Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yake ba.

Murya... Ya d'aga cikin k'osawa da zaman jira da yake ya ce " man wai me hakane, sai b'ata mana time kake pls ka fito mu tafi ba party zuwa da beb bane in dan wannan kake ja mana...…"

Ganin ya fito yasa ya had'iye sauran maganan shi yana bin shi da kallo ko makiyin shi ne bai isa ya kushe shi ba, toh duk iya dai bin kwakwafin mutum babu abin kushewa a halittar sa dan ko dama aka bashi aka ce yayi kan sa iya kar sa kenan.

Ya matukar had'u cikin dark blue polo shirt da wandon jeans baki sosai kayan sun matukar dacewa da farar fatar shi sai canvas dark blue dake kafar shi sai zuba kamshin tsadaddun perfumes din shi yake kasancewar sa mai son kamshi shiyasa baya amfani da turare daya kusan 4 ko 5 yake amfani dasu at a time dan haka ba zaka tab'a bambamce kamshin da yake ba.

Yana gyara agogon Rolex dake hannun shi ba tare da ya kalli inda sadiq yake zaune ba yace,' muje"

Girgiza kai kawai yayi ya mike yabi bayan shi dan har ya fita basu tsaya b'ata lokaci ba suka fad'a wata sport car d'in sa suka fice daga gidan.

********************

Gidan mu dai yana nan yanda kuka san shi babu abinda ya canza cikin zamtakewar da muke, cikin shekaru 2 da suka shud'e sai dan abinda ba za'a rasa ba, muna final year a makaranta sai shirye-shirye rubuta waec muke hankali kwance.

In ka san ni a shekaru 2 da suka wuce ba lalle ne ka gane ni yanzu ba na canza matuka na kara wayewa ga girman jiki dana kara sosai ,kyau na kuwa ba'a magana duk inda na wuce sai an dad'e ana magana ta wasu ko cewa suke wai ni balarabiya ce,ko a makaranta na sha raba musu musu cewar ba abinda ya had'a ni da larabawa ni asalin hausa Fulani ce amma wasu basa yarda sai dai suce b'oyewa nake bana son asan gaskiya.

Godiya sun tabbata ga Allah mahallacin komai da kowa sannan ga mutane 2 na cikin rayuwa ta wanda a dalilin su na zama abinda na zama wato Yaya na da besty na Maryam, dukan su 2 sun taka muhimmiyar rawa a rayuwa ta.

Yaya na shine gata na shine abin alfahari na ba dan shi ba da ban kai wannan matsayin da nake ba, sai Maryam ita ta kasance kaman roll model na domin komai na 'yan gayu ita ta koya min na fito cikin 'yan mata masu aji, dalilin Maryam da ta nace muka shiga wani catering school da sai da muka shafe watan ni sannan aka yaye mu yanzu ba wani nau'in girki da ban iya ba da snacks da drinks kala-kala, mostly in Yaya na zai zo sai nayi mishi.

Auren Yayan Maryam shi muka saka a gaba da za'ayi nan da wata 3 masu zuwa,sosai muke zuba tsare-tsaren mu dan so muke muke mu fita daban cikin 'yan biki.

Soyayyar mu da Yaya na kuwa sai abinda ya karu domin a kullum kaman kara wutan son junan ake a cikin zukatan mu tun Inna tana d'ari-d'ari har ta saduda ta tabbatar son so yake min lokaci kawai ake jira da zaran na kammala secondary school na za'a saka mana rana, tsakani na dashi ban san wa yafi zumud'i ba kullum cikin kirga kwanaki muke na zuwan lokacin.

Tsakanin su da Baba kuwa 😂😂 babu abinda ya canza dan Baba baya tab'a yarda su had'u duk yanda Yaya na ya kai ga son su gana amma yaki yarda kowani lokaci akwai excuse da zai nemo ya bada dan kaurace had'uwan nasu.

Dije anyi auren ta kusan wata biyar da suka wuce ta auri mijin ta mai suna Bala ba mai arziki bane amma akwai wadatar zuci da rufin asiri, ko bikin ma kowa sai son barka yake kasancewar anyi komai cikin tsari.

Hajara tana gida an kawo ta wanka satin da ya wuce bayan ta haifi d'a ba rai sakamakon yawan dukan da take sha wajan mijin nata ga yunwa da yake barin ta dashi sai dai Gwaggo Aisha tayi musu aike na kayan abincin domin yanzu tana samu ko sana'a ta daina yi duka bukatun ta Jameela ta d'auke mata su sakamakon samari masu kud'i da ta samu amma fa a cewar Gwaggo Aisha kenan dan ni dai ban tab'a ganin wani yazo kofar gidan mu neman ta da sunan zance ba sai dai inga taci kwalliya cikin matsattsun kaya ta fita kan zata je gidan kawaye in anyi sa'a ta dawo cikin dare ta kwana a gida wata rana kuma sai tayi kwana biyu bata dawo gidan ba, ta goge ta kara haske da kyau duk da hasken na shago ne.

Dawainiya kula da Yayar ta ma itace ta d'auka babu abinda ta rage ta dashi shi kuwa mijin tunda aka kawo ta gida bai kara bi ta kansu ba balle yazo ya duba ta ko yayi musu aike, wannan dalilin yasa Gwaggo Aisha d'aukan alwashin 'yar ta ta gama auren shi ko uban wa yayi mishi tsaye ta gama auren shi kenan.

Hura hanci da d'aukan kai da Gwaggo Aisha take a cikin gida sai wanda ya gani Inna Asabe take kula ta wani lokacin suyi tayi dan Inna ta kam ko iskar daya d'ebo ta bai ishe kallo ba.

Sosai take kokari na son ta burge Baban mu dan ta dawo da matsayin ta na da amma hakan ta bai cimma ruwa ba kasancewar Baban mu gaba d'aya hankalin shi ya dawo kan Inna ta domin ita komai zata yi mishi ko ta bashi bata yi mishi gori tsabanin Gwaggo Aisha da sai ta tsaya a tsakar gida take mishi terere kowa yana ji yana gani hakan yasa Baban fifita Inna fiye da kowa a gidan ita kuma Gwaggo Aisha wannan dalilin yasa tace asiri Inna tayi mishi kuma ko zata tafi tsirara sai ta karya shi.

*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

*14*

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Addu'ar Mash'arul Haram*

Jabir, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hau taguwarsa mai suna Al-Kaswa har ya zo Mash'arul haram, sai ya fuskanci alkibla ya yi addu'a ga Allah, ya yi kabbara, ya yi hailala, ya kadaita Allah. Bai gushe ba a tsaye yana addu'a har sai da gari ya waye sosai, sannan ya dauki hanya kafin rana ta fito.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*14*

Gwaggo Aisha tana riƙe da ƙudirinta a zuciyarta na sai ta warware asirin da Inna tayi wa Baba ta maida hankalin shi kanta tayi mulkin ta a gidan son ranta saidai rashin kud'i shi yake kawo mata cikas dan Jameela ta kwana 2 bata dawo gida ba amma ta kudirta tana dawowa zata karb'a a hannunta taje ta gabatar.

Bayan kwana 2 Jameela ta dawo daga yawonta ba b'ata lokaci ta same ta da zancen ta bata dubu ashirin zata je gwaza wajan wani gawurtaccen boka da kawarta lantana ta bata labari dan yayi mata maganin Inna.

Ba musu balle bata lokaci Jameela ta cake mata dubu ashirin da biyar tace tasha ruwa da dubu biyar d'in,in so samu ne zata so ta had'a da ni a shafa min bakin jini ko d'an yankan kai daya makale min zai guje ni su ga ta tsiya . (hmmm wai Yayana take nufi.)

"Jameela wallahi kaman kin shiga zuciyata daman ita da kinibabbiyar uwarta duk shine takamarsu, kin ga in ya rabu da ita shikenan kowa ya huta tabbas hakan zamuyi zan fad'awa bokan ya shafa mata bakin jini da ko wani namiji sai ya guje ta muga ta tsiya".

Dariya Jameela ta kwashe da shi har suna tafawa da uwarta kaman wasu kawayen juna sannan tace"shiyasa nake son ki ummata".

Gwaggo Aisha ta bud'i baki zatayi magana suka ji muryan Hajara tana cewa "haba Umma wannan wani irin rayuwa ce,wayan nan bayin Allah babu ruwan su damu suna zaune da kowa agidan nan da zuciya d'aya amma ku burin ku shine ku cutar dasu ya kamata mu d'auki darasi ko akan abinda ya faru dani ga Jameela ta saka yawon karuwanci a gaba kina gan............"

Buge mata baki da akayi shi ya hana ta karasa maganan da tayi niyyan fad'a musu,hannu tasa ta dafe bakin ta daya fara mata zugi tana bin binsu da kallo idon ta cike da hawaye su kuma suna aikin aika mata muguwar harara

"Hajara ni kike gayawa magana akan wata banza can, ni mahaifiyar ki?" Gwaggo Aisha ke yiwa Hajara tsawa tana nuna kan ta da yatsa.

Gyad'a kai tayi kana tace "Ko da yake ba laifin ki bane ina ganin harda ke suka had'a suka tsafe dole sai na tashi tsaye ko kuma Bintu ta kaini ta baro,in banda aikin asiri tayaya zaki kira 'yar uwar ki wacce ta d'auki nauyin kulawa dake da wannan suna,. Kai jama'a kaji tsoron mutum Allah ya isa Bintu ki jira kiga yanda Allah zai wulakanta ki". Ta karasa cikin wani irin d'acin rai da tsantsan tsana.

Jameela da har ta fara jin haushin 'yar uwar ta amma jin abinda mahaifiyar su ta fad'a yasa taji ta huce ashe ba yin ta bane itama asirce ta sukayi, haba abin da mamaki a ce wai Hajara ke kare mu bayan a baya ta san yanda tafi kowa tsanan mu.

Da washe gari da sassafe Gwaggo Aisha ta fita tasha dan tafiya Gwaza domin cika nufin su akan mu.

**************************

A cikin wani tsadadden Hotel Zafar yayi parking motan na shi ba tare da ya cewa Sadiq ci kan ba ya kwashi wayoyin shi tare da bud'e murfin motan ya fita.

Fitowa shima Sadiq d'in yayi suka nufi hall da ake partyn tun kamin ka shiga zaka ji cool music na tashi ga wajan ya matukar tsaruwa komai cikin tsari da aji akayi shi.

Angon yana ganin su ya karaso da sauri ya tare su fuskar shi cike da farinciki, ricewa wajan yayi da hayaniyan zuwan nashi, ya d'an sake fuska kad'an yana amsa gaisuwan abokan shi bayan ya zauna a mazaunin shi.

Hankali kwance aka fara party shima Zafar ya saki ran shi sosai akayi shagali dashi tsab'anin wasu parties da yake guduwa saboda 'yan mata masu takura mishi amma wannan har aka tashi yana nan dan babu mace ko d'aya .

Yau tunda na tashi sai shirye-shiryen zuwan Yaya na nake saboda yau kwanan shi kusan 3 kenan baya gari yayi tafiyan nan nashi da na tsana dan yanzu sosai wannan tafiyan nashi yake bani haushi ko wani sati sai ya ciri tafiya har ta kai ina yawan fad'a mishi kan wallahi in munyi aure babu inda zai tafi ya barni kafa ta kafar shi ko kuma ya daina tafiyar gaba d'aya, dariya kawai zai min a duk lokacin da na fad'i haka baya ce min komai.

Tun kamin sha biyu tayi na gama girkin da zanyi mishi harda su drinks na adana su na shiga wanka,ko da na fito azahar tayi,alwala nayi na tada sallah.

Light makeup nayiwa fuska sannan na kama kalaba da Inna tayi min da ribon dan gashi na baya kitsuwa sam.

Riga da skirt na wani material peach color na saka kayan sun zauna a jikina duk da ba wani matse ni suka yi ba,ban saka hijabi ba rolling kawai nayi da gyalen mai d'an fad'i sannan nabi jikina da turaruka kusan kala hud'u amma duk masu sanyi ne wanda sai ka zo kusa dani kamin kaji kamshin sa.

Ina gama shiryawa kiran sa na shigowa cikin tsantsan farinciki da zumud'i na daga cikin tsigar shagwab'a da zallan so na ce" Yaya naaaaa"

Ina jin shi ya sauke nannauyen ajiyan zuciya ya kasa magana sai can ya samu daman cewa " pls Baby ki fito mana in gan ki ko zan samu natsuwa I'm damn missing you "

Dariya na kyakyale dashi tare da make kafad'a kaman yana gani na nace" ni fushi nake da kai dan haka ko gobe ba zaka ganni ba ina gama fad'a na kashe wayan gaba d'aya ina mishi dariyan muguta.

Dariya shima yayi yana girgiza kai ya san fad'a kawai nayi ko baiga fuskata ba ya san na fishi zumud'i.

Na share kusan minti 15 sannan na d'auki karamin basket dana shirya mishi abinci a ciki na fita, fuskata a d'aure tam na fito tsab'anin da, da nake fitowa daga gida kuma ko kad'an naki yarda mu had'a ido dashi.

Ciki-ciki nayi mishi sallama ina kawar da kaina gefe ni a dole ina fushi, amsa sallaman yayi da murmushi akan fuskar shi yana leka fuskata, cikin tsigan tsokana yace"wannan duk fushin ni kad'ai akewa,ban san me zai biyo baya ba in nace miki gobe da safe zan koma wajan aiki."

A wani dame na juyo ina kallon shi da ido duk a waje hannu na na dama kuma dafe da kirji na.

Dariya ya kwashe da shi har yana rike ciki ganin yanda duk na rikice lokaci 1 yace "nima na rama munyi one-one kenan,ba ni kika shanya ba har na minti 15 ba".

Kukan shagwaba na saka mishi har da bubbuga kafa a kasa rarrashi na ya fara tare da cewa inyi hakuri ya daina da kyar ya samu na daina kukan shagwaban na gabatar mishi da abincin da nayi mishi, asual yaci sosai har da santi kaman yanda ya saba yace yayi missing d'in abinci na.

"Kaine kake ja mana lokaci da kaso da anyi komai ya wuce abinci kuma sai ka ture" nace ina hararrar shi ta kasan ido.

Murmushi kawai yayi ba tare da ya tanka ba, ni dai kwana 2 nan wannan abin nashi yana damu na sai dai ban nuna mishi ba a duk lokacin da zanyi maganan auren mu ba zai tab'a ce min komai ba.

Haka yau ma na daure zuciya ta mukayi hirar mu da zai tafi ya kwaso tsaraba ta harda na 1su Inna da Baban mu ya bani sannan mukayi sallama ya wuce.

Karfe tara da kusan rabi sannan su Gwaggo Aisha suka d'auki hanyan Gwaza bayan sojoji sun tabbatar musu da hanya lafiya babu wani abin tsoro,shiru motan nasu kake ji tunda suka bar gari suka shigo cikin jeji kaman babu kowa a ciki sai karan engine motan, mafi yawan mutane dake ciki sai addu'an Allah ya sauke su lfy suke banda Gwaggo Aisha data rufe ido tana ayyana yanda zata taka kowa a gidan son ran ta sannan ta shimfid'a mulkin ta har yafi na baya.

Kiiiiiiiii karan kama buriki da taji da karfin gaske shi yasa ta bud'e ido a firgice tana dube-dube, salati da taji 'yan motan suka fara yasa ta kalli gaban ta ba shiri.

Kululuuuu taji cikin ta ya bada wani kara a take taji guduwa na son zubo mata hannaye duka 2 ta d'aura akai ta zunduma ihu tana " wayyoo Allah na shiga uku yau me zan gani haka ni shatu?"

Mutane ne sun kai kusan su hamsin fuskar su a rufe kowanne d'auke da bindiga su tare gaban motan nasu sai muzurai suke.

Kowa na cikin motan jikin shi sai karkarwa yake masu kuka nayi masu addu'a nayi Gwaggo Aisha kuwa sai ihu take zunduma musu iya karfin ta gaba d'aya ta fita hayyacin ta yau ga ita ga boko haram.

A fusace wani daga cikin su ya d'aga AK47 din dake hannun shi ya fara harbin sama ba shiri kowa yayi tsit, Gwaggo Aisha ko harda sake fitsari saban rud'ewa da firgita da tayi.

Su kaman 5 suka matso gaban motan suka bud'e kofan motan suka ce kowa ya fito kuma duk wanda ya musu wani rawan kai ko kuma taurin kai yanzu zasu aika shi barza'u.

Tsimi-tsimi duk suka fito matan su da mazan su aka saka sukayi layi , su kuma sauka rabu kashi-kashi wasu suka tsaya nan dasu Gwaggo Aisha wasu kuma suka tafi taro sauran motoci masu wucewa.

"Kowa ya kawo kudin da yake jikin shi da wayan ku gaba daya" cewar wani a cikin su gashi da babban murya kana jin hausan zaka san koya yayi.

Layi sukayi suna jefa kud'add'e da wayoyin su a cikin wani katon kyale da suka shimfid'a a k'asa.

Suna gama zuba duk abinda suka mallaka babban cikin su wato Amir din su yace musu saura suturan jikin su duk su ciro su kawo suma ba mata ba maza.

Kallon kallo suka fara a tsakanin su dan basu fahimci me suke nufi ba.

"Ku cire kayan ku duka ku zuba su anan nace" ya kara daka musu tsawa daya kara hargitsa su suka kama karkarwa amma babu wanda yayi yunkurin cirewa.

Tau kake ji suka d'auke wani saurayi da bindiga babu wani nisa tsakanin shi da Gwaggo Aisha.

Kaman kiftawan ido suka fara rige rigen cire kayan jikin su, aka kwashe duka aka zuba su cikin wani buhu sannan suka umarci driver da su shiga mota su koma cikin Maiduguri a haka.
[1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

*15*

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*15*

Shiru cikin motan kaman ba wani mai rai a ciki sai muryan mata da suke kuka kasa-kasa saboda kukanta su da akai babu mai kallon d'an uwan sa duk sun takure waje d'aya suna tunanin tayaya zasu shiga gari a haka? Ita kuma Gwaggo Aisha tana ganin kaman kaifin asirin Inna shi ya hana ta zuwa ga wannan mashahurin bokan har 'yan ta'addan suka samu daman yi mata aika-aika.

A wani kauye driver ya tsaya Allah ya sa akwai wani tsumamun riga da ya maida duster yana goge-goge dashi a cikin motan, shi ya saka ya fita ya karasa cikin kauyen yayi musu bayanin halin da suke ciki, nan da nan mai garin yasa aka hado musu suturu na maza da mata ya kai musu dan ba karamin tausaya musu sukayi ba.

Koda ya kai musu kayan kowa ya d'auka ya suturta jikin sa sannan suka mike hanya zuwa cikin gari.

Azahar dai-dai suka shigo driver ya zubar da kowa nan cikin tasha ya kama gaban shi, Gwaggo Aisha da kyar taja kafafun ta da har yanzu rawa suke saboda firgita ta fito ta samu adaidaita sahu zuwa gida duk da ta san bata da ko sisi a hannu.

A hanya ji take kaman kada taje gida ta wuce ko gidan 'yan uwan ta ko zata samu canza suturan dake jikin ta wai kada su Inna su raina ta, canza akalan tafiyan tayi daga gidan mu zuwa gidan kanwar ta.

Da yake duk tafiyar su d'aya da kanwar nata da taji abinda ya faru da Gwaggo Aisha maimakon ta nutsar da ita ko ta d'aura ta kan hanya saima kara zuga ta da ta rinka yi harda cewa ta samu kudi ta kara komawa, kuma kar ta kuskura ta nuna gazawar ta har sai ta kawo karshen Inna ta.

Da wayan nan kalaman nata ta kara karfafa mata guiwa, sai bayan sallahn magriba ta dawo gida hankalin ta kwance kaman babu abinda ya faru, anyi sa'a Jameela tana gida cikin murna ta tarbe ta kannuwan ta duk sun zaku da son jin daddadan labarin yanda sukayi da boka, Hajara tana yi mata sannu da zuwa ta fice ta bar musu d'akin tare da nema musu shiriya daga rabbi.

"Umma wannan wani irin magana ne haka kike cewa ko kuma dai sabon rainin hankali da kika zo dashi kenan?" Muryan Jameela ke tashi daga cikin dakin nasu cikin tsawa kaman ba da mahaifiyar ta take magana ba.

"Na lura tunda nace ki daina sana'a zanyi miki komai kika koyi wasa da kud'i saboda baki sha wahalan neman su ba, toh wallahi nima daga rana rin ta yau na daina baki kud'i na sai dai ki koma yin sanar ki dan ba zan iya ba" ta karashe tana harare-harare ita kad'ai.

Gwaggo Aisha kin kula ta tayi ta shige can d'aki ta rabu da ita domin ta lura asirin ta take son tonawa gaban kishiyoyi wanda ba zata tab'a bata daman hakan ba duk da kwanan nan alamun karara sun fara bayyana cewa Jameela ta fara tab'a shaye-shaye.

Hajara kam tana gefe tana sauraron su bata da daman saka.
baki Gwaggo Aisha
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment