Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

shi kaga dan albarka shima, ko ba shi bane na gan su tare kwanakin baya?" Ya tambaya yana ta washe baki.



"Shine mana ma'aikacin hukuma ne ai, ni ko soja tace min ne ko d'an sanda, na manta dai" Inna ta bashi amsa ta kauda kai kada dariya ya sub'uce mata ganin yanda nan da nan Baba fuskar shi ta canza ya koma kalan fargaba da tsoro.



"Oho ashe hukuma ne, toh yayi kyau madallah da har ina cewa in naga ya dawo zanje in mishi godiya kuma muna gaisawa ashe yafi karfina". Baba ya fad'a bakin shi na rawa.



Inna had'iye dariyar ta tayi ta juyo tana kallon shi can ta ce," haba Mallam wani irin magana ne wannan, uhum sirikin naka shine yafi karfin ka?"



"Kema dai Bintu da son jan zance kike kin san bana shan inuwa d'aya da hukuma, Allah yajikan Baban ki ai ta nan ya rinjaye ni nayi ta bashi kud'i mudin in ya tambaya ko a wani waje sai naje na ciwo bashi na kawo mishi duk da shi na san yayi ritaya amma nake tsoron sa balle wanda yake saurayi mai jini a jika?



Hmmm ke dai kawai ki cewa 'yar albarka ta mik'a godiya ta a wajan sa".



"Toh shikenan Mallam zan fad'a mata" Inna ta bashi amsa.



Tun daga wannan rana Baban mu shima ya koma d'an gaye daga ya canza wannan sai ya cire wancan har a majalisan su yanzu shi yake mulki kowa so yake ya zama makusancin shi, maimakon kud'in nan daya samu ya juya su a kasuwanci suyi albarka ya rike gidan sa kaman kowani magidanci saima lalacin nasa ya karu d'an masarar da yake sayowa ma yanzu ya daina ba abinda ya shafe shi da lamarin cikin gida illa ya d'au wanka ya shigo d'akin mu yayi breakfast ya tura kud'i a aljihu yayi ficewar shi.


Aike kuwa Yaya na bai daina yi mishi na kaya dana kud'in duk bayan kwana bibbiyu yake aikowa, ranan da ya rasa na kashewa kuwa ni yake tambaya in bashi dan ya san ko ya tambayi Inna ba bashi zatayi ba.



Wahalar da muke ciki yanzu ya dawo kan Inna Asabe dan itace mai yara dayawa a gidan ga babu abinci babu jari balle ta daurawa yara sana'a, kananan yaran ta kullum a d'akin mu suke cin abinci.




Rannan Gwaggo Aisha bata gida Inna ta fito ta kawo mata rabin bugu na shinkafa da kuma carton na taliya sannan ta bata dubu goma tace tayi jari ita mai yara kanana zama haka ba zai yiwu ba.



Kuka wiwi ranan Inna Asabe tasa tana Inna ta yafe mata abubuwan da tayi mata a baya gashi wacce ta biyewa sukayi mata rashin mutunci yanzu babu ruwan ta da ita koda zasu wuni su kwana basu ci ba kuma basu sha ba ko a kwalar rigar ta sai wacce suka wulakanta itace yau ta mutumta ta haka?



Inna Asabe tun daga wannan rana ta samu abinyi itama kuma tun daga wannan rana ta fita harkan gwaggo Aisha tsakanin ta da Inna ta kuma sai mutunta juna.



**********************************



*Rubby private school* makaranta ce mai matukar tsada ta 'ya'yan masu kud'i ko manyan 'yan kasuwa, anan Yaya na ya nemo min gurbin karatu na fara fita ss1 abina kuma ya ajiye min mai napep da yake zuwa ya kaini kullum da safe kuma ya d'auko ni in an tashi, wata nayi kuma ya biya shi kud'in sa.



Maryam Alhaji idris itace seat mate d'ina tun ranan mu na farko da had'uwa muka kulla k'awance da ita domin Allah ya had'a jini mu sosai.



Kasancewar Maryam tana kusa dani yasa al'amarin makarantan yazo min da sauki, sosai take taimaka min kana ganin ta kaga wayayyiyar yarinya 'yar gayu tsabanin mu namu wayewar kauyenci ne a wajan su.



Ba'a magana da hausa sai turanci a makarantan abinda ya fara bani matsala kenan sannan kuma in ana koyarwa shima sai turanci ko kad'an basa d'an sirka hausa yanda irin mu zamu fahimta sai dai in an gama koyarwa Maryam ta kara wayar min da kai.



Term d'aya kawai mukayi na canza nayi wayewan 'yan gayu ga turanci ya fara zama a bakina domin makarantan ba wasa.



A wannan lokaci ne kuma aka saka bikin Hajara da Alhaji data samu ,wata biyu kawai aka saka Gwaggo Aisha sai habaice-habaice take 'yar ta zata je gidan hutu gidan kud'in halal bana yankan kai ba, wai kud'in Yaya nane na yankan kai.



Suna ta shirye-shiryen bikin su mu kuma muna shirye-shiryen walimar saukar mu a islamiya dan haka kona dawo daga makaranta banida lokacin zama sai na islamiya dan hadda muke kuma abinda ya rage mana bai fi izu biyar ba gashi har kuma date d'in da aka saka na saukan ya kusa shiyasa muka bada himma sosai, a yanda aka saka date d'in in anyi bikin Hajara da sati zamuyi walimar namu.


A boye Gwaggo Aisha filin ta na gado ta sayar tayiwa Hajara kayan d'aki dashi wai 'yar ta zata shiga babban gida kada su raina ta, ba laifi kaya kam sunyi kyau dan a bakin Dije nake jin wai Italian bed 'yan dubu dari uku ta saya mata da kujeru dubu dari da hamsin, Allah ya sanya alkhairi nayi na shi a wajan toh me zance ? Nida anko ma sunce kada na kuskura inyi na bikin d'akin su.


Ina gani su jamila suna ta rawan kai a shiga a fita sai shirye-shirye take itama wai zatayi nata shagalin daban dan haka ankon ma nata kala daban ne da k'awayen ta.


Ana saura sati d'aya gidan mu ya fara cika da baki 'yan uwan Baban mu da nasu Gwaggo Aisha ga hayaniya ga rashin zaman lafiya saboda kullum sai an raba fad'a, ba shiri na tattara kaya na zuwa gidan Maa ko zan samu natsuwa in ida hadda ta kuma a zuciya ta na kuduri sai sun gama bikin su zan koma gida.



Ana gobe daurin aure da yamma Yaya na yazo amma ya kasa parker motan shi inda ya saba saboda jama'a sunyi yawa anata shiga da fice sai gaba da gidan Maa yayi sannan ya kira ni a waya na fito wajan shi.



"Meke faruwa a gidan naku ne naga jama'a haka?" Ya tambaya ko gaisuwan kirki ba muyi ba.



Turo baki nayi ina mai jin haushi dan duk wanda zai min zancen auren nan haushi yake bani tayaya za'a ce wai ana biki a gidan ku amma ace wai an hana ka yin anko wani irin kiyayyane, me nayi musu da zafi haka??


Ina aiyana haka a raina naji hawaye ya zubo min wanda ya tayar da hankalin Yaya na ya shiga tambaya ta meya faru cikin damuwa.


Maimakon in bashi amsa sai na fashe mishi da kuka tsakani da Allah, nan ya kara ricewa yana tambaya ta amma na kasa magana sai shassheka nake.



Da kyar nayi shiru shima sai da naga hawaye a idon shi ba shiri na had'iye kukana na fara goge hawaye na da hijab.



Sai da muka natsu sannan ya ce," in ba so kike zuciyata ta buga ba kanwa ta ki gaya min meya faru??"



Cikin kara turo baki na ce," Auren Hajara za'ayi gobe"


Wacece kuma Hajara?"


"Yaya tace wacce a baya in kazo zaga ganta tana wucewa da abincin sayarwa"




Nan da nan ko ya gane ta na cigaba," yar Gwaggo Aisha ce kuma itace babba a gidan mu dan ni ba yar d'akin su bace suka ce kada inyi ankon auren" na karasa wasu sabbin hawaye na bin kunci na dama abin yana cina a rai sai yau na samu daman amayarwa.



Kallo na ya tsaya yi with expiration a fuskan shi, can ya girgiza kai ya ce," tunda can suke miki haka ko sai da auren yazo suka fara??" Ya tambaya fuskar sa na fallasa bacin rai da yake ciki.


"Tun muna kanana na taso naga haka ware ni suke suna hana 'ya'yan su wasa dani, ni kad'ai nake al'amura na, nake wasa na kaman mayya in Dije bata nan.



Shiru yayi na wasu dakiku sannan ya fara magana," dama bai kamata kiyi ankon su ba saboda kin fi su class shiyasa suke miki haka kuma ina so ki kwashe kayan ki zuwa gidan ku yanzu auren gidan ku ne dole dake za'ayi.


Zan kawo miki kayan da zaki saka a bikin zuwa dare nd...."



"Ba sai ka kawo min kaya ba ina da wayan da ban saka dayawa cikin wayan daka kawo min kuma ni ba zan je biki...."



" I don't care about that zan kawo kayan anjima kuma dake za'ayi bikin" yana gama fad'an haka ya fad'a motan shi ya fita a guje.



Da ido na bi shi ina jinjina girman irin son da yake min ko kad'an baya son gani na cikin damuwa.


"Allah sarki Yaya na Allah ya bar mu tare" nace na juya zuwa gidan Maa raina fess dan aiwatar da abinda ya saka ni.




*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/30, 2:28 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Addu'a Idan Mutum Ya yi fushi.*


أَعُوذُ بِاللهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ.

A'oothu billahi minash-shaytanir-rajeem.
Ina neman tsarin Allah daga shaidan tsinanne.



*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._


Duk da kin ki fad'a min sunan ki hakan ba zai hana ni nuna miki farinciki tare da godiya ta a gare ki ba,naga kyauta na yaba nagode Allah ya bar kauna wallahi ina kaunar ku fiye da yanda kuke zato ina kuma alfahari daku.


Lots of luv 😘😘😘😍😍😍


*11*


Inna tana tsakar gida tana taya su aikace-aikace duk da habaice-habaice da suke bin ta dashi bai dame ta sai gani na tayi nazo na wuce ciki da jakan kaya na.


Na shiga d'aki ban dad'e ba Inna ta biyo ni tana," har kin gama shanye yajin da kika daka ne? Ai na zata zaki yi wata kina sha kamin ya kare ki dawo sai kuma ya kare da wuri".


Turo baki nayi tare da marairaice fuska na ce," Allah sarki Inna ni ina can ina ta kewar ki shiyasa na kasa zama na dawo amma ke ko kewa ta ba kiyi ba".


"Wani abun dai ya dawo dake ba kewa ta " Inna ta fad'a tana shirin ficewa.

"Shikenan tunda baki yarda ba amma a ina zan iya zaman sati ban gan ki ba inna taaaa" naja zancen ina murmushi,karasa ficewa tayi bata kuma kula ni ba.


Kwanciya ta nayi nima a d'aki ina chatting da Maryam ban kuma lek'a waje ba, ina jin su a waje anata mayar da zance wai ashe yau akwai dinner da angon yace za'ayi da farko sai kuma wata 'yar uwar sa tazo da yamma tace an fasa dinnern saboda wata kanwar Maman su tayi hatsari a hanyan ta na zuwa bikin.


Gyara kwanciya ta nayi ina ko akwai dinner ma wa zai je, can ta matse musu nace a zuciya ta tare da jan dogon tsaki ni kad'ai.


Kusan isha'i sai ga wayan Yaya na yace yana waje, Inna har yanzu tana cikin mutane dan haka banyi mata magana ba na fita wajan sa, yana tsaye a inda ya saba tsayuwar yasha gayun sa kaman yanda ya saba sai zuba kamshi yake.



"Naji dad'i da naga kin dawo gida kaman yanda na umarce ki" yace yana kallon karamin gyalen da nayi rolling dan kullum in zan fito wajan shi hijab nake sakawa sai yau nasa gyalen saboda dare ne kuma bai tab'a zuwa wajena da daddare ba sai yau.



" Allah kada ya kawo ranan da zaka bani umarni in kasa bi, ka wuce duk wani matsayi na duniya da ka sani a waje na, u re my every thing". Na fad'a mishi cikin shaukin kaunar sa da yake d'iba ta.



Murmushin nan nashi mai sanyi ya kara fad'ad'awa yana kallon na ya ce," nagode kanwata amma bake ya kamata ki fad'i wannan Kalmar ba sai ni domin na kasance maraya banida kowa kece kika zama dangina kika zama kanwata sannan above all kika zama masoyiya ta kin ga kuwa nine zance miki u re my everything".



Kasa cewa komai nayi sai murmushi da nake saboda kalaman shi sun kara narkar min da zuciya ji nake ba zan iya rayuwa babu shi ba.



"Wannan gyalen yayi matukar yi miki kyau amma ki daina saka shi in zaki fita ki cigaba da saka hijabi yanda kika saba " ya katse min tunani na.


"Insha Allah Yaya na " na amsa mishi ina sunkuyar da kaina kasa.




Wata katuwar jaka ya d'auko a seat d'in bayan motan shi ya mik'a min ya ce," ga kayan da nake son ki saka gobe ,zan zo kaman da karfe goma sha biyu dan kai ki beauty saloon make sure kin shirya before inzo"



Na bud'i baki da niyyan godiya ya katse ni ki shiga gida sai nazo " gyad'a kai nayi ina murmushi na juya na shiga gida.



Da ni da Inna ta duk saka kayan mukayi a gaba muna kallo cike da mamaki, wani haddaden gown ne light blue adon da akayi a jiki ma ya isa mutum kallo sannan ga wani karamin box da yake d'auke da wani tsiririn sarka mai d'an karan kyau da d'an kunnen shi wanda Inna tace tabbas gold ne sai kuma takalmi mai tudu da pos d'in sa suma ko makaho ya shafa su yasan naira tasha kashi wajan sayan ta.



"Wannan hidima anya batayi yawa ba, yau kuma harda zinare?" Inna ke fad'in haka cike da jimami.


" Yaya ne fa Inna meye abin damuwa saboda ya saya min kaya, ai ya riga ya saba yi " nace hankali na kwance kuma tsakani na da Allah na fad'a.



Shiru kawai Inna tayi ba tare da ta kara cewa wani abu ba kasancewar ta gane in banda tarin kuruciya babu komai a cikin kaina, abu d'aya yake sanyaya mata zuciya shine yanda bata sakaci wajan tsayuwar dare kuma duk a kaina.


A baya bata damu da lamarin Yaya na sosai ba kaman da yanzu na girma, duk da cikin hikima irin tasu ta manya tana jin yanda muke tsakani na da shi ko hannu na bai tab'a tab'awa ba.



Addu'an Allah yayi jagora ya tsare daga duk abin ki tayi ta tashi a wajan ni kuwa cikin zak'uwa da zumud'i na jawo kayan na fara kallo saboda dazu idon Inna ya hana in sake in kalla da kyau har na kosa goben tayi in saka kaya na.




Da washe gari da hayaniyan mutane muka tashi gidan mu ya cika ba masakar tsinke gaba d'aya sai naji na takura dan da naje da niyyan shiga bayan gida da gudu na dawo ina kakarin amai saboda yanda mutane suka b'ata shi, ba shiri na samu 'yar karamar jaka ta na had'a duk wasu abubuwa da zan bukata na zuba a ciki na wuce gidan Maa bayan na fad'awa Inna a can zan shirya sai in dawo.



Ko da na je gidan Maa itama bata zauna ba gidan namu ta tafi aka bar ni kad'ai a nan Inna ta aiko min da abincin safe da akayi na d'aurin aure,da yake safe ne sai na kasa ci na fito na samu yaro a waje na aike shi wajan mai shayi ya had'o min breakfast na nayi na kwanta bacci ni ban tashi ba sai kusan sha d'aya .



Ina shirin shiga wanka naga an ajiye min wani abincin bayan na safe, Allah sarki Inna ta na san wannan duk aikin ta ne, ban ci abincin ba sai bayan na fito daga wanka.



Lotion kawai na shafa na saka kayan da Yaya na ya kawo min jiya da daddare, aiko ya zauna das a jikina kaman an gwada ni irin gown d'in nan da bayan yafi gaba tsayi wani sarka da d'an kunnen kira Dubai data sayo min a baya shi nayi amfani da shi dan gold din Inna b'oye shi tayi tace ba zanyi amfani da shi ba,ko minti goma banyi da gama shiryawa ba kiran Yaya na ya shigo waya ta hijabi na d'aura akan kayan na fito.



Yau manyan kaya ne a jikin sa tsab'anin da ya murza hulan Ahaiyye a kan sa ya matukar kyau sai zuba kamshi yake.


"Yaya naaa ka gan ka kuwa kayi kyau sosai sai kace kai ne angon" na ce mishi ina dariya.



Murmushin sa mai sanyi ya yi min sannan ya ce" hmmm ke ba?"



"Ni me?" Na tambaye shi ina turo baki.


"Ke kanwa tace na ce".

"Kanwa only?" Na kara tambaya ina fiddo da ido waje.


"Baki kyauta min ba kin ki fad'a min auren nan in time balle in kawowa Baba wani abin kirki shiyasa na ki zuwa daurin auren,amma ki min magana da shi in bashi hakuri da gudumuwa na ko kad'an ne". Ya ce saboda kawar da wancan maganan da muka fara.



Gyad'a kai kawai nayi na juya ina dan dariya tun kamin inga draman da zai faru tsakanin Baba da Yaya na.



Allah yasa a hanya muka had'u da shi yana dawowa gida da yake ba a kofar gidan mu aka d'aura auren ba a can wani masallaci dake kan kwanan layin mu, yanzu haka suna tare da wasu 'yan uwan sa da sauran abokan shi ne a wajan bayan mutane sun watse.



"A'a 'yar albarka ke ce, ina zuwa kuma?"


"Baba dama wajan ka zan je, ummm...hmmmm wannan d'in nan da yake aiko maka da kaya shine ya zo yana so wai ku gaisa kuma ya baka hakuri da gudumuwan sa" na karasa kai na a kasa saboda kunya.


"Wai wannan mai zuwa wajan ki nan?" Ya tambaya yana zaro ido.



Danne dariyar daya taso min nayi ina gyad'a mishi kai.



"Toh meye sai mun gaisa da shi,naga a baya ke yake bawa ki kawo min ba yau ma ya baki d'in mana".



"Baba nima ban san dalilin da yake son ku gaisa ba yau amma tunda ya bukata kila yana da wani dalilin" na fad'a ina kallon yanda naga duk hankalin Baba ya tashi kaman ba yanzu na gan shi cikin annashuwa ba.



"Ki ce ya zo nan ya same ni ina jiran sa a nan " .


"Toh Baba" na ce tare da juyawa na koma wajan Yaya na sannan na fad'a mishi sakon Baba.



Naso bin shi inga yanda zasu kare da Baba sai kuma naga rashin cancantan hakan na tsaya jiran shi.



A nesa Baba ya hango shi yana zuwa yana saka wayar shi a aljihu wanda shi kuma Baba kallon bindinga sak ya yiwa wayan, nan da nan ko zuciyar Baba ta fara zillo kaman zata fito.


Cikin matukar sauri ya juya ya fara tafiya kaman zai kifa ya nufi masallaci inda ya bar mutanen shi suna jiran shi, yana cikin tafiyan kuma wani tunani ya fad'o mishi ya canza hanya zuwa bayan layin mu.



Yaya na yana zuwa wajan ya ga wayam bai ga kowa ba kaman zai koma kuma ya fasa ya karasa har bakin masallacin aka ce mishi baya nan, haka ya hakura ya dawo ya ce bai gan sa.



A hanyan mu na zuwa saloon sai murmushi nake dokawa ina hana dariya ta fitowa na san Baba k'in tsayawa yayi saboda tsoro.



Babban wani tsadadden saloon ya kai ni a west end wanda ba abinda basa yi na gyara da kamshi har da lalle, gefe naga Yaya na ya kira wata da alama ita ce babban su a wajan ban san me suka tattauna ba naga ya bata kud'i masu yawa ya fita, nan da nan suka shiga hidima da ni har da su drinks da snacks suka kawo min.



Ba b'ata lokaci suka warware yalwantaccen gashi na suka wanke suka gyara shi nan da nan kuwa ya kara kyau sai d'aukan ido yake, wanke min kafa suka yi a wani abin wanke kafa ni dai ban tab'a gani ba sai ranan,fara ce na su ma sun gyara sannan suka yaryad'a min lalle mai ja da baki.


Light makeup suka yiwa fuska ta daya kara fito da ainihin kyawu na, wani haddaden net mai kauri da yayi matching da kayan jiki na suka d'auko a shagon nasu suka nad'a min shi in a unique way.



Fad'an irin kyan da nayi ma b'ata lokaci ne dan sai in rantse da Allah ban tab'a sanin ina da irin wannan kyau ba sai yau, sai kallon kai na nake a madubi, su ma 'yan wajan sai yaba kyau na suke.



Da zan fita na fara kokarin saka hijabi na, 'yan wajan ne suka min caa wai kar in saka daurin net d'in zai lalace tun ban isa gidan auren ba,tunda a mota muka zo in tafi a haka.



Ba dan naso ba na fito a cikin saloon d'in ina takawa a hankali kaman mai tausayin kasa saboda tudun takalmin kafa na har na iso bakin motan Yaya na bai sani ba kasancewar ya kwantar da seat ya kwanta da earpiece a kunnen shi ban san me yake saurara ba.



Bud'e kofan motan nayi na shiga na zauna kamshin turare na shi ya isar da sakon isowa ta a gare shi ya bud'e ido ya sauke su a fuska ta da nima shi nake kallon, mun dad'e muna kallon juna daga baya nice na sauke nawa idon kasa ina d'an murmushi.




Ina jiyo shi sai da ya sauke ajiyan zuciya har sau uku sannan ya tashi ya zauna tare da gyara kujeran, ya juyo ya kara kallo na kaman zai ce wani abu kuma ya fasa ya tada mota muka kama hanyan gida,har muka iso babu wanda ya yi magana.



Yana yin parking na ce," nagode Yaya naaa zan shiga ciki sai anjima".



Har na bud'e kofan na fita bai amsa min ba na fara tafiya, nayi kaman taku uku naji muryan shi ya ce," Zareefa...."



Da matukar mamaki na juyo dan jin suna na a bakin shi yau.


" Kinyi matukar kyau....,kyan da baki ba zai iya furawa ba, amma dan Allah in muna tare ki rinka saka hijabin ki" yana gama maganan shi yaja motan shi ya tafi.



A hankali na juya zuwa cikin gida ina murmushi da mamakin me yasa yake yawan cewa in saka hijabi ba.



Ina saka kafa gidan mu ido ya dawo kai na kowa ni yake kallo da gudu Dije ta zo ta rungume ni cikin ankon da suka hana ni yi sai naga ashe da a lokacin ma naga ankon ba sai sun hana ni ba da kaina zance ba nayi.



Can b'angaren su taja ni muka tafi tana in bata labari meye sirrin?


A nan muka zauna ina bata labarin saloon d'in da muka je na fara jin sautin kid'a daga waje.


Da mamaki na ce", kaman kid'a nake ji?"


"Eh dama naji Hajara da kawayen ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment