Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tayi joining next year, naga ashe matakin mu daya da ita a karatu.

*****************

Tun goma da rabi na safe gidan mu ya fara tara mutane amma na jiki sun zo ne dan raka Inna taga gida na, su Aunty's dina sune farko-farkon zuwa amma Inna tace musu babu inda zata je bata shirya zuwa a yau ba sai wani lokacin.

Ba yanda ba suyi da ita ba tace su suje kawai ta riga ta shirya duk kayayyakin da zasu kai min kaman su kayen lefe na da sauran kayan da ba'a samu kaiwa a ranan bikin ba, Aunty Batul cewa tayi shikenan tayi zaman ta tunda hankalin ta yaki kwanciya da zuwan nata.

Ita kuma Aunty Fatima bata yiwa kowa magana cikin su ba ta fita a gidan zuwa gidan Yar uwar su wato Maa ta same ta zaune cikin shirin tafiya su kawai take jira, tana ganin Aunty Fatima ta mike tana nad'a latfayan ta tace " aini tun d'azu ku nake jira sai yanzu Bintun ta gama ne?"

"Bintu fa cewa tayi babu inda zata je wai sai dai mu muje..." Ban gane babu inda zata je ba, zuwan uwa taga gidan 'yar ta ranan bakwai ai al'ada ce da ta kafu tuntuni balle tace akan ta za'a fara, maza wuce kice mata ta fito yanzu kuzo mu tafi".Maa ta katse ta a zafafe.

Ba musu Aunty Fatima ta juya zuwa gidan mu dama zuwa tayi ta fad'awa Maa ta san ita kad'ai ce zata iya saka ta zuwa ko bata so.

Masu rakiya duk sunyi jigum jin cewa uwar Amarya ba zata je ba Aunty Fatima ta shigo taja ta gefe tace mata maza ta shirya inji Maa su tafi, ba yanda ta iya haka ta shirya suka kama hanya a motoci kusan 3 da aka aiko musu daga gidan su Zafar.

Ni kuwa hira sosai muka Sha da yasmeen Wanda yawanci labarin Yayan ta take bani kan yanda yake tsoron Abban shi Kuma hakan baya hana shi tsula tsiyar shi Mom tana rufa mishi asiri, sosai nake ta shan dariya harda rike ciki bamu tsagaita ba saida su Maryam suka zo sannan ta bar labarin nashi muka shiga wata daban.

Sai bayan azahar su Inna suka iso baki na ya kasa rufuwa da gudu na fad'a jikin ta na kenkeme ta ina hawayen farinciki, ajiyar zuciya Inna take ta saukewa akai akai na kwanciyar hankali dan bata ga alamun tashin hankali a tare da ni ba.

Sai a lokacin ta samu kwanciyar hankali ganin gida tana ta jero min addu'oi a zuciya na samun farinciki mai daurewa a gidan mijina, duk wani abu na tarban baki maman Yasmeen ta aiko mana har manyan kuloli na abinci dan haka bamu nemi komai ba aka shiga serving din baki mu dai muna can ciki muna ta hayaniyar mu.

A daidai wannan lokacin Momyn Zafar da gayyar ta suka iso ,sai huhhura hanci suke suna kallon mutane a d'age su Inna basu kula su suka karbe su da hannu 2 har ana ce musu ga wajan Zama budan bakin wata daga cikin su tace;

"Yau naga ikon Allah mu da gidan dan mu wasu bare ke kokarin nuna mana iko" ta karasa harda rike haba irin abin ya bata mamakin nan, Aunty Batul da bata da hakuri kaman gudawa ta yunkura zata basu amsa Inna da take kusa da ita tayi saurin rike hannun ta Maa da suke zaune opposite da ita ta girgiza mata kai alaman kada tayi magana.

Haka ta koma ta zauna tana ta girgiza kafa bala'i na cinta, su Kuma sai da suka gama dariyar su na wulakanci sannan suka nemi waje suka zauna suna zama cikin ikon Allah ko sai ga Maman Yasmeen da wasu mata 3sunyi sallama sun shigo da fara'ar su a take fuskar Momyn Zafar da mutanen ta ya kuntata dan basuyi tsammanin zuwan ta a wannan lokacin ba sun so su gama tsula tsiyar su kamin ta iso ba dan wai suna tsoron ta ba sai dan sun san duk abinda da sukayi zaije kunnen Abba kuma bata manta warning din da yayi mata ba akan bikin ba.

A mutunce suka gaggaisa dasu Maman Yasmeen har suna tambayan ina 'yar su take basu ganta ba , Aunty Fatima ce ta shiga ta fito dani bayan ta nada min laffaya ta kara bulbule ni da humra.

A kunyace Kuma kaina a kasa na gaishe su suka amsa da kulawa banda su Momyn Zafar da suke amsawa kaman anyi musu dole ko masu ciwon baki, ina gama gaishe su ko minti 1 ban kara ba na koma ciki daman gaba daya a takure nake jina a wajan.

Zuwan Baawa duk ya rusawa Momy badget kuma zaman su a inuwa daya babu riba dan haka suka mike da niyyan tafiya Baawan taso tsaida su amma suka ki tsayawa suka Kara wuta, suma ba wani jimawa sukayi ba suka ce zasu tafi aka rabu cikin mutunci.

Karfe 3 su Inna suma sukayi haraman tafiya suka saka ni a gaba da nasihu sosai masu ratsa jiki sannan suka tafi suka bar ni ina ta kuka, su Maryam dasu Yasmeen suna ta bani baki suka taya ni gyara gidan sannan suma suka wuce suka bar ni.
[6/16, 9:20 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*37&38*

A hanyar su ta komawa gida sauran mata suna ta hira da santin gida na amma banda Inna da tayi jigum duk abin duniya ya ishe ta dama shiyasa bata son zuwa Maa ta tilasta mata dole tazo gashi ta ga abinda ya tayar mata da hankalin, alamu ya nuna cewa ni da Zafar babu matsala a zamanta kewar mu amma mahaifiyar shi itace babbar kalubele a cikin rayuwar aure na.

Duk yanda miji ya Kai ga son matar shi in har dangin shi basa kaunar ta toh fa babu zaman lafiya balle ace mahaifiyar shi ce sukutum bata son ta ai babu kwanciyar hankali, ajiyan zuciya ta sauke mai nauyi har Maa da take kusa da ita ta dago suka had'a ido, alama tayi mata da ido cewa kada ta tada hankalin ta sai sunje gida zasu nemi mafita.

Wani ajiyan zuciyan ta sauke tana mai lumshe idanun ta alamun ta fahimta, a bakin kasuwa mafi yawancin matan suka sauka kowacce zata nemi motan da zai Kai ta Anguwan ta sai su Inna, Maa, Maman Dije dasu Inna Asabe sune kad'ai aka karasa dasu kofar gida.

Maa bata shiga gidan mu ba ta wuce gidan ta su kuma suka shigo gida, a tsakar gida suka iske Gwaggo Aisha tana wanke wani abinta cikin bucket, sallama kawai sukayi kowacce ta wuce bangaren ta ba tare da sun tanka mata ba domin habaice-habaice take tana bin su da harara wai kwadayi yasa suka bi Inna, ita kuwa har duniya ta nad'e bata ga abinda zai sa tabi ta ba dan har abada a matar cushe matar biyan bashin take kallon ta.

Wankin ta bari tana cizon yatsa dan ba haka taso ba taso koda Maman Dije ce ta tsaya acikin su ta tanka mata sanin halin ta na bata barin ta kwana sai dai yau harda itan suka ki kulatan.

"Ai duk hanyan da zan bi sai nabi naga bayan ki Bintu baki isa kiyi walwala ba muddin ina numfashi a doron kasa sai nabi na kuntata rayuwar ku keda wancan kod'add'iyar 'yar taki" tana magana ne da dukan karsashi dake zuciyar ta fuskarta kuwa na nuna zata iya aikata koda kisa ne dan cimma burin ta.

Hajara da shigowar ta kenan gidan tana tsaye a bakin gate kuma tana jin duk kalaman da mahaifiyar ta take furtawa akan mu, hawaye take na tausayi mahaifiyar tasu kan rayuwar da ta zabarwa kanta kullum cikin addu'an neman shiriya take mata amma da alamu tayi nisa sai a hankali, hawayen fuskarta ta goge tsab tana ayyanawa dole ne tayi wani abu na dakatar da duka Shirin ta in ba haka ba ta san halin mahaifiyar ta zata iya aikata komai da ta fada koma fima.

Bayan ta tabi zuwa cikin parlour su da ko carpet din arziki babu, da tsaki ta shigo maimakon sallama ta zauna a kasa tana kara jan tsakin da karfi yanda zata ji tayi magana.

" Ke kuma lafiya zaki zo ki saka mutane a gaba kina ta jan tsaki kaman wata tsaka?" Gwaggo Aisaha ta tambaya tana mata wani mugun kallo dan harda ita cikin wayan da take jin haushin su kan ko kad'an bata son taji anyi maganan mu balle a fad'i laifin mu.

"Umma ki taimake ni zuciya ta zata buga, wannan kyakkyawan mijin da gida kaman aljannar duniya dani ya dace ba wannan kod'add'iyar yariyan ba" ta karasa tana kara b'ata fuska kaman zata fashe da kuka.

A mamakince Gwaggo ta juyo tana kallon ta fuskarta d'auke da alamun tambaya tace " wai maganan wa kike min kuma wwni gida?"

Sai da Hajara ta tab'e baki kaman abinda zata fad'a har cikin ran ta ne tace " hmmm maganan wannan kod'add'iyar yariyan mana 'yar gidan Bintu".

Cikin wani irin sauri tazo gaban Hajaran ta zauna tare da kamo hannayen ta duka 2 ta rike cikin nata fuskarta cike da tsansan farinciki tace " Hajara da gaske kike ?"

"Gyad'a kai tayi ta kwakulu hawaye tace" Umma kin gan shi kuwa kaman wani balarabe ga gidan ma yanda kika San a kasar waje kike, ni dai gaskiya ki taimaka in kwace su duka a hannun ta" ta karasa tana goge hawayen ta

"Alhamdulillahi!!! Allah nagode maka wannan mugun asiri da matar cushen tayi miki ya karye Hajara ta ta dawo gare ni" tace tana rungume ta harda kwallan farinciki a idon Gwaggo.

"Asiri gaskiya ce ni shaida ce tunda gashi nagani akan 'yata mafi soyuwa a gare ni amma kiri-kiri aka raba mu ba kya son a ambaci sunan su koda da wasa da mutum ya tab'a su gwara mutum ya shararawa uwar ki mari goma" Gwwggo ke fadin haka cikin kuka dan da gaske take farinciki dawowar tan domin tun ada baya itace abokiyar shawarar ta daga baya Kuma da ta gane gaskiya sai taja baya da ita.

Ta dad'e tana da burin yin wasu abubuwa da dama akai na da Inna ta amma ta rasa dawa zasu had'a Kai suyi domin Jameela kullum bata gida koda ta dawon ma a buge take shigowa.

"Kinga yanzu 'yar uwar ki halin da ta zabarwa kanta kenan bana ma samun ganin ta sai bayan satika ko kwanaki koda na ganta ma ba a cikin hayyacin ta take shigo min ba sai cikin maye dama kece kad'ai kika rage min ta raba mu da mugun asirin ta sai dai ta Allah ba tata ba gashi komai ya karye Alhamdulillahi" ta karasa cikin tsantasan farinciki da ta dad'e bata ganta a ciki ba.

Mayar hawayen idon ta tayi na tausayin mahaifiyar tasu sannan ta maye gurbin da murmushi tace " toh yanzu meye abin yi Umma?"

"Tun kwanaki Lantana ta min alkawarin kaini wajan wani boka da aikin shi yake kaman kaifin wuka, dama rashin ki a kusa dani yasa na bar maganan amma tunda komai ya warware zanyi mata magana mu tafi cikin kwanakin nan komai da suka mallaka sai ya dawo gare mu ".

***************

Shiru gidan kake ji kaman ba shine dazu take cike da mutane ba, duk sai naji babu dad'i Ina nan zaune a inda suka bar ni na kurawa tv da yake ta karaji shi kad'ai ido kaman kallon nake amma kuma hankali na ba anan yake ba ya tafi ga tunanin haka rayuwa ta zata kasance zama da wanda bai san daraja ta ba wanda yasha fada min da bakin sa ba sona yake ba, tunda aka kawo ni gidan nan ban abu wai shi farinciki ba ina dai zaune ne kawai in mun hadu banda mugunta ba abinda yake shiga tsakani na dashi.

A da nima haushi yake bani kuma in yayi min muguntan bana samun kwanciyar hankali har sai na rama amma a kwanakin nan ban san me yasa ba ko me yayi burge ni yake maimakon inji haushin sa, in yana zaune a parlor ko yana cin abinci nakan buya inyi ta kallon shi tunda ya min iyaka da inda yake yace kada in kuskura in zauna inda yake, so must time ko ina parlour in ya shigo zan tattara in koma nawa inyi ta leken shi wani lokacin nakan ji haushin kaina tare da tambayan toh me hakan yake nufi amma babu mai bani amsa.

Wani abin takaici ko cikin dare na tashi wani lokacin na kan leka d'akin shi,ina iya hango shi yana baccin shi cikin kwanciyar hankali, cikin d'an hasken dim light dake bari na gefen gadon shi ba na sanin ko minti nawa nake a wajan all I is ina dadewa sannan in koma in kwanta

Sallamar shi cikin azzakar muryan shi naji ya daki kunne na duk da ciki-ciki yayi ta dan na san baiyi tsammanin da mutum ba a parlorn ba, kasa amsawa nayi saima bin shi nayi da kallo har ya shige , yayi min matukar kyau cikin wani lallausan yadi maroon da ya saka anyi mata dinkin zamani irin iya cinyan nan kan shi babu hula sai bakin gashin kan sa dake sheki yana d'aukan ido.

Kara fitowa yayi sai dai wannan karon ya cire rigan sai farin vest ne a jikin shi murdadden jikin sa a wake, hannun shi d'auke da laptop yana duba wani abu gaba daya hankalin sa yana kai, ni kuma ina nan tsaye yanda ya barni na kasa motsawa a wajan duk da naga inda nake yake nufowa amma na kasa matsawa ina kallon yanda shima vest din ta zauna a jikin shi, wato shi komai ya saka sai tayi mishi kyau.......

Ina cikin zancen zuci naji mutum ya fad'o min mukayi baya tare kan kujera dake bayana ya kasance yayi min rumfa da faffadan kirjin shi, wani irin yanayi da ban tab'a tsintan kaina a ciki ba yau naji ni a ciki ganl kamshin jikin shi da kuma d'umin jikin sa da suka had'u suka bada wani yanayi na musamman, lumshe ido na nayi Ina addu'an Allah yasa mu dauwama cikin wannan yanayin Mai wuyar fassara.

Cikin wani irin zafin nama ya d'aga ni tare da hamb'are ni gefe na fad'i kasa dole na waro idanu na dana lumshe na sauke su a kan shi, kaman wanda ya tab'a Kashi haka yake ta kakkab'e jikin sa yana watso min mugun kallo kaman idanun shi zasu zubo kasa.

"Wannan kuma wani sabon iskanci kika fito dashi kizo ki tare min hanya kawai dan wannan kazamin jikin naki ya rab'i nawa, how dare you tayaya ma zakiyi irin wannan tunanin ko ban fad'a miki matsayin ki ba kamin ma ki shigo" ya karsa yana zaro min ido waje cikin sauri nayi kasa da nawa domin na razana.

"Wallahi kika kara bin hanyan da nake bi sai nayi mugun tsab'a miki da alamu ina raga miki dayawa shiyasa har kika samu daman baza kolin ki yanda kike so" still ni dai bance mishi komai ba sai kallon shi da nake ta kasan ido cos duk yanda naso hana kaina kallon shi na gagara.

D'aukan laptop dinsa yayi ya dudduba yaga tana nan lafiyan ta qalau babu abinda ya same ta, Kara saka kafa yayi ya hamb'are ni yana " get out of my sight da idon ki kaman na mayu a wajan ana magana kin zuba min su kaman zaki cinye ni".

Tashi nayi ba tare da nace mishi kala ba na wuce kitchen na hado mishi drinks da abinci na kawo na ajiye mishi na wuce daki ina jiwo muryan shi yana in dawo in kwashe jagwalgwalo na ko waiwayowa banyi ba balle yasa ran zan dawo in kwashe.

A bakin gado na zauna a hankali Ina mai lumshe ido tare sakin kayataccen murmushi ni kad'ai yanayin da muka kasance yanzu Yana min gizo a ido, kwanciya nayi rigingine ina kallon pop saman d'akin with a blushing face sai juyi nake akan gadon.

Zaune na tashi ina yamutsa fuska ni kad'ai tare da tambayan kai na what's wrong with me? Na rasa mai bani amsa nayi nayi ko zan samu haske amma ban samu ba, tagumi na zuba kawai na zauna shiru can naji zuciya ta na azalzala ta kan in leka inga ko yana cin abincin?

Cikin sand'a na iso bakin kofan na leka ta bulin makulli, laptop din naga ya ture gefe yana ta kwasan gara harda lumshe ido alamun abincin yana mishi dad'i, rufe baki nayi da tafin hannuna kada dariyan da nake rikewa ya fito fili ya ji ni.

Ina kallon shi ya cinye abincin tas ya kora da juice sannan ya tattara kayan ka Kai su kitchen yazo ya zauna ya cigaba da aikin da yake yi a laptop din, ni ko sai da naga ya gyara komai ya zauna sannan na fito nayi hanyan kitchen ba tare da na kalli inda yake ba .

Da ido ya bini har na shige yana tunanin me zai fad'a wanda zai kare kan shi kan cewa ba shine yaci abincin ba, har na fito bai samu wata gamshasshiyar magana da zai gaya min in gamsu ba.

Tafiya nake a hankali ina kallon shi da alaman tambaya akan fuskata na waye ya cinye abincin?

Cikin kame-kame ya fara magaa " hey look don't think negative dan ko yunwa zata kashe ni banga abinda zai saka inci wancan jagwalgwalon ba I just gave it to the driver suka cinye ya dawo da...." Kasa karasawa yayi ya tsaya kallon yanda nake ta gyad'a mishi kai tare da murmushin rainin hankali.

"Meye kika wani zuba min ido kina dariya kaman wanda ke miki karya?". Saurin girgiza kai na nayi Ina danne dariya da yake son kufce min.

A fusace ya tashi yayi kaina yana " dariya kike min ni zaki maida mahaukaci?"

Aiko Ina ganin ya mike na kwasa a guce ina sakin dariyan da na danne na shige bangare na gudu ban tsaya a parlour ba na wuce daki na fad'a kan gado Ina dariya sosai .

Shima daya biyo ni da gudu bai san lokacin da ya saki murmushi har hakoran sa suka fito ba ya girgiza kai yana " lallai yarinya nan ta fara raina ni".

Nagode da addu'oin ku Allah ya bar zumunci nd Alhmdlh jiki na yayi sauki sosai .
[6/16, 9:21 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

Assalamu alaikum yan uwa da fatan munyi sallah lafiya, Allah ya karb'i ibadun mu ya nuna mana na gaba Ameeen.

*39&40*

"kada abinda kika gani ya tayar miki da hankali domin matan masu kud'in nan haka suke sun fi son 'ya'yan su su auri 'ya'yan masu kud'i kamar su, bakomai yasa kika ga tana mana wannan kallon ba sai dan sanin mu talakwa ne.

Idan muka cigaba da yi musu addu'a sannan kuma ita Zareefa zata iya samo soyayya surukan ta wajan dagewa da kyautata musu tare da yi musu zallar biyayya" Maa ce take fad'awa Inna cikin kwantar mata da hankali.

"Hmmmm hakane Maa har hankali na ya kwanta da tunda na dawo na kasa sukuni domin na san yanda wannan matsalar take" Inna ta amsawa mahafiyar ta cikin sanyin murya..

" Ki kara kwantar da hankalin ki saboda mun yarda da tarbiyan da muka bata ba zata tab'a yin abinda zai b'ata sunan ta ko na gidan ku ba" Maa ta kara tabbatar mata nan dai ta daura da shawarwari da hira masu sanyaya zuciya sai ga Inna da tazo mata wani cikin damuwa da sanyi jiki ta ware suna ta hira harda kyalkyalan dariya.

Bayan kwana 2 Gwwggo Aisha ta had'a duk wasu 'yan kud'ad'e da suke hannun ta tare da sayar da wasu kayayyakin ta saboda ta samu isassun kud'in zuwa wajan boka, dama haka take duk tabi ta sayar da abinda take dasu dan ko dakin Inna Asabe yafi nata kyan gani domin ita ta fawwalawa Allah lamarin ta ta rungumi sana'an ta kuma alhmdlh tana samu daidai gwargwado domin tana sayan kayan daki da kadan kadan tana gyara dakin ta.

Sun je wajan bokan ita
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment