Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

[2/28, 1:08 PM] Aysha Dansabo Lemu😘😘: 📱 *NUFIN ALLAH...!* 🤲🏻 _*Arewabooks@ayshadansabo*_

*Paid book:500*

*Chapter 1*

_Free page_


Misalin ƙarfe biyar da rabi shida saura na asuba, kyakykyawar baƙar budurwar ta isa ƙofar gidan Hakimin garin giwa. Mai suna Alhaji Haruna Musa giwa, wanda shine Hakimin garin kuma aminin mahaifinta marigayi Malam Mahmuda. Tana kuka wurjajan ta ci burki daga bakin zauren shiga gidan, tana faman raba idanu jin sautin karatun da ke fitowa daga masallacin kusa da gidan.Da alamu lokacin ake sallar asubi a masallacin,sai ta dawo da baya tana zama akan dakalin ƙofar gidan.Kuka sosai take yi iyakan ƙarfinta,baƙin kyakykyawar fuskarta gaba ɗaya ya tasa idanunta sun kumbura domin tun cikin dare take aikin kukan tashin hankalin halin da Innarta ke ciki. Tana nan zaune tana sharan hawaye da sauke ajiyar zuciya, su Hakimi suka fito daga cikin masallaci. Tun daga nesa yake hango wata da jan hijab zaune bisa dakalin ƙofar gidan nasa, hakan ya sanya shi ɗaga ƙafa yana riga Yaransa isa ƙofar gidan domin zuciyarsa na gaya masa cewa ba lafiya bane.

"Najmatu lafiya, ko jikin Mairo ne ya sake motsawa kuma? Hakimi Alhaji Haruna Musa giwa ya furta hakan, a lokacin da ya isa wajen dakalin da take zaune akai ya fahimci cewa Ƴar amininsa ce zaune mai suna Najma. Wacce ya kira da Najma tayi saurin dubansa wasu hawayen na zarya akan fuskarta,taja ajiyar zuciya tana faɗin "Jikin ne Baba Hakimi, kwana mukai bamu runtsa ba.Yanzu haka na baro tana jin jiki." Ta kai ƙarshen maganar tana rushe masa da kuka mai motsa zuciyar mai saurarenta. Hakimi ya ja salati yana faɗin, "Subhanallah!" Ya waiwaya bayansa yana yafuto ɗansa Auwalu da hannu, wanda ya tsaya suna magana da wasu samari. Ganin Hakimi na kiransa ya sanya shi isowa da sauri yana faɗin, "Baba gani." Hakimi ya dubesa da zallar damuwa akan fuskarsa ya ce, "Maza shiga cikin gida ka ɗakko mukullin mota ka fito mu wuce asibiti, jikin Mairo ya sake motsawa." Auwalu ya ruga a guje zuwa cikin gidan yana jan salati a zuciyarsa, domin suna tsananin son Inna Mairo da ganin mutuncinta.

Cikin hanzari ya fito daga cikin gidan hannusa riƙe da mukullin motar Hakimi.Ya isa garejin gidan ya fiddo motar, Hakimi ya shiga gaba yayinda Najma ta shiga baya tana faman jan ajiyar zuciya.

Kamar yadda Najma ta sanar da Hakimi Inna Mairo na tsananin jiki, a haka suka sameta. Da taimakon Auwalu da Najma suka kamota zuwa mota, suka wuce da ita asibitin zaɓawa dake garin. Taimakon gaggawa aka bata har aka samu ta dawo hayyacinta.Likitan da ya dubata ne ya basu tabbacin cewa rashin shan magungunanta akan ƙa'ida shike maido da komi baya, don haka dole a kula da sayensu akan lokaci da zaran sun ƙare. Ya kammala dukkanin jawabinsa sannan Ya rubuta musu wasu magungunan kala biyu, Ya ce idan ta shayesu bata ji daidai ba su wuce da ita babban asibitin koyarwa dake shika domin ta samu ganin babban likita. Hakimi sukai godia bayan sun amsa takardan maganin. Najma da sai lokacin hankalinta ya fara kwanciya, ganin Inna ta dawo hayyacinta. Sai ta kama hannunta suka fito daga ofishin Likitan, wanda duk yawancin sanda za a kawo Inna Mairo shi ne ke dubata, kuma shi ne babban likita baki ɗaya a asibitin Zaɓawan.

Suna tafe cikin mota don komawa gida Hakimi na mitan yadda ƴan uwan Inna Mairo da matar mahaifinta da suke kira Gwaggo suka juya mata baya. Ya cigaba da faɗin, "Yanzu saboda Allah Mairo idan su sun yanke zumunta dake sai ke ki biye musu ki daina zuwa inda suke? Karki manta fa kece ƙaramarsu Mairamu, duk yadda zasu gujeki su juya bayansu gareki don sun yi arziƙi, ke bai kamata ki yanke zumunta dasu ba. Ina giwa ina kaduna da za a ce kin yanke dukkan alaƙa da ƴan uwanki, kin zaɓi ki cigaba da rayuwa cikin tsananin maraici da ciwan zuci?" Ya dakata da maganar zuciyarsa na shiga ƙunci mai yawa, domin yana tsananin jin ciwon yadda Ƴan uwan Inna Mairo duka biyu suka wofintar da ita tun bayan rasuwan Mahaifinsu. Inna Mairo dake sauraren Hakimi ta kasa magana sai kuka, kukan da ke tasowa tun daga ƙarƙashin zuciyarta yana ƙona ruhinta.

Sanin da Hakimi ya yi Inna Mairo har da ciwon zuciya ke barazanar kamata,sai ya koma yin rarrashi da nusar da ita illar yanke zumunta koda ace an yanke maka, kai ance ka sadar ga wanda ya yanke maka ɗin. Har suka isa ƙofar gidan Inna Mairo Hakimi nasiha yake mata cikin rarrashi, Inna ta dinga saurarensa kalamansa na ratsa zuciyarta da sake raunatata.

"Najma kamata ku shiga daga ciki,zuwa anjima Auwalu zai je ya samo magungunan da aka rubuta ɗin. Mairamu Allah ya ƙaro afuwa, ki daina sanya yawan damuwa a zuciyarki domin kin fi kowa sanin cewa ba a son mai hawan jini na yawan tunani da sanya damuwa a rai. Musamman ke da zuciyarki ke barazanar kamuwa.Na horeki da ki daina sanya yawan tunani ki maida dukkan lamuranki zuwa ga Allah. Na sani ke ɗin mai tawakkalice amma ki ƙara ninka jururiyarki domin shi komi na rayuwa NUFIN ALLAH ne Mairo, yadda duk Yaso haka yake kasancewa. Allah zai baki lafiya ya kuma ganar da ƴan uwanki da Gwaggo cewa sun yi kuskure, sun kuma ci amanar dattijon arziƙi marigayi Alhaji Muhammad da basu rungumi wasiyyarsa sun riƙe amanarki da ya bar musu ba." Hakimi ya dakata da maganar yana kallon Inna Mairo da hawaye ke gudu akan fuskarta, ta gyaɗa kanta murya a shaƙe ta furta, "Na gode Hakimi, Ubangiji ya biya maka buƙatunka na alkhairy duniya da lahira. Allah Ya duba gaba da bayanka Ya albarkaci zuriyya.In Sha Allah zan yi ƙoƙarin ganin na rage yawan damuwar." Ta kai ƙarshen kalamanta lokacin da Najma ta zagayo ta buɗe mata murfin motar ta fito. Hakimi ya sake mata fatan samun sauƙi yana jin tausayinsu ita da Ƴarta Najma na sake mamaye zuciyarsa. Tabbas Ya yi rashin amininsa mai ƙaunarsa, Yana kuma jin cewa kulawa da Iyalinsa tamkar tilas ne a garesa domin ba zai iya zuba ido rayuwar su Inna Mairo ya tagayyara ba. Shiyasa tun bayan rasuwar aminin nasa Malam Mahmuda shi ne yake ɗawainiya da su Inna Mairon,bai taɓa gajiyawa ko gazawa ba,da taimakon Ubangijinsa yake musu komi.

Najma a hankali take takawa hannunta riƙe dana Inna Mairo har suka dangana da cikin gidan nasu, wanda ginin ƙasa ne da ya samu aka filascesa da siminti.Tsakar gidan ma an filascesa babu ƙasa sam a tsakar gidan,ko'ina fes yake don suna da tsanani tsafta da kula da muhalli.

Ƙaramin ɗakin nasu mai ɗauke da falo da ɗakunan bacci biyu a jere suka buɗe, Inna Mairo ta zame hannunta daga na Najma tana nufan hanyar ɗakin baccinta.Najma tabi bayanta da kallo tana mata sannu cike da tausayi. Inna Mairo ta amsa ba tare da ta waiwayo ba, don burinta shi ne ta dangana ga tsohuwar katifarta ta yi kukan da take riƙewa na tunawa da gwarzon mijinta da Mahaifinta da suka kwanta dama. Domin tabbas da suna raye da sun share mata baƙin ciki mai yawa na rayuwa,da bata yi kukan rashin gata ko makusantar da zata kwanta a kafaɗunsu ta yi kuka ba. Sai dai dukkanin gatan nata sun ƙare, ta rasa uwa tun tana tsummar goyo. Gashi yanzu ta rasa miji da uba,duka sun tafi sun barta cikin wannan duniyar mai cike da tarin rikita-rikita da ruɗin zuciya.

Ta kifa ciki tayi kuka mai yawa har Najma dake zaune a falo ta zabga uban tagumi, sai da ta jiyo sautin kukan da Innar ke yi. Ta nufo cikin ɗakin baccin Inna Mairo a rikice, tana mai durƙushewa a gaban katifar da take kwance ta ce, "Inna lafiya, jikin ne? Don girman Allah Inna ki tausayamin ki daina sanya damuwa a ranki, domin ke kaɗaice kika rage gatana a yanzu. Sannan lafiyarki ita ce abinda tafi komi muhimmanci.Ki dubi girman Allah karki bari lafiyarki ta salwanta akan baƙin cikin waɗanda basu san ma kina yi ba." Najma ta ƙare maganan tana riƙo hannun Inna Mairo ta saki kuka mai ban tausayi, hakan ya sake karya zuciyar Inna Mairo.Ta riƙe hannun Najma da kyau tana faɗin, "Ba don su nake wannan kukan ba Najma, ina kokawa ne don rashin Mahaifinki da nawa.Tuni na daɗe da cire damuwar su Gwaggo a cikin zuciyata,na danne dukkan ƙawazucinsu a raina.Bana ganin laifin su Yaya Kabeeru, laifin Gwaggo nafi gani Najma domin na san ita ce tayi musu katanga dani, ta kuma hana su raɓemu sabida da tsananin ƙiyayyarta garemu ni da Mahaifinki." Inna Mairo ta dakata da maganar zuciyarta na mata wani irin suya, ta kai hannu ta dafe saitin zuciyarta da ke mata wani irin zafi. Ganin hakan ya sanya Najma taya ta dafe wajen tana mata sannu cikin tsananin jin tausayin Innartata.

Sun ɗauki lokaci a haka hannunsu na dafe da ƙirjin Innar,kafin ta zare hannun Najma tana faɗin, "Tashi ki kunna wuta ki ɗaura abin karin kumallo Najma." Najma ta jinjina kai tana tashi tsaye ta zare hijab ɗin jikinta, idanunta akan Inna ta ce, "Sannu Inna, bari in je kicin ɗin in ga ko akwai ragowar gawayin da za a iya kunnawa." Daga haka ta fito daga ɗakin cikin takunta mai cike da nutsuwa ta halitta. Na dinga bin budurwar da kallo, wacce zata kai shekaru sha bakwai.Ina yaba kyawu da tsarin halittarta,domin babu ƙarya Allah Ya yi mata baiwar kyawu da cikar halitta mai asalin fisgar hankali. Baƙace sosai amma kyakykyawar da aka ƙera halittarta tamkar ita tayi kanta. Tana da tsayi matsakaici ba mai yawa ba, sannan tana da gaba da baya wanda suke a cike. Musamman ƙirjinta da yake a tsaye cir! Da cikakkun dukiyar fulani.Dogon hanci gareta har baka,sai manyan idanu farare tas! Masu turawan ƙwayar ciki baƙi siɗik! Ɗan ƙaramin bakinta so cute da cinkusassun gashin giranta baƙaƙe siɗik! Sun fi komi ƙawata kyawun fuskarta. Bata da jiki kuma ba za a kirata siririya ba, sai dai a kirata mai murjajjen jiki.saboda fatar jikinta a cike yake da tsoka babu alamar rama ko siranta a tattare da ita. Koda ta nufi cikin kicin ɗin kai tsaye wajen robar da suke zuba gawayin ta nufa, ganin akwai ragowarsa da ɗan yawa ya sanya ta ɗakko murahun gawayin guda biyu ta zuzzuba wanda zai isheta amfani. Bayan ya ruru ne ta ɗaura ruwan wanka a guda ɗaya, ɗaya kuma ta ɗaura ɗumamen ragowar tuwo miyar kuka da suka ci a daren jiya suka rage.......✍🏻


🤳🏻 *INA MASU RIƘE DA WAYAR HANNU KUNA TA'AMMULI DA KAFAFEN SADARWA? TO ALBISHIRINKU DOMIN KUWA GA A.ƊANSABO DATA SERVICES.* *TA ZO MUKU DA TSARIN SAYEN DATA AKAN FARASHI MAI SAUƘI. DATA BUNDLES KAMAR NA👇🏻*
*MTN*
*GLO*
*AIRTEL*
*9MOBILE*
*MONTHLY VADILITY 💃🏻*


*DUK AKAN FARASHI MAI SAUƘI KUMA A SAUƘAƘE.KE DAI KAWAI KI NEMI A.ƊANSABO DATA SERVICES AKAN WANNAN LAYIN NATA 08167768704 DOMIN ƘARIN BAYANI KO BIYAN KUƊINKI DOMIN SAYEN DATARKI A SAUƘAƘE* 💃🏻💃🏻💃🏻

















#Najma#
#Hot lovestory#
Aysha Ɗansabo ce✍🏻
[2/28, 1:09 PM] Aysha Dansabo Lemu😘😘: 📱 *NUFIN ALLAH....!* 🤲🏻
_*Arewabooks@ayshadansabo*_

*Paid book:500*

*Chapter 2*

_Free page._


Kafin ruwan ya tafasa tuwan ya ɗumamu Najma ta kammala sharan ɗakinsu, wanda ba wani girma bane da shi. Bayan ta haɗa musu shayi ruwan bunu(ruwan lipton), ta juye ɗumamen a kula ta nufo ɗakin Inna Mairo da shi. A falo ta aje komi ta nufi bedroom ɗin wajen Inna Mairo, ta sameta a kwance har lokacin tayi lamo akan katifarta tana faman zurfafa tunani. Cikin sanyin murya Najma ta zauna daga bakin bed ɗin tana faɗin, "Inna na kammala, ga ɗumamen da ruwan lipton can a falo. Inna Mairo ta muskuta ta tashi zaune tana sauke manyan idanunta da Najma ta gada a kanta, ta sauke numfashi a hankali ta ce, "Sannu Najma da ƙoƙari, Allah ya yi albarka ya zaɓa muku mazajen aure na gari." Najma da tuni ta gane jam'u da Inna Mairo tayi tana nufin ita da su Luban gidan hakimi take wa addu'ar, sai ta kauda kai tana amsawa a zuci. Inna Mairo ta cigaba da cewa, "Da zaran mun kammala karin kumallon sai ki bani ruwan wanka, watakila idan nayi naji ɗan ƙarfin jikina." Najma ta murmusa ta ce, "To Inna!" Daga haka suka fito zuwa falon da Najma ta shareshi tsaf, ta goge yagaggen ledar tsakar ɗakin. Suna cin abincin suna taɓa hira akan ciwon Inna Mairo da irin yadda ake samun kuɗin sayen magungunan da ƙyar.Ba don Hakimi ba da tuni watakila Innar ta mutu,sabida rashin gata da wanda zai tsayawa lamuransu har ya ɗauki nauyinsu. Ba kuma don Innar ta rasa Ƴan uwa ba, sai don Ƴan uwan nata sun gujeta sun juya mata baya shekaru kusan bakwai kenan rabonta dasu.Tsakaninta dasu sai dai aiken kayan abinci da zanin sallah da suke mata duk shekara, amma baya ga haka babu mai takowa inda take domin sunyi arziƙin da suke ganin tamkar ci bayane su tako ƙauyen garin giwa su ce suna da ƙanwa bare har su ga halinda take ciki su tallafa mata. Wani irin abu mai ɗaci ya tsayawa Inna Mairo a maƙoshinta, lokacin da ta tuno zuwan Gwaggo na ƙarshe garin giwa, bayan rasuwar marigayi Malam Mahmuda. Najma ta kwashe komi ta kai kicin ta aje, ta ɗauki bokiti ta ɗebowa Inna ruwan zafi ta surka, ta kai mata banɗaki don tayi wanka ko zata ji daɗin jikinta kafin Baba Hakimi ya aiko da magungunan da zata sha.

Ɗakinta da ke kusa dana Inna ta shiga ta share tare da gyara shinfiɗar lafaffiyar katifarta, wacce tun ta makarantar kwanan da suka yi ne ta dawo da abin ta tana kwanciya akai. Gefen katifar ta samu ta zauna ta sauke numfashin a hankali, zuciyarta na kwaɗaita mata son jin asalin tarihin Innarta da yadda aka yi ta auri Mahaifinta Malam Mahmuda. Tana matuƙar son sanin musabbabin da Gwaggon kaduna take nuna wa Inna ƙiyayyar da har ta kai ta rabata da Ƴan uwanta, ta hana su raɓeta ko ita Innar ta rabesu. Tana nan zaune tana zurfafa tunani har ta ji shigowar Inna ɗaki alamun ta dawo daga banɗaki yin wanka, tayi saurin tashi ta fito tana faɗin, "Inna har kin fito?" Inna Mairo ta dubi tilon Ƴarta da take duba ta ji sanyi a ranta ta bata amsa da faɗin, "Na fito Najma, ke ma sai ki je ki yo wankan kafin asan abin yi zuwa rana ko?" Najma ta jinjina kai tana faɗin, "To Inna, amma ina ga da rana ɗinnan da wuya mu samu abin girkawa domin babu sauran kayan abinci sun ƙare." Inna Mairo tayi shiru, kafin daga bisani ta dubi Najma tana faɗin, "To shikenan Najma, Allah zai rufa asiri. Ina ga Hakimi ya shafa'a ne ba a kawo kayan abincin wannan satin ba.Ki yo wankan ki fito akwai ɗari biyar sai ki je ki auno mana garin kwaki muyi kwaɗonsa da ƙuli muci kawai." Najma ta jinjina kai cike da gamsuwa da maganar Inna ta ce, "To shikenan Inna, bari in je in yo wankan." Ta nufi ƙofar fita daga ɗakin ta bar Inna Mairo da bin bayanta da kallo, tana mai jin matuƙar tausayin Najmar na danne zuciyarta.A kullum ta tuna cewa Najma ita kaɗaice a gareta, kuma bata da sauran dangin uba a raye da zasu tallafeta sai ta ji hankalinta ya sake tashi. Domin ita kanta ya ta ƙare da nata Ƴan uwan bare har ta sanya ran watarana zasu tallafesu ita tilon Ƴar nata Najma. Ta ɗanɗana zafin rashin Ƴan uwa ko Ƴar uwa shaƙiƙai da bata da su, ta san zafi da illar hakan ga duk wanda ya taso cikin tsangwaman Ƴan uban da kansu ba a haɗe yake ba. Ta san illar ƙiyayyar matar uba, domin shi ne silar shigarta duk wani halin ƙuncin da take ciki a yanzu, bayan ƙasa ya rufe idanun Abbah da gwarzon mijinta Malam Mahmuda. Domin a lokacin Abbah na raye duk irin ƙiyayya da jin zafinta da Gwaggo ke yi, bata iya nuna mata wani abun sabida shakkar idanunsa. Amma tun daga randa ya kwanta dama, ta sake gane irin ƙiyayyarta da ke zuciyar Gwaggo, wanda bakomi ya sake assasa ƙiyayyar ba sai mugun riƙo da Gwaggon ke da shi.

Inna Mairo ta faɗa ɗakinta don shafa mai ta sanya kaya, tana yi zuciyarta na sake tariyo mata da irin rayuwar da tayi a garin giwa ,tun daga zuwanta tana amarya, har kawo yau da wanda ya yi silar zuwanta garin bashi a raye. Ya tafi ya barta da tarin kewa da ƙuncin zuciya, Ya barsu a lokacin da ita da tilon Ƴarsa ke matuƙar buƙatar kulawarsa. Hawaye masu tsananin zafi da sam bata iya riƙesu a duk lokacin da tunaninsa ya bijiro mata suka silalo daga idanunta,ta kai hannu ta sharesu tana jin ƙunci mai yawa na sake mamaye zuciyarta. Cikin sanyin jiki ta kammala kintsa kanta ta sanya riga da zani na wata atamfar chiganvy, wanda ke ɗaya daga cikin irin zannuwan da ake aiko mata dasu daga hannun Ƴan uwanta su Yaya Kabeeru.

Najma wanka tayo ta shirya kanta cikin wata doguwar rigar atamfar roba, kalar atamfar ja ce da ta haska baƙar fatarta mai laushi.Fuskarta ya yi fayau babu ɗigon kwalliya illa tozali da ta zizarawa fararen idanunta, waɗanda ke da wani irin haske da ƙyalli tamkar ruwan hawaye na taruwa a cikinsu. Gashin kanta sassalka irin na asalin fulanin da ta gado wajen Inna, ta ɗaureshi a tsakiyar kanta kafin ta ɗaura ɗankwalin kayan nata. Lokacin da ta fito daga ɗakin ta samu Inna Mairo zaune a falo, ta nema waje ta zauna daga ƙasan ledar tsakar ɗakin ta ce, "Inna na kammala shirin, bani kuɗin siyan garin kwakin in je in dawo kafin rana tayi." Inna Mairo ta dubi Najma tana yaba kyawunta, wanda ta gado a wajenta. Baƙar fatarta ce kawai na Malam Mahmuda, amma kyawun fuskar da surar jikin duk nata ne, domin babu inda Najma ta barota a kamanni sai bambamcin kalar fata kawai. Ita Inna farace tas! Wacce a kallo ɗaya zaka gane cewa jinin fulanice sosai. Ta miƙa hannu ta ɗakko naira ɗari biyar ɗin da shi kaɗai ya rage musu a gidan ta miƙawa Najma, ita kuma ta sanya hannu ta amsa tana miƙewa tsaye ta tashi ta nufi ɗaki don ɗakko hijab.

Lokacin da Najma ta dawo ta samu Auwalu ya kawo ma Inna magungunanta, sai dai ba a samu guda ɗaya ba sabida tsadarsa. Ta dubi Inna a lokacin da take mata bayanin ta ce, "Yanzu Inna to ya za a yi kenan?" Inna Mairo tayi murmushin ƙarfafa guiwa ta ce, "Allah zai kawo yadda za a yi Najma, ni burina ma mu sake samun jarin da zaki cigaba da toya ƙosannan tunda sana'ar ya amshemu dashi muke samun na rufin asiri." Ta kai ƙarshen maganar da sanyin murya. Najma ta jinjina kai ta ce, "To Inna ina zamu sama jarin? sai dai idan za a sake ɗaga wani abin a siyar ko?" Inna ta ɗanyi jim...Kamar ba zata tanka ba, sai daga bisani ta bai wa Najma amsa da faɗin, "Najma na yanke shawaran mu sai da katifar ɗakin Malam tunda babbace zata yi daraja." Najma da zuciyarta ke sake raunana ta dubi Inna ta ce, "Hakan ya yi Inna, Allah sa tayi darajar da za a samu jarin mai ɗan kauri."

Inna Mairo ta amsa da cewa, "Ameen Najma, idan kin kammala ayyukan zuwa anjima sai ki je gidan Adama dillaliya ki yi mata maganar katifar." Najma ta ce, "To Inna!" Daga haka ta zare hijab ɗin jikinta ta nufi kicin don haɗo musu kwaɗon garin kwakin. Cikin ƙanƙanin lokaci ta kammala yin kwaɗon wanda yaji ƙuli dasu tumatir da albasa da ta yankasu gunin sha'awa a ciki, ta juyosa cikin baban faranti ta nufi ɗakin Inna dashi. Ta samu Inna ta shige ɗaki don yin sallar azuhur, hakan yasa ita ma ta fito ta ɗauki buta ta nufi bayi don kama ruwa da ɗauro alwala.

Bayan sun idar da sallar ne suka haɗu suka ci kwaɗon cikin kwanciyar hankali. Najma ta ɗebo musu ruwan rijiyarsu mai daɗi suka sha suka yi hamdala,sannan ta ɗakko ma Inna magungunanta ta sha.

Suna zaune suna ɗan taɓa hira Najma ta dubi Inna Mairo ta ce, "Inna don Allah ki sanar dani tarihinki dana aurenki da Babana, ina son sanin dalilin ƙiyayyar da Gwaggon kaduna ke miki." Ta dakata da maganar tana duban fuskar Inna Mairo don ganin yadda ta amshi maganarta. Inna da idanunta ke kan Najma tuni ta haɗe fuska, tana mata wani duba na mai yasa kike son sani? Kafin ta buɗe baki ta ce, "Najma sau nawa zan sanar dake babu ruwanki da sai kin san abinda ya faru? Ki rufe wannan maganar bana sonta." Najma da zuciyarta ke matuƙar son sanin cikakken tarihin Innarta da yadda aka yi aure ya wanzu tsakaninta da mahaifinta, sai ta narke murya tana matso hawaye ta ce, "Don girman Allah Inna karki gwaleni a wannan karon, wallahi ina matuƙar son sanin cikakken asalina da tarin yadda aka yi kika auri Babana? Ki taimaka ki sanar dani tarihin rayuwarki ko na ƙaru da wani abin." Inna Mairo ta jinjina kai cike da jin tausayin Najma, don ta san tana son jin tarihin baya ne ko zata gano ita ce mai laifi ko Ƴan uwanta su Yaya Kabeeru da suka wofintar da rayuwarta.
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment