Join Our WhatsApp Group

KISAN GILLA Complete Hausa Novel Document by KISAN GILLA


KISAN GILLA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 34420



KISAN GILLA

Reading Time: 2 Hours

Added On: 18, Jul 2023

Author: Abdulaziz Sani Madakin Gini ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 186.46 kb

File Type: txt

Views: 1161+

Download: 356+

Last download: 2 days ago

Description/Story: KISAN GILLA 1
Littafi na biyar
Na Abdulaziz sani madakin gini
Ebook creator:- Shuraih Usman 99%
Domin download na wasu kayatattun littatafan Hausa a matsayin Hausaebooks tayadda zaku iya saukewa ku karanta acikin wayoyinku sai ku ziyarci wannan shafi www.shuraih.waphall.com Sannan ku zabi littafin da kuke so

For more download of some non- fictional hausa books as a hausaebooks so that you can download it to your phone and read it at any time (offline reading) then visit our wepsite at www.shuraih.waphall.com Adress and select your books for offline reading
Gargadi:- wannan ebook din bana sai ruwa bane kuma ba anyishi bane don batanci ga wani koh ga wata
Sannan ni shuraih Usman 99% bana tura littafi ta private kuma bana whattsapp sannan banda group a whattsapp ga wanda yaga wani kuskure da muka making acikin wannan littafi sai kiramu akan wannan nombar 08170707521

Ga duk wanda baisan yadda ake downloading na littatafanmu ba sai ya ziyarce mu akan wannan adireshin yanar gizo gizon http://keffians.xtgem.com/forum Sannan yayi tambaya in sha'Allah muku ma zamu mai bayani dalla dalla akan yadda ake sauke littatafanmu
Sannan ina kara maimaitawa bana whattsap kada wani ya ha'ince ku ta hanyar amfani da sunana a whattsap asha karatu lafiya
Hakkin mallaka (m) Abdulaziz sani madakin gini

KISAN GILLA
Littafi na Daya (1)
Part A.
.
Marubucin Littafin
Abdul Aziz Sani M/Gini
Typing AA Misau
Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa...
MARUBUCIN YA RARA DA CEWA,
A wani zamani can baya mai tsawo da ya shude anyi
wani babban birni mai suna madinatul haswar
a cikin daular larabawa
birnin madinatul haswar ya bunkasa a kan karfin
arziki girman kasa, karfin mayaka da yawan al umma
sarkin dake mulkin birnin madinatul haswar ya kasance adali mai tausayi da jin kan
talakawa ana kiransa da suna HISHAM IBN UBAIDA
.
SARKI HISHAM yana da matar aure guda daya jal mai suna
shamilat wadda ta kasance yar wani babban sarki mai
mulkin wata kasa da ake kira da hushush ana kiran wannan
sarki da SAHIBUL HILAYAT
sai da sarki hisham ya auri shamilat da shekaru goma sha daya sannan Allah ya
albarkace su da samun juna biyu nan fa sarki hisham da shamilat suka cika da tsananin farin ciki
domin
a duniya basu da wani buri wanda yafi ganin sun sami haihuwa saboda a shekarun
baya babu abin da basuyi ba, domin su sami
haihuwar amma abu ya gagara,
lokacin da mahaifin
shamilat ya samu labarin cewa 'yarsa ta sami juna
biyu sai ya kamu da tsananin farin ciki fiye da ita
kanta shamilat din da mijinta saboda shi kuma bashi da burin da yafi yaga jikansa
kafin ajali ya riske shi kasancewar tsufa ya
riske shi
a ko yaushe ta Allah zata iya kasancewa
Al amin Ahmed Misau, Guyson nake magana,
bisa wannan dalili ne sarki sahibul hilayat ya
tashi manzanni da dukiya mai yawa ya aiko su izuwa ga sarki
hisham yace ga wannan ayi
renon ciki kuma idan haihuwa tazo daf yana son
shamilat ta je gida ta haihu, yayin da wannan sako ya isa ga
sarki hisham sai hankalinsa ya dugunzuma domin
baya son ya rabu da matarsa dai dai da dakika daya
amma kuma yana matukar jin nauyin surukin nasa don haka
sai ya amince da hakan ita kuwa shamilat sai ta kamu
da matukar farin ciki saboda a rayuwarta babu abinda
take so sama da ta kasance tare da mahaifinta a ko yaushe
saboda ita kadaice 'yarsa a duniya
sarki Hisham yana da dan uwa yarima ZAMARU wanda
ya kasance azzalumi kuma mara imani mai tsananin son duniya
uwa daya
uba daya suke dashi da hisham, a zahiri yarima zamaru
yana nuna cewa yana matukar kaunar dan uwansa
sarki hisham amma a karkashin zuciyarsa babu
abinda ya tsana sama da shi ba wani bane ya haddasa
wannan gaba ba a tsakaninsu face kawai hassada da
kyashi da kuma tsananin son KARAGAR MULKI
TUN mahaifin su sarki hisham na raye ya futa cewa hisham
ne zai gaje shi daga
wannan lokaci ne yarima zamaru yaji ya tsani
dan uwansa sarki hisham ya fara tunanin hanyar
da zaibi ya kawar dashi daga doron kasa sau bakwai
yarima zamaru yana bayar da kwangilar a kashe
hisham amma yana kubuta kasancewarsa sadauki mai
dakawa maza gumba a hannu
Guyson nake magana Al amin Kenan
Lokacin da yarima zamaru yaga ya kasa ganin bayan
sarki Hisham sai ya
zuba ido izuwa lokacin da tsufa zasu riskeshi har
rai yayi halinsa
saboda ya tabbatar da cewa indai babu sarki hisham
dole shine zai hau karagar mulki, ana cikin wannan hali ne
na jiran lokaci kwatsam sai shamilat ta sami juna biyu
hm Al amarin da ya kara dugunzuma hankalin yarima zamaru kenan saboda ya
san cewa idan matar hisham ta haihu to fa
sarautar ta kara yi masa nisa, a ranar da zamaru ya sami labarin cewa shamilat
ta samu juna biyu sai ya kasa zaune ya kasa tsaye
har dare ya raba bai rintsa ba
Babban abinda ya kara jefa
shi cikin bakin ciki shine shima matarsa ba ta taba
haihuwa ba don haka duk ranar da ya mutu shi
kenan bashi da magajin mulki, cikin tsakar dare yarima
zamaru na kai kawo a cikin turakarsa ya kasa barci sai matarsa sarima ta farka
daga barci koda taganshi a tsaye yana kai kawo saita dube shi
cikin tsananin damuwa ta mike da sauri tasha gabansa
tana mai rike kafadunsa, tace yakai mijina menene
ya tayar maka da hankali a yau har ka kasa bacci?
Koda jin wannan tambaya sai yarima zamaru ya yi ajiyar zuciya sannan yace
baki da labarin cewa matar sarki ta samu juna biyu ne?
Sarina tayi ajiyar zuciya tace haba maigida yanzu
a kan haka ne ka tayar da hankalinka har ka kasa bacci koda jin haka
sai zamaru ya rufe sarina da fada yana cewa bata da
hankali bata da kishin rayuwarta,
sarina ta bushe da dariya sannan ta ce ka kwantar da hankalinka mijina ina so ka
sani cewa ni na san abinda ba ka sani ba idan har kana so ka san abinda na sani yanzu ka
tashi mu tafi izuwa can bayan gari wajan wani bakon boka da yazo
cikin alamun karayar zuciya yarima
zamaru ya dubi sarina yace ke nifa na gaji da maganganun bokayan nan
tunda an dade ana ruwa kasa na tsotsewa kuma na gaji da gafara sa har
yanzu banga kaho ba
Guyson nake magana, sarina tayi murmushi tace aiko bokaye
suna suka tara wannan bokan ya wuce yadda duk kake
tsammani duk wani bayani da zan yi maka ba zaka
gamsu ba don haka gani ya kori ji kawai kazo muje wajansa
yanzu a cikin wannan daren cikin sirri
koda jin wannan batu sai yarima zamaru ya cika
da farin ciki kawai sai ya mike zumbur ya kama shiri
yayi badda kama itama sarina yasa ta ta batar da kamanninta sannan sukayi
hawa suka fice daga cikin birnin madinatul haswar a sirrance ba tare da kowa ya shaida su ba
sai da suka yi tafiyar kusan rabin
Sa a sannan suka iso gaban wani katon dutse
wanda a kansa akwai wata yar karamar bukka
abinda ya daurewa yarima zamaru kai shine ganin matattakalar bene a kan dutsen tamkar sassake dutsen akayi
aka samar da ita shi dai
zamaru ya san wannan dutse sama da shekaru
talatin baya amma bai taba ganin wannan matattakala
a jikinsa
ba tabbas wannan matattakala aikin aljanu ne
bana mutum ba abinda zamaru ya ayyana kenan a cikin
zuciyarsa
bayan zamaru da sarina sun tsaida dokunansu a gaban dutsen sun sauka
sai suka daure dawakan nasu a jikin wata bishiya sannan suka taka
wannan matattakala suka hau kan dutsen
suna isa gaban wannan bukka sai sukaga bokan tsulum ya
bayyana a gabansu yana kyakyata dariya al amarin da ya dan razana yarima zamaru
kenan ya dan ja da baya kadan , shi dai wannan boka
ya kasance dogon mutum garjeje mai kirar mutanan
farko jikinsa gaba daya a murde yake alamar
karfi ta bayyana karara a tare da shi yana da yar
faffadar fuska kyakkyawa cike da kasumba da gajeran gemu
babu riga a jikinsa face wata fatar damisa
wacce ya yafata bisa kirjinsa ta zagayo izuwa bayansa
daga cikinsa zuwa gwiwoyinsa a rufe suke
da bante irin na fatar damisar da ya yafa kuma
takalmin dake kafarsa ma anyi shine da wannan fatar damisa
gaba dayan damatsansa na hagu dana dama a cike
suke da gurayen tsafi , tabbas wannan boka yana da kwarjini da cika ido kai da
ganinsa kasan cewa murucin kan dutse ne wato bai fito ba
sai da ya shirya
bokan ya dubi yarima zamaru yayi murmushi yace
kada kaji tsoro ya shugabana ni mai taimako ne a gareka
ko ince zamu yiwa juna taimako ku biyoni
izuwa cikin bukkata mu zauna domin mu tattauna sosai
koda gama fadin haka sai bokan ya juya ya shiga
cikin bukkar nan take yarima zamaru da sarina
suka bishi a baya ba tare da fargabar komai ba
da shigarsu cikin bukkar sai yarima zamaru ya sake cika
da tsananin mamaki domin kansa ne ma ya kusan juyewa
saboda ya tsinci kansa ne a cikin wata makekiyar fada wacce
ta kawatu ainun ninkin
fadar sarki hisham sau uku wadansu kuyangin aljanu sunata hidima da kai kawo
bokan yaci gaba da tafiya a tsakiyar fadar ya nufi inda karagar mulki take
su zamaru na biye dashi amma basu isa inda karagar mulkin take ba sai
da suka yi taku dari da arba in, da zuwa sai bokan ya zauna akan karagar mulki yarima zamaru da sarina kuwa sai kuyangin aljanun
suka kama hannayansu suka kaisu izuwa kan wadansu
kujeru dake daf da karagar mulkin suka zaunar
dasu
nan da nan aka kawowa yarima zamaru da sarina
ruwan inibi a cikin tambulan na zinare da
kofuna suka fara jika makoshinsu a sannan ne bokan ya dubi yarima zamaru a karo na biyu yace lale maraba
da yarima zamaru dan uwan hisham sarkin gobe
Al amin Ahmed Misau
Guyson Sunana Kenan
koda jin wannan batu zamaru ya natsu sosai
bokan ya ci gaba da bayani yana mai cewa
ka kwantar da hankalinka ya kai wannan dan sarki
kayi sani cewa matarka tazo nan kafin kai kuma
mune mukace ta kawo ka
mun san duk abin dake damunka da kuma burin dake
zuciyarka
tabbas mune zamu magance maka dukkan matsalarka muddin muma zaka bi umarnin
mu shin ka amince da wannan sharadi?
Koda jin wannan batu sai yarima zamaru ya dubi bokan cikin alamun rashin
fahimta sannan yace menene sharadin da kake so ka gindaya mun
bokan yayi murmushi yace ina so ka dauki
alkawari cewar idan bukata ta biya zaka raba birninka
biyu ka bani kaso guda na mallakeshi haka kuma zaka bani rabin dukkan
dukiyarka
lokacin da yarima zamaru yaji wannan batu sai
hankalinsa ya dugunzuma ainun ya rasa abin dake masa dadi yayi shiru yana tunani
bokan ya tuntsure da dariya alamun da ya janyo katsewar
tunanin yarima zamaru kenan ya dago kai a
firgice
ya dubeshi yace ni ne Hizainu ibin Markasi masanin sirrin gobe,
yakai wannan dan sarki ina so ka sani cewa babu wani
abu da mutum ke samu a saukake kuma a banza face
ya rasa wani abu
ina mai shawartarka daka dauki sharadina ni kuma na
taimaka maka na sanar dakai duk abinda zaka yi ka
samu biyan bukatarka kuma
yanzu ne kadai damarka
idan ka bari wannan dama ta wuce ka har abada ba zaka samu wata ba
sa adda yarima zamaru jai wannan batu sai ya kawo gwauron numfashi ya ajiye gami da ajiyar zuciya ya sake yin dan guntun tunani
sannan ya dubi boka
hizainu yace na yarda idan ka taimakeni burina ya cika zan raba mulkina da dukiyata
gida biyu na baka rabi amma bisa shardi guda
sharadin kuwa shine sai dai kayi rantsuwa da girman
tsafi da kuma darajar iyayenka cewar a gaba ba zaka yi yunkurin
rabani da mulkina ba
domin ka mallaki kasar gaba daya kuma ba zaka taba cutar
dani ba ko wani nawa
koda jin wannan batu
sai idanun boka hizainu suka zazzaro ya kamu da tsananin
mamaki saboda bai taba zaton cewa yarima
zamaru zai daureshi ba da jijiyarsa haka, al amarin da ya jefa
shi cikin shakku da wasu wasi kenan ya kama muzurai yana
kallon kuyanginsa dake kai kawo a cikin fadar suna hidama
sai da yayi dan tunani da nazari sannan ya bushe da dariya
nan take yayi rantsuwa da girman tsafi gami da darajar iyayansa bisa kan cewa ba zai taba neman
wani abuba daban a wajan yarima
Zamaru a nan gaba kuma ba zai cutar dashi ba koda jin haka
sai farin ciki
ya lullube yarima zamaru yace shima ya amince da bukatar
boka hizaunu
boka hizainu ya kyalkyala da dariyar murna yace
gobe da safe idan kaje fada zaka iske dan uwanka sarki hisha,
a kwance cikin cutar ajali kuma ba zai wuce kwana bakwai ba a kwance rai zaiyi halinsa
abu na biyu da nake so dakai shine a yanzu haka
matar sarki hisham ta haifi da namiji kuma har ta
gama wankan jego ta baro can birnin
darul hushush ta taho izuwa nan birnin madinatul
haswar tare da jaririnta da kuma dakaru dubu biyar masu tsaron
lafiyarta
wadanda suka kasance zakwakuran mayaka fasa taro lallai ka shirya
wadansu zakwakuran dakarun da suka fisu
jarumtaka wadanda zasu je su yake su su kashe matar
sarki ya zamana cewa baka da wata barazana a mulkinka ina mai
tabbatar maka da cewa a daren da dan uwanka sarki hisham
zai mutu ne shamilat da jaririnta
zasu iso cikin garin nan
don haka duk yadda zakuyi kusa a tare su a can cikin daji
kafin su iso kusa da wuri, kuma kada ka kuskura ka shiga
cikin mayakan da zasu je yin wannan aiki kuma ka
tabbatar da cewar anyi wannan aiki a cikin sirri
ba tare da wani ya sani ba lokacin da yarima zamaru
yaji wannan batu sai hankalinsa ya kara dugunzuma fiye da ko yaushe ma ya dubi boka hizainu cikin alamun tsananin
tsoro da damuwa yace yakai wannan boka mai daraja
yanzu a ina zan samo dakarun da zasu iya kashe
dakarun da sarki sahibul hilayat masu yiwa shamilat da
jaririnta rakiya izuwa nan birninmu? Ka sani
cewa dakarun birnin darul hushush mayaka ne na asali kada su ba wasa bane
boka hizainu ya sake bushewa da dariya lokaci guda
kuma ya turbune fuskarsa yace babu wanda zai iya
yi maka wannan aiki face sarkin yakinka amzadu ibn karlyas
koda jin haka sai yarima zamaru ya cika da tsananin mamaki gami da tsoro yace
to yaya amzadu zai amince yayi min wannan aiki alhalin kasan cewa ya kasance
babban aminin sarki hisham wanda a shirye yake ya
sallama rayuwarsa domin kare ta sarki da iyalansa
koda jin haka sai boka hizainu ya sake bushewa da dariya
sannan yace
da zarar sarki hisham ya mutu kaine sarki komai
ya dawo karkashin ikonka da mulkinka
a wannan lokaci kana da ikon sarrafa komai da kowa da karfin karagarka
a daren da sarki
hisham ya mutu ka tura akamo sarkin yaki amzadu da iyalansa a matsayin kana zarginsa
da laifin sawa sarki wannan ciwon ajali tunda kowa ya
san cewa dare da rana yana tare da sarkin
bayan an tsare su a kurkuku shida iyalan nasa sai
kasa a fito dashi shi kadai azo dashi har cikin
turakarka ka kadaita dashi a sannan ne zaka gaya masa
bukatarka ta son ya
debi zakwakuran yaransa suyi
bada da kama suje su kashe matar sarki shamilat da jaririnta
da duk dakarun da sukayi musu rakiya
izuwa nan birnin madinatul hashwar idan
kuma yaki koyayi wani abu ba dai dai ba sabanin umarnin da ka bashi
zakasa a kashe iyalansa idan kuma yayi aikin daidai
bisa nasara zaka bashi babban matsayi a fadarka fiye
da wanda yake da shi a yanzu...
.
Nan zan dan dakata Dafatan Littafin ya kayatar daku
comment da like saimu cigaba
kafin nan
Nidinne Al amin Ahmed Misau
Guyson sunana Kenan Daga
Zauran Labarai NakeKISAN GILLA
Littafi Na Daya (1)
Part B.
.
.
Marubucin Littafin
Abdul Aziz Sani M/Gini
Typing AA Misau
Ke Magana
.
Labari ya isowa AA Misau cewa...
Fiye da wanda yake dashi a yanzu.
lokacin da boka hizaunu yazo nan a zancensa
sai yarima zamaru ya kamu da tsananin farin ciki
nan take ya kama kyalkyala dariya saboda murna sannan ya dubi...


Read / Download KISAN GILLA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

4 Comments On KISAN GILLA
avatar
daiy

10 months ago

Reply

Good

avatar
ibrahim-9-5

6 months ago

Reply

Nice thanks a lot

avatar
taskar

6 months ago

Reply

Replying to ibrahim-9-5

Aha thanks for feedback keep following our site and enjoying our new hot hausa novels

avatar
kabir-mariya

6 months ago

Reply

Tnx alot

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album