Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

da shegun idanunki kaman na mujiya" cewar Gwaggo Aisha tare da aika min mugun kallo.



"Ke Aisha ba kya kula da lokacin daya kamata ki tari mutum da magana,ni yanzu a gajiye na shigo hutu nake nema" yana gama fad'a kuwa yayi hanyan d'akin shi ya shige ya bar Gwaggo Aisha baki bud'e.

Kuyi manage ba yawa



*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 500 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Addu'a Idan Mutum Ya ga wani abu mai ban Mamaki, ko na farin ciki*

سُبْحَانَ اللهِ!
Subhanal-lah!.

Tsarki ya tabbata ga Allah.

اللهُ أَكْبرُ!
Allahu akbar

Allah ne mafi girma.

*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._


*6*


Yanda Gwaggo Aisha ta bud'e baki ta kasa rufewa saboda mamaki kowa a wajan sai da ya wangale baki muka bi Baba da kallo har ya shige d'akin shi abin sa ko waigowa baiyi ba.


Wata wawiyar Ajiyar zuciya na sauke na samun tsira daga rankawshin Baba, kasancewar a tarihin rayuwa ta yau shine karo na farko da Gwaggo Aisha ta kawo kara ta yaki fad'a ko kuma duka na dan haka cikin jin dad'i fuska ta d'auke da murmushi na wuce d'akin mu.



"Ni kikewa dariya dan uban ki,toh ba dani kike ba da lusarar uwar ki kike " cewar Gwaggo Aisha cikin matukar fushi.


"Ni wallahi Inna banyi mata magana" na fad'awa Inna cikin marairaicewa saboda ganin irin kallon da take bi na dashi.



Kwafa kawai tayi ta cigaba da d'inkin hular ta da take,cire uniform na nayi na saka kayana na gida har mukayi sallah Gwaggo Aisha nata bala'in ta babu wanda ya kula ta sai can Inna Asabe ta saka baki.



"Kema dai Aisha akwai ki da son surutu,kullum Mallam yana biye miki ya zane 'yar nan amma dan yau kad'ai ya fad'i haka kika tashi hankalin ki,ya kamata ki mishi uzuri ki...."


"Eh lallai Asabe kike kowa kin samu kaina har ni kika kalla kike cewa ina son surutu saboda wuyan ki yayi k'wari, ba surutu nayi ba uban surutu nayi sai inji bugu ga uwa ta nan" tana yi tana kara matsowa kusa da Inna Asabe wai tana jiran taji bugu.



"Hmmm Allah ya tsari gatari da saran shuka kema kin san inda kika baro ta bani ba" cewar Inna Asabe tana kawar da kai gefe.



Wannan kalaman sun fi k'ona mata rai akan na farkon nan da nan taci d'amara da d'an kwallin kanta suka fara zagin juna,har baka jin me suke cewa tsabar ihun da suke.



Cikin tab'e baki na kai loman abinci na baki na kalli Inna da hankalin ta yake kan hular ta naja tsaki na ce," ni wallahi ihun nan ya ishe ni har ciwon kai na fara ji".



"Ina ruwan ki da ihun su ko akan ki suke" da sauri na girgiza mata kai.



"Toh kiyi abinda yake gaban ki" da kai na amsa ina jin haushin su suna da daman suyi ta zagin mu son ran su suyi mana abinda suka ga dama amma ko da wasa ita Inna ba zata bar mutum ko d'an gulman su yayi yaji dad'i ba.



Basu fasa ba sai da suka tsinci muryan Baba yana magana," ni ban tab'a ganin fitina irin wannan ba,mutum ba shida daman hutawa a gidan shi saboda bala'in ku,mtswww sai ku cinye kan ku na bar muku gidan tunda zama nawa ne ba kwa so" yana gama maganan shi yasa kai ya fice.



Duk takaici ya gama rufe shi dama ya dawo gida ne ko zai samu d'an abin sakawa a bakin salati amma hakan ya gagara saima kara mishi tension da sukayi.



Majalisan nasu babu dad'i yau yana gani kowa ya sayi abu kiri-kiri suke hana shi dan yau ba shida ko ta sayan soyayyiyar gyad'a ne.



Inna Asabe ita ta hakura taja tsaki ta shige d'akin ta ya bar Gwaggo Aisha na cewa taji tsoro da ta tsaya mana taga yanda zatayi da ita.


************


Haka rayuwar gidan mu ya cigaba da tafiya babu wani canji saima kullum kara gaba yake na yanda suke mana a gidan,shi kuwa Baba bayan wancan girkin Inna daya fita yanzu tayi kusan girki uku amma ya rasa taya zaiyi ya shawo kan ta a rinka cin dad'in nan dashi.



Kullum in Inna tace da girki tun daga zaure zaka fara shak'an k'amshi mai saka yawu tsinkewa,haka Baban duk magariba zai dawo yayi ta b'uda hanci yana shak'an wannan kamshin yana," ikon Allah wai yau Bintu ce ke irin wannan girke-girke a gidan nan,da zan samu shawo kanta har na aljihu zan samu kashh Allah kawo hanya" haka zai zauna yayi ta sumbatu shi kad'ai kuma kullum cikin tsammanin zai ganni da tiren abinci yake.



Kusan sati na 2 kenan a makaranta hankali na kwance nake zuwa, Alhamdullilahi karatun ma yana shiga k'wanya ta sosai tsab'anin da,ko assignment aka bamu da kaina nake yi in na dawo gida.



Makaranta yayi min dad'i sosai dan yanzu har k'awaye gare ni,na murmure nayi kyau na k'ara haske abina yo kullum sai naci nayi nak abina,wani lokacin na saka Inna ta zubo min abinci na in tafi dashi makaranta kasancewar yanzu banda mu cikin way'an da ake rabawa abincin makaranta daga primary 6 ne zuwa kasa mu kuwa yanzu muna j.s.s1.



Abdulbasit tun ranan daya tafi bai k'ara dawowa ba yau kusan sati uku kenan,kayan abincin mu sun fara d'an yi k'asa kad'an saboda yawanci Inna in tayi girki ko ba ranan girkin ta bane sai ta zubawa k'ananan yaran gidan sun ci,albarkacin wannan abincin da suke samu sun daina mata rashin kunya ko iyayen su sun nemi suyi kememe suke k'i.



Ko aike zatayi in ni ina makaranta har rige-rigen karb'a suke suyi mata hankali kwance.



Ranan wani asabar bayan sallah la'asar ina zaune a d'akin mu ina duba English textbook na kasancewar yau babu islamiya ana auren wani Malamin mu Inna kuma tana gefe tana ninke mana kayan mu data wanke muka ji sallaman wani yaro a k'ofar d'akin mu Inna ta amsa tana tambayan waye ne,ya amsa mata da shine Alai gana yaron Yakura dama wani ne a mota yake k'iran zareefa a waje.



Kallon Inna nayi da sauri zuciya ta tana bugawa kaman ta fito ina jiran inji tayi min fad'a amma naji tace inje mu gaisa ince itama tana gaishe shi amma kada na dad'e.



Ni dai mamaki ya hana ni tashi dan sam bata tab'a gaya min yanda sukayi dashi ba dan haka ban san komai akai ba.


"Wai bada ke nake magana ba" ta fad'a a d'an tsawa ce tana ajiye kayan hannun ta, jiki a mace na tashi na saka hijabi na na fita, tsakar gidan mu babu kowa sai k'ananan yara da suke wasa iyayen su sun tafi biki can gaba da layin mu.



K'ananan kaya ne a jikin shi yau wandon jeans baki da riga t shirt fari sol sai takalmin sa shima baki yana tsaye hannayen shi duka biyu cikin aljihun wandon shi.



Ina fitowa muka had'a ido ya sake min murmushin sa mai kyau ni kuwa had'a rai nayi ina turo baki na tsaya d'an nesa dashi kad'an.


"K'anwata babu gaisuwa ne?" Ya tambaya yana murmushin.



Cikin turo baki na ce," ina wuni" bana buka rik'e kayan ki tunda sai da na rok'a". Yace Shiru nayi bance mishi komai ba.



"Bud'e seat d'in baya yayi ya ciro wasu manyan shopping bags guda uku yace biyu nawa d'aya kuma in bawa Aunty wai yana sauri ne shiyasa ba zai samu su gaisa ba kuma in bata hakuri yayi tafiya ne shiyasa taji shi shiru.


Ido na cike da hawaye na ce," in na karb'a fad'a Inna ta zata min kuma aini ban san Auntyn naka ba ta ina zan kai mata" na karasa hawaye na zubo min.



Murmushi yayi yana ," cry cry Baby,ke sam ba kya gajiya da kuka ne?" Nan ma ban kula shi ba ya cigaba," ammm Innar ki babu abinda zata miki saboda last time da nazo ita ta yarda in dinga zuwa muna gaisawa nd Aunty na kuma ba kowa bace Innar kice".



Sai a lokacin naji hankali na ya kwanta duk da dai ban yarda da abinda ya fad'a ba.



"Ki shiga gida ina jiran ki anan in tayi miki fad'an sai ki dawo min da kayan,kin ji ko?" Yace min ganin har yanzu ban yarda da maganan shi ba.qa



Da toh na amsa mishi na d'auki kayan da kyar saboda nauyin su na shiga gida zuciya ta cike da fargaban me Inna zata ce.



Kayan na ajiye ina kallon idon ta bayan na shigo da sallama ta amsa min.


"Har ya tafi?" Naji ta tambaye ni.


Da eh na amsa sannan na fad'a mata abinda yace sai banga wani tashin hankali akan fuskar ta ba saima cewa da tayi tana amsa gaisuwan shi.


Cire hijabin nayi na koma kan takardu na na cigaba da abinda nake ba tare da nabi ta kan kayan da na shigo dasu ba.



Sai da Inna ta gama abinda takeyi sannan ta bud'e jakan daya ce nata ne, turmin zani masu kyau guda 2 da lace guda d'aya sai kuma dubu ashirin a k'asan kayan ta gani.



Shiru Inna tayi tana kallon kayan cikin wani yanayi na damuwa da tsoro,ita in ba dan Maa tace mata bakomai ba data taka mishi brick.



A hankali kuma ta jawo nawan ta bud'e shima 'yar kantuna ne masu tsananin kyau da d'aukan hankali kusan su biyar riga da skirt biyu sai dogagen riguna biyu da kuma riga da wando irin wanda rigan yake sauk'owa har guiwa shi kuma guda d'aya da katon baby na a k'asan.



Shima ta dad'e shiru tana nazari sanna ta bud'e na karshen, roban ice cream manya biyu da sauran tarkacen su biscuit da chocolates sai kaji gassasu har biyu suma a kulle a ciki.



Yanzu kam tagumi ta zuba tana tunani anya akwai wanda zaiyi maka haka saboda Allah babu komai a zuciyar sa, zamani ya lalace dole tayi shakkan wannan al'amari.



Sanin gidan babu kowa yasa tace inje in kira mata Maman Dije ince tazo yanzu dan Allah.



Matan k'anin Baban mu ne,tun fil azal a wajenta Inna ta ke samun sauki dan ita babu ruwata da haukan su sai kishiyarta ce bakin su d'aya dasu Inna Asabe.



Batayi nawa ko gardama ba muka taho tare amma sai Inna ta ta dakatar dani shiga d'akin tace inje inyi wasa zasuyi magana.



Ina jin haka ni kuwa na fice daga gidan zuwa gidan kakata nayi zama na acan.



Inna tun daga farkon had'uwa ta da Abdulbasit har zuwa yau ta bata labari tare da fad'a mata abinda Maa tace da kuma yanda ita hankalin ta yaki kwanciya akan lamarin,dubu ashirin fa banda sauran sayayya da yayi gaskiya abin abun dubawa ne.



Bayan d'an nazari itama exactly kusan abinda Maa ta fad'a shi ta fad'a mata tare da cewa ta rike Allah ta kuma rike addu'a insha Allah babu abinda zai faru.



Godiya Inna tayi mata tare diban mata kayan makulashen tace ta bawa yara karb'a tayi tana godiya ta koma b'angaren su.



Ban dawo gida ba sai da Inna tasa aka kira ni sannan na dawo nan ma kayan makulashen ta d'ibarwa Maa tare da dubu uku tace in kai mata ince Abdulbasit ne yazo yau.




Karb'a nayi na fita ina maimaita sunan a raina wai Abdulbasit ni dai ban tab'a jin suna haka ba sai yau.



Maa kin karb'an kud'in duka tayi dubu d'aya ta d'auka tayi godiya na komawa Inna da kud'in ta karb'a tana zata je anjima da daddare da kanta wajan ta.



Kayan makulashen Inna ta bani, ice cream d'in nayi ta sharba dan ya min mugun dad'i sosai duk da rabi da kwata sun narke amma abinka da baka tab'a sha ba sai naji kaman madara empty nake sha,sai da ya kare muka ci kazar mu mukayi nak abin mu ranan ko girkin dare ba muyi ba.



Sai bayan sallah magariba sannan Inna ta nuna min kayan da Abdulbasit ya kawo min, aiko kaman in haukace saboda murna kayakin da ban tab'a tsammanin zan mallaka sai gasu har kala biyar duka nawa ni kad'ai harda Baby na.



Da kyar na samu nayi bacci a ranan saboda murna ina rungume da Babyn nawa nayi bacci a ranan.



Da washe gari da safe na fito ina share kofar d'akin mu naga Jameela ta fito dasu ledan alale da sob'o ta ajiye a wajan wanke-wanke tana kallon ido na tana murmushi irin su jiya sun ci kayan dad'in biki.



Ban kula ta ba sai da na kwashe sharan da nayi sannan na shiga d'aki nima na fito da robobin ice cream da kuma takardan naman kaza da muka ci harda warwarewa yanda za'a ga kasusuwan cikin sannan na ajiye a wajan wanke-wanke nima inayi mata murmushi na koma d'aki karb'o omo da zanyi mana wanke-wanken.



Da na karb'o omo sai da na d'auko Baby na na fito ina danna madannin jikin ta fara wak'an larabci,ina fitowa na tarar da Gwaggo Aisha tana leken inda na ajiye kwanukan mu.



Dariya nayi na ajiye Baby na a gefe na fara wanke-wanke na hankali kwance,ina jin Gwaggo Aisha tana jan tsaki tare da cewa," karyar banza bayan mun san komai me za'a nuna mana. Tana magana ne tare da shigewa d'akin ta sai dai tana shiga naji suna rigima da Jameela wai a saya mata irin Baby na,tun tana rarrashi naji an kai mata maka ta tsala ihu tayi waje da gudu.



Ko a ido ka kalli babyn ka san mai tsada ce shiyasa tayi mata haka domin bata da kud'in sayan shi.



Ranan muna zaune a d'aki bayan magariba ana gobe Inna zata karb'i girki muka ji muryan wani abokin Baban mu yazo yana ta masifa kan wai Baban ya ranci kud'in shi naira dubu biyu bai biya ba, ashe tun bayan la'asar Baba yake gida ya kasa fita majalisa saboda bashin da ake bin shi bamu sani ba.




Abu kamar wasa fitinan yayi girma dan ana ta bashi hakuri yace babu inda zai je sai Baba ya biya shi kud'in sa yau kusan wata 2 kenan ana abu d'aya kuma shi ya gaji da yanda Baba ke cewa yau ko gobe.



Jakar kayanta Inna ta bud'e ta ciro dubu biyun tace min in kaiwa Baban mu,karb'a nayi na fito kai mishi ba dan raina yaso ba saboda shima baya tausayin mu baya nuna kulawa gare mu sai sauran 'yan gidan shiyasa nima banga dalilin da yasa zamu tausaya mishi ba.



Sai dai ina zuwa saida na tausaya mishi,yana rab'e jikin k'ofan shi yayi abin tausayi shi kuwa mai bashi sai ci mishi mutunci yake, ga kanin Baban mu da muke kira da baffa shima sai hakurin yake badawa amma a banza


Ina zuwa kusa dashi na tab'a shi ya d'ago ya kalle ni da idon shi daya canza kala, mika mishi kud'in nayi na ce," gashi inji Inna tace ka biya su kud'in.



Baba kasa karb'an kud'in yayi ya tsaya kallo na haka sauran matan ma suka tsaya kallon kallo.



*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/3, 9:06 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


حَدَّثَنَا سَعِيدُ بْنُ مَنْصُورٍ وَقُتَيْبَةُ بْنُ سَعِيدٍ وَأَبُو كَامِلٍ الْجَحْدَرِيُّ وَاللَّفْظُ لِسَعِيدٍ قَالُوا حَدَّثَنَا أَبُو عَوَانَةَ عَنْ سِمَاكِ بْنِ حَرْبٍ عَنْ مُصْعَبِ بْنِ سَعْدٍ قَالَ دَخَلَ عَبْدُ اللَّهِ بْنُ عُمَرَ عَلَى ابْنِ عَامِرٍ يَعُودُهُ وَهُوَ مَرِيضٌ فَقَالَ أَلَا تَدْعُو اللَّهَ لِي يَا ابْنَ عُمَرَ؟ قَالَ إِنِّي سَمِعْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ لَا تُقْبَلُ صَلَاةٌ بِغَيْرِ طُهُورٍ وَلَا صَدَقَةٌ مِنْ غُلُولٍ وَكُنْتَ عَلَى الْبَصْرَةِ.

*It was narrated from Simak bin Harb, that Mus`ab bin Sa`d said: "`Abdullah bin `Umar came to visit Ibn `Amir when he was sick and he said: `Won`t you supplicate to Allah for me, O Ibn `Umar?` He said: `I heard the Messenger of Allah (s.a.w) say: "No Salat is accepted without Wudu` (purification), and no charity (is accepted) that comes from Ghulul," and you were the governor of Al-Basrah."`*

[ Sahih Muslim ]



*7*


Baban mu jikin sane yayi sanyi sosai, wai Bintu ce ta biya mishi bashi. Bayan duk abubuwa da yayi mata basu da misali bayan wa'yan da ya fifita duk suna tsaye babu wanda yayi gigin biya mishi alhalin suna dashi, more especially 'yar gaban goshin sa wato Gwaggo Aisha, ga Baffan mu duk suna wajen taya zai iya kallon idon ta nan gaba?.



"Amma Mallam Hassan ka cika mugu azzalumi,wato yanzu a baka kud'in da zaka biya ni shine ka rike ka maida ni d'an iska wato inyi in gama ko? Allah ma yasa a gaba na aka aiko da kud'in da shikenan sai ka cigaba da raina min hankali kana cewa babu" yana banbani ya matso kusa da Baban mu ya kwace kud'in a hannun sa ya fita yana," Allah ya so ka Mallam".



Da ido kowa ya bi bayan shi har ya ida ficewa, bai san cewa mamaki ne daya cakud'u da mutuwar jiki su suka hana shi bayar da kudin ba, bai kara kallon kowa a wajan ba ya koma d'akin shi ya zauna a bakin gado tare da rafka uban tagumi yana tunanin ta yayane zai shawo kan Bintu yaci dad'i kuma ya samu na kashewa, dubu biyu fa?.



Can shi kad'a ya saki murmushin jin dad'i alamun ya samu mafita kenan.



A waje kuwa Baban mu yana shiga d'akin sa Baffan mu shima ya bar wajan yana tab'e baki dan bai ga dalilin da zai saka ya biya mishi bashi ba, da ace wannan kud'in yayi amfani dasu wajan ciyar da iyalin shine zai iya biya amma tunda kansa kad'ai ya sani bai san hakkin daya rataya akan sa ba shi ya sani yaje can ya karata.



"Allah sarki Bintu Allah dai yasa ba mugun halin kema kika fara kaman sauran matan ba saboda mugun halin d'an uwana duk shi ya jefa iyalin shi cikin halaka" yana magana ne tare da shigewa b'angaren shi.



Gwaggo Aisha da Inna Asabe duk sun kasa barin wajen suna tsaye a wajan kaman wanda aka dasa su kowacce da irin tunanin da take a zuciyar ta saboda Abin ya mugun daure musu kai sosai ita da duk gidan itace wacce bata dashi amma yanzu ta dara kowa a gidan.



Gwaggo Aisha fargaban ta d'aya shine kada Inna tazo ta kwace mata matsayi a wajan Baban mu domin ta san halin shi tsab zai iya juya mata baya dama saboda tafi kowa kud'i a gidan yake fifita ta, kai dole ne tayi wani abu akai dan ba zata tab'a zuba ido Inna ta ta kwace mata ba.



Da washe gari ina dawo daga makaranta a nesa na hango motan Abdulbasit a k'ofar gidan mu, aiko da gudu na karaso wajan motan cike da murna dan yanzu na daina tsoro tunda Innata da kanta take cewa inje mu gaisa bayan haka ga kayan dad'i da kullum in zai zo yake kawo min, yana zaune a ciki motan amma kafafun shi a waje hankalin shi yana kan wayar shi ban san me yake dan dannawa ba.


"Sannu da zuwa Yaya na" na fad'a da d'an karfi bayan na karasa kusa dashi,a d'an razane ya d'ago sai kuma ya saki murmushin sa mai kyau da baya barin fuskan sa.


"Har kin tsorata ni saura kad'an in ruga da gudu" ya ce yana dariya.



Nima dariyan na kyakyale dashi sannan na ce," toh ya zakayi da motan ka in ka gudu ka barta?"



"Sai in bar miki ita ki rink'a zuwa makaranta dashi" toh ai ban iya yanda ake tukawa ba" na fad'a a shagwab'e.



"Kada ki damu zan koya miki, kije ki cewa Aunty zan shigo mu gaisa".



Da toh na amsa sannan na juya na shige gida da sauri na, su Hajara duk sun tafi tallah iyayen nasu ma ban gan su ba da alamu duk sun fita.



Inna tana k'ofar d'aki tana shara na shigo da sallama ta amsa tana yi min sannu da zuwa,ciki na shige na ajiye jaka ta sannan na kara fitowa na ce mata," Inna Yaya yazo yana waje yace zai shigo ku gaisa".


"Ciki nan zai shigo yace?" Ta tambaya da alamun tsoro da damuwa akan fuskan ta, gyad'a mata kai nayi ina kallon duk yanda ta zama wani iri.



"Toh ya shigo" ta ce tana komawa d'aki ni kuma na fita waje na sanar dashi kan ya shigo, a bakin k'ofan d'aki muka tadda Inna zaune cikin tagumi amma tana ganin mu ta saki ran ta tana mishi sannu da zuwa.



Kallon gidan namu yake tare da nazarin sa,har k'asa ya duka suka gaisa da Inna a mutunce tare da bata hakurin rashin zuwan sa akai-akai kaman yanda yayi mata alkawari, nuna mishi tayi babu komai kana ta d'aura dayi mishi godiya tare da addu'oin gamawa da duniya lafiya.



Cikin jin dad'i yake amsawa da Ameen sannan ya mike yace zai wuce dai-dai lokacin kuma iska mai karfi ya d'aga d'an yalolon labulen mu karaf idon sa sai a d'akin mu da ko arzikin leda babu sai siminti dasu ghana must gon mu a gefe.


Tare muka fito dashi har zuwa wajan motan sa ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment