Join Our WhatsApp Group

BAKIN ARTABU BOOK 2 Complete Hausa Novel Document by BAKIN ARTABU BOOK 2


BAKIN ARTABU BOOK 2

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 7788



BAKIN ARTABU BOOK 2

Reading Time: 0 Hours

Added On: 17, Feb 2024

Author: Abdulaziz Sani Madakin Gini ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Adventure novels

File Size: 42.56 kb

File Type: txt

Views: 435+

Download: 118+

Last download: 3 days ago

Description/Story: ***★BAKIN ARTABU**cigaban
**JARUMA*YAZILA★***
Littafi Na Biyu {2}
TYPE A
***Nasiru**Muhammad**Tijjani***
Marubucin ya cigaba da cewa:
==============================
=============================
KOFAR birnin misra ta cika ta batse da dakarun yaki, babu masakar tsinke. Amma gaba dayan mayakan adadinsu bai wuce dubu dari uku da ashirinba.
Tsaye a gaban rundunar masu jagorantarsu mutun ukune. Na farko shine sarki Raihan, na biyu kuwa JARUMA YAZILA, sai kuma JARuMA DABIRA.
Yazila da dabira sun yi shigar yaki ne iri daya kuma duk sun sanya kayan karfe, kowannensu ya rufe jikinsa ruf! Baka isa ka gane cewa sun kasance mata ba saboda sun rufe kansu da hular karfe sun boye gashin kansu.
Shikuwa sarki raihan shigar bakin sulke yayi, kuma takalminsa ma bakine na kafa. Hatta kufen takobinsa da garkuwarsa duk bakake ne.
Kwatsam! Sai aka jiyo bugun tambura da ganguna yana tashi daga sama. Nan da nan sautin ya cika dodon kunne, kai kace makadan duniya ne suka taru suke buduri.
Lokacin da tawagar mayakan ta matso kusa kuwa aka ga yawansu sai kowa ya firgice, aka razana ainun, saboda yawansu ya ninka na mayakan birnin misra sau dubu.
Kura ta tshi ta turnuke sama, karar kofatun dawakai da haniniyarsu ta cika dodon kunne.
Kai! Komai jarumtakar mutun idan ya hango wannan runduna ta susarki DAKSUR dole ne ya firgita ya yi zaton ma yakin duniya ne ya barke.
Bisa mamaki sai rumdunar su sarki daksur suka ga kokadan abokan fadan nasu basu razana da ganinsu ba. Maimakon masu firgice ko su dimauce sai suka kara nutsuwa kuma kowa ya tsaya a inda yake, jira kawai yake yaji umarnin daza a bashi.
Bawani abubane yasa basu razanaba face addu'ar da suke ta. Faman karan tawa acikin zukatansu gami da neman taimakon allah.
Lokacin da su sarki Daksur suka hango abokan gamansu suka gansu 'yan kadan a gabansu tamkar a ajiye dan tsako a gaban shirwa. Kuma suka ga kokadan basu firgitaba, sai al'amarin yayi matukar basu mamaki, ya zamana cewa allah ya juya tsoro da shakku a zukatansu.
In ka dauke mutum uku da suke dasuke jagoran tarsu, gaba daya sauran mayakan duk sai tsoro ya darsu a cikin zuciyarsu harma suka sauka fara nokewa abaya kadan-kadan kawai jira suke yi suga yadda zata fara wakana ga manyan jarumansu a baban dogaronsu.
Sarki Uhaisu ne akan gaba, yana tafiya kai tsaye ba tare da shakkar komaiba , har maji yake kamar ya sauka daga kan dokinsa ya ruga da gudu izuwa cikin abokan gaba ya hausu da sara da suka saboda zakuwa da dakewar zuciya irin ta JARUMAN KWARAI.
A hannun daman sarki Uhaisu, sarki Daksurne. A hagunsa kuma sarkin yakine.
Lokacin da ya rage saura baifi taku arba'inba tsakanin rundunadunonin biyu sai rundunar su sarki daksur suka yi tirjiya aka fara kallon-kallo.
Sai da kura ta lafa sannan aka fara ganin juna sosai. Sarki daksur da sarki Raihan suka kurawa juna ido jaruma dabira da sarki uhaisu ma suka zubawa juna idanu. Ita kuwa yazila ta kurawa sarkin yaki idanu.
Jaruman shida suka kama tsuma ya zamana cewa kowannensu ji yake kamar ya zabura ya afkawa abokan gabarsa.
Da yake rundunar tazo kusa sai yazamana cewa babu bangaren da yake tunanin yayi amfani da mayakansa masa kibiya. Nan take sarkin yaki ya fara baiwa 'yan kasansa masu mashi da garkuwa umarnin su fara kai hari.
Ai kuwa sai suka hau kan sawun gaba, kowannensu ya saita mashinsa yana mai fuskantar a bokan gaba koda ganin haka sai shama sarki raihan ya baiwa nasa mayakan kasan umarnin su fito gaban filin daga wadanda adadinsu ai wuce su dubu arba in ba. Su kuwa dakarun arnan. Yan kasa adadinsu ya kai kusan dubu dari biyu da hamsim lokacin guda aka baiwa kowanne bangare umarnin su afkawa juna aikuwa sai kowanne banagare suka rugo da gudu suna kartar kasa kafirai suna ihu. Musulmi suna kabbara. Ahaka aka kacame da mummuna azababen yaki aka fara sokaiya da bugegeniya sai aka ga masu na fasa kirazan maza. Jini na tsartuwa da fallatsi. Mazaje na zubewa kasa suna zama gawa kai kace sassabe ake yi a gona. Sai da aka shafe sa a daya da rabi ana wannan bakin artabu sai gashi gaba dayan dakarun sun zama gawa. Dayansu bai tsira da raiba. Al amarin dai ya matukar dugunzuma hankalin kafirai ke nan suka cika da tsananin mamakin yadda aka yi wadannan kalilan din musulmin suka yi ragas da dakarunsu na kafirai wadanda suka nin kasu sau biyar a yawa? Koda sarki uhairu yaga wannan abu daya faru sai ransa ya baci zuciyarsa tafara tafarfasa kamar zata kone nan take ya zare takobinsa ya dagata sama ai kuwa sai sarki daksur da sarkin yaki ma suka zare nasu takobin. Koda ganin haka sai sarki raihan dabira da yazila ma suka zare nasu takubban. Kamar hadin baki sai kowanne runduna ta zabura ta durfafi abokiyar gabarta. Wohoho! Masifa idan ta zo babu makawa saita afku. Saboda tsananin karfin takun sawun mutane da dawakai sai da suka haddasa girgiza kasa a wannan wuri tamkar zata ta rufta. Kururuwar maza kuwa da haniniyar dawakai ta yawaita ainun har kai cewa da yawan mayakan sun firgice tun gabannin a hadu a fara gumurzu. Ai kuwa ana haduwa aka kacema da azabebban bakin artabu mai tsanani firgitawa daban tsoro nan fa aka bude kasuwar daukar rayuka. Sai gashi sassan jikin bil adama na shawagi asama tamkar ruwan samansu akeyi ji kuwa ya rinka fantsama yana malala akas kai kace teku ce ta balle. Babu abin da zai baiwa mutun mamaki face yadda arna ke ihu aya yin da suke mutuwa. Sannan kuma babu abin da zai baiwa mutun sha awa yajefashi cikin farin ciki face yadda musulmai suke kabbabra aya yin da mutuwarsu tazo duk sa adda sarki uhaisu sarki daksur dasu sarkin yaki suka kutsa cikin dakarun musulmai sai dai ka ga mazaje na zubewa kasa suna yin shahada. Haka ma a bangaren musulmai duk sa adda yazila dabira da sarki raihan ma suka kutsa cikin arna saidai kaga kamar sassabe sukeyi agona.
Komai lurar mutun bai isa ya gane bangaren da kke samun nasara ba. Wani babban abin mamaki shine babu yadda su sarki Daksur basu yi ba don su hadu da su sarki raihan ba amma ya gagara saboda yawan turmutsutsu da cakudewa gami da rudewar mazaje.
Sai da aka shafe sa'a uku da rabi ana wannan masifaffen yaki a sannan ne kowanne kowanne bangare ya gane kurensa domin an gane cewa babu bangaren daya samu rinjaye don gawarwakin kowanne bangare sun yawaita a kas.
Koda sarki Uhaisu ya lura da cewa ya kasa gane abin da ke faruwa a filin yakin sai ya fisge wani kaho da ke hannun wani badakare nasu ya busashi.
Nan take yaki ya tsaya kowanne bangare suka ja da baya. A sannan ne aka tsaya ana kallon-kallo. Nan take su sarki Daksur suka cika da tsananin mamaki bisa yadda kalilan mutane suka yi Ragas da mutanensu. Al'amarin daya matukar kona zukatansu ke nan aka sake yin cirko-cirko ana kallon juna. Nan take sarki Uhaisu ya nuna yazila da tsinin takobinsa yana mai nuni da cewar da ita yake son karawa yanzu.
Sarki daksur yai nuni izuwa ga sarki Raihan. Shi kuwa sarkin yaki yai nuni izuwa Dabira. Ba tare da sanin ko da wa zai gwabza ba.
Abinda suka sani kawai shine wadannan mayaka guda biyu wadanda suka saanya kayan yaki iri daya kuma suka rufe fuskokinsu da hular karfe, ba wasu bane face JARUMA YAZILA da DABIRA.
Da gudu. Aikuwa suna a tsakiya suka rufe junansu da sara da suka cikin tsananin zafin nama juriya da bajinta.
Tun kafin yazila ta fara gumurzu da sarki uhaisu tayi ta karanta wata addu a ta musamman a cikin zuciyarta. Bisa mamaki kuwa sai taji ta sami wani irin gagarumin karfi ya shiga jikinta irin wanda bata taba jinsa ba gami da azababban zafin nama na gaban kwatance. Aikuwa sai gashi ta zamewa sarki uhaisu alakakai ya rasa yadda zai yi da ita ya zamana cewa karfi yazo daya. Al amarin daya matukar baiwa sarki uhaisu mamaki ke nan. Domin shi a saninsa bai taba haduwa da jarumin dazo daya ba sai wannan karon.
Babban abin bakin ciki ma shine. Sarki daksur yayi masa bayanin cewa lallai da mace yake yaki. Kuma ba zai wuce jaruma yazila ko dabira ba.
Lokacin da sarki uhaisu yaga ya mace na neman bashi kunya sai zuciyarsa ta kufulo ta kama tafarfasa kamar zata kone don haka sai ya kara zage dantse iya karfinsa yaci gaba da kai mata wawan sara da suka cikin sauya salo al amarin da janyo ta rude kenan ta daina cigaba da karanta addu ar dake bakinta. Aikuwa damar da uahisu ya samu ke nan ya yai mata wani wawan duka da hannunsa cikin shammata a fuska saboda karfin dukan saida jini ya fetso daga cikin bakinta tamkar an yi wurgi da takarda haka ta fado daga kan dokin ta baje a kasa cikin matukar galabaice koda ganin haka sai sarki uhaisu ya dako tsalle daga inda yake tsinin takobinsa na kallon kas da nufin ya tsire cikin yazila. Duk da cewa yazila tana cikin wani mugun hali idanunta na gani dishi dishi. Koda ta hango sarki uhaisu yana shirin tsire mata ciki sai kwallah kabbara da karfi ta kaucewa harin nasa cikin matukar zafin nama. Take tsinin takobin tasa ta chaki kasa ta lume cikin kasar kafin yazare takobin tayi wuf ta mike tsaye zumbur kamar sifirin kawai sai ta daka tsalle sama ta doki kirjinsa sau uku. Yayi taga taga da baya kamar zai kife kasa amma sai ya cije saboda jarumta da juriya irin tasa ya tsaya cak yana kallon cikin tsananin mamaki domin itace bil adama ta farko wacce ta sami nasarar iya taba jikinsa haka.
A dai-dai wannan lokacinne abokan gaba suka yanyame jaruma yazila zasu hallakata. Ai kuwa sai ta tarwatsasu duk inda takai sara ko suka sai dai kaga ana zubewa kasa tana samarwa kanta hanya da karfin tsiya tana durfafar inda sarki Uhaisu ke tsaye.
A haka ta samu ta karaso inda yake suka sake ruguntsumewa da sabon masifaffen yaki.
Koda Uhaisu yaga cewa lallai karfi yazo daya shi da abokiyar gwaminsa sai ya sake shammatarta ya doki hannunta mai rike da takobin. Takobin tayi tsalle sama sai yazila ta daka tsalle sama domin ta cafo takobinsa shima sai ya daka tsalle saman ya doki kafafunta da kafarsa guda.
Nan take yazila ta rikito kasa arude kuma a hargitse, kanta na buguwa da kasa sai hular karfen ta ta cire, kyakkyawar fuskarta ta baiyana a fili karara.
Har sarki uhaisu yaji ya kamu da tsananin son jaruma yazila, don haka sai ya mike tsaye daga durkushen da yake yaja da baya a lokacin da suka fara kallon-kallo tsakaninta da shi tana mamakin abinda yasa ya fasa kasheta. Itama a lokacin ne ta lura da irin tsananin kyawunsa da kyawun surar halittarsa. Bisa mamaki sai itama taji ta kasa afka masa suci gaba da yaki.
A can bangaren jaruma dabira da sarkin yaki kuwa, labari ya shabanban domin kwarmazuwa suke yi har ta kai cewa kowannensu ya yiwa dan uwansa rauni sau biyu. Ita ta yankeshi a damtsensa na hannun dama da kuma gefen kirjinsa jini na zuba amma ko gezau bai yiba. Shikuma ya yanketa a gadon bayanta da cinyarta ta hagu gashi itama jini na diga amma bata sare ba sai dada fafatawa suke.
A bangaren sarki raihan da sarki daksur kuwa al'amarin ba kyangani domin nema suke yi su yi RAGAS saboda kowannensu ya yiwa dan uwansa rauni sama da guda biyar, duk jikinsu yai fata-fata da jini, har ta kai cewa suna layi, jiri na dibansu, suna layi kamar za su bingire kasa.
A na cikin wannan hali ne kawai aka ji an busa kahon tsayar da yaki. Faruwar hakan keda wuya sai sarki Uhaisu yaruga izuwa inda dokinsa yake yai tsalle ya haye kansa sannan ya zabureshi da gudu ya nufi can baya inda sansanin su na yaki yake amma yana juyowa yana waigen jaruma yazila alokacin da itama ta bishi da kallo kawai.
Sarki raihan da sarki Daksur kuwa, sai suka yanke jiki suka fadi kasa sumammu.
Dabira da sarkin yaki kuwa, suka ja da baya suna kallon juna cikin cizan yatsa da tsananin ta kaici domin ba haka suka soba.
A binda suka so shine a barsu su fidda raini ya zamana cewa daya ya kar daya. A guje kowanne bangare suka rugo suka dauke sarkinsu.
Nan take kafirai suka kwashe gawarwakin mutanensu da marasa lafiyarsu suka koma da baya izuwa can sansanin nasu sukuwa musulmi sai suka kwashe jama'arsu da dukkan kayayyakin nasu suka koma cikin birnin misra aka mayar da kofar birnin aka rufe.
A guje aka tafi da sarki raihan a cikin keken doki izuwa gidan sarauta. Jaruma yazila da dabira na biye da shi hankalinsu a dugunzume bisa ganin halin da yake ciki ko kadan ma basu damu da raunikan dake jikinsuba.
Cikin hanzari aka shigar da sarki cikin turakarsa aka kwantar da shi akan gado. Nan da nan aka kirawo likitan sarki yashiga aikinsa. Ai kuwa ba a dadeba sai sarki ya farfado ya dawo cikin haiyacinsa.
Yana bude idanuwansa yayi arba da Humaira tsaye akansa tana zubar da hawaye, dabira mana tsaye kusa da ita tana kuka, sai kuma Yazila a can gefe daya ta kura musu idanu cike da kwalla.
Bisa mamaki sai suka ga sarki raihan ya dubesu cikin matukar mamaki, kawai sai ya yunkura ya mike zaune yana mai cewa, "mu yiwa allah godiya daya bamu nasara akan makiya".
Koda jin haka sai mamaki ya dada kamasu. Dabira ta matso dab da shi ta zauna akan gefen gadon ta dubeshi tace, "haba ya abbana saboda me zaka ce mun sami nasara alhalin bamu kashe manyan shugabannin abokan gababa , kuma bamu kai tutarsu kasba? Ai burina shine mu ragargazasu kuma mu cafkesu a matsayin bayi sannan mu kwashe dukiyoyinsu a matsayin ganima kuma muje har can birninsu mu kafa tutar musulunci".
Lokacin da Dabira tazo nan a zancenta sai sarki Raihan ya sake yin murmushi a karo na biyu yace, "ai abinda da nake nufi da mun sami nasara shine, basu cimu da yaki ba. Duk da cewa sun ninkamu ninkin-ba-ninkin a yawa kuma mun yi matukar basu mamaki da tsoro domin basu taba tsammanin cewa hakan yakin zai kasance ba. Kuna ganin dai da kansu suka busa kahon tsayar da yakin suka ja da baya. Babban abin daya kara faranta min rai shine, wannan bakon jarumin da suka zo da shi bawani bane face sarki Uhaisu sadaukin da babu wani mayaki da ya kaishi jarumtaka da sa'ar yaki kamarsa, amma sai gashi ya kasa karar damu kuma a karshe ma sai na ga jikinsa yayi sanyi, haka kawai ya janye yakin ya ruga da gudu ya hau dokinsa ya bar filin dagar.
Ko shakka bana yi addu'ace ta kwacemu a wannan yaki, amma ba dabarar muba ko iya yakinmu ko jarumtakarmu. Yanzu abinda nake so daku shine, kuje ku yiwa jikinku magani sannan kowa...


Read / Download BAKIN ARTABU BOOK 2

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album