigicewa yayi yace yanzu Mallam ya zanyi kenan? Me ya kamata ayi? Mallam farin ciki ya kamashi ya samu gara zai cuce shi,yace dubu dari zaka kawo ayi aiki me zafi a kansu,Farooq yace an gama bani Address din gidan naka yanzu banda kudi a hannuna,Nan take Mallam jiki na rawa yace ya bada address Affan ya wuce gida,Yana cikin palonsa dake estate din kowa bangarensa Palo da 2 Bedroom ne a hadadden Estate a haka ma Sai me kudi ko ma'aikata ke Kama gida a ciki da gate dinsu da komai kowa da part
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download AUREN MU

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album