Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

na ce," Inna kuka kike,meya same ki?" Duk na jero mata wayan nan tambayoyi a lokaci guda.


Murmushin nan nata mai ciwo tayi min kana ta ce," babu komai ba kuka nake ba wani abu ne ya shiga ido na".


Ba dan na yarda ba nayi shiru nasan ko abinda ake mata a gidan nan dole tayi ta kuka kullum,komawa gefe nayi na zauna ina kallon ta tana dinke min wuyan uniform d'ina daya yage bata kuma yarda ta zubar da hawaye ba.



Da washe gari da safe bayan na sayo alale na naci Inna ta bani 200 a cikin kudin daya saura ta ce in kai makarantan nima a bani bani sabon uniform d'in inya so ko shekara mai zuwa sai in zana jarrabawan.



Cikin matukar farinciki na nufi makaranta yau nima za'a bani kyautan kayan makaranta kaman sauran d'alibai.



Direct office d'in principal na wuce ina jin kaina yau kaman bani ba,bayan na gaishe shi na bashi kud'in na ce ni jiya ban samu daman zuwa ba shiyasa ban samu komai na rabo ba.


Tambayan shekaru na yayi na fad'a mishi ya ko duba ya ciro uniform sabo dal ya miko min,murna fal jikina na karb'a amma sai na kasa tafiya ina jiran jaka da sauran tarkace.



Ganin na ki tafiya ya ce," me kike jira kuma?" Kasa nayi da kaina na ce," Sir su jaka da takardu suma ban samu ba".



"Okay toh sai gobe ko anjima dan suna store,ya suna ki kuma a wani class kike?"



"Suna na Fatima Hassan,kuma ina class 6A" na bashi amsa.



"Toh kije anjima zan sa akai miki" cike da farinciki na juya na koma ajin mu feeling proud.


A wajan assembly akayi announcing cewa duk wanda bai biya kud'in common entrance ba ya koma gida dan zuwa nan da awa 2 za'a fara kuma ba barin mu za'ayi mu shiga ba,nan take murna ta ya koma ciki.


Jiki a mace na kama hanyan gida dan nasan zaman nawa bashi da amfani,ina tafiya ina hawaye saboda na kwallafa rai na akan jarrabawan,shikenan inaji ina gani mates d'ina zasu wuce ni.



Ina tafiya cikin tafiya naji horn a kusa dani ,matsawa gefe na karayi maimakon ya wuce sai naga ya tsaya kusa dani yana kallo na ya ce," kanwata meya same ki kike kuka akan titi?"


Kallon shi na tsaya yi d'an kyakkyawa dashi duk da ba fari bane.


"Kiyi magana mana kanwa ta?"ya katse ni.


"Kud'in common entrance ake nema shine aka kore ni dan ban biya ba" na bashi amsa sabon hawaye na bin kunci na.



"Oh stop crying,kiyi shiru muje makarantan naku in gani" yace yana fitowa daga cikin motan shi.



Tsayawa nayi kallon shi ba tare da na motsa ba, murmushi shimfid'e a fuskar shi ya zagayo inda nake tsaye ya rankafo da kan sa kusa dani ya ce," me kike tunani ?"


"Inna ta zata min fad'a ta hana ni magana da wanda ban sani ba" nace ina kara komawa baya.



"Kada ki damu ni Yayan kine muje zan miki bayani kin ji?" Gyad'a mishi kai nayi muka koma makaranta dama banyi nisa ba.


Office d'in principal muka tafi bayan sun gaisa ya mishi bayanin cewa shi Yaya nane yazo biya min kud'in common entrance,ni dai ban ce komai ba sai bin su da nake da ido,a take ya cire kud'i d'ari biyar- biyar sabbi fil ya biya muka fito ya ce," kije class kuma kiyi kokari sosai kinji kanwata?"



Murmushi ne ya kwace min na gyad'a kai na tare da rugawa zuwa aji.
[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```


*_And now_*


*_💃🏻UBA SONTA NAKE BA💃🏻



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*


*Abin Da Musulmi Zai ce idan aka yabe Shi:*

اَللَّهُمَّ لاَ تُؤَاخِذْنِي بِمَا يَقُولُونَ، وَاغْفِرْ لِي مَا لاَ يَعْلَمُونَ (وَاجْعَلْنِي خَيْرًا مِمَّا يَظُنُّونَ)

Allahumma la tu'akhizni bima yakuluna waghfir lee ma la ya'alamun, (waj alne khayran mimma yazunnun).

Ya Allah! Kar Ka rike ni da abin da suke fada, Ka gafarta mini abin dab a su sani ba, Ka sanya ni fiye da yadda suke zato.



*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._


*3*

Koda na tafi class naga kowa harkan gaban shi yake kasancewar sai zuwa nan da awa 1 za'a fara jarrabawar, dan haka kawai sai na wuce bayan gida na canza sabon uniform nawa, na sanin cewar daga yau na gama amfani dashi dama Inna tasa na karb'a ne kan cewa zan ƙara wata shekarar amma Allah ya taimake ni ya kawo wannan mutumin da yake cewa shi Yaya nane.


Kayan ba ƙaramin kyau suka yi ba, sun zauna sosai a jikina dama gani ba za'a kira ni mai jiki ba kuma ba za'a kira ni da sirirya ba,ga fata ta irin mai tsadan nan ce, wato chocolate colour wanda yayiwa round face na kyau,bani da dogon hanci can amma inada daidai gwargwado sannan manyan idanu na da d'an ƙaramin baki na su suke sa mutane suke min kallon wata kyakkyawa,wajan gashi ma dai babu laifi dan ina dashi ba laifi.


A bola na watsar da tsohon uniform d'in nawa dan inada yakinin in aka bawa wani ko goge-goge ba zaiyi dasu ba,na kama hanyan class d'in mu sai na zama abin kallo ga sauran d'aliban wasu na min dariya wasun kuma na cewa sun min kyau,ni dai ban kula kowa ba nayi wucewa ta class d'in mu.



Nan ma bata canza zani ba dan wasu har tsokana ta suke,kala bance musu ba sai harkan gaba na nake zuciya ta fari kal zan rubuta jarrabawa tare da 'yan uwana.




Bayan wani lokaci malamai suka shigo raba mana paper, nan kowa ya natsu bayan sun gama raba mana kowa ya fara rubutu sai naga ashe abun ba wuya ba kaman yanda na tsorata da shi bane a farko,cikin kankanin lokaci na kammala na fito abu na ina mai jin farinciki a rai na.


Da daddaya kowa ke fitowa bayan mun gama fitowa aka raba mana abinci mai d'an karan dad'i jallof na shinkafa harda naman kaza da bobo.


Kin cin nawa nayi na kama hanyan gida da abinci na,ina tafiya ina ta dube-dube ko zan kara ganin bawan Allah nan amma ko mai kamanin sa ban gani ba har na iso gida.



Duk 'yan matan gidan mu yau suna nan basu fita tallah dan azahar batayi ba sai dai kowacce suna bakin murhu da uwayen su suna aikin kayan sana'ar su sai yara mazan ne da suka fita sai da pure water.



D'akin mu na wuce direct sanin cewa Inna ta tana ciki ko lura da kallon tsana da Gwaggo Aisha ke auna min banyi ba nayi sallama na shiga d'akin mu.



Inna ta na zaune da sabuwar multi na hula a hannun ta tana tsakawa ,da sauri na ida shigowa ina cewa," laa Inna hula kika fara,yaushe kika koya ko dama can kin iya?" Na jero mata tambayoyin nan duk lokaci d'aya cikin zak'uwa.



Murmushi shimfid'e a fuskar ta tace," kinga yanda sabuwar uniform d'in ya miki kyau kuwa,kinga har shekara mai zuwa zakiyi amfani da kayanki hankali kwance".



Zama nayi ina ajiye takeaway da bobo na hannu na, nace mata," ai Inna bana bukatan uniform d'in hasalima daga yau amfanin shi ya kare domin dani aka zana jarrabawan".



"Dake aka zana sun tausaya ne suka bar miki ko kuwa?"ta tambaya fuskarta d'auke da farinciki mai cakude da mamaki.



"Ko kad'an basu ji tausayi na ba Inna,kora tama sukayi har na fito daga makaranta zan dawo gida...." Nan na bata labarin abinda ya faru tsakani na da wanda ya ce shi Yaya nane.



Maimakon inga tana farinciki sai naga ta tsuke fuska ta fara min fad'an da kada in sake yarda da wani kan titi wanda ban sani ba ko ya bani abu in karb'a,a irin haka suke maida yara doya su tafi dasu suyi tsafi dasu ko kuma a yanke kan su.


Tsoro sosai ya kama ni nayi ta zare ido ina ganin na tsallake rijiya da baya ashe,nan na bata hakuri tare da alkawarin bani ba wanda ban sani ba nan gaba.



Daga nan hira muka zauna yi da Inna ta bayan na bud'e mana takeaway nace muci tare,kallon abincin tsaya yi kana tace,"yanzu dama irin wannan abincin ake raba muku harda naman kaza?"



Dariya na kyakyale dashi sannan nace," Inna baki ga harda bobo na ba?"


"Ikon Allah tunda nake ban tab'a jin labarin governor mai son talakawan shi haka ba sai akan bawan Allah nan,Allah ya kiyaye mana shi" cewar Inna .


Da "Ameen na amsa sannan nace mata muci mana,amma taki ci d'an tab'awa kawai tayi ta bar min kaya na anan ne take gaya min ashe 'yar wata makociyar mu mai suna Ya'ana ita ta koya mata d'inkin hula,shikenan ta huta da zaman banza inta gama ance ana saya da kud'i da d'an yawa,murna nayi tayi muma mun samu sana'a da zamu rinka samun kud'i kaman sauran 'yan gidan mu.



Tun daga wannan rana na mayar da hankali na kan makaranta islamiya da nake in kuma safiya ce Inna ta kan tura ni gidan kakanni na saboda gudun rigimar 'yan gidan mu sai lokacin islamiya yayi sai in dawo in shirya inyi wucewa ta domin Gwaggo Aisha tafi kowa iya tuggu kuma Baban mu sosai yake jin maganan ta in fact itace 'yar gaban goshin shi ba dan komai ba sai dan tafi sauran matan shi kud'i kuma tana bashi kud'i shiyasa yake ji da ita sosai.



Maganan shiga secondary school mun ajiye ta a gefe kan cewa sai inna ta dinka hula 2 ko 3 sai ta had'a kud'in ayi min komai dashi.



Cikin ikon Allah satin hulan 4 Inna ta kammala shi baiyi kyau irin na kwararre ba amma da yake cikin tsafta ta dinka shi babu datti ko kad'an a jiki sai ya zama abin sha'awa.



Ya'ana wacce ta koya mata itama ta gama nata zata kai sayarwa Inna tace muje tare sai ta sayar a bani kud'in kasancewar ita zata wuce gidan kakanni ta daga can kuma zata kwana 2 kamin ta dawo.



Bayan ta shirya ta biyo min muka tafi can London ciki wai can sun fi sayan hula da daraja, dubu da dari biyar aka sayi na inna ta ita kuma Ya'ana dubu tara aka sayi nata da saboda ita nata tangaran ne.


A leda baki ya'ana ta kulle min kud'in ta saka ni a napep na zuwa anguwan mu ita kuma ta wuce,muna zuwa kusa da layin mu suka sauke ni suka wuce.


Har nazo kusa da layin mu na had'u da wani mutum yace min," ke ana sadaka a wacan kwanan" kamin in bashi amsa wasu yaran su 4 suka zo wucewa ya fad'a musu ba musu suka bi hanyan daya nuna nuna musu,ganin sun bi hanyan yasa nima na bisu a guje muna shan kwanan ashe mutumin yana bin mu sai muryan shi muka ji yana cewa," kai ku tsaya in akwai abu a hannun ku,ku kawo in ajiye muku kar ya fad'i wajan karb'an sadakan".



Gaba d'aya mu muka mika mishi duk kud'add'en hannun mu da alamu suma sauran yaran aiken su akayi,yana karb'a yace mana ga gidan can mu shiga shi yana jiran mu anan.



Ga gudu muka shiga gidan da sunan karb'an sadaka amma me sai aka ce mana ai ba anan akeyi ba,wata da zata girme mu a ciki tana jin haka ta fita da gudu muka mara mata baya amma muna fita muka nemi mutumin nan sama ko kasa muka rasa shi,kuka ko wannen mu ya fara dan sai yanzu muka gane cewa ashe b'arawo ne yayi mana dabara ya sace mana kud'add'en mu.



Gefen titi na samu nayi zama ta ina kuka na kasa komawa gida in naje me zan cewa Inna ta bayan kwanaki tayi min fad'a akan irin haka sai gashi na maimaita,bayan haka hulan nan yanda ta dage tayi ta d'inka shi ba dare ba rana dan ta samu saka ni a secondary school amma sai in koma ince mata wani ya min dabara ya kwace? gaskiya ba zan iya komawa ba.



Ina zaune ina kuka na d'aya daga cikin yaran da shima an sace mishi kud'in yazo ya zauna kusa dani muka cigaba abin mu,kaman daga sama naji ance," kanwata yauma kukan kike?"



Da sauri na d'aga kaina dan ganin waye sai naga wannan bawan Allah daya biya min kud'in jarrabawa ne hannun shi rike da bottle water inaga a shagon kusa damu ya saya ga mutane a wajan suna ta shiga da fita babu wanda ya kula mu sai shi da yazo yanzu.


Kin kula shi nayi na d'auke kaina ina goge hawayen ido na.


"Kai meya same ku kuka zauna anan kuke kuka?"ya tambayi yaron kusa dani.



Shi kuwa kama jira yake ya fad'a mishi duk abinda ya faru nan ya tambayi shi nawa ne kud'in?.

"Dari uku ne akace in sayo taliya da mai da maggi" ya bashi amsa.



Dari biyar ya ciro a aljihu usual sabo dal ya bawa yaron,cike da murna yaron ya karb'a yana godiya ya ruga da gudu ya tafi shagon kusa damu ya sayi kayan yanda ya fad'a ya dawo mishi da canjin shi,amma sai yaki karb'a yace ya tafi ya bar mishi.



Murna fal ranshi ya kama hanyan gida da gudu ya bar mu a wajan,ganin ban bi yaron ba yace min," ba tare kuke bane?" Jiki a mace na girgiza kaina saboda na zata yaron yana amsan kudin zai zama doya kaman yanda inna ta ta fad'a sai naga ba haka bane lafiya lau yayi sayayyar shi ya tafi gida.


"Ke kuma nawa ya sace miki?" Muryan shi ya katse min tunanin da nake.



"Kud'in hulan Inna ta ya karb'e gaba d'aya" na bashi amsa.



"Stop crying kanwata kinji,gashi karb'i ki kai mata".


Kallon kud'in na tsaya yi ina tunanin in karb'a ko a'a?



"Karb'a mana ki goge hawayen ki" saka hannu 2 nayi na karb'a cikin sanyin murya nace," nagode!"


Girgiza min kai yayi ya ce," kada ki damu tashi ki tafi gida".


Da azama na tastashi nayi gidan mu ba tare da nasan nawa ya bani ba.



A gida kuwa Inna duk ta damu tana tunanin me yasa na dad'e haka,tana ganina ta sauke ajiyan zuciya ta ce," zareefa me yasa kika dad'e haka?"


Banyi kasa a guiwa ba na kwashe duk abinda ya faru na gaya mata,karban kud'in tayi ta kirga taga dubu uku ciff,fincikoni tayi da karfin tsiya na fad'i akan simintin d'akin na bud'i baki zanyi ihu ta ce kada na kuskura inyi mata ihu anan dole na had'iye kukana ina zaro ido saboda ganin Inna ta ta fusata yau sosai.


" Wato ke ba kya jin magana ko zareefa duk abinda na gaya miki ta bayan kunnen ki suka wuce ko,baki san ki kama kan ki a matsayin ki na ya mace ba duk ko wani d'an iska ya baki kud'i karb'a kike yau kuma harda bin wani, Inna ilahi wa inna ilahi rajiun!!!

Toh tunda kunnen kashi gare ki yau zanyi maganin ki wallahi" ta karasa tare da murd'e min kunne.



Sosai ranan inna tayi min abinda tunda na san kaina bata tab'a yi min ba daga baya tayi min nasiha sosai mai ratsa jiki.



Tun daga wannan rana nayi hankali ya kasance babu ruwana da duk abinda zai had'a ni da wanda ban sani ba sosai na kama kaina.




Kullum Baba inya shigo gida Gwaggo Aisha itace zatayi ta dawainiya dashi dan ko Maman su Hafsa bata samu wannan matsayi a wajan shi ba,shi irin mazan nan ne da mace in zata rike shi tayi mai komai toh dad'i zaiji kwata-kwata bashi da zuciya d'aukan nauyin iyali da Allah ya d'aura mishi shiyasa gidan namu kullum sai kara hargitsewa yake.



Maman su Hafsa abin na damun ta sai dai babu yanda ta iya tayi-tayi amma ta kasa kamo Gwaggo Aisha dan tafi ta samu nesa ba kusa ba.



Ranan wani juma'a daya kasance girkin inna ta ne kuma a ranan munyi sa'a Baba ya kawo mana masara kusan kwano 10 ya ce a nik'a tunda babu garin tuwo.



Maimakon manyan gidan su kai sai suka ce ba zasu kai ba tunda ba girkin iyayen su bane,shikenan sukayi zaman su babu wanda ya ce musu wani abu.



Dole yasa wheelbarrow inna ta aro ta saka min a ciki ta ce in kai, ina turawa da kyar na kama hanya na fita a gida ga kuma inda zan kai nikan da d'an tazara da gidan mu.


Inna ta ana cewa tana da girki a gidan ne amma baba baya shigowa d'akin ta kaman yanda yake shiga sauran d'akin matan shi kuma baya cin abincin ta,na sha jin yana cewa nima Allah ne ya kaddara sai na taka duniya amma har yau yana jin takaicin wannan abin.



Na isa lafiya sannan nabi layi har aka zo kai na aka nik'a min mutumin shiya taimaka ya mayar min cikin wheelbarrown na kama hanyan dawowa gida.



Ina cikin turawa jikina duk gumi ban san taya wannan yaron ya shiga gaba na ba da keken sa da alamu ma dan koyo ne dan da kyar ma in ya kaini shekaru,duk yanda naso kaucewa amma abin bai yiwu ba saboda nik'an da nauyi kamin kace me dani dashi duk muka zube a wajan tare da kurkurjewa buhun nik'a na kuma sai cikin kwata da yake kusa damu.



Hannu 2 na d'aura a kai na rusa ihu ina gari na dan ko zafin kurjewan na daina ji saboda nasan in na koma gida babu garin nan wallahi Baban mu zai iya babbake ni da raina.



Sosai nake kuka kaman raina ya fita mutane sun taru suna mana sannu ko jin su bana yi har yaron ya d'auki keken shi ya tafi babu wanda ya hana shi kasancewar karami ne babu abinda zai iya yi.



"Oh not again yauma kuka take,meya same ta?"naji muryan shi kaman daga sama.



"Karo sukayi da me keke nik'an ta ya fad'a kwata" wani yaro ya bashi amsa yana nuna mishi buhun da aka ciro a kwata wanda ko akuyoyi ba zasu iya cin garin da yake ciki balle mutum.



Baice komai ba ya koma ya motan shi ya wuce,ajiyar zuciya nayi da Allah yasa bai ce zai ban wani abu ba yau,mutane suna bani bakin in tashi in tafi gida amma kirmitsitsi naki motsawa balle su saka ran zan tashi.



Bayan kaman mint 5 na kara jin muryan shi yana cewa," ga wannan tashi in ajiye ki a gidan ku".



Kallon inda yake nayi naga buhun shinkafa da wasu kwalaye harda jerrican mai ana saka mishi a boot din mota,kaman wanda aka jona da remote na tashi jiki na na b'ari na fara tura wheelbarrow na da gudu nayi hanyan gida na bar shi tsaye anan.


Ana gama saka masa kayan ya tambaya ko akwai wanda ya san gidan mu anan?


Wani yaro yayi caraf yace ya san gidan mu gashi can babu nisa sosai daga nan.



Motan shi ya shiga tare da cewa yaron yazo ya raka shi,ba musu yaron ya shiga suka bi baya na.
[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```


*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*

*_4_*

*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*


*Addu'ar Tsayuwa a Kan Dutsen Safa da Na Marwa*

Jabir, Allah ya yarda da shi ya ce, yayin da yake siffanta hajjin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; yayin da ya kusanto dutsen Safa sai ya karanta:

إِنَّ الصَّفَا وَالْمَرْوَةَ مِنْ شَعَائِرِ اللهِ.
أَبْدَأُ بِمَا بَدَأَ اللهُ بِهِ.

Bers Safa: Innas safa wal marwata min sha'a'irillah
Abda'u bima bada'al lahu bihi.

Hakika Dutdsen Safa da na Marwa suna daga cikin alamomin da Allah Ya sanya (na addininsa)".

Ina farawa da abin da Allah ya fara da shi.

Sannan ya fara da Dutsen Safa, ya hau shi har sai da ya hango dakin Allah, sai ya fuskanci alkibla, ya kadaita Allah, (ya yi hailala), ya girmama shi (ya yi kabbara) ya ce;

اللهُ أَكْبرُ! اللهُ أَكْبرُ! اللهُ أَكْبرُ!

Allahu akbar. Allahu akbar. Allahu akbar.
Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma, Allah ne mafi girma.

لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ، اَللهُ أَكْبَرْ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَدِيرٌ، لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللهُ وَحْدَهُ أَنْجَزَ وَعْدَهُ، وَنَصَرَ عَبْدُهُ، وَهَزَمَ اْلأَحْزَابُ وَحْدَهُ.
Bers la Ka'aba: La ilha illallahu, allahu akbar, La ilaha illal lahu wahdahu la sharika lahu, lahul mulku wa lahul hamdu, wa huwa ala kulli shay'in kadirun. La ilaha illal lahu wahdahu. Anjaza wa'adahu, wa nasara abdahu, wa hazamal ahzaba wahdahu.

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Mulki ya tabbata a gare shi, kuma yabo ya tabbata a gare Shi; kuma Shi Mai iko ne a kan komai. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Shi kadai. Allah ya gaskata alkawarinsa, Ya taimaki bawansa, Ya ruguza rundunonin kafirai Shi kadai.

Ya karanta wannan zikiri sau uku, yana yin addu'a bayan kowace marra. Da ya hau Dutsen Marwa ma ya yi kamar yadda ya yi a kan Dutsen Safa.

*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._


*_4_*


Ina isowa kofar gidan mu shima sun iso abinka da mota,ina ganin motan nayi jifa da wheelbarrow a nan bakin k'ofar gidan mu na shiga ciki da gudu ban tsaya a ko ina ba sai d'akin mu a d'akin ma a bayan k'ofa na b'uya ina lek'e.

Inna da tun shigowa ta take kallo na fuska d'aure ta ce," wa kika tsokono a wajan da kika shigo min a guce haka?"

Ban iya bata amsa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment