Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

shi yana kan mu.

Zungurin Sadiq yayi tare da yi mishi magana da ido, cikin sauri Sadiq yabi bayan mu ya tsaida mu yace " nan anguwan abin hawa yana wahala bari mu sauke ta tunda muma fita zamuyi"

Cikin farinciki Maryam ta fara musu godiya tare da jan hannu na zuwa wajan wata mota daya bud'e mana, da ido nakewa Maryam nuni da ba zan shiga motan su ba ita kuma ta min nuni da babu komai 'yan gida ne, rashin karfin jiki da hajijiya da nake ji ya bata daman tusa ni a bayan motan ta rufe tana d'aga mana hannu.

Kwantar da kaina nayi a jikin seat d'in tare da lumshe ido na fara shak'an wani fitinannen kamshi da ban tab'a ji ba a rayuwa ta, ina ji motan ya fara tafiya amma na kasa bud'e ido na can naji Sadiq d'in yana tambaya ta wani anguwan zasu sauke ni? Sai da naji a jiki na alaman ana kallo na ban damu da in bud'e ba saboda nasan sunan anguwan mu da na fad'a ne ya bashi mamaki kasancewar duka gidajen talakawa ne a anguwan.

"Sai ki nuna mana inda zamu bi mun shigo anguwan naku" muryan Sadiq ya katse min tunani, a hankali na bud'e ido sannan na nuna mishi hanya da zamu bi can nesa da gidan mu nace ya sauke ni anan.

Parking yayi daga gefe na bude kofan na sauka sauka a hankali cikin muryana mai sanyi da baya fita sosai nace " nagode jazakallahu khairan" na kama hanyan gida ina layi,da ido Sadiq ya rakani har na shige ciki.

Gyaran murya Zafar yayi wanda ya dawo da hankalin Sadiq ya juyo yana kallon shi yace" sai ka gaya min ma'anan kawo ta gida sannan dan wulakaci kaja baki kayi shiru na tabbata bata san mu 2 muka kawo ta ba.

"Mu tafi Mallam ba wai ka kama min tambayoyi ba" Zafar yace hankalin sa na kan wayan shi, girgiza kai kawai Sadiq yayi yaja motan suka fita daga layin dan wannan halin abokin nashi ya ci ace ya saba.

Da kyar na kai kaina d'akin mu na zube a gefen Inna da take kwance a kan gado,a firgice ta tashi zaune saboda ta fara bacci kuma bata ji shigowa ta ba.

"Wani irin rashin hankali ne wannan zaki shigo min d'aki ba sallama sannan kuma ki fad'o min a ka sai kace wata 'yar maye, ko daga wajan bikin kika koyo ne..." Shasshekan kuka na da taji shiya dakatar da ita daga fad'an da take min cikin fargaba ta d'ago ni ta fara dudduba jikin na tana tambaya ta meya faru???

"Inna Yaya na yau kusan sati da yin tafiya amma har yanzu babu labarin shi ga wayar shi bata shiga, Inna tsoro nake ji anya yana lafiya kuwa? Yaya na ba zai tab'a mantawa dani ba har na tsawon sati ba tare da yaji lafiya ta ba Inna kin..." Rufe min baki da Inna tayi da hannun ta yasa nayi shiru ina kallon ta hawaye na bin fuska ta.

"Babu abinda ya same shi insha Allah yana cikin koshin lafiya,bana son kina sawa kanki damuwa dayawa ki bari zuwa gobe da safe sai mu san yanda zamu bullowa lamarin" duk cikin rarrashi take min magana hannun ta kuma na kaina tana shafa gashina daya sha gyara ya kwanta yayi lub.

Jin ina sauke ajiyan zuciya kuma numfashi na fita d'aya-daya yasa ta gane nayi bacci, gyara min kwanciya tayi tare da zuba tagumi ta zauna tunani yanda zata bullowa wannan al'amarin domin babu abinda yake d'aga mata hankali kaman ganin tilon 'yar ta cikin tashin hankali, balle ma wannan na soyayya.

Kusan raba dare Inna tayi kan sallaya tana nafilfilu tare da kai kukan ta wajan Rabbi izzatti ya shiga lamuran 'yar ta ya zaba min abinda yafi alkhairi.


Koda gari ya waye da kyar na tashi daga kan gado nayi sallah na kara komawa na kudundune cikin bargo ina rawan dari saboda sabon zazzab'i da ciwon kai daya tsanan ta min, cikin matukar damuwa Inna ta had'a min tea mai kauri ta lallab'a ni na sha kad'an sannan ta b'allo paracetamol 2 ta bani tace in sha zuwa azahar in babu sauki sai mu tafi asibiti.

Cikin ikon Allah ina kwanciya bacci mai nauyi yayi gaba dani sakamakon jiya ban samu ishasshen bacci ba, gaba d'aya fita daga d'akin Inna tayi wai kada tayi wani babban motsi ta katse min bacci anan ta cigaba da ayyukan ta cikin dauriya.

Kaman a cikin mafarki naji waya ta tana ringing, da kyar na bud'e ido na da suka min matukar nauyi.

A zabure na tashi na zauna ganin sunan da na gani yana yawo kan screen d'ina, a hanzarce na d'aga kiran na kai kunne na kamin ya min magana na fashe mishi da matukar kuka kaman zan shid'e.

"Ki fito ina waje" yace min cikin wata murya da ban san shi da ita ba, amma duk da haka ban tsaya b'ata lokaci ba na diro daga kan gado dama da hijabin da nayi sallah asuba a jikina na kwanta dan haka takalmi kawai na zura na fito kofar gida ko lura da Inna dake tsakar gida banyi ba burina shine inje in saka shi a idanu na ko zanji sanyi a cikin raina.

Inda ya saba parking anan na gan shi tsaye ya juyawa kofar gidan mu baya haka kawai sai naji jikina yayi sanyi sosai a haka naja kafa na isa inda yake cikin murya na daya dashe saboda kuka da nasha nayi mishi sallama.

Amsawa yayi yana juyowa muka fuskanci juna, kasa tsaida hawayen ido na nayi ina kallon fuskar shi mai sanyaya min rai nace" barka da zuwa Yaya na aikin ne ya rike haka, wannan karon ka dad'e sosai har ya saka ni cikin matukar damuwa ga number ka bata shiga".

"Lafiya lau mana, hmmm kema dai Zareefa meye abin damuwa anan kin san in nayi tafiya bana saka miki ranan dawowa balle kice har kwanakin sun wuce ban dawo ba sannan tun a baya na gaya miki wajan babu network shiyasa bana iya kira ko a kira ni". Ya bani amsa hankali kwance.

Amsar yasa duk naji wani iri amma na daure tare da share hawayen fuska ta da gefen hijabi na ina sakin mishi murmushin da nasan yana saka shi farinciki nace" hmm ka gama komai ka yanzu dan wallahi in akayi mana aure ba zan yarda kana tafiya kana bari na ba
kafar ka kafata".

Sun glasses na fuskan shi ya gyara yana kallo na ta ciki yace" Zareefa kenan kin ga matsalar ki kenan wanda yasa nake ganin ba zamu iya zama inuwa d'aya ba".

Rass-rass naji zuciyata ta wani irin bugawa da har sai da na kai hannu na kan tsaitin wajan ido a waje nake kallon shi dan na rasa bakin magana, can dai nayi dariya kad'an ganin bai kara ce min komai ba nace " Allah Yaya na ka bar min irin wannan wasan zaka saka zuciya ta bugawa wallahi".

"Wasa!! Wasa fa kika ce, u see kina da matsaloli dayawa a rayuwar ki da in mutum ya duba koya auna ba zai fara ma kusantar inda kike balle maganan aure ya shiga tsakani, ke ko irin kunyan nan da aka san mace dashi baki da ita kullum maganan ki d'aya aure-aure mtsw..." Yaja dogon tsaki yana kawar da kai gefe kaman yaga abin kyama.

Ko kifta idona na kasa yi balle in iya cewa wani abu kawai ji nake wasa yake min jira nake in ga ya juyo yace min wasa yake amma ko kallon inda nake bai kara yiba.

Murya na rawa da son kara tabbatarwa kai na ba mafarki nake ba nace" Yaya na kaine kuwa ,nice fa kanwar ka Zareefa".

"Zareefa my foot me mutum zaiyi da macen da bata kamun kai, tunda can daure zuciya ta nake tare da saka ran zaki canza wata rana sai dai da alamu nayi kuskure dan abin naki kara gaba yake.

Pls ki bar nan in daina ganin ki ko zuciya ta zatayi sanyi saboda yanzu ko ganin ki nayi zuciya tafasa yake, dama abinda ya kawo ni kofar gidan ku kenan kada ki kara kira na a waya cos I don't have time for cheap girls like u". Yace yana min wani kallon tsana.

Wani irin kuka na fashe da shi na juya zuwa cikin gida da gudun tsiya har bana iya ganin gaba na, saura kad'an in mangaje Baban mu da yazo fita yayi sauri ya bani hanya na wuce shi zuwa cikin gida ko waiwayowa banyi ba duk da kira na da yake ta faman yi.

A masifance yace" wani d'an kwal uban ne ya tab'a ki a anguwan nan, bari inje in gani duk wanda na gani mai raba ni dashi sai Allah" ya faman gyara babban rigan shi ya nufi hanyan fita.

Da sauri ya dawo da baya yana zare ido tare da dafa kirji yace" wai-wai dama da wannan hukuman ne?????
[1/26, 7:08 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*19*

"Masha Allah an gode ranka ya dad'e har zaku tafi kenan?" Su Zafar suka tsinkayi muryan Baban mu a bayan su, wani malalacin murmushi yayi sannan ya juyo yana yiwa Sadiq signal da ido.

"Eh Baba zamu wuce tunda jikin nata da sauki sai mun kara dawowa" Sadiq ya bashi amsa ya juya zuwa ga motan nasu.

Zafar gaban Baban mu ya dawo ya tsugunna yana wani sunkuyar da kai kaman mutumin Kwarai yace" nagodewa Allah daya had'a ni da kai Baba, dama na dad'e ina son muyi magana amma ta ki hadani da kai".

"A'a ranka ya dad'e ni kuma gani na abu ne mai sauki me kake bukata?" Baba ya amsa jiki na rawa.

Sai da ya d'an sosa keya alamun yana jin nauyin abinda zai ce yace" Abba ne yake son su zo ayi maganan aure na da ita, shine nace bari in fara fad'a maka in ka amince sai su zo" wannan karan Baba rasa inda zai saka ran sa yaji dad'i yayi ji yake kaman ya kurma ihun murna sai dai ba hali cikin sauri har muryan shi na rawa yace" kai amma yaro yaro ne meye na wani sai an tambaye ni, bayan babu inda zan je kullum ina gida. Ko yau suke so su zo ina jiran su kaji?".

"Toh Baba nagode, mu zamu tafi" yace tare da mikewa ya kara ciro wasu bundles d'in ya zubar da su a gaban Baba sannan ya mike har suka fita daga compound d'in Baba bai dawo daga suman ganin makudan kud'ad'e daya tafi ba.

Sun hau kan hanya ba tare da Sadiq ya kalle shi ba yace " Zafar it's wrong, it's totally wrong".

"And who are you to say so?" Zafar ya tambaye sh yana kara cin magani, Sadiq bai kara ce mishi uffan ba sai ma kara maida hankalin shi da yayi kan tukin da yake.

A nan asibiti kuwa Gwaggo Aisha kasa zaune ta kasa tsaye sai jujjuya ido take wai me yake shirin faruwa ne, bata gama da wancan ba kuma ace ga wani ya bullo? Ita abinda yafi d'aga mata hankali shine ita 'yan matan ta basa samun masu kud'i sai ni, shi wannan kam bayan mai kud'in ne kuma gashi balarabe.

"Wallahi ba zata tsabu ba wai bindiga a ruwa wannan karan sai ta raba ni da komai na jin dad'in rayuwa ko da duk abinda ta mallaka zasu kare ba zata tab'a zuba ido Bintu da 'yar ta su kasance fiye da ita da yaran ta ba.

Kaman wacce aka tsikare ta da allura muka ga zuruf ta mike fuuu tayi waje kaman wata kububuwa,da ido kowa ya bi ta dan tunda su Zafar suka fita babu wanda yayi magana cikin d'akin kowa da kalan tunanin da yake a cikin zuciyar shi.

Tashin hankali da Gwaggo Aisha ta tarar a waje yasa taji kaman ta kurma ihu dan bakinciki, akan idon ta Zafar ya yiwa Baba kyautan makudan kud'ad'e suka shiga mota su dashi kad'ai ta kalla ta san cewa kud'in sa ya wuce duka tunanin ta.

Ganin Baban mu ya hangame baki ya kasa dawowa hayyacin sa tunda yaga ruwan kud'i ya kara tunzura ta, ta taho a fusace ta cikin d'aga murya tace "kai Mallam meye haka?" sai a sannan yaja doguwar ajiyan zuciya ya juyo ya kalle ta,ba tare da yace mata ci kanki ba ya kwashi kud'add'en sa yayi gaba abin shi.

Sosai Gwaggo Aisha ta shak'a wato ya mai da ita mahaukaciya ko? Zasu gani zata nuna musu ainihin true colors d'in ta zasu san da ita suke zancen, sai matsayin ta na da ya dawo ta cigaba da mulkan gidan baki d'aya.

Bayan fitan Gwaggo Aisha Inna abu da Hajara suka mike sukayi mana sallama tare da yi min Allah kara sauki suka fita, cikin sauri Inna tabi bayan su dan basu kud'in mota d'akin ya kasance daga ni sai Maryam da Maa da ta juya mana baya ta kwanta da alamu dai tayi bacci.

"Ni fa na kasa yarda Yaya na zai min haka, saboda yana matukar so na Maryam wallahi yana so na" na karasa ina fashewa da sabon kuka.

Gyad'a kai kawai Maryam ta iya yi min tana share hawaye itama saboda ta shiga duhu sosai a yanda muke matukar son junan mu ace ya juya min baya lokaci d'aya, tabbas babban al'amari ne zai iya raba mu , addu'an ta Allah ya daidaita tsakanin mu.

"Kiyi hakuri Zareefa ko wani tsanani yana tare da sauki, mu cigaba da addu'a insha Allah komai zai daidaita" ban iya bata amsa ba sai kuka da nake ina jin zuciya ta na min wani irin suya.

"Hmmm ni ban san su Ya Sadiq me ya kawo su nan ba abin ya daure min kai" cikin sauri na d'ago da kaina ina duban ta dama tambayoyin dake cin raina kenan su waye su, kuma menene dalilin zuwan su har asibiti duba ni ba dan ni dai ban san su ba.

"Ai na zata wajan ki suka zo " na fad'a da dashassiyar murya ta.

Girgiza kai ta shiga yi kana tace " ko d'aya, na shirya ina shirin zuwa duba ki kiran Ya Sadiq ya shigo bayan na d'aga mun gaisa yake tambaya ta labarin ki shine fa nace mishi nima yanzu zan zo duba ki anyi admitting d'in ki a Kanem Hospital, sai naji yace suma gasu nan zuwa in sun iso zai kira waya ta in shigo da su. Ni dai da toh na bi shi ina mamakin ya akayi ya samu number ta".

Ido kawai na zuba mata ina sauraron ta itama tace haka toh ni kuma in ce me kenan.

"D'ayan kuma shine Zafar Baban shi multi millionaire ne maybe ma zaki san shi sunan shi....."

Saurin katse ta nayi nace" bana bukatan ji koma shi d'an wanene wannan damuwar shi ce nima ki bar ni inji da nawa damuwar".

Shigowan Inna yasa muka bar zancen ta cigaba da bani baki, cikin dabara ta zubo min pepper soup na kayan cikin rago da ta kawo min naci ba laifi da yake tana ta Jana da hiran Yaya na sai gashi na d'an ware muna hira.

Sai kusan azahar sannan Maryam tayi mana sallama ta tafi, a takaice sai da nayi kwana 2 a asibiti sannan aka sallame mu.

Cikin kwanaki 3 nan da nayi a asibiti kullum ido na yana kan hanya wai ko zanga Yaya na yazo duba ni yace min wasa yake amma shiru kuma kullum cikin gwada layi shi nake amma ko sau d'aya bai tab'a shiga ba.

Cikin kwanaki 3 nan da mukayi a asibiti abubuwa da yawa sun faru cikin su kuwa yanda Zafar ya bi ya shiga jikin Baban mu yayi amfani da son abin duniya na Baban mu ya saye shi tsaf har yayi mishi alkawarin bani da wani miji a duniya sai shi, hakan kuwa ba karamin dad'i yayi mishi ba dan ya san yanzu bashi da matsala ta ko Ina .

Da yamma muka dawo gida nan da nan gidan ya cika da makota da basu samu daman zuwa asibiti duba ni ba suka shigo suna min ya jiki, har mutanen suka watse Gwaggo Aisha bata shigo ba dama rabon ta da asibitin tun ranan da suka je duba ni dukkan su daga nan bamu kara ganin ta ba sai Inna Asabe ce mai zuwa ita da Hajara, Jameela kam tunda aka kwa tar dani bamu ga keyar ta ba balle kuma yanzu kila ma bata gidan ta fita wannan gantalin nata.

Zafar da Sadiq sai da suka kusan samun tsab'ani a kaina wai lalle sai Sadiq yazo ya same ni ya min bayanin auren shi kuma yace ba da shi ba wannan dan wallahi in ya kuskura ya turo shi wajena ce mishi zaiyi sona yake kaman rayuwar shi shiyasa ya turo shi in taimaka inji tausayin shi in aure shi.

Wannan magana da Sadiq yayi ba karamin tunzura Zafar yayi ba wai kaman shi za'a ce wai k'aramar yarinya mara class mara kyau wacce yake ganin in ba dan takurar Abban shi ba ko a mai wanke-wanke gidan shi ba zai d'auke ni ba balle ace wai sona yake Allah ya kiyaye.

Cikin fushi yaja motan shi yayi hanyan gidan mu dan dole ayi ta ta kare saboda yau ne deadline da Abban shi ya bashi, shi kuma Sadiq yayi hakane dan yaje da kan shi saboda gaba yake jiye mishi amma shi sam baya gani.

Ina zaune kan sallaya dana idar da sallah isha'i nayi zuru ina tunanin ta yaya zan iya rayuwa ba tare da Yaya na ba, shine komai nawa na taso da soyayyar sa cikin jinin jikina duk wata rayuwa da shi na tsara yanzu rana tsaka ace ya rabu dani, to ya zanyi da rayuwata?

Muryan kani na Ibrahim naji yana cewa Inna ta daya tarar a waje wai ana sallama da Zareefa.

Ban tsaya jin me Inna tace mishi ba na fita da sauri kaman zan had'a da gudu, a zuciya ta ina haba na sani mana shima ba zai iya rayuwa babu ni ba na san dama wasa yake min.

Murmushin dana fito da shi a fuska tace ta b'ace bat ganin wanda ban tab'a zato ba tsaye a kofar gidan mu.
[1/26, 7:08 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*19 & 20*

Ina fitowa na ga ya ajiye motan sa a inda ya saba ajiyewa yana sanye da kaftani na farar shadda ya d'aura waya a kunne yana magana, farinciki naji kamar ya kashe ni Yayana ya dawo gare ni wayyoo ni.

Da gudu na Ζ™arasa ta bayan shi saboda farinciki ya rufe min ido nayi abinda ban tab'a yi ba wato ina zuwa banyi wata-wata ba na rungume shi ta baya ina sauke tagwayen ajiyan zuciya cikin muryan kuka na fara magana ;

" Yaya naaaaa ni na san ba zaka iya ba dole zaka dawo gare ni i know u truly love me idon ka kad'ai nake kallo in gane hakan"". Cak ya tsaya ya kasa juyowa kuma ya daina wayan mun kusan minti 1 a haka ya juyo tare da banbare ni a jikin shi ya watsar a gefe yace;

"Yuck how disgusting baki da hankali ne daga gani na zaki wani zo kiyi huging na haka ko ance miki irin samarin nan naki ne marasa kan gado?" Yanayi yana watsa min wani kallon kaskanci, muryan da naji kad'ai yasa gaba na fad'uwa dan wannan dai ba muryan Yaya na bane amma kuma na san mai muryan sai dai a sani na da tunani na babu abinda zai kawo shi gidan mu.

Cikin fargaba na d'aga ido na dan tabbatarwa kai na cewa bashi bane, amma me ina dagowa idona sai cikin nashi da yake aiko min da munanan sakonni.

D'auke nawa idon nayi cikin second d'aya ganin wanda ban tab'a zato balle tsamani ba a kofar gidan mu, na had'iye wani bushashan yawu da ya tsaya min a makoshi sai yanzu na lura da yanayin shigar sa tsayin sa fatan jikin sa komai daban dana Yaya na.

Kara d'agowa nayi naga yana min wani kallo kaman yaga
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment