You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
wurin,shi kuma ya wuce 6angarensa yyi saurin cire wannan kayan, israt da khulood kuwa har sunyi bacci don su da suka ga basu ganta ba sun dauko tana 6angaren prince ne, washegari, tun prince na jiran bimbii har ya hkr taqi zuwa 6angaren nasa ta wuce tabi su israt debo kayan marmari,tasan lkcin wankansa yyi amma ta share ta cigaba da huldar gabanta, shi kuwa prince sanye yake da wata rigar wanka fara sol, ya zauna yana jiran bimbii,lkci ya qure sosai amma bimbii bata zo ba, kwantar dakansa kawai yyi a jikin kujerar dayake zaune ya lumshe idanu, ita kuwa dawowarsu kenan ta kalli 6angaren prince, kamar zata shige abinta sai kuma ta dawo da baya ta wuce ciki, tana isa masu tsaron wurin suka bata hanya ta shige,tana shiga ta duba ko'ina bata ganshi ba tana shirin fice ta hangoshi tsaye wurin windows din nan ya harde hannunsa dukka a bayansa ya qurawa waje idanu tun dawowarsu dasu israt yake hangenta, yanzun ma yaji motsin shigowarta kawai juyowa ne beyi ba, matsawa tayi kusa dashi ta rissinar dakai,juyowa yyi yana kallonta fuskarsa babu yabo babu fallasa sannan ya qetarata ya wuce ya zauna ya dora kafarsa daya kan daya yana kallonta yace" na miki afuwan gocewa aikinki da kkyi yau amma idan kk sake maimata hkn toh zan dauki akan wadanda suke janyeki daga bakin aikin ki" gabanta ne ya fadi don ba qaramin tausayin su khulood takeyi baza ta6a yarda wani abu mara kyau ya same su silarta ba,durqusawa tayi akan guiwowinta gabansa tace" kayi hkr bazan sake ba amma kar ka cutar da yan uwana" kallonta yyi sai kuma ya dauke kanshi gefe guda yace" idan na dauki mataki akansu daman ai shine daidai tunda suke saki rashin jin mgn, sune silar dayasa kk tura kanki cikin rikici har da zuwa sace gawa a kogi" a mutuqar razane ta dago kanta tana kallonshi cike da mamakin yadda akayi babban prince yasan wannan sirrin nasu, harararta yadanyi daidai lkcin kuma ubaid ya shigo, rissinar dakansa yyi ya ajiyewa prince wani dogon akwati a gabansa, kallonta yyi yace" baki san aikinki bane koh kuma saina krt miki" wata irin zabura tayi da sauri ta miqe ta nufi cikin dakin wankan nan ta soma hada masa ruwan wanka cikin kwarmin wanka, shi kuwa prince da gangan ya mata hk yasan tana son su khulood sosai shiyass yake mata wannan barazanar, ita har yau batasan shine dakansa ya cecesu lkcin da suka tafi kogi ganin gawar layla ba,shine dakansa ya dauke hnklin bayin da suke shirin kamasu ya basu damar gudu shiyasa ya rufe fuskarsa da baqin kyalle, gani yyi taurin kan bimbii yyi yawa gata da kafiya kamar shi,dawowa da kallonsa yyi kan ubaid suka soma tattaunawa game da sabuwar takobin da mahaifinsa ya aiko masa dashi, bude masa akwatin ubaid yyi shi kuma ya fito da takobin sai sheqi take da walwali,murmushi yyi sosai sannan ya mayar da ita cikin akwatin,dagawa ubaid hannu yyi shi kuma ya sunkuyar dakanshi qasa sannan ya fice,komar da kallonsa yyi wurin dakin wankan yana jiran fitowarta, fitows tazo gabansa ta rissinar dakanta qasa alamar komai ya kammala, batayi saurin dagowa dakanta ba don tasan tunda bataji motsin miiqewarsa ba toh tabbas ita yake kallo,a zucci tace" haba mutum sai kallon tsiya kamar wani maye" tashi yyi yaxo ya wuceta ya shige dakin wankan, ranar dai kam ta jima tana masa tausa cikin dakin wankan kafin ya kammala wanka ya fito, kwanciya yyi kan gadonsa ya lumshe idanu,tasan sarai tausa yakeso kafin yyi bacci don shi baya iya bacci hk sai an masa dabara, bimbii kam ita yanzu kam tana tsayuwa ne tare da bata da yalwatacciyar tazara tsakaninta da royal bed na prince, tana mugun shakkar hawa gadon nan yanxu, jin taqi hayowa sai abun ya bashi dariya har ya murmusa sbd ya fahimci abunda take tsoro, daga mata hannu yyi tayi saurin sake masa curtains din data rufe kusurwar da gadonsa ke ciki ta wuce ta fice,shi kuma yabita da kallo yasan abunda tafi so kenan shiyasa ya bata umarnin tfy, washegari bimbii tayi masa rakiya wani taro da sarauniiya dakanta ta shirya a 6angarenta na yanta wasu bayi, prince baya taba sake bimbii ta 6acewa ganinsa duk inda tayi yana binta da kallo a sace, sarauniyya mar'atussaliha kuwa uwace wacce tasan halayyar dan nata ciki da waje, ta lura da kallon dayake bin bimbii dashi a sace, kiran bimbii tayi tazo gabanta ta rissinar dakai sannan ta maida dubanta kan kwayar idanun prince dake kallon bimbii nan take ta warware kanta komai tace" bimbii ta tafi, bimbii ta dawo inda take ta tsaya,sarauniyya mar'atussaliha ta kalli prince da murmushi a fuskarta sosai tace" idan na nemi alfarma a wurinka zakamin kai tsaye" kallonta mahaifiyar tasa yyi cike da mamaki yace" umarninki kawai nk jira na aiwatar" fadada murmushinta tayi tace" toh ina son ka bani wannan baiwar taka" saurin dago da idanunsa yyi yana kallonta, murmushi tayi masa sannan tace" kar damu saika maida tsohuwar baiwarka lenah ko ka sake za6en wata cikin bayi na" qaqalo murmushi yyi ya kalleta yace" meyesa kkson wannan baiwar kawai" itama murmushi tayi tace"kallonta kawai nayi naji ta kwantamin daka ganin tana da zuciya mai kyau" shiru yyi ssnnan ya dago dakansa yace" shikenan ranki ya dade na baki ita saidai......." sai kuma yyi shiru tace" kayi magana dana, fadi abunda kkson fada" murmushi yyi yace" aa, babu komai"ranar dai bimbii ta tattara ta koma 6angaren sarauniyya tabar 6angaren babban prince, wannan abu yyiwa mutane da dama dadi ban dasu israt da basu ji dadin hkn ba,itako bimbii abu yyi mata dadi sosai don hkn yafi nono fari a wurinta, wasu bayin har mamaki suke da suka ga bimbii na nuna farin ciki, lenah itama 6angaren abu yyi mata haske ta koma hidimtawa prince akbar, 6angaren prince kuwa abun babu kyau..........
Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan acct...0100790419,alhaji shahida nasir,union bank, zaki turomin da screenshrt na payment dinki a whatsapp ta wannan layi...07041195806..
Alkalamin Bintuu ne.....
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔
Written By Bintuu Seer
22
*Miss each movement spend with you* you are my medicine.......💕💕
Bangaren sarauniyya mar'atussaliha yana da girma sosai kuma suma bayin dake 6angaren nata wajensu yana da yalwa sosai,bimbii bata samu daki ita kadai ba yadda take a 6angaren prince,hadata akayi da wasu bayi su hudu ita ta zama ta biyar, neman wuri tayi daga can gefen dakin ta ajiye kayanta, yanayin bayin data hadu dasu anan ba kamar su khulood bane ta fahimci akwai tsugumi da baqin ciki a lamarinsu sbd tunda ta aka kawota dakin ba wacce ta mata kallon arziki,ummu nana ta sanar da ita aikinta shine baiwa furannin dake 6angaren gbdy ruwa safe da yamma sannan da tatso nonon raqumi, washegari da sanyin safiya bimbii ta tashi ta bawa furanni ruwa sannan ta dauki kwarya ta tafi tatso nonon raqumi anan suka hadu dasu khulood suna ganinta suka taho da gudu suka rumgumeta, israt tace" bimbii daman arzikinki muke ci jiya kina tfy lenah ta dawo dakin tayi mana korar wulaqanci muka koma dakin hadaka yanzu mu takwas ne a dakin da muke" murmushi bimbii tayi ta janyo hannun israt tace" karki damu komai na duniya dan hkr ne wani lkcin baka cimma kyakykyawar qaddararka kai tsaye har saika qetare'''' manyan qalubale na rayuwa" murmushi sukayi gbdy, khulood tace" wannan hk yake" sunkuyawa sukayi suka soma tsatsar nonon raqumi duk suka cika kwaryoyinsu sannan suka dora bisa kawunansu suna tafe suna hira har suka iso hanyar da zasu rabu su khulood suka wuce 6angarensu itama ta wuce nata 6angaren, prince akbar kuwa ranar kasa runtsawa yyi sai tunani yake dalilin dayasa sarauniyya ta nemi ya bata bimbii har yanzu ya kasa fahimtar manufarta saidai yana da tabbaci tana da manufa nayin hkn don mace ce mai mutuqar hange da fahimtar lamura kuma gata da tarin hikima, kiran ubaid yyi ya shigo ya rissinar dakai a gabansa cike da ladabi,dago dakansa yyi dake jingine bisa wata tattausan kujera ta alfarma ya kalli ubaid dakansa ke sunkuye, yace" kana da wata fahimta kan manufar sarauniyya na amsar wannan baiwa" shiru ubaid yyi na y'an daqiqai yana tunani sannan ya dago dakansa ya kalli babban prince yace" ranka ya dade bani da wata fahimta kan hkn saidai abunda ya bani mamaki shine me yasa sarauniyya ta kira bimbii har gabanta sannan tace ta tafi batare data furta komai ba sannan ta maida dubanta kan idaniyarka, abunda na fahima anan shine akwai wani sirri data gani cikin kwayar idanunka bisa al'muran wannan baiwa taka, ka gafarceni ranka ya dade da wannan hasashe nawa" shiru prince yyi domin amsar ubaid kadai ta haska masa manufar sarauniyya mar'atussaliha,wato ta fahimci sirrin zuciyar prince game da bimbii da take qasqantacciyar baiwarsa, kallon da prince ke yiwa bimbii kawai ya ankarar da sarauniyya cewa d'an nata yana da wani feeling kan wannan baiwa, abunda yasata aikata hkn shine tana gudun faruwar wani babban al'amari zuwa gaba mutuqar bimbii ta cigaba da kasancewa da prince, hkn da tayi na amshe bimbii daga wurinsa tana tunanin shine mafita, cikin kwana biyu kacal prince ya gama jigatuwa da kewar bimbii, hknne yasa ya buqaci ubaid ya kawo masa su israt yana son ganinsu, ubaid yaje ya taho dasu israt da jikinsu har rawa yake sbd tsorota da sukayi na jin wai babban prince nason ganinsu sai sukayi zaton ko wani laifin sukayi, suna shiga bangaren prince suka same shi a zaune kan wata kujerar mai ruwan zinare yana rubuta wata wasiqa,zubewa sukayi bisa guiwowinsu duk suka rissinar da kawunansu, saida ya dauki dogon lkci sannan ya dago da kansa ya kallesu, miqawa khulood wannan takarda yyi yace" gashi ina son ku miqa wannan takardar ga yar'uwarku, idan har kk bari wani yaji ko yaga wannan takarda toh hukunci mai tsauri na tanadar muku" qara sunkuyar dakai sukayi, khulood tasa hannu biyu ta amshi takardar da take nannad'e cikin wani siririn abu tamkar alqalami, yana miqa ya daga musu hannu suka miqe da sauri suka fice, ranar basu hadu da bimbii ba don hk da dare suka fita suka nufi bangaren sarauniyya, masu tsaron 6angaren sarauniyya ba kowanne bawa suke bari ya shiga 6angaren ba saidai idan a wurin kk aiki ko kuma kana hidimtawa daya daga cikin iyalan sarki,hk suka hana su khulood shiga 6angaren, qin tfy sukayi suka koma gefe suna ta tsaye ko zasu gano fitowar bimbii amma shiru, wani wuri suka samu suka tona rami suka binne takardar sbd basu son su koma 6angarensu da ita tsautsayi yasa wani ya gani, su kansu basu san meke rubuce cikin wasiqar ba, washegari da sanyin sfy suka fito suka nufi wurin da suka binne wasiqar suka tono wurin suka dauki wasiqar suka nufi 6angaren sarauniyya suka tsaya bakin kofa suna jiran fitowar bimbii, ita kuwa bimbii tana ciki ta bawa furanni ruwa tana gamawa ta dauki kwaryarta ta fito don tatso nonon raqumi, tana fitowa ta miqe hanya sai kawai ganinsu khulood tayi sun sha gabanta dukkaninsu a dan rikice, kallonsu tayi da mamaki tace"lfy kk kuwa" basu bata amsa ba sai 2waige suke kamar wasu marasa gsky saida suka tabbatar babu kowa wurin sannan israt ta sanya hannu cikin rigarta ta ciro saqon babban prince ta bawa bimbii, sannan suka sanar da ita gargadin daya musu,shiru bimbii tayi tana kallon wasiqar, khulood ta sake waigawa taga ba kowa ta matso kusa da bimbii tace" kiyi sauri ki 6oye ki tabbatar babu wanda yaga wannan saqo wurinki" sauri bimbii tayi ta chusa wasiqar cikin rigarta sannan ta rabu dasu khulood don su ranar qorama suka nufa, ranar bata samu lkcin kanta ba bare ta bud'a wasiqar taga abunda ta qunsa sai da dare data koma dakinsu ta saci jiki ta fito farfajiyar 6angaren ta nemi wurin da babu yalwar kilmawar bayi ta zauna gindin wata bishiyar dabino ta ciro wannan wasiqa ta bud'e, yyi rubutun ne da haruffan larabci, dayake itama tasan baqi hk ta soma karanta wasiqa, gabanta ne ya soma dokawa 2gudu lkcin data soma ganin kalmomin da prince yyi amfani dasu wurin rubutun wasiqar, ba wasu kalmomi bane sai tsantsar yabo da kuma mutunta darensu na farko, yyi mata gdy da kyautar budurcin da tayi masa sannan qarshen wasiqar kalmomi ne dake bayyana kewarta daya yyi cikin wadannan kwanaki sai kuma wasu zafafa kalmomi na soyayya daya soma furta mata karo na farko,bata qarashe karanta wasiqar ba tayi saurin rufe takardar jikinta na rawa ta dafe qirjinta dayake bugawa tamkar ze fashe sbd tsananin tsoro da razana da tayi, kallon takardar take tana tantaman anya prince ne dakansa ya rubuta wannan wasiqa, addu'a ta somayi cikin ranta Allah yasa su israt basu bud'a wannan wasiqar ba, duqunqune takardar tayi ta kutsirtsirata mitsi mitsi ta din ga tfy da nisa tana cillar da kowanne 6angare na takarda wuri daban daban sbd tsantsar tsaro, jiki a sanyaye ta koma dakin nasu ta tarar da abokan zaman dakin nata suna hirarsu ko kallonta ba wacce tayi itama bata sanya musu baki ba sbd akwai abu mafi girma dake dawainiyya da ruhi hade da gangar jikinta don hk bata da lkcinsu, samun wuri tayi ta kwanta, tana rufe idanunta kyakykyawar fuskar prince akbar zata soma mata gizo, miqewa tayi da sauri ta soma mutsitstsike idanunta,kunnuwanta taji tamkar muryarsa yana furta mata wadannan zafafan kalmomi da suka rudata suka gigita tunaninta baki daya,hannu tasa ta soma toshe kunnuwanta, duk bayin dake dakin suka soma kallonta suna tunanin ko ta samu matsalar kwakwalwa ne,6angaren prince kuwa ya rasa kansa sosai, be ta6a tunanin tarkon son wata diya mace zeyi masa irin wannan kamun ba amma sai gashi dare daya ya fada soyayyar qasqantacciya baiwa baqar fata da sun bambamta a komai, tun daga kan nahiya, asali,tushe har ma da kalar fata,riqe kansa yyi kawai ya rasa meke faruwa dashi, jin zuciyarsa yake tamkar zata zage sbd wani irin bugawa da take da qarfi, ga kewar bimbii dake azabtar da gangar jikinsa har ma da ruhinsa,miqewa yyi da sauri ya kira ubaid, kallon ubaid yyi yace" ina son ganin bimbii a wannan dare kasan duk yadda kayi ka kawo min ita" kallonsa ubaid yyi a nutse cike da girmamawa yace"an gama ranka ya dade" fita yyi da sauri, israt ya samu cikin sirri ya buqaci taje 6angaren sarauniyya ta fito da bimbii, sanar dashi tayi bata da damar shiga yankin sarauniya matsayinta na qasqantacciyar baiwa, wani qaramin gate pass ya ciro daga aljihunsa ya bata yace"ki nunawa bayin dake tsaron kofar wannan zasu bude miki kofa ki shiga" amsar gate pass din israt tayi ta tafi da sauri ta nufi yankin sarauniya tana zuwa ta nunawa masu tsaron kofa wannan gate pass suka bata hanya ta shige, bata sha wahala ba ta gane dakin da bimbii take, tana shiga dakin taga kusan dukkanin bayin dake dakin sunyi bacci sai bimbii kawai dake zaune ita kadai kamar wata mara gata, bimbii kamar ance ta kalli kofa taga israt tsaye tana kallonta,tasowa tayi da sauri tazo wurin israt, jan hannunta israt tayi suka fice daga dakin, israt ta kalleta tace" meke damunki hk bimbii yanayinki ya nuna kina tattare da damuwa" bimbii tayi shiru sai kuma ta kalli israt tace" babu komai" kallonta israt tayi kadan sannan ta kawar da waccar mgnr tace" babban hadimin babban prince ubaid shike son ganinki yanzu" dafe kirji bimbii tayi ta kalli israt tace" israt me kk zaton zemin" israt tace" gsky ban da sani kan hkn amma ga dukkanin alamu prince ne dakansa ke buqatar ganinki" take gaban bimbii ya yanke ya fadi, ta soma ja da baya, israt tsayawa tayi tana kallonta cike da mamaki,hannunta tasa ta riqo hannunta tace" akwai abunda ke faruwa ne tsakaninki da prince" girgixa kai tayi da sauri alamar aa, jan hannunta israt tayi suka soma tfy har suka fice daga yankin sarauniyya suka din ga wuce kusurwa kusurwa har suka qarasa inda ubaid ke jiransu, yana ganinsu yyi murmushi yace israt ta tafi sannan ya kalli bimbii yace" babban prince nada buqatar ganinki" juyawa yyi ita kuma ta soma bin bayansa cike da sanyin ciki kamar kaxar da kwai ya fashewa a ciki, gabanta kuma sai cigaba da faduwa yake har suka qarasa 6angaren prince, suna shiga suka tarar dashi zaune lenah na tsiyaya masa green tea, shigowarsu ne yasa shi dago da lumsassun idanunsa ya saukesu kan bimbii,lenah kuwa tana gama zuba masa tea din ta sunkuyar dakanta qasa sannan taja baya tana jira umarninsa,daga mata hannu yyi alamar ta tafi,rissinar dakanta ta sakeyi sannan ta juya da niyyar fita, mamki. tayi sosai na ganin bimbii tsaye a gefe,wata uwar harara ta aika mata sannan ta fita ranta a mugun 6ace, ubaid yana shigo da bimbii shima ya rissinar dakai,prince ya daga masa hannu ya fice, suna fita dukka ya rage sai bimbii kawai, yana daga zaune idanunsa na kanta ya kasa dauke kai,ita kuma ta kasa gaba ta kasa baya tana tsaye kawai wuri daya, sun dade a hk kanta na qasa ya taso a hnkli ya tako har inda take, matsowa yyi sosai tamkar zasu manne, ita kuwa take zuciyarta ta tsananta dokawa ta soma neman matsawa amma sai yyi saurin take mata kafa, zafi taji sosai ta dago dakanta tana kallonshi, dage mata gira daya yyi, cikin tsantsar dabara da hikima yyi mata jan bazata ta afko kirjinsa ya hannunsa duka ya mata daurin kazar kuku ta yadda bata da damar raba jikinta da nashi, kallonsa take cike da tsoro saita fara masa kuka, murmushi yyi ya dora fuskarsa saman nata ya rufe idanu itama ta rufe idanu suna sauraron bugawar zuciyoyinsu dake bugawa a tare kuma da qarfi, hannunsa ya dora kan kirjinta sannan ya kamo hannunta ya dora kan nashi qirjin, yace" wannan kawai ya tabbatar miki prince bazai iya rayuwa babu ke kusa dashi hkma kema bazaki rayuwa babu ni ba sbd bugawar zuciyarmu daya" shiru tayi tana jinsa amma taqi bude idanu gashi jikinta ya mutu murus bata da qarfin aiwatar da komai, sunkuyawa yyi yasa hannu ya cire mata wannan tsohon zoben dake yatsan hannunta na dama ya sanya mata wani na danyar azurfa daidai hannunta, jin jikinsa yake wani iri ya tabbatar idan har ya cigaba da kasance da bimbii toh ze sake tabargaza, janye jikinsa yyi a hnkli ya juya mata baya, daga mata hannu yyi ya bata izinin tfy batare daya juyo ya kalleta ba don baya son ta fahimci halin dayake ciki, juyawa tayi ta soma tafiya zata fita sai kuma ta jiyo ta dawo da baya, muryarta kawai yaji tace" idan za'a fara soyayya dole sai zuciyoyi biyu sun aminta da juna don cikin soyayya babu izzah bare nuna fin qarfi, idan daka shawarceni ko ka nemi amincewa ta zan fada mk cewa akwai wanda nkso, na bashi zuciyata tunkan yanzu kuma har gobe shi nk so, ka huta lfy" jin maganganunta yyi tamkar saukar ruwan dalma don prince mutum ne mai tsananin kishi musamman ga abunda yakeso, juyawa tayi zata tafi kawai taji ya damqo hannunta, idanunsa jajir dasu yace" soyayyata tana da tsada sosai nikaina na rasa yadda akayi qasqantacciyar baiwa kamarki ta samu zuciyata a araha da rahusa dare daya, toh ki sani duk wanda zaki so a baya na yake ko kin manta nina amshi budurcinki ba wani ba, ki sani soyayyarki itace babban kuskuren dana aikata ga dukkanin wani jini na sarautar burham, wannan irin soyayya ita ake kira haramtacciya a ilahirin wannan masarauta......ki amshi soyayyata ko karki amsa wannan za6in ya rage naki amma ina qara tuna miki ki kwana kullum cikin tuna matsayinki gareni ba kowa bace illah qasqantacciya baiwa mai mini hidima, ina da cikakken iko akanki" kallonsa bimbii tayi sannan tayi murmushi tace" idan da zaka zare kalmar so kabarni matsayin qasqantacciyar baiwa hkn shine farin ciki na" tana gama fadar hk ta juya ta fice daga sashin nasa tabarshi zaune ya dafe kansa dake juya masa, gani yake idan har bimbii taqi aminta da soyayyarshi zuciyarshi zata iya tarwatsewa........babbar baiwa ga sarauniya mar'atussaliha kuwa ummu nana tuni ta miqa zancen zuwan bimbii ga babban prince wurin sarauniya, shiru sauraniya tayi sannan ta dago dakanta ta kalli ummu nana dakanta ke sunkuye tace" ina son ganin azeez" jikin ummu nana har rawa yake ta fita don kiran azeez....azeez shine sarkin hukuncin dauri...............
Littafin nan na kudi ne, idan kina da buqata zaki tura #300 ta wannan acct....0100790419,alhaji shahida nasir,union bank....saiki tura screesht ta whatsapp a wannan layin 07041195806......
Alkalamin Bintuu ne.....
9/26/20, 7:47 PM - Anti qamshi🌷: *DAREN GOMA SHA HUD'U*🪔🪔
Written By Bintuu Seer
23
*Believe the power of love which make a king to be a servant and a servant to be the king*............I miss you like crazy......💕💕
Tana hakimce a wata kujerar ta alfarma cikin fadarta, ummu nana suka shigo tare da azeez sanye yake da baqaqen kaya,fuskar nan tasa babu yalwar fara'a duk suka rissinar dakansu a gabanta suna jiran umarninta, kallon fuskar azeez tayi yyi saurin dago da kansa,tace" ina son ka sace babbar baiwar prince dake hidima a 6angaren nan ka miqata babban kurku, bani son kowa yasan tana wannan kurku,sai a yad'a cewa tsohuwar baiwa ga prince ta gudu, wannan sirri ne tsakani na daku kawai bani son kowa ya samu wannan labari cikin wannan masarauta sbd wannan itace hanyar dazan ita ku6utar da prince daga fadawa fushin mahaifinsa sannan na dakatar da faruwar wani al'amari mai girma cikin wannan masarauta" gbdy suka sake rissinar da kawunansu alamar yin biyayyar ga umarnin sarauniya, daga musu hannu tayi suka juya suka fice daga fadar nata,dare nayi bimbii ta fito shan iskarta, batason zaman wannan daki sbd duk bayin dake suke zaune daki daya da ita basu kulata shiyssa duk dare take fita shan iska,tayi nesa sosai da farfajiyar 6angaren nasu ta nemi wani qaramin tudu ta zauna ta tsirawa wannan zobe da prince akbar ya bata idanu, motsi taji a bayanta tamkar motsin mutum, miqewa tayi da sauri cike da tsoro sbd wurin babu yalwar jama'a tana waigawa taji an toshe mata baki, tuni ta fadi a wurin suka dauketa suka sanyata cikin wani keken doki, hk suka din ga tfy har suka isa babban kurku, masu tsaron kofar basu san wacce bimbii sudai suna ganin azeez suka bude musu katuwar kofar kurkun suka shige da bimbii, sun samar mata da daki na qarshe a jerin dakunan dake kurkun, dakin tsagaye yake da manya qarafa masu kauri yadda babu wani mahalukin dazai iya 6allasu, kasan kurkun busassun ciyayi ne aka zuba,hk suka shigar da ita ciki suka watsata tamkar wata shara, har lkcin bimbii bata dawo cikin hayyacinta batasan abunda ke faruwa da rayuwarta ba saida sanyin asubahi ya soma ratsata ta bude idanunta a hnkli tana qarewa inda ta samu kanta kallo,wasu hawaye ne masu dumi suka soma ambaliya a fuskarta ta tashi zaune a hnkli tana cigaba da kallon inda ta kuma tsintar kanta, wahegari, bayin dake kwana tare da ita suka ga basu tashi da ita, basu kawo komai sai sukayi zaton tashi wuri tayi ta fice bakin aikiinta, jita jita ne ya soma yawo cikin wannan masarauta cewa daya daga cikin bayi dake hidima a 6angaren sarauniya ta samu nasarar gudu,su israt kuwa basu ta6a kawowa cewa bimbii ce ta tsere ba, ranar dai basu ganta, yamma nayi suka gama 2aikacensu suka koma dakin da suke suna shirin kwanciya suka ji ragowar bayin dake dakin suna hirar, israt ce ta juya da sauri ta kalli daya daga cikin bayin dake hira tace" don Allah wacce baiwa ce ta gudu" kallonta dayar tayi tace" tsohuwar babbar baiwar da prince yabarma sarauniya mn" daya daga cikinsu tace" ai kamar ma ina yawan ganinku tare da ita a bakin qorama" israt da khulood