Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nan basuyi kama da patient ba kama suke da wanda a kayi kidnapping, momy ina ki ka samo yaran nan?” ta kai ƙarshen maganar babu alamun wasa


“baby kin fi kowa sanin mahaifiyarki ko dabba bazata iya sacewa ba bare mutum, ki yarda da ni yaran nan taimakonsu kawai nake son yi”
“idan taimakonsu ki ke son yi mi yasa baki turosu a Flight ba amma ki ka turo su a container bakunan su a rufe,mi hakan yake nufi?”

“ki yarda da ni baby taimakonsu nayi” ta faɗa cike da shagwaɓa kamar bada ƴarta take magana ba

“gaskiya banji daɗin yanda ki ka sa aka ɗaure su ba,kamar wasu dabbobi”
“sorry baby na amshi laifin hakan bazai sake faruwa ba, sorry” ta faɗa tana ɗan kama kunnenta, tsaki Nailarh taja tana rejecting kiran.


umarni ta bada akan su fito da yaran bayan ta tura securitys ɗin orphanage ɗin sun kira doctors ɗin dake hospital ɗin orphanage ɗin, ɗaya bayan ɗaya su ka shiga fito da yaran sai layi su ke kamar za su kifa ƙasa da alama wani abun aka basu wanda ya gusar masu da hankalin su.



doctors da nurses dake ɗauke da stretcher ( gadon ɗaukar marasa lafiya) su ka ƙaraso wasu sun su sai hamma suke da alama daga bacci su ke, cike da girmamawa su ka shiga gaishe da Nailarh bata wani amsa masu ba ta bada umarnin a ɗauki yaran, babu ɓata lokaci su ka shiga ɗaukar yaran a gadon ɗaukar marasa lafiya suna nufar hospital ɗin, bayan su Nailarh tabi, ganin haka ne yasa Joseph bin bayan su.



cikin gaggawa likitocin su ka shiga ba yaran emergency treatment dan ganin sun dawo cikin hayyacin su, sun shafe awanni da yawa suna abu ɗaya sai da ƙyar su ka samu yaran suka farfaɗo amma sun gagara gane taƙamaimai abunda ke damun yaran.



kallon Nailar dake zaune saman waiting chair Joseph yayi, idanunta a lumshe bacci ne sosai a idonta amma saboda san ta san mike damun yaran taƙi tafiya gida, cike da tausasa murya joseph yace “boss ya kamata ki tafi gida ki huta”
“bazan tafi ba sai na san abunda ke damun yaran nan”
“am sorry boss, da dai kin tafi har yanzu bincike doctors ke yi kuma na san idan suka gama bincike har gida za su kawo maki result ɗin”

“kana ba kanka wahala Joseph babu in da zan tafi bansan abunda ke damunsu ba”
lallashinta ya shiga yi shida securitys ɗin amma babu wanda ta saurara a cikin su sai ma cewa tayi idan ba so suke suyi ta aikin su ba to karsu sake mata magana.


ganin dai da gaske ba amincewa za tayi ba ne yasa Joseph yanke shawarar kiran mahaifiyarta, number mahaifiyarta ya shiga dannanama kira amma ba tayi picking ba, canza akalar kiran yayi ga Aunty sophia, baiwar Allah tunda Nailarh ta fita bata rintsa ba, ta kasa zaune ta kasa tsaye hankalinta duk a tashe yake saboda inda Nailarh ta tafi, kiran Joseph na shiga wayarta har sai da gabanta ya faɗin, jiki na rawa tayi picking ko da ya sanar da ita dalilin kira ba ƙaramin kwanciya hankalin ta yayi ba.


“please bata wayar” ta faɗa, da sauri ya miƙa mata wayar“boss miss sophia na son magana dake” a hankali ta buɗe ido tana jifanshi da harara, saurin sadda kanshi yayi ƙasa, kauda fuska tayi gefe ba tare da ta amshi wayar ba, kara wayar yayi a kunnenshi “taƙi karɓar wayar” ya faɗa
“sata a speaker” shine kawai abunda Aunty sophia ta faɗa,ok ya furta yana sa wayar a speaker
“hello baby kina jina?” Aunty sophia ta faɗa


da wata kalar kasalalliyar muryar ta wanda bacci ke neman fin ƙarfinshi ta furata “Aunty sopei ”
“baby mi yasa baki son ki dawo gidan, kin san yanda hankali na ya tashi da fitar da ki ka yi, tunda ki ka fita ko bacci na kasa yi please ki dawo gida”


“zan dawo Aunty sopei kawai ina son na san abunda ke damun yaran”
“karki damu har gida doctor zai kawo maki result ɗin su kuma nayi maki alƙawarin tare da ni zamu zo duba su idan doctors sun kallama bin cike amma yanzu ki dawo gida”
“shikenan sai na dawo”
“yawwa ko ke fa keda na sanki babu ruwanki da shiga abunda bai shafeki ba?”
“ke ki ka fara koyaman damuwa da damuwar mutane” murmushi Aunty sophia ta saki da alama taji daɗin maganar Nailarh.



“sai kin dawo” da ok ta amsa mata, rejecting kiran Joseph yayi yana sauke ajiyar zuciya, harara Nailarh ta watsa mashi murmushi kawai ya saki, tashi tayi ta leƙa ɗakin da yaran suke kafin ta nufi ƙofar fita,har inda motocin su suke doctors ɗin suka rakata kafin sukayi mata sallama.


a guje motocin su ka fice daga orphanage ɗin, tun a hanya su ka rabu da su Joseph su kuma suka kama hanyar gida, Nailarh bata san sun iso gida ba saboda tun a moto bacci yayi awana gaba da ita, sai da Aunty sophia tasheta tukun ta san sun ƙaraso,fitowa tayi su ka nufi cikin gidan, direct bedroom ɗinta Aunty sophia ta nufa da ita, suna shiga ta faɗa kan bed ko takalman dake ƙafarta bata cire ba.



murmushi kawai Aunty sophia ta saki, da kanta ta shiga rage mata kayana jikinta, rigar suit ɗinta ta zame mata haɗe da earring ɗinta da wristwatch tukun ta zame mata takalman ƙafarta, idanunta ta sauke akan gun ɗin dake suke a ƙugunta har zata wuce sai kuma tasa gefen suit ɗinta ta zame gun ɗin, a cikin rigar ta naɗeta,dressing room ɗinta ta nufa, maida komai tayi a mazauninshi, a saman locker ta ajiye mata gun ɗin saboda bata san password ɗin locker ba kuma Nailar tafi amfani da eye I D, ficewa tayi daga dressing room ɗin ta koma bedroom ɗin, gyara mata kwanciya tayi kafin ta fice daga ɗaki baki ɗaya.



*ABUJA NIGERIA*


Nainarh da yumnah ne suka fito daga bedroom ɗin mom,less ne a jikin yumnah ɗinkin bubu ta yafa mayafi saman kanta yayinda Nainarh ke sanye da riga da skirt na atamfa hijab ne a jikinta saɓanin yumnah dake da gyale, hannunsu riƙe da na su Ammar, Aman da jamala da alama fita za suyi.


Part ɗin dady su ka nufa,da sallama a bakin suka shiga a parlor su ka sameshi shida mamy,ciki suka ƙarasa, kallo ɗaya mamy tayi masu ta ɗauke kai dady kuwa da fara'a sa yake kallon su, a saman rug carpet su ka zauna cike da girmamawa su ka gaishe da su dady kawai ya amsa masu amma mamy yi tayi kamar ma bata san da zaman su a parlorn ba.


“my friends sai ina haka?” dady ya faɗa yana kallon su Ammar, Aman ne ya bashi amsa da
“gidan papah” ɗaure fuska dady yayi “shine za ku fita ba tare da ni ba, kodai mun dai abotar ne ban sani ba?” jamal ne yayi saurin cewa “A'a ka tambayi Aunty Nainarh idan tace aje da kai shikenan” gaba ɗayan su suka kai duban su ga Nainarh da
kwata kwata hankalinta baya kansu tunda su ka shigo idanunta suka sauka akan wani ƙaton photo dake manne a bango,sosai ta shagala da kallon photon, tayi mamakin ranar da su ka shigo bata ganshi ba tunanin ta fara yi to kodai ba'a jima da sashi ba.



ɗan taɓo ta yumnah tayi “dady na magana” da sauri ta kai dubanta ga dady “Aunty Nainarh jamal yace sai kin amince za'a tafi dani, za kuje dani kuwa?” saurin sadda kai ƙasa tayi tana sakin murmushi, murmushi shima dadyn ya saki yana leƙa fuskarta “idan na fahimta wannan shirun alamace ta ba'a zuwa dani” da sauri ta ɗago tana faɗin “A'a dady zamuje da kai”


“wasa nake maku sai kun dawo ina gaishe da mutanen gidan”
tashi yumnah tayi tana kama hannun Nainarh
“za su ji in sha Allah, ku tashi mu tafi”sallama su kayi masu suka fice, taɓe baki mamy tayi tana kallon dady “wai ni kam Janar da sanenka wannan yarinyar take zaune a gidan nan?”
“wace yarinya kenan” dady ya faɗa yana kai duban shi gareta dan bai fahimci akan wa take magana ba


“wacce su ka fita yanzu da yumnah”
“wai kina magana ne akan Nainarh”
“ni ban ma san sunanta ba amma ita nake nufi”
“da sani na take zaune gidan akwai matsala ne?”
“ni gaskiya bana son zamanta a gidan nan”
“miye matsalar ki da zamanta a gidan yarinyar da ba'a kanki take ba”



“kamarya miye matsalata, gidan mijina ne fa,kawai sai mu zuba ma zulaihart ido tayi ta yin abunda taga dama, hakanan zata kwaso mana yarinya idan ta cutar damu fa??” tunda ta fara magana dady ya kafeta da ido tsantsar mamaki ne akan fuskarshi ko miye abun masifa kamar wacce ke jiran mutane
“ni gaskiya bana son zamanta gidan”
“ta kawo duk wanda zata kawo gidan mijinta ne kuma gidan ƴaƴan tanada ƴancin ajiye duk wanda ta so”


“haba Janar wai miyasa kullum kake fifita zulaihart a kaina ne, komai tayi dai dai ne a wajenka amma ni kuskure ɗaya zanyi ka ɗau mataki a kaina” ta faɗa rai a ɓace,mamaki yaƙi ɗaukewa akan fuskar dady lamarin mamy har tsoro yake bashi
“ni gaskiya bana son zamanta a gidan”
“to sai mi dan baki son zamanta a gidan, naga ba'a kanki take ba kuma gida gidana ne kuma ni na amince da zamanta dan haka bana son na sake jin kinyi tari akan Nainarh, idan ba haka ba ranki ne zai ɓaci”


“hakama za kace,kenan Zulaihart tafini?”

rai a ɓace dady yace
“Zulaihart tafiki komai mabaruka, ko ƙafarta baki kama ba, dan Zulaihart ban taɓa bata umarni ta saɓa man ba, Zulaihart bata man rashin kunya kamar yanda ki ke man,Zulaihart bata sa'insa dani,nayi mata cin mutuncin mafi muni a rayuwa amma haka nan tayi haƙuri dani take zaune da ni har kawo yanzu duk da a ƙasarta da Al'adarta bata saba ganin irin haka ba sannan ki sani Zulaihart ta fiki haƙuri mabaruka”


wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare zuciyar mamy, idan da abunda ta tsana a rayuwa taji ana yabo mom musamman dady abun na ɓata mata rai, rai a ɓace ta fice daga part ɗin gaba ɗaya, da kallo kawai dady ya bita.



Su Yumnah suna fita daga part ɗin dady ficewa su kayi daga gidan baki ɗaya,suna fitowa motar ya Naeem na kunno kai cikin parking space ɗin, ɗan dakatawa su kayi, daidaita parking ya Naeem yayi, kusan a tare aka buɗe car doors ɗin su fito,ya Naeem ne ya fito daga driver seat yayinda ya Adanan ya fito daga front seat.


Uniform ne a jikin ya Naeem yayinda ya Adnan ke sanye da suit back color, da gudu su Ammar su ka nufe su, hugging ɗin ya Naeem su kayi ɓata fuska ya Adnan yayi kamar ƙaramin yaro yana faɗin
“abun ƴar haka ce ya Naeem kawai ku ka sani, shikenan nima ai ga Autar dady nan” ya faɗa yana buɗema Yumnah hannayen shi, da sauri ta nufeshi tana sakin dariya, faɗawa tayi jikinshi tana hugging ɗin shi.



murmushi Nainarh dake tsaye ta saki, yaran mom na matuƙar burgeta Irfan ne kawai take ganinshi daban a cikin su kamar ya banbanta da su.


“dady mun fara gaishe da second father ne fa”Aman ya faɗa yana turo baki
“ba wani nan, bana dai yi daku, da Autar dady nake yi”

“ku rabu dashi kishi ne kawai” ya Naeem ya faɗa yana basu hannunshi suka tafa
“sai ina haka?” Ya Adnan ya faɗa lokacin da yake raba jikinsu
“gidan uncle Mustafa” yumnah ta bashi amsa
“a dawo lafiya muna gaishe da mutanen gidan”
“za suji in sha Allah”


kama hannun ya Adnan ya Naeem yayi yana faɗin “sai kun dawo” da sauri Nainarh ta gaishe da su ganin za su bar wajen,duban suka kai gareta
Murmushi ya Naeem ya saki “lafiya lau Nainarh, ya gidan” da Alhmdllh ta amsa mashi, ya Adnan tunda ya kafeta da idanu ƙala baice ba, duk tsawan wannan lokacin da Nainarh ta ɗauka bai taɓa ganinta ba in fact ma baisan wacece ba, ɗan taɓoshi ya Naeem yayi


“baka ji ana gaishe ka” washe mata baki yayi yana faɗin “lafiya” murmushi ta sakar mashi
“muje ko, Yumnah sai kun dawo” ya Naeem ya faɗa yana nufar ƙofar shiga gidan, ya Adnan kasa ɗauke idonshi yayi a kan Nainarh har su ka nufi motar Yumnah su ka shiga, yumnah har ta buɗe driver seat zata shiga yayi saurin jawo Arm ɗinta, bayan motar yajata.



da tsantsar mamaki take binshi da kallo, hannu yasa ya kauda fuskarta gefe “kin wani tsare ni da ido, tambayarki zanyi wacece waccan?” ya faɗa yana nuna cikin motar

“wai Nainarh?”
“sunanta kenan?”
“eh sunanta kenan, ɗiyar fa mom Asma'u ce” ɗan zaro ido waje ya Adnan yayi “amma ya akayi ban santa ba?”
“may be baka zuwa gidan ne”
“eh gaskiya bana zuwa, wajen mom ta zo?”
“ai ka san abunda ya faru da mom Asma'u to shine mom ta dawo da ita nan gidan”


“ok na tuna”murmushi Yumnah ta saki tana kallon fuskarshi
“na tafi?”
“idan kin tsaya wani abun za kiyi man ne?”
“ok sai mun dawo” ta faɗa zata bar wajen,muryar Noor ce ta dakatar da ita, da sauri su ka kai duban su ga Noor dake fitowa daga cikin mota,palazzo trouser ne a jikinta haɗe da shirt open shoulder,daga sama rigar ta kama jikinta sosai kusan rabin brest ɗinta a waje,ga wasu irin high hills masu shegen tsini tasa, ɗan siririn mayafi ne a saman kanta.


fuskarta da fara'a ta nufo su, tana ƙarasowa tayi hugging ɗin ya Adnan, saurin tureta yayi daga jikinshi rai a ɓace yace“wai Noor har sau nawa zance maki kidaina hugging ɗina, wai ke baki san cewa ni ba muharraminki bane akwai fa Aure a tsakanin mu” ɓata fuska tayi kamar zata fashe da kuka
“ya Adnan daga kawai nayi murnar ganinka”harara ya watsa mata yana kallonta tundaga sama har ƙasa


“yanzu dan Allah miye amfanin wannan suturar dake jikinki, yanzu mom Fatilah na kallonki ki ka fito a haka?”

cike da shagwaɓa tace
“miye aibun kayan dake jikina ya Adnan?”
“ban sani ba” ya faɗa haɗi da jan tsaki, bari wurin yayi gaba ɗaya ya nufi cikin gidan.


taɓe baki tayi tana kallon Yumnah “ina zaki na zo wajen ki?”
“kin dai zo wajen ya Irfan kuma duk yau baizo gidanan ba”
“ke fa banza ce wa yace maki wajen shi nazo, na zo gaishe da Mom ne”
“a haka?” Yumnah ta faɗa tana kallon kayan jikinta, ɓata fuska Noor tayi “wai miye matsalar kayan jikina ne?”
“ok bama kiga matsalar su ba, na so ace second father ki kayi hugging ba ya Adnan ba,da kuwa kin san matsalar kayan jikin ki”
“shikenan ni dai naji, ina zaki?”
“gidan Uncle Mustafa”
“kai Yumnah yanzu sai ki tafi duk da na zo?”
“eh mana saboda na san ba wajena ki ka zo ba, idan kuma kina zuwa to?”
“kin san halin mom Maryam ina zuwa zata rufeni da mashifa ita komai nayi rashin kunya ne”
“da gaskiyarta Noor kuma tana yi maki haka ne dan ki gyaru, ki zo muje kawai”


gyaɗa kai Noor ɗin tayi, motar Yumnah su ka nufa, back seat ta buɗe kusa da su Ammar tashiga Yumnah kuma ta buɗe driver seat, key Yumnah tayi ma motar
“sorry kinjini shiru ko,ga sister Noor nan ku gaisa” ta faɗa tana kallon Nainarh.
Juyowa Nainarh tayi “sannu, ya gida” da lafiya lau Noor ta amsa mata, gaishe da Noor ɗin su Ammar su kayi da fara'arta ta amsa masu tana tambayar “wane ɗan kasadar ne ya baku wayarshi?” ta faɗa tana kallon wayar dake hannunsu suna buga game
Aman ne ya bata amsa da
“ta Aunty Nainarh ce” taɓe baki tayi tana kai dubanta ga Yumnah
“sister Yumnah wai da gaske ya Irfan baizo ba, daga Villa nake fa can ma baya nan kuma sai kiran wayarshi nake bana samu”
“ni dama na san ba wajen mom ki ka zo ba”
“ni dai naji, dan Allah yana ina?”
“wallahi rabona da ganin ya Irfan tun jiya da muka dawo daga gidan Abbah, amma yau da safe naji sunyi waya da mom, ki gwada kiran ya Waseef na san dole suna tare”
“kin kawo shawara” ta faɗa tana zaro wayarta daga cikin Aljihun wandonta, Number Waseef tayi dialing, bugu biyu ya ɗaga
“hello Noor, ya ki ke ya gida?”
“lafiya lau ya Waseef, wai ina ka kaiman ya Irfan ne tun jiya nake faman neman number shi baya picking??”
“amma kin raina man wayo Noor wato nima na kai Irfan ɗin wani waje ko”
“eh mana” ta faɗa a shagwaɓe.
shiru taji baice komai ba, jin Waseef yayi shirune yasata faɗin “dan Allah yana ina?” muryar Irfan taji daga cikin wayar
“hello beb”
“haba ya Irfan ka san kuwa halin daka jefani ciki kuwa, sai kiraka nake bana samu dama jiya ka bani haushi shine ma ka kashe wayarka ko nayi duk abunda zanyi?”
“sorry Noor ba haka bane, kina a raina wani uzuri ne ya sani kashe wayata amma kiyi haƙuri, kina ina ne yanzu?”
“gajiya nayi da nemanka na zo gidan big dady ko zan sameka”
“ok kina can yanzu?”
“A'a mun fita tare da su Yumnah zuwa gidan Uncle Mustafa”
“sorry gani nan zuwa kinji”
“zan jiraka fa karka shanya ni?”
“karki damu zan zo kinji”
“ok sai ka zo”
“ok bye” ya faɗa yana rejecting kiran, ajiyar zuciya ta sauke tana turu wayar cikin Aljihun wandonta.
murmushi yumnah ta saki “gaskiya na kusa tona maku asiri keda ya Irfan kowa ya san abun da ke tsakanin ku” saurin kallonta Noor tayi
“ban gane abunda ke tsakanin mu ba?”
“zan fallasaku kowa ya san soyayya ku ke” ajiyar zuciya Noor ta sauke tana dafe saitin zuciyarta da “da kuwa kin kyauta min Yumnah dan na gaji da hiding ɗin da ya Irfan ke yi”


dariya Yumnah tayi “da ɗina dake fa Noor rashin kunya, yanzu ya Irfan na hiding amma ke so ki ke a faɗa ko, idan basu amince ba fa??”
“wallahi har poising zan iya sha idan har su kace za su rabani dashi” da wani mugun sauri Nainarh ta juyo tana kallonta dan kalamanta sunyi matuƙar bata mamaki.


murmushi ta sakar mata tana kashe mata ido ɗaya, saurin juyawa Nainarh tayi tana girgiza kai.

murmushi Yumnah ta saki
“za ki iya fiye da haka,dan na lura baki da hankali a kan ya Irfan”

“duk ma wanda yace maki inda hankali akan ya Irfan yayi maki ƙarya”
“Allah ya shirye ki” shine kawai abunda Yumnah ta ce yayinda take shiga compound ɗin gidan Uncle Mustafa, parking tayi
“Ameen idan da gaske ki ke” Noor ta faɗa tana fitowa daga cikin motar, girgiza kai kawai Yumnah tayi.


A tare Yumnah su ka fito ita da Nainarh, back seat Yumnah ta nufa tana buɗema su Ammar.
sojoji ne ta ko ina a harbar gidan, da gudu su Ammar su ka nufi ƙofar shiga gidan.


mom maryam na zaune a katafaren mai parlorn gidan su ka shigo da gudu su ka faɗa samanta har sai da ta ɗan tsorata
“wane mai son gamawa da duniya lafiya ne ya kawo man ku?” dariya su kayi suna faɗin “su Aunty Yumnah ne” da sauri ta kai dubanta ga ƙofar shigowa saboda sallamar su Yumnah da taji.


zambur ta miƙe tsaye tana rabka salati “innalillahi wa Innah ilaihi raji'un” wani irin mummunan faɗuwa gaban su Nainarh yayi da sauri su ka juya...
Da sauri su ka juya suna kallon bayan su dan duk a tunanin su wani abu ta gani a bayan su.


“amma Allah wadaran naka ya lalace, yanzu ke Noor fatilah na kallonki ki ka fito haka ƙirji a waje, ubanwa zaki nunama ƙirji da ki ka fito haka” gaba ɗayansu su ka sauke ajiyar zuciya dan ba ƙaramin tsoro ta basu ba.


turo baki Noor tayi gaba“ni dama shiyyasa bana son zuwa gidan nan idan muzo”
“dama yaushe zaki so zuwa gidanan tantiriyar banza, wallahi Noor kiyi ma kanki faɗa kwata kwata wannan ba ɗabi'a bace mai kyau, kina zubar ma kanki da mutunci ne”
“haba Momy yanzu dan Allah miye laifin kayan jikina?”


baki mom maryam ta saki “shaiɗaniyar banza tambayata ma kike, kin wuce kinje ɗakin Kainart kin nemi kaya na mutuncin kin sa ko kuwa”
baki Noor ta turo gaba“ni gaskiya bazan sa wasu k...” bata ƙarasa ba saboda yo kanta da mom maryam tayi,ai kuwa babu arziƙi ta kwasa da gudu zuwa cikin gidan.

“mara kunyar banza ai dakin tsaya” ta faɗa tana nufar sofa data tashi ta zauna,dariya Yumnah da Nainarh su kayi suma suna samun wajen zama su ka zauna, cike da girmamawa su ka gaishe da ita, da fara'arta ta amsa masu tana tambayar mutanen gidan.


“suna nan lafiya sun ma ce mu gaishe ku”
“muna amsawa,wallahi ku riƙa yima yarinyar can faɗa tunda uwarta ta kawo ido ta sa mata, kwata kwata shigar da take bata dace ba, da wanan shigar sai ta rasa mijin Aure dan duk wanda ya san kanshi baizai kwashi wannan tarkacen ba, dan ni wallahi AHMER ya kwaso man mace irin wannan da sunan zai Aure sai nace ubanshi daga shi har ita”


dariya Yumnah ta kwashe da ita“mom itafa Noor zaman waje ne ya maida haka”
“ke ni dallah rabani,ku da kuke da alaƙa ta jini da turawa mi yasa baki shiga irin haka ƙarshen dai rashin kunya kenan ko, mi yasa Zulaihart bata zuba maki ido kina shigar da ki kaga dama ba,saboda ta san ciwan kanta”

murmushi kawai Yumnah tayi ta san da ace mom maryam ta san Irfan ke son Noor da ya shiga uku dan saita rabasu may be shima dalilin da yasa kenan yaƙi bari kowa ya sani.


“ku riƙa yi mata nasiha”
“insha Allah mom zamu riƙa yi mata”

“hakan shi yafi”
“mom ina papah?” a cewar su Ammar
“papah na wajen aikin, sai anjima zai dawo”
“Allah ya dawo dashi lafiya” da Amee su duka su ka amsa.

Noor koda ta shiga bedroom ɗin kwanciyart tayi saman bed ɗin ɗakin, wayarta tashi latsawa.



*Uncle Hashim's House*



Zaune suke a parlorn Uncle hashim Laatifa ce kawai babu, mom maimunatu na daga zaune saman sofa mai mazaunin mutum uku Balqis na kwance tayi pillow da laps ɗinta yayinda Uncle Hashim ke zaune saman
rocking chair hannunshi riƙe da jarida yana dubawa.


juyowa Balqis tayi tana fuskantar shi da ƴar shagwaɓa tace “dady wai har yanzu shiru maganar fara aiki na?”

“ayyah sorry my daughter, shaf na manta na faɗa maki munyi magana da ya mutallaf harma na bashi takardunki”
“na gaji da zaman gida ne”
“karki damu zuwa next week za kuyi interview”
“thanks u dady, momy nima na kusa fara fita aiki kamar Aunty Laatifa”
murmushi mom maimunatu ta sakar mata tana shafa gefen fuskarta.


“amma dady a wane hospital ya samar man aiki?”
“muna da wani hospital ne bayan namu?” ya faɗa ba tare da ya kalleta ba
“eh mana dady akwai S J Hospital, ni nafi son can”
“wane hospital ne S J”
“SAM Internati...” kasa ƙarasawa tayi saboda wani kallo da barrister ya watsa mata, dan dole ta shanye sauran maganar,maida hankalinshi yayi kan jaridar da yake dubawa yana jan tsaki.


taɓe baki mom maimunatu tayi “ni da wannan sama mata aikin da miji kasa su ka fitar ita da ƴar uwarta kayi masu Aure in yaso sunyi Aikin a ɗakin mazajensu”


“idan kin tashi Aurar da ƴarki babu wanda zai hanaki amma ni ƴata ba yanzu za tayi Aure ba”

“ban gane idan na tashi Aurar da ƴata ba, wai kai barrister har yanzu bazaka sauko daga dokin zuciyar daka hau ba ka yafe ma ƴarka?”

“bayan Balqis bana da wata ƴa a duniya, karki sake dangantani da ƴarki dan ranki ne zai ɓaci” tashi yayi yana kwashe Jaridar shi, juyawar da zaiyi yaga laatifa a tsaye bakin ƙofa kaf maganganunsu a kunenta, ɗauke kai yayi kamar ma bai gantaba ya nufi bedroom ɗinshi.


juyawa tayi da nufin barin wajen, da sauri Balqis tace“laa Aunty Laatifa yaushe ki ka dawo?” juyowa mom maimunatu tayi tana kallonta

“dawowata kenan ƙanwata, ya kike ya gida?” ta faɗa tana nufo cikin parlorn
“lafiya lau Aunty Laatifa” murmushi kawai Laatifa tayi mata tana nufar mom
“momy barka da rana ya gida?”
“lafiya lau Laatifa, harkin dawo?”



“eh mom,bari na shiga ciki na watsa ruwa duk a gajiye nake” ta faɗa yayinda take juyawa ta nufi bedroom ɗinta, da kallo kawai

Please Login or Register in order to submit comment