Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yau shine karshen gyaran fata da ake min sai lalle da aka shiga yarfa min na jan lalle gwanin sha'awa taso a yi min kitso nace mata bana so ta bar min gashi na haka, ba dan taso ba ta kyale ni suka maida hankali kan lallen.

Sai bayan sallah isha'i muka samu daman komawa gida ta d'eba min wasu kayan gyaran tace in rinka yi a gida tunda auren saura kwana 3, karb'a kawai nayi na amsa mata da toh amma ba dan ina da niyyan yi ba.

A kofar gida suka sauke ni Maryam bata shiga ba saboda dare yayi suka wuce tana ta santin lallen da akayi mata wai yayi kyau, ni dai ban iya biye mata na juya zuwa gida abina kasancewar na kwaso gajiya.

Mutane na gani cike a cikin gidan mu ana ta cece kuce kuma kana jin maganan kasan kaman fad'a ake , d'an d'aga kai na nayi naga matan gidan mu ne harda makota, ban kara gigin d'aga kai na ba na wuce b'angaren mu tunda banga Inna ta a wajan ba.

A parlour na samu Inna da 'yan uwan ta zaune sun saka kaya a gaba suna maida abinda ya faru duk fuskan su babu dad'i sai ita Inna ce ba zaka gane mataa ba.

Zama nayi a kasa kan carpet na fara gaishe su d'aya bayan d'aya duk suka amsa min fuska sake, muna gama gaisawa na wuce kitchen neman ruwan sha anan ma wasu kayan abinci na gani gari guda.

Ina cikin shan ruwa ne naji Ya Maaji tana magana cikin b'acin rai wanda ya sani maida hankali kan zancen nasu I really want to know what happened.

"Ni dai idan kun san ba zaku canza halin ku ba wallahi karshen ta ba dani za'a yi bikin nan ba, haba wannan wacce irin rayuwa ce ayi ta cutan ka ana kunsa maka bakinciki amma ka kasa ramawa, wa za'a nunawa hakurin muma ai muna da itan matsalsr idan yayi yawa sai a maida ki kwandon shara yanda kowa ya kwaso nashi kan ki zai juye".

"Gaskiya ne hakurin Bintu yayi yawa sosai har ta doke Yaya wajan sanyin hali, amma wannan zalincin ne dai ba zamu bari ba dole ne a d'auki mataki saboda gaba" cewar Aunty Batool.

"Kina ji fa ita Bintun da bakin ta yanzu take cewa ba yau ta fara yi ba wai ranan da aka fara musu gini an ga wasu layu wanda aka kona ita kuma a take ta fara iface-iface wani babban abin takaici wai ita da Zareefa su sukayi mata addu'a har ta samu lafiya...."

"Har ta samu kafan komawa wajan bokan ta zaki ce Batool, in ba dan Allah ya takaita wannan yaro Ibrahim ya ganta yazo ya fad'a ba, da shikenan auren nan ya fasu amma da yake bata da kunya bakin ta bai mutu ba ana magana tana mayarwa" fad'in Ya Maaji.

"Ban ki ta naku ba nima ba wai kuma fad'an ne ban iya ba, amma abinda nake son in tuna muku duk wanda ya rike Allah in ba wani ikon sa ba babu abinda zai same ka, ku duba mana sau 2 tayi yunkurin cutar da mu Allah yana mayar mata da abin ta.

Ban so kuka kula ta ba, jibi yanda asirin ta ya tonu cikin bainar jama'a wannan ma ya ishe ta ishara, mu kuma bama gajiya da d'aga hannayen mu sama insha Allah, Allah zai kare mu" Inna ta basu amsa cikin sanyin murya babu wacce ta kara cewa kala da alamu maganganun ta ya kashe musu jiki.

"Innalillahi wa Inna ilahi raji'un" shi kawai nake ta maimaitawa tare da sulalewa na zauna dabas kan tiles na kitchen d'in, cikin tashin hankali amma ni kam Ibrahim bai kyauta min ba da yazo ya fad'a har aka dakatar da ita, ina ma tayi nasaran sake binnewa da shikenan na fita daga wannan cakwakiyar matsalan.

"Gata da hassada da ya gama bin jinin jikin ta dubi yanda ta fito wai tana nuna adawar ta a zahiri kan kayan cin-cin da aka kawo" naji muryan Aunty Fatima tana magana cikin d'acin rai.

Sai ana na fahimci ashe kayan da na gani kayan cin-cin ne kenan, shikenan yanzu da gaske ake aure za'a yi min, auren ma da wanda bai san daraja ta ba?

Hawaye sai rige-rigen saukowa suke banyi yunkurin hana su ba na bar su suna kwarara domin yana rage min rad'ad'in dake cikin zuciya ta.

Muryan Inna naji tana kwala min kira ba shiri na mike daga zaunen da nayi ina share hawaye na na fito duk suka bini da kallon tausayi .

"Me kike yi a kitchen d'in tun d'azu" ta jeho min tambaya,

"Ruwa na sha " na amsa mata cikin murya kuka, kan kace me kuma hawaye suka fara kwaranya.

"Daga tambayan ki shine zaki fara min kuka? Bari in tashi inyi miki abinda zakiyi kukan da hujja" Inna ke fad'an haka tana shirin mikewa, da gudu nayi d'aki na maida kofa na rufe ina jin su Ya Maaji suna mata fad'an kada ta kuskura ta tab'a ni ta bar ni inyi kuka na, ban ji karshen maganan su nayi shirin kwanciya na kwanta abina.

Da washe gari ga mamakina ashe duk basu tafi ba anan suka kwana sai ya Maaji da ta kwana gidan Maa, da rana ya fara yi sai ga gidan mu ya fara cika da 'yan uwa ashe wai yau ake cin-cin ni dai ganin sun fara yawa na wuce bangaren su Maman Dije saboda kowacce ta ganni sai ta kira ni da sunan amarya basu san hakan kona min rai yake ba shiyasa na gwammace in tattara in bar musu gidan su kara ta.

Kamin in wuce naji sun fara sa-in-sa da 'yan uwan Baba da suka zo cewar su zasuyi, su Aunty Batool kuma suka ce anyi magana da professional bakers su zasuyi kasancewar komai ya zama na zamani ita kuma Gwaggo Hinde ta fara masifa wai ai zagin su akayi a fakaice meye basu iya ba da za'a ce zasu kira wasu suyi dama sun raina su.

Wucewa ta nayi abina ban san ya suka kare ba, ina can b'angaren su Dije Ni kad'ai duk abin duniya ya ishe ni zuwan su Maryam da sauran 'yan class d'in mu yasa naji d'an dama-dama.

Kusan azahar Dije ma ta iso da yaron ta da yayi wayo gidan ya gama kacamewa saboda surutun ta, hatta Hajara nan tazo tana d'an kqma jiki tana baya-baya saboda abinda ya faru jiya, sai da naja ta da wasa sannan ta saki jiki suka cigaba hayaniyar su Jameela ce dai ban san ina take ba domin yanzu abin nata kullum kara muni yake dan sai tafi sati bata gida kuma koda ta dawo to a buge take dawowa ta zama cikakkiyar 'yar kwaya.

Muna nan a b'angaren Maman Dije Har dare a lokacin mafi yawancin 'yan matan sun wuce Dije ma ta tafi sai Maryam da Hajara ne kad'ai suke tare da ni amma itama Maryam d'in shirin tafiyan take wai sai gobe zata taho gaba d'aya ba zata koma ba sai an gama bikin.

Har bakin gate muka raka ta nida Hajara inda driver gidan su yake jiran ta, ta shiga yaja suka tafi mu Kuma muka koma cikin gida, Hajara har tana shirin shiga kofan su na tsaida ta nace " Dan Allah Hajara muje mu kwana tare a d'aki na kin ga har yanzu da sauran mutane a b'angaren mu".

"Kina ganin babu matsala?" Tambayan da ta jeho min kenan idon ta na cikowa da kwalla.

"Wani matsala kuma ko kin manta ke'yar uwa tace" na bata amsa tare da jan hannun ta muka wuce, a parlorn muka tadda su Ya Maaji sun baje suna rarraba snacks da akayi da wayan da aka bayar akayi cikin different containers wai suna rarraba su.

Za'a cire na gidan su Ango da wanda za'a rabawa baki sai kuma w so hg6xhanda za'a rage min "wai" atoh dole ince wai dan ni har yanzu na kasa gaskata aure na ake.

Hajara duk ta kasa sakin jikin ta akan abinda ya faru jiya ga ya ma'aji sai binta da kallon banza take,ganin haka yasa na jata zuwa d'aki da yake mallaki na a yanzu, tunda muka shiga naga jikin ta ya kara sanyi sai bin d'akin da ido take alaman d'akin yayi mata kyau dan sai ince zan iya kira shigowan ta d'akin mu tun kamin ayi mana wannan ginin.

A bakin gado nace ta zauna ni kuma ina shiga bayi nayi wanka tare da dauro alwala na fito na fara shirin bacci,duk tana zaune a inda na bar ta"tashi kema ki watsa ruwa zaki fi jin dad'in baccin" nace mata ina saka kayan bacci na ba musu ta mike ta shiga kamin ta fito na fitar mata da rigan bacci sannan na haye gado na kwanta,ko da ta fito ta mayar da kayan jikin ta nace ta canza tare da nuna mata kayan da na fitar mata.

Ba zan iya cewa nayi bacci ko banyi ba a wannan daren saboda zanyi kaman bacci ya fige ni kuma duk juyi da Hajara tayi ina ji,ni dai gani nan har aka kira sallahn farko na tashi nayi alwala na fara nafila har aka kira na sallahn asuba mukayi tun da sanyin safiya mutane suka fara hidiman gaban su gidan ya d'auki hayaniya na ana shirin biki a gidan da gaske.

Breakfast da aka kawo mana ban iya cin komai illah tea dana sha kawai nayi wanka muka koma can b'angaren Maman Dije a lokacin 'yan uwan sun fara cika gidan na kusa da nesa

'Yan mata da muke mates duk wajan mu suka zo suka dasa sabon hira sunayi suna ta tsokananta amma na kasa kula kowa cikin su sai yake da nake binsu dashi.

Kusan 12 rana sai ga masu decor sun zo wai daga gidan su Ango aka turo su suyi decoration na wajan da za'ayi wushe-wushe.

Duk yanda nayi gudun kitso bai yiwu ba dan Maa ce da kanta ta turo wata mata tace in zauna a min kitso,dole na na zauna aka yaryad'a min kitson KELEYASKU.

Ba karamin kara fito dani kitson yayi ba, da yake step 2 akayi min wasu ta baya wasu Kuma ta gaba,na gaban nan ya sauk'o min har kan kirjina na baya kuma har gadon bayana kowa na wajan sai santi kitson suke,bayan sallah la'asar wasu masu make-up kusan su 4 wai suma daga can aka turo su harda photographer da masu video coverage kan kace kabo duk sun fara abinda ya kawo su,kamin ayi sallahn magriba naga 'yan mata sunyi wanka kowacce ta fito cikin ankon ta na atamfa mai tabarma da Maryam ta jagoranta sukayi.

Nima ina yin sallah aka tilasta ni nayi wanka ina fitowa masu make-up din suka rufu kaina kowacce tana baza fasaharta,cikin lokaci kankani na fito kaman wata tauraruwa ni kaina kasa daina kallon kaina nayi ta cikin mirror.

Maryam ce ta d'auko min akwati da kayan da zan saka suke ciki,ashe kowanne sun manna sunan event din da zan saka a jiki,ban tab'a gani ba duk da boxes d'ina a d'akina suke ko dan basa gaba nane oho.

Wani atampa ce da ban san sunan ta ba amma kana gani kasan kud'in ta ba na wasa bane anyi mishi d'inkin GUMJE KANURI daya sha aikin stones kaman ba gobe sai Kuma laffaya wacce zata shiga da kayan shima duk ya Sha adon stones sai Kuma jewelry na d'anyen gold.

Ba zan iya misalta muku irin kyan da nayi ba ku dai kawai ku hasaso da kan ku.

Fito dani waje akayi nan bakin gate din mu inda yasha decorations dada fararen fitulu kaman rana, su Maryam na min jagora Aunty Fatima na bin mu da turarrn wuta har zuwa inda aka tanada wai wajan zaman mu ni da shi suka zaunar dani wai ana jiran zuwan ango.

Ni dariyar suma nake a zuciya ta da suke saka ran wannan d'an rainin hankalin ne zai zo nan lalle suna da babban aiki.

Kaman daga sama naji gud'a da kid'an GANGA KURA ana shelan isowan ango da jama'arsa, tun daga nesa na hango shi cikin wasu dankareriyar shadda wanda yayi shige da kayan jikina wato sky blue.

Tun kamin ya karaso naji zuciya ta nata bugawa kaman ya fito Dan na San halin shi ban san yau Kuma da me yazo ba.
[6/16, 9:16 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*28&29*

Duk kamshin turaren wuta da yake wajan dana sauran mutane sai da wannan mayen kamshin nashi ya cika wajan,Kara sadda kaina kasa nayi ban kara gigin d'agawa ba tunda na d'aga na farko zuciya ta kuwa kaman zai faso kirji na ya fito haka nake ji tsabar bugu da yake.

Ba komai ya saka ni shiga wannan halin ba sai dan sanin halin sa na wulakanci da disgi, ina gudun kada ya gwada su a nan a gaban kowa ba abinda na tsana a rayuwata kaman mutum ya wulakanta ni ko ya disgani a bayyanar jama'a.

Ina cikin zancen zuci naji alamun mutum a kaina d'aga ido da zanyi na ga shine ya rankwafo da kan sa daidai fuska na yana sake min wannan shu'umin murmushi nasa yana kallon na, ni d'in ma shi nake kallo ya bala'in kara had'uwa cikin light blue shadda shi ga hula da ya saka itama light blue ce ba zan iya kwatanta muku yanda yayi kyau ba just imagined him.

Na shagala da kallon shi naji yana dariya kasa-kasa yace " please da baki wahalar da kan ki wajan wannan abubuwa da kika shafa ba domin kara miki muni sukayi" ya karasa da kara sautin dariyar shi sannan ya zauna a gefe na inda aka tanada domin zaman shi.

Hawaye naji sun cika min ido amma ban bar su sun zubo ba, I knew it na san dole ne ya shimfid'a min wulakanci son ran shi wai kara min muni sukayi ko ina ruwan shi da kwalliya ta.

Kuma abin takaicin salon da yayi amfani dashi ya min maganan zaka d'auka hiran soyayya muke sai wani narke ido yake dan haka abin ya birge mutane sukayi ta mana hoto a wannan yanayin .

Kawar da kai na nayi gefe ina jin kaman in tashi in gaggaura mishi maruka amma na danne zuciya ta ina hasaso yanda zaman namu zaya kaya nida shi.

Ina cikin zancen zuci naji wannan mayen kamshin nashi ya kara cika min hanci wanda yake kara tabbbar min da kusancin namu ya karu, ban juyo ba balle inga wace irin zama mukayi da shi.

A zabure na juyo ina kallon shi da ido na duk a waje sakamakon jin hannun shi a cikin nawa, muna had'a ido ya sake min wannan killer smile d'in nan nashi da in yayi babu alkhairi a cikin ta

Aiko kamin in tantance me yake faruwa naji ya fara murza min hannu cikin kwarewa da cin zali da mugunta, a take naji kaman in saki fitsari a wajan amma da yake nima ba baya ba wajan iya basar da abu dan haka na basar kaman ba ni yakewa wannan muguntan ba.

Cikin abokan shi wasu suka zo suna mu fito muyi rawa amma kememe yaki ko matsawa balle ya tashi , da suka ga bashi da niyyan tashi duk suka rufu kan mu tare da fara mana barin kud'i kaman basu san zafin su harda wasu cousins d'in shi 'yan mata da naga suna yi min wani kallon kasa-kasa ko me suke nufi oho dan ni Yayan nasu ma bai ishe ni kallo ba balle su.

A cikin gida kuma iyaye na sun yiwa nashi tarba na mutunci sannan aka fara wasu events na al'ada game da wushe-wushen, dama wushe means welcome da yaren kanuri so they are welcoming them to our family wato an zama family d'aya kenan suma sun bada kayyaki na al'ada da ake bayarwa sannan su Inna ma sun mayar musu da wasu kayan suma.

Sun d'auki lokaci mai tsawo sannan suka gama nasu a cikin gida suka fito gaba d'ayan su harda nawa iyayen, wata mata ce cikin 'yan uwan sa naga ta nufo mu kai tsaye tana murmushi tace " wannan wani irin Ango ne da ba zai cashe ba a ranar bikini sa?"

Turo baki yayi kaman wani karamin yaro sannan ya bata amsa " Baawa ni ban iya rawa ba Kuma..." Mugun kallo da yaga ta watsa mishi yasa ya mike babu shiri da hannu na a cikin nasa wanda yanzu nake ji kaman ba a jiki na yake ba tsaban mugunta da yasha.

A yanda ya mike ya tabbatar min da yana matukar shakkan matar nan jibi yanda ya mike babu shiri, a raina ina ashe duk wannan muzuran nashi na banza ne tunda da wanda yake. tsoro har haka.

Yanda kika san statues haka muka tsaya musu kikam ba wanda yake da yunkurin yin motsi balle a je ga zancen rawa, iyaye na da nashi suka fure ruf sai barin naira suke mana.

Ni dai duk mamaki ya ishe ni a raina yanda suke zubar da kud'i kaman basu san zafin su ba, a zuciya ta nace ina Gwaggo Aisha Mai cewa Yaya na d'an yankan kai ne tazo taga wayanan da ko ni kaina zan iya kiran su da hakan dan barnan kud'in yayi yawa.

Ana cikin filin Sadeeq yazo ya fara mishi magana a kunne wanda yaja hankali shi ya saki hannu na ba tare da ya sani ba, ban san me suka tattauna ba sai dai naga yana murmushi ya juyo zai kara rike min hannu kan zamu koma mazaunin mu nayi azamar janyewa nayi gaba yabi baya na har muka zauna basu daina mana liki ba.

Sai wajan sha d'ayan dare sannan taron ya tashi suka shiga motocin su suka tafi mu kuma muka koma cikin gida muka bar masu decor da tattare wajan.

Muna shiga ban tsaya a ko ina ba sai bathroom na samu ruwa mai d'umi sosai nayi wanka tare da gasa hannu na da nake jin sa kaman ba a jiki na yake ba dan tsabar jin zali daya sha.

Ina fitowa a wanka naji su Maryam da sauran cousins d'ina da muke mates sun zo taya ni kwana suna ta yaba mugun da basu san halin shi ba.

"Wow kai Zareefa tayi babban sa'an samun hadadden miji mai iya love ga kyau ga naira ohh so romantic" cewar Zainab tana zama kusa da Maryam.

"Allah ya samu a danshin ta abun yana bala'in burge ni samun classic miji haka" inji Hanan.

"Ni abinda yafi birge tunda ya iso yake makale da hannun ta kaman za'a kwace mishi ita" Hauwa ta katse ta.

Kallon hannun nawa nayi wanda ya koma jajawur saboda azaba su kuma a haukan su suna yabawa sun zata zallar soyayya ce, cike da jin haushin su na juya musu baya tare da jan duvet na rufe har kaina, ina jin su suka cigaba da suratan su daga baya suka hakura suka kwanta bacci.

Basu dad'e da kwanciya ba duk sukayi baccin su hankali kwance, tashi nayi na zauna ina kallon su cikin sha'awa ni da nake jin ido na a bushe babu alaman d'igon bacci, ba yau kad'ai ba tunda maganan auren nan ya tabbata na rabu da bacci mai dad'i dan sai in d'auki lokaci Mai tsawo ban runtsa ba, ko kuma na samu baccin ya kwashe ni daren yana rabawa rabi sai in farka kuma wani lokacin ya tafi kenan wani lokacin kuma sai kusan asuba zai kara sace ni.

Yanzu ma da naji kwanciyar ya ishe ni na shiga bayi nayi alwala nazo na tada sallah tare da neman agaji wajan ubangiji na.

A b'angaren su Zafar kuwa yan uwan Abba cikin farinciki da Kuma yaba yanda iyaye na suka karrama su suka isa gida yayin da yan uwan Mom sai tab'e baki suke wai ya rasa inda zai nemo aure sai a wannan gida kaman akurkin kaji.

Shi kuwa Zafar ko bai kula kowa ba ya shige part din shi ya kulle kan shi a ciki dan kowa ma haushi yake bashi, duk yanda abokanen shi suka so su gan shi bai yiwu suka wuce.

********************
Hausawa sun ce rana bata karya sai dai uwar d'iya taji kunya, toh hakane ya kasance a yau asabar itace ranar daurin auren kaman yanda naji suke fad'a kuma nake gani a yanzu duka gidan ya kaceme da hayaniya kowa sai hidiman gaban shi yake, masu gyaran gida nayi masu girke-girke nayi masu wanka ma nayi.

Ni kuwa ina can kuryan d'aki abin duniya duk ya ishe ni ganin cewa fa da gaske ne auren nawa za'a daura maimakon na tsinci kaina cikin farinciki kaman kowace amarya sai dai ni a bakinciki na tsinci kai na dumu-dumu ga kewan Yaya na da ya dawo min sabo fil, na san da aure na da shine da nafi kowa farinciki a rayuwa amma sai gashi yau da wanda bai sona bai san daraja ta ba za'a had'i ni aure.dashi wace irin rayuwa zan shiga???

Kuka naji mai tsanani ya taho min na tausayin kai na, mikewa nayi ba tare da na kula 'yan mata da suke ta hayaniyar su ba na shiga
bathroom dan in samu sukunin yin kuka na ko zan ji saukin rad'ad'in da zuciya ke min.

Zama nayi dirshan a ciki na kama kuka kaman rai na zai fita ji nake kaman rayuwa ta tazo karshe ji nake shikenan nayi ban kwana da farinciki a rayuwa ta ji nake kaman na yanki ticket na shiga kunci na har abada.

Ban san iya adadin lokaci da na d'auka a bathroom d'in ba sai knocking da naji ana yi a kofan yasa na d'an tsagaita kukan tare da maida hankali na kan mai bugawan.

"Zo ki bud'e kofan nan Zareefa" naji muryan Inna daga waje, goge hawaye na na shiga na nufi kofan na bud'e tare da komawa gefe kai na a kasa naki yarda mu had'a ido da ita, shigowa tayi ciki tana bin fuska ta da kallo.

"Rufe kan ki kikayi kina kuka ko?" Ta tambaye ni still tana karantar yanayi na ta maida kofan ta rufe, maimakon in bata amsa fad'awa nayi jikinta ina mai kara rushewa da kuka mai tsuma zuciyan mai sauraro balle ita da take mahaifiya a gare ni.

Rungume
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment