Subscribe for N1000/month for downloading access and an ad-free site. Contact WhatsApp +2348140419490 if you can't pay / subscribe. SUBSCRIBE

24 yin

LAUNIN FATA Complete Hausa Novel Document by LAUNIN FATA


LAUNIN FATA

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 52946



LAUNIN FATA

Reading Time: 4 Hours

Added On: 08, Sep 2023

Author: Rabi'atu Abubakar Nasidi ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Love Novels

File Size: 267.48 kb

File Type: txt

Views: 1049+

Download: 813+

Last download: 4 days ago

Description/Story: LAUNIN FATA
Littafi na daya 1
Rabi'atu Abubakar Nasidi
Ebook creator:- Shuraih Usman
@http://fb.com/hausaebooks


Showing posts filed under Launin Fata
Launin Fata 1-01
Posted by ANaM Dorayi on 10:04 AM, 03-Oct-15
Tare da Alkalim
Rabi'at Abubakar Nasidi
Fatan zaku karance da Dan
Uwaku ANaM Dorayi
Falon ya yi tsit gaba daya iyalan gidan na ciki
kowanne kansa a kasa suna sauraron abinda zai
ci gaba da biyo bayan bambamin da dattijo sir
Abdulkareem baba ke zazzagawa diyarsa
Rabi'atul Badawiyya wadda ke durkushe a
gabansa rungume da yarinyar goye da bata
wuce watanni goma ba a duniya. Ya ci gaba da
fadin na taraku ne a nan don ku zama shaida
kamar yadda na taraku a baya kuka zama
shaida a kan abinda na gayawa Rabi ko ba ayi
haka ba? Sai da ya maimaita tambayar babban
cikinsu Rufa'i ya ce an yi haka Abba, duk da
haka muna baka hakuri..... Ya daka mai tsawa
tunda ka tabbatar mini an yi haka bani bukatar
a bani wani hakuri dole a yi abinda na ce. Kar bi
wannan bakar 'yar da ta zo mana da ita ta
rakaka har inda ta yi auran ta mayar musu da
'yarsu. In ba haka ba wannan bata zama min
gida. Ya juya har ya kai bakin kofa ya dawo ya
ce kar in dawo in samu yar nan a gidan nan ran
kowa zai iya baci idan ba a yi abin da na ce ba
a kiyaye. Yana fita Rabi ta dora hannu aka ta
fashe da kuka ta ce ni na shiga uku, yaushe
zanji dadi ne a duniya. Yarinya yar watanni
goma za a kai gidan daba a kaunata ni kaina
ake ba? Gidan da wahalarsa ta sa na fito ba dan
bana son mijina ba. Wacce irin rayuwa za ta yi a
gidan wannan yar. Ko shakka babu ba zan bada
yata ba a kai ta gara in hakura da zaman gidan
nan. Mahaifiyarta ta taso cikin tausayawa ta ce
Rabi rayuwa fa Allah ce duk wanda Allah ya
nufa zai rayu babu wanda ya isa ya hanashi
rayuwa. Ke ko duk duniyar nan zata hadu a kan
bata son rayuwar wani idan Allah ya nufa
rayayye ne zai rayu. Ci gaba da kafiya ga
mahaifinki abu ne da zai ci gaba da kawo illa ga
rayuwarki ba zai bari ki samu nutsuwa da
walwala ba. Idan kika yi hakuri Allah ya ji kanta
ya kaita hannu na gari ki tuna rayuwarki ba
itace rayuwar wannan yarinya ba, idan kin dage
sai kin rayu da ita sai Allah ya karbi rayuwar taki
ta kuma ta na raye tunda rayuwar ta Allah ce
rai da yake jikin mutum kayan aro ne, duk
wanda wa'adi ya cika mai shi zai karbi abinsa
ne kiyi yaya.Rabi ta kalli diyar ta nono na
bakinta, baiwar Allah bata san abin da ake yi ba
tana barci ta dagata ta rungume kam kam tana
kukan da ya baiwa kowa tausayi ta ce nabila zan
bada ke ba dan raina ya so ba sai dan babu
yanda zanyi ina fatan Allah ya kaiki hannu
nagari wanda zai tausaya miki dangin babanki
basa kaunata na san kema ba zasu kaunaceki
ba amma na san rayuwa ta Allah ce.wannan
jarrabawa ce wata rana lbr zata zama, domin
babu wani abu da ya taba dawwama dadi ko
wahala.
A hankali ta maida ita cikin zanin goyonta ta
mikawa yayanta Rufa'i ya karba ya rungumeta a
jikinsa a sanyaye.
Ya ce ki yi hakuri Rabi dole ne komai girman da
uwa bata son rabuwa ballantana yarjaririya
kamar wannan.
Allah yana sane da halin da kike ciki shi ne mai
magani zai miki magani kin sani babu yadda za
mu yi da maganar Abba in banda haka ba mai
rabaki da yarki a yanzu.
Ta zaro yan kayan nabila daga cikin nata ta kulle
a leda ta dauko wata yar sarka ta azurfa siririya
ta rataya mata a wuya ta mike ta shigo daki ta
kwanta.
A wannan lokaci fatanta mutuwa kawai ta zo,
nono na zuba hawaye na zuba dan tsanani sai
ta kama karanta adu'ar.
Allahumma la sahla illa ma ja'altahu salha
wa'anta taj alul hazna iza shi'ata sahla.
A hankali sai barci ya dauketa zuciyarta dauke
da tunanin baya
ASALIN ALHAJI ABDULKAREEN BABA LABARAN
Dan kasar yamen ne, ya zo Nigeria dalilin
kasuwanci, tun yana zuwa ya koma har ya dawo
da iyalansa gaba daya ya gina gidan shi a kano
suke zaune a wanan lokaci yayansu uku.
Hajiya maryam itace matar tasa muhammad
Rufa'i shine na farko sai nafisa sai muhammad
narardin, wadanda ta hafa a can na nan wadda
ta fara haifa itace Asiya sai muhammad Bashir
sai Rabi sannan fatima zahra sai idris dan auta
da suke cewa khalifa.
Duk inda mace mai saukin kai da hakuri ta kai
hajiya maryam ta kai, ko kusa bata dauki duniya
da zafi ba, tana tafiyar da rayuwarta cikin sauki,
yayin da mijinta Alhaji Abdulkareem yake
mafadacin gaske, babu hakuri a harkarsa, duk
wanda yake tare da shi ya san wannan.
Tun daga kan makota da abokan huldarsa a
kasuwa ballantana iyalinsa.
Ya shigo Nigeria da kafar dama bai jima ba ya
shiga sahun masu kudin da ake fadarsu a duk
fadin jihar kano.
Alhaji abdul mutum, ko abokan harkarsa a kasu
sai larabawa yan uwansa.
Saboda yadda ya tsani bakar fata ko mi son da
yake wa abu in har a gun bakin mutum zai saya
to ya hakura. Zirga zirgarsa tsakanin Ngr da
kashashen lrbw irin su Sudan, saudi arabiya,
egypt da malaysia da can kasarsa yemen da
sauransu.
Duk karshen sati ya kan tara iyalinsa kaf a gana
hirar tuna baya a yi raha ayi addu'o'i ga
wadanda suka mutu a ci a sha, kafin a tashi
gargadin da yake musu shi ne baya son hulda
da talaka.
Baya son hulda da bakin mutun idan sun
kaucewa wanan za su zauna lafiya da shi. Idan
ba haka ba zasu gamu da hushinsa wanan
huduba bata yiwa hajiya maryam dadi tana
ganin kuskure ne babba yake dorasu a kai.
Talaka da bakin mutum duk Allah ne ya halicce
su bata isa tayi mai musu ba saboda masifarsa
gaban yayanta sai ya iya rufe ido ya ci mata
mutunci ba damuwarsa bane.
Dan haka duk lokacin da ya gama nashi
hudubar ya tashi in gari ya waye zata tarasu in
bai nan ta ce da su Yanda nake matsayin
mahaifiyarku a gunku nake da hakki kuyi mun
biyaya akan duk wata hanya da nake son kubi
matukar ba ta kaucewa hanyar Allah ba haka
mahaifinku yana da hakkin kuyi mai biyayya. Sai
dai bana jin dadin muguwar da bi'ar da yake
doraku a kai. Ko wannenku a anan yasan Allah
ne ya halacci mai kudi ya halacci farin mutum
ya halacci baki, duk mai hankali da tunani ba
zaiki wani dan bai da dukiya ba, ba zaiki wani
don bai da farar fata ba. Watarana rufa'i ya
kada baki ya ce da ita ummi idan bamu bishi ba
yaya zamuyi? Sanin kankine gaba dayan mu
karkashin sa muke da zarar mun kaucewa
abinda yake so sai ya wulakantamu ya kore mu.
Itama Rabi ta sami bakin magana ta ce ummi
wlh nima raina ba karamin baci yake yi ba in
naji abba yana fadar haka sai in dinga ganin
kamar ba magana bace irin ta dattijo mai ilimi
wanda yasan abun da yake yi ba. Nafisa ta ce
to wai me akeyi da talauci, annabawa ma da
sukafi kowa daraja agun Allah naiman tsari
sukeyi da shi balantana mu? Ni banga laifin
baba ba dan ya ce mugujewa talaka. Ai nufinsa
mu diyansa ne mata kada mu dauko mai talaka.
Haka ku maza kada ku dauko mai aure gidan
talakawa, yanda yake mai kudi yafison harka da
daidai shi, kwarya tabi kwarya. Idris ya tabe
baki yace nima haka dai naganiNura ya ce to
ma in banda abinsu gida kamar namu yadda
abbanmu ke kashe mana kudi gun cin abinci
mai kyau mu sha mai kyau suturu da kayan ado
masu kyau, amma sai mu lalace a auren talaka?
Haba in anyi haka ai anci baya, ina amfanin
shuka idan ba a yi girba ba?
Abba ya sha gaya mana cewa yana kashe
kudinsa a kanmu ne dan mu zame masa riba,
idan mun tashi aure mu na da tagomashin da
zamuyi tsadar da zamu auro mata masu tsada a
gida mai tsada.
Ku kuma mata duk wanda zai zo auranku ko
kallon fatarku yayi ya san an kashe muku kudi
dole sai yana da kudin da zai iya daukarku idan
wanan bai samu ba ina amfanin kudin da yake
narkarwa a kan mu?
Rabi a ta ce kai ni a ganina wannan ba tunani
ne mai kyau ba yaya nura, ni dai a guna talaka
da mai kudi duk daya ne, don a Alkur'ani mai
girma Allah ya ce babu wanda yafi wani a
cikinku a gun Allah sai wanda ya fi tsoron Allah.
Duba da wanan ayar za ku ga cewa fifiko gun
Allah shi ne abin nema a rayuwar mutum ba zai
samu wannan fifikon ba kuwa sai ya kasance
mai tsoron Allah.
Fifikon jinsi ko yare ko dukiya ba sa amfanarwa
mutum komai a ranar lahira matukar bai bi
Allah ba. Nafisa ta zabga mata harara ta ce to
sarkin wa'azi sai ki dauko duro ki hau ki yi ta yi.
Muhamma Bashir ya ce kyaleta ta fadi ra'ayinta
kowa ba ra'ayinsa yake fada ba.
Fatima ta ce ni dai ba ruwana duk wanda Allah
ya bani ina so in mai kudin in talakan mi dai
nafi son in yi auran soyayya ba auran kudi ba.
Babu wani kudi da zai tsolewa gidan nan ido mu
da abbanmu ke buf mana dakin kudi mu debi
yadda muke so mu yi abin da muke so.
To wane kudi zamu je kwa dayi a
Domin cigaba da karantawa sai ku downloading.
Yadda ake downloading na littafin: ku tabbata kunyi register da shafinmu sanna kunyi login, idan bakuyi register a kasa zakuga maballai guda biyu daya an rubuta LOGIN dayan kuma an rubuta REGISTER sai ku taba su kuyi register, daga nan sai ku yi subscription koda na naira 1000 ne, domin sai kunyi subs dinann ne kadai zaku iya dauko littatafanmu.

Ya ya akeyin Subscription namu : Bayan kun yi Login ko register daga kasa zaku ga wani jan maballi (button) an rubuta SUBSCRIBE sai ku taba shi zai kaiku inda zaku zabi package wato tsarin subs na ku da mu. akwai na wata guda, watanni biyar da shekara guda. da zarar kun zaba zai kaiku inda zaku biya kudin, wanda daga nan sai ku cigaba da downloading kawai abunku

ABUN LURA : duk wani littafi da kuka gani a shafinnan kyauta ne, wannan tsari mun zo da shine don mu samu hanyar da zamu iya rike shafin muna managing na shi, izan ku kayi subs na mu tamkar DONATION ne ku ka yi mana, ku ka bamu kwarin guiwa don mu ciagaba da kawo muku sabbin littatafai, amma duk wanda ya ga bazai iya ba toh zai iya karanta littafin kyauta a cikin shafinnan namu batare da ya downloading ba, kawai ya yi kasa zai ga Koren maballi (button an rubuta) START READING sai ya taba zai kaishi inda zai karanta littafin.

Sannan duk wanda yaga kamn wannan process din zai bashi wahala kai tsaye zai iya min magana ta whatssApp +2348140419490, ya tura min kudin ni kuma zan dora mai subs din akan account na shi

NB: iya ta haka ne zaku iya karanta wannan littafi a shafinmu babu wata hanyar. DAN ALLAH KU DAINA MANA MAGANA AKAN MU TURA MUKU LITTAFI TA WHATSAPP, BAMA TURAWA HANYA GUDA MUKE TURA LITTATAFANMU SHINE WEBSITE NA MU https://taskarnovels.com.ng DUK MAI BUKATAR LITTAFINMU YA JE CAN YA KYAUTA NE, AMMA DOWNLOADING KUWA BA KYAUTA BANE SAI YAYI SUBSCRIPTION NA WEBSITE NAM
This is not the real Download Button


Read / Download LAUNIN FATA

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

This is not the real Download Button
Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album