Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na nunama Nailarh kuskurenta,zan tabbatar mata da ƙarfin ikona akanta,sai tayi data sanin sanina a rayuwarta” hankalin Aunty Sophia ne ya tashi jin abunda Malika tace,ta san ko wacece Malika zata iya aikata komai akan biyan buƙatarta.
“ma'am Nailarh yarinya ce,idan ki...” bata ƙarasaba Malika tayi saurin ɗaga mata hannun “ko me za kice Sophia bazan saurareki ba,nafi ki sanin Nailarh yarinya ce amma zan nuna mata tsantsar yarinta” tana gama faɗa ta nufi ƙofar fita ta fice,da kallo Aunty Sophia ta bita tana jin wani iri a zuciyarta dama ta san dole hakan ta faru idan har Malika ta san Nailarh ba ita take so ba,tashin hankalinta hukuncin da Malika zatama Nailarh.
dressing room ɗin Nailarh ta nufa tana kiran sunanta.
samun Nailarh har ta sauya kayan jikinta ta shirya wasu kayan cikin box.
lallashinta Aunty Sophia ta shiga yi tana bata haƙuri akan ta zauna,amma bata bi ta kanta ba dan yanzu har ita haushinta take ji,dan gani take kamar tana goyan bayan Malika ne,tana gama ɗaukar duk abunda zata ɗauka taja box ɗinta ta fice ba tare da ta ko kalli Aunty Sophia ba.
girgiza kai kawai Aunty Sophia tayi bata san me zatama Nailarh ta gane kuskuren faɗa da Malika da take ba,bin bayanta tayi tana shiga bedroom ɗin wasu jibga jibgan ƙati daga cikin securitys ɗin gidan na shigowa Malika na bayan su,hannunsu ɗauke da ɗan wani madaidaicin box,wani irin faɗuwa gaban Aunty Sophia yayi da sauri ta nufi Malika
“please ma'am na roƙe ki karki kiyi haka,Ni da kaina zan shawo maki kanta karki kice zaki hukuntata”
ko kallon inda Aunty Sophia take Malika ba tayi ba.
box ɗin dake hannunta ta ajiye buɗe box ɗin tayi,kwalaben allura ne ciki sai tururi suke na sanyi
“kar kiyi haka Malika Nailarh na sonki kawai yarinta ce ke damunta,amma idan ki ka ce zaki mata allurar nan lafiyarta zata samu matsala, Please karki mata allura”
“sophia miye matsalarki da abunda zan yi mata, Nailarh ƴata ce ina da ikon hukuntata yacce na so” tunda su ka fara taƙaddama Nailarh na tsaye tana kallonsu ko a jikinta iya abunda ta sani ko mai zai faru bazata bari suyi mata allurar nan ba.
“na sani Madam,amma ki sani idan ki ka kasheta babu abunda zai sauya,Please kiyi tunanin” murmushi Malika ta daki “nafi ki sanin babu abunda zai sauya Sophia,bana buƙatar Nailarh a yanzu,samun wacce zata maye man gurbinta ba abu bane mai wahala a wuri na” Malika ta faɗa tana miƙama ɗaya daga cikin security allura,da kai ta basu umarni da suyi ma Nailarh allura.
hawaye ne su ka wanke fuskar Aunty Sophia Bata taɓa tunanin Malika zata iya kawar da Nailarh ba.
gadan gadan wanda babu allura ya nufi Nailarh,yana kai hannu zai riƙota ta kai mashi naushi a ido saurin ja da baya yayi yana dafe idonshi,saurin ajiye allurar dake hannunshi ɗayan yayi yana nufarta,da gudu ta juya ta nufi ƙofar toilet ɗinta sai da kafin ta buɗe ƙofar har ya cimmata,damtse hannunta ya kamo ya fisgota baya,gaba ɗaya ta tafi ƙasa,ɗagowar da za tayi ta sakar mashi naushi a gefen ciki,dambe ta shiga yi da su kafin Allah ya bashi sa'a ya sauke mata lafiyyan mari da gaba ɗaya ta faɗin kan floor,rintse ido Aunty Sophia tayi hawaye na bin cheek ɗinta,wata ƴar iskar dariya Mrs Malika tayi tana faɗin “good job,kumata dukan mutuwa idan taƙi tsayawa”
wanda ta dakar ma ido ne ya ɗagota,wani wahalallan naushi ya kai mata aciki,jini ne ya shiga fitowa ta hancinta,da gudu Aunty Sophia ta fice daga ɗakin dan bazata iya jurar ganin rashin imanin da Malika tasa su yima Nailarh ba,shiyyasa kullum take bata shawara amma Nailarh ba taji ba,ta san wacece Malika sosai,muguwace ta ƙarshe amma Nailarh ta kasa fahimta.
Kamar sun samu jaka haka su ka shiga dukanta sai da su ka ga ta daina motsi tukun su ka ƙyaleta, Malika na daga zaune tana kallonsu,ko a jikinta hakan ma ba ƙaramin daɗi yayi mata ba.
da kanta ta ɗauki allura tayi mata,umarni taba security da su ɗauketa,a kafaɗa ɗaya ya saɓata su ka fice daga ɗakin.
wayar Nailarh da laptop ɗinta Malika ta ɗauka ta bi bayan su,a bakin ƙofa ta samu Aunty Sophia,kuka kawai take musamman da taga yanda su ka fito da Nailarh.
wuce Malika tayi,part ɗinta ta nufa,a tsaye ta samu security a bakin ƙofar wani daki dake part ɗinta.
buɗe ƙofar ɗakin tayi suka shiga da ita ciki,cikin ɗakin su ka shiga da Nailarh,ɗakin baya da girma,ɗan ƙaramin bed ne a ciki ko window ɗakin baya da ita kamar ɗakunan prison.
a saman bed ɗin ɗakin ya jefar da ita,ficewa su ka yi daga ɗakin,maida ƙofar ɗakin Malika tayi ta rufe haɗi da dannan wasu Numbers jikin ƙofar wanda ba tantama security ne tasama ƙofar..

*ABUJA NIGERIA*

yau ta kasance ranar juma'a ranar da uncle Jonas yace za su zo,tun jiya dady yasa yumnah tasa masu aiki su ka gyara part ɗin sam,bai sanar da su harda Sam za'a zo ba sai a yau da safe,zo kaga murna wurin yumnah musamman laatifa,kiran Number wayan shi ta shigayi amma bata samu ba,tunani ta fara ko har sun taho ne.
da gudu yumnah ta nufi ɗakin su dan ta sanar da Nainarh zuwan sam ɗin ta san dole tayi farin ciki may be ma haka yasa ta daina fushin da take da ita.
tana shiga ɗakin Nainarh na fitowa daga toilet,bathrobe ne a jikinta da alama wanka tayi,da gudu yumnah ta nufeta “sis labari mai daɗi” kallonta Nainarh tayi ba tare da tace komai ba,yar dariya yumnah tayi tana faɗin “kin san cewa harda ya sam a cikin masu zuwa,yanzu dady ke sanar da mu, Nainarh ba kiji daɗin da naji ba Finally dai Allah ya amshi Adu'ar ki ya Sam zai zo Nigeria bayan tsawan shekaru,am very happy to you” ta kai ƙarshen maganar tana sakin murmushi haɗi da kallon Nainarh,ga mamakinta ko a fuska ba taga alamun labarin yayi ma Nainarh daɗi ba,abun ya ɗaure mata kai,duk irin son da Nainarh kema sam amma ta faɗa mata cewa zaizo amma ba tayi farin ciki ba
“nainarh wai me ke damunki, ya sam fa nace maki yana hanya?” kauda kai Nainarh tayi tana raɓawa ta gefenta ta nufi dressing room ɗin su, hooking yumnah tayi a nan tsaye lamarin Nainarh ya fara bata tsoro,anya ba aljanune suka shiga jikinta ba,gaba ɗaya ta canza idan wani yace mata Nainarh za tayi action irin wannan idan taji labarin zuwan sam baza ta taɓa yarda ba.
bayanta tabi zuwa dressing room ɗin,harta kama handle ɗin ƙofar zata buɗe ta fasa,ta ƴar ƙofar dake jikin ƙofar ta leƙa cikin ɗakin,zaro ido tayi lokacin da idonta ya sauka kan Nainarh da tayi sujjudu shukur a tsakar ɗakin,bata gama fita daga mamakin ba Nainarh ta miƙe ta shiga taka rawa tana faɗin “Allah Alhmdllh, Alhmdllh Allah na gode maka,ya Allah kacika man buri na, Allah kasa na samu soyayyar shi cikin sauƙi, gaskiya nayi farin ciki Alhmdllh” ta faɗa tana sakin dariya kamar zautatta, yumnah bata san lokacin da itama ta saki dariyar ba ko ba komai ta san ƴar uwarta tata lafiyar ta lau kawai fushin da take da ita ne ya hana ta nuna farin cikinta.
saurin barin bakin ƙofar tayi dan karma Nainarh ta fahimce tana kallonta,ficewa tayi daga ɗakin.
shirye shirye su ka shiga yi na tarbar baƙi,dady kallo ɗaya zaka mashi ka hango tsantsar farin cikin da yake ciki hakama mom,su ya Naeem tun wuraren ƙarfe 10 na safe su ka zo gidan tare da su Aunty Nadeeya,mom Maryam ma ta zo tare da su Ammar,ta zo duba jikin kainart da taji labarin zuwan su sam ɗin ne yasa ta tsaya.
Ƙarfe 4 na yamma mazan suka nufi airport Dan tarbosu harda uncle mustapha,ƙarfe 5 jirginsu zai iso amma dady yace su tafi da wuri,ya ƙosa yayi ido biyu da sanyin idaniyarshi, yumnah babu yanda bata yi ba dan a tafi da su amma ya Naeem yace A'a, Laatifa ma ta so tare da su za'a je Airport ɗin amma da ya Naeem ɗin yace A'a sai ta hakura.
Ƙarfe biyar daidai aka fara sanar da isowar jirgin daya ta so daga los Angles California,zambur dady ya miƙe daga saman waiting chairs ɗin da su ke zaune,fuskarshi ɗauke da murmushi ji yake kamar ya nufi filin jirgin ya taraso a can,farin cikin shi ya kasa ɓoyiwa,zuba mashi ido su ya Adnan su ka yi ya Naeem na faɗin “gaskiya dady mun fara kishi,irin wannan damuwa haka” murmushi dady yayi mashi “baza ka gane bane Naeem” murmushi ya Naeem ɗin yayi yana girgiza kai.
passengers ne su ka fara ɓullowa ta ƙofar da aka rubuta Arrivals.
mutane ne suka shiga fitowa ɗauke da boxs ɗin su.
tunda passengers su ka fara fitowa su ka baza ido burin su kawai su ga ta inda za su ɓullo.
Wani kyakkyawan baturen matashin tsoho ne ya ɓullo daga ƙofar,sanye yake cikin blue black ɗin suit, idanunshi a manne suke da farin glasses,sumar kanshi kamar ba ta dattijo ba sai sheƙe take tana ɗaukar ido,fuskarshi ɗauke da murmushi yayinda wasu zaratan samari masu jini a jika ke biye da shi su biyu,hannunsu riƙe da trolleys ɗin su,ƙananan kaya ne a jikinsu,Allah yayi su da surar jiki mai matuƙar jan hankali,fuskokinsu a rufe su ke da mask,walking majestically su ke nufo cikin filin airport ɗin.
su dady ne su ka nufo su fuskokinsu ɗauke da murmushi,hugging juna dady su kayi shida wannan dattijon yana masu barka da zuwa,raba jikinsu suka yi,kallon wannan samarin dady yayi fara'ar fuskarshi na daɗa ninkuwa,ɗaya bayan ɗaya suka shiga hugging ɗin su dady ba tare da sun zame mask ɗin dake fuskokinsu ba,kasa haƙuri dady yayi har sai da yace “wai baza ku ɓuɗe fuskokin ku ba ne” dan ya fara zargin wani abu daga muryoyinsu,zame mask ɗin su ka yi suna sakin murmushi da ya ƙarama fuskokinasu kyau,Masha Allah na furta a yayin da nayi arba da fuskokin kyawawan samarin,kyawawa ne na gaske,komai nasu iri ɗaya hatta gyaran gashin su iri ɗaya ne kamar twins haka su ke,launin fata ne kawai ya banbanta su sai zanen tatto da earring da ɗaya ke dashi wanda ko ba'a faɗa maka waye shi ba tsananin kamar da yake da dattijon nan da yumnah zai tabbatar maka da ɗan sa ne,ɗayan kuwa kallo ɗaya zaka mashi ka hango kamaninshi da mahaifiyar sa Aunty mariya.
yanayin fuskar dady ne ya sauya,a hankali ya furta “james,Alyar!” da fa'arsu su ka amsa mashi
“ina sam ɗin yake?” ya faɗa yana bin fuskokinsu da ido, kallon juna su ka yi fara'ar dake fuskokinsu na ɗauke,kasa ce mashi komai su ka yi,cikin ƙunar rai ya ce “yanzu ma bai zo ba?” jinjina mashi kai su ka yi “eh dady, uzuri ne na gaggawa ya taso mashi shiyyasa bai zo ba”
hawaye ne su ka taru a idonshi dama ya daɗe yana tunanin ta yarda sam zai biyo su cikin sauƙi ba tare da gardama ba.
cikin tsantsar ɓacin rai ya shiga faɗin
“wai me sam yake nufi da ni ne a rayuwar nan,me na aikata mashi da yake wannan fushin da ni,Ni mahaifinshi ne amma ya ɗauki karan tsana ya ɗaura man,irin tsanar da yayi man ko maƙiyinshi bai kamata yayi ma ita ba,na lura yafi son mutuwa sama da rayuwata,kullum cikin azabtuwa nake da soyayyar shi,amma hakan bai sa yayi man adalci ba,nayi ban haƙurin,nayi lallashin,ban san iya adadin zuwan California dan na ganshi ba,amma duk a banza haka zan ƙaraci zamana na dawo ba tare da na ganshi ba,me sam ya ke so nayi mashi wanda zai sa ya fahimci halin dana shiga saboda rashin shi a tare da ni,me zan mashi wanda zai sa ya fahimci irin son da nake mashi???” ya kai ƙarshen magana hawayen dake kwance cikin idonshi na bin cheek ɗin shi,da sauri uncle Jonas yasa hannu yana goge mashi hawayen,babu wanda jikinshi baiyi sanyi ba a wurin ba
“kayi haƙuri Tahir, uzuri ne ya taso mashi kamar yarda Alyar ya faɗa,da badan uzurin mai girma ba ne nima da bazan barshi ba,amma ya tabbatar man da yana nan zuwa kafin mu tafi,kayi haƙuri” uncle Jonas ya faɗa
“baya son ganina ne kawai Jonas,har yanzu fushi yake dani” girgiza mashi kai uncle jonas yayi yana sake bashi haƙuri.
wani irin ɓacin rai ne ya rufe ya Naeem ganin halin da dady ya shiga,bai taɓa jin haushin sam irin na yau ba,dan me zai dinga wahalar masu da mahaifi dan kawai ya fahimci yana sonshi
“dady ka daina zubar da hawayenka akan shi,ni nayi maka alƙawari a yau ba sai gobe ba zamuje har California ni da Adnan,komai zai yi sai mun kawo maka shi har gida” ya Naeem ya faɗa
“ba sai kunje ba Naeem,da kaina zanje na sameshi,idan ma kashe ni zaiyi ya kashe ni,amma nagaji,nagaji!!” uncle mustapha ne ya yayi saurin cewa
“A'a baza'ayi haka ba yaya,tunda har yace zai zo nan kwana biyu,mu jirashi mu gani idan bai zo ba ni da kaina zanje na zo maka da shi,kayi haƙuri”
“baza ka gane ba mustapha,ku barni kawai na tafi,bazan iya jira har tsawan wannan kwana kin ba,ni ka ɗai na san yanda nake ji”
“na sani yaya,amma kaga baƙo ka yi bai cancanci ka tafi ka barshi ba”
“kayi haƙuri Tahir,idan ma bai zo ɗin ba sai mu tafi tare da kai” a cewar uncle Jonas,
ya Naeem ne yace“uncle to ku bari ni da Adnan ɗin mu tafi”
“A'a Naeem,babu wanda zai tafi”
lallashin dady su ka shiga yi akan ya jira nan da kwana biyu idan sam ɗin bai zoba sai su tafi,da ƙyar su ka samu suka shawo kanshi.
babu wanda ranshi bai ɓaci da rashin zuwan sam ɗin ba.
haƙuri uncle mustapha ya sake ba dady yana kamo hannunshi,bin bayan su suka yi har inda su ka yi parking motocinsu,motar uncle mustapha dady da uncle Jonas su ka shiga yayinda Alyar da James su ka shiga mota ɗaya da su ya Naeem,reverse su ka yi su ka fice daga Airport ɗin.
ya Naeem tunda su ka shiga mota yake dialing number Sam amma kiran baya tafiya
tsaki yaja,kallon shi ya Adnan dake driving yayi yana faɗin “lafiya dai ko,waye ka ke kira??” kamar jira yake ya Adnan yayi magana ya shiga surfa masifa ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,shiru su kayi motar babu wanda yace mashi wani abu har ya gama dan sun fahimci ranshi yayi mugun ɓaci.
“ni gaba ɗaya a wannan al'amarin nafi ganin laifin dady,Allah ya bashi mu da yawa amma dan me zai hana kanshi zaman lafiya saboda shi,da ace tuntuni ya watsar da lamarinshi da bai rika ɓata mashi rai irin haka ba kuma shima da bai gujeshi ba,amma dady ko za kayi me kana bashi shawara akan Sam baya ɗauka,ya ɗauki son duniya ya ɗora mashi” ya Adnan ya faɗa rai a ɓace
“tun yaushe nake nunama dady haka amma kwata kwata baya ganewa,ya fi son depression ya kamashi saboda sam”
“dan Allah second father kuyi haƙuri,uzuri ne ya riƙe shi amma ba da gangan yaƙi zuwaba,dashi mu ka yi shirin zuwa Allah ne bai nufa ba” Alyar ya faɗa,suna matuƙar son ɗan uwansu duk sai su kaji ba daɗi da maganganun su ya Naeem,duk da suma kan su basa jin daɗin halin da ya ke nunama dady,basu da yanda za suyi ne kawai
“uhmm kana son kareshi ne kawai Alyar,amma ni na san babu wani uzuri daya riƙesa,kawai yayi ne dan yaga halin da dady zai shiga,sai dai ya sani muddin dady ya faɗi ya mutu da ɓaƙin cikinsa Allah bazai barshi ba”
“ya subahanallah,dan Allah ya Naeem ka daina faɗar haka,da badan uzurin daya riƙesa ba da babu abunda zai hanshi zuwa,amma in sha Allah yana nan zuwa soon”
“dole na faɗin haka Alyar,sam ya matuƙar ɓata man rai yau,a iya sanina baya da jahilcin addini,ya san cewa iyaye ba abun wulaƙantawa bane,amma ya koma kamar wanda bai taɓa sanin komai a addininsa ba,shi ko tsoron Allah ya kamashi da alhakin mahaifinsa bayayi??”
“haka ne second father,in sha Allah komai zai wuce,nan da two days yana nan zuwa”
“wallahi kar Allah ya sa ya zo,ai duniya ce wanda bai zo ba ma jiranshi take bare wanda ke cikinta” girgiza kai Alyar yayi baya jin daɗin kalaman da ya Naeem ɗin ke faɗa,haƙuri su ka shiga ba su shi da James, ya za suyi da halin ɗan uwan nasu lamarin nashi ne sai Adu'a.
dady tunda su ka shiga mota ƙala baice ba kana kallonsa kasan yana cikin damuwa,haƙuri uncle Jonas ya sake bashi yana sake tabbatar mashi da uzuri ne ya riƙe sam ɗin amma yana nan zuwa kafin su tafi,jinshi kawai dady yake amma ya san babu wani uzuri daya riƙesa kawai baya son ganinsa ne,kullum cikin Adu'a yake Allah ya rage mashi son shi amma ina yanzu ya fara tunanin sonshi ne ajalinshi.
har suka iso gida babu wanda ya sake cewa komai.
mom tayi matuƙar farin ciki da zuwan kawun nata sai dai ta wani ɓangaren tayi takaicin ƙin biyo su da sam ɗin yayi sai dai ba ta nuna hakan ba ta barshi akan da sun tashi tafiya ƙafarta ƙafarsu,ita za taje da kanta ta dawo da shi.
babu wanda baiji haushin rashin zuwan sam ɗin ba musamman laatifa da Nainarh,dan Nainarh ɓoyewa tayi a bedroom ɗin su tasa kuka,taci burin ganinshi amma yaƙi ya zuwa,Abbah ma yaji haushin rashin zuwan sam ɗin,har kiran wayarshi yayi amma bai sameshi ba da yake gidan shi su ka fara zuwa,uncle Jonas baiji daɗin rashin samun uncle mutallab da mom Fatilah da yayi ba,yaso ace yayi masu ta'aziyya ido na ganin ido,sun ɗan jima a gidan Abbah kafin suka nufi gidan dady,acan su ka sa mu uncle Ubaid da uncle Hashim sun zo yi ma uncle Jonas barka da zuwa ba su san sun tafi airport ba da sun je tarbosu.
Tarba ta musamman uncle Jonas ya samu daga ahalin Abbah hakan kuwa baƙaramin daɗi yayi mashi ba,ya sake tabbatar da karamcin su,ba wannan bane zuwanshi na farko ba.
Alyar basu wani jima a Estate ɗin ba su ka nufi gidan su shi da James duk da dady ya so su zauna part ɗin sam amma Alyar yace zuwa gobe za su dawo.
su uncle Ubaid sun jima sosai a gidan,fira sosai su ka sha da uncle Jonas,sai da dare yayi sosai tukun su ka yi mashi sallama su ka koma gida.
su uncle ubaid na tafiya dady ya rakashi bedroom ɗin dake kusa da nashi wanda mom ta gyaramashi,zama dady yayi,kwantar mashi da hankali uncle Jonas ya shiga dan ya lura har yanzu da sauran damuwar duk da yana ƙoƙarin dannewa,murmushi kawai dady ya mashi yana faɗin bakomai zai jirashi nan da kwana biyun,mom ce ta shigo ɗakin,tashiga ɗakin dady bata ganshi ba yasa ta zo nan,kusa da kawun nata ta zauna tana sake mashi sannu da zuwa da tambayar lafiyar mahaifiyarta da matarshi,duk suna lafiya yace mata yana tambayar Irfan da tunda ya zo bai sa shi a ido ba.
tunda safe ya fice daga gidan zuwa aso Villa,tunda aka yi rasuwar bai fita ba sai yau.
sun ɗan jima a ɗakin sosai suna buɗe wani babin firar yaushe gamo,sai da dare ya raba sosai tukun su ka yi mashi sallama su ka fice.
bedroom ɗin dady su ka nufa
“Naeem ya sanar dani komai daya faru,ni kaina banji daɗin rashin zuwan sam ɗin ba amma dan Allah kayi haƙuri ka cire damuwar sam a zuciyarka,ganin ka damu dashi ne yasa yake wahalar da kai,kuma bai kamata kana nuna tsantsar soyayyar shi a gaban ƴan uwanshi ba”
“Zulaihart ni kaina ban san wane irin so nakema sam ba,bana iya ɓoye soyayyar shi a ko ina”
“na sani ƴallaɓai amma daurewa za ka yi,ko dan saboda ƴan uwanshi,kullum burin su su faranta maka,Ni na san basa jin daɗin banbancin da kake nunawa tsakanin su da ɗan uwan su kawai suna daurewa ne yasa ba su taɓa nuna maka ba” ta san su ya Naeem kawai baza su faɗa bane amma dole suna jin ba daɗi da irin soyayyar da yake nuna ma sam ɗin
“in Allah zan gwada yin hakan”
“Allah ya sa” lallashin shi ta shiga yi tana sake kwantar mashi da hankali har bacci yayi awan gaba da su.
dady sai da ya tabbatar da mom tayi nisa a cikin baccin tukun ya tashi, toilet ya shiga bai wani jima ba ya fito,jikinshi da damshin ruwa da alama wanka yayi, dressing room ɗin shi ya nufa,mom na nan kwance tana bacci ya fito har ya shirya cikin suit silver color,wayar shi dake ajiye saman nightstand ya ɗauka,matsawa yayi kusa da ita, kissing forhead ɗin ta yayi kafin walking calmly
ya fice daga ɗakin.
lokacin da zai isa compound har driver shi ya fito da mota da alama ya jima da sanin tafiyar,back seat ya buɗe mashi ya shiga kafin shima ya shiga mazaunin driver,reverse yayi su ka ɗauki hanyar ficewa daga Estate ɗin.
tunda ya fito yake laɓe jikin Piller yana kallon su sai da ya daina ganin motar ta su tukun ya fito,baƙaƙen kaya ne complete a jikinshi,ya rufe ko ina a jikin shi,hannu ya zura cikin trouser pocket ɗin ya ciro waya,dialing wata number yayi,wanda ya kira na picking yace “boss yanzu nan ya fita daga gida” bana iya jin me na cikin wayar ke faɗa mashi sai ji nayi yace “ok sir an gama” zame wayar yayi daga kunnenshi,ya nufar bayan gidan.


*A ROUND 3 AM*

Ƙarar wayarta ne yayi sanadiyar farkawarta,hannunta ta zura tana laluben switch ɗin bed-side lamp ta kunna,hasken ne ya ɗan haska gadon,idanunta ta kai ga dady dake kwance kusa da ita ga mamakinta baya nan, tunanin ta fara ko yana toilet,
a hankali ta kai hannunta ta jawo wayar tana duba mai kiran nata,faɗuwa gabanta yayi ganin number dady, saurin kallon agogon dake manne jikin bango tayi wanda ke nuna ƙarfe 3:40 na dare kafin ta kalli wayar tana mamakin to ina yaje a wannan lokacin da har yake kiranta a waya,har kiran ya katse ba tayi picking ba wani ya sake shigowa, picking tayi tana kara wayar kunnenta,on the other side taji wata murya saɓanin ta dady nayi mata sallama,saurin sauka tayi daga saman bed ɗin gabanta na wani irin mummunan faɗuwa,to waye wannan me ya kai wayar mijinta hannunshi,da ƙyar ta samu tayi ƙarfin halin faɗin “bawan Allah waye kai,ina mai wayar yake ⁉️”
“dan Allah da katte nake magana” bugun zuciyarta ne ya tsananta jin sunan da na cikin wayar ya ambata,cikin rawar murya tace “Eh itace,waye kai,ina mai wayar yake⁉️”
“ya gamu da haɗari ne a...” ai tun kafin ya ƙarasa ta saki wayar hannunta,kamar saukar aradu haka taji zancan nasa,ficewa tayi daga ɗakin kamar zata tashi sama ita kanta bazata iya cewa ga halin da take ciki ba,tana shiga main parlor ya Naeem da ya Adnan na faɗowa,tana ganin su kawai ta yanke jiki ta faɗi.....
*INNALILLAHI WA INNAH ILAIHI RAJI'UN,ALLAHUMMA AJIRNI FI MUSIBATI WA'AKLIFLI KHAIRAN MINHA,LAHAULA WALA QUWWATA ILLAH BILLAHIL ALIYUL AZIM*

*ina dady zashi,waye ke sanar da fitowarshi,wa yake sanar mawa,ta ya akai wannan haɗarin ya faru da shi⁉️*
*Shin bari mu koma baya*
*Wacece wannn baturiyar data haihu a ɗakin hotel har tayi sadaka da ƴarta ba tare da ko taji ɗumin jikinta ba,sannan su waye mata da mijin data yima sadaka da ƴarta⁉️*
*Su waye ke bibiyar rayuwar Nainarh,taya akai Abid ya rayu bayan an shida ma court mutuwarshi,wane flash ne mahaifin Nainarh ya bata,ina Flash ɗin yake,shin da gaske ne yumnah ce ke bibiyar Nainarh,su waye su ka kashe mahaifin Nainarh⁉️*
*Shin da gaske Zaabith na tare da uncle Mustafa ko dai kawai zargi ne⁉️*
*Waima waye ya kashe Noor,wace masifa ce tasa kanta a ciki,su waye bayin Allah data taimaka,menene a cikin Flash ɗin data ba Irfan,wane zaɓi ne take cewa tayi mashi⁉️*
*Shin kuna ganin hukuncin da uncle mutallab ya ɗauka akan mom Fatilah ya dace❓*
*Wacece Carol ne❓*
*shin kuna tunanin Nailarh ta rayu bayan duka da Allurar da mahaifiyarta tasa aka mata,waye CEO dake bibiyar Nailarh,wacece Aunty Sophia,Allurar mecece taba Noah ya ba Mrs Malika,waye mijin Mrs Malika,wane yara ne Nailarh ta gani a container lokacin da mahaifiyarta ta turo masu da kaya,Mrs Malika wace irin uwa ce ita dake neman ƴarta,wace irin uwace da zata lalata rayuwar ƴarta,wane irin business ne ma take yi⁉️*
*Club ɗin waye su Irfan ke kula da shi,wacece yarinyar

Please Login or Register in order to submit comment