Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

dole zai tsoratani.

"Ke tsaban kin raina mutane shine har zaki shigo ki fita ba zaki gaida mutane ba?" Ya fad'a cikin tsawa.


Sai da na turo baki na dan kalle shi na watsar nace" ni dai banga mutane ba,mutum daya na gani a parlorn".

Mamakin da yake fuskar shi kasa boyuwa yayi yana bina da wani irin kallo, had'iye abin shi yayi ya Kara wani tsare gida yace" ohk in ma mutum dayan kika gani ba zaki gaida shi ba kenan, nd what do you mean by ki shiga daki ki zauna shan tea sauran mutanen gidan ba zakiyi musu girki bane?"


Sai da na kuma kurban tea na hankali kwance sannan na bashi amsa " I don't feel like cooking today"

"What!! Ni kike fad'awa u don't feel like cooking, kin ga ina bin ki a hankali shiyasa ko jira ni ina zuwa zaki min bayanin yanda ya dace" yana fad'an haka ya fuce fuuu kaman zai tashi sama, tab'e baki nayi na raka shi da ido wai ni zai rainawa hankali wai mutanen gidan me zasu ci, yace min dai me zai ci?.


No Abba da tun jiya nayi saving a wayata na kira na saka a handsfree na ajiye kusa da ni muna gaisawa Ina karasa shan shayi na daya rage ya shigo dakin a zafaffe da belt a hannun shi har zai bud'i baki yayi magana jin muryan Abban shi yasa yayi tsit yana zare ido, kallon up nd down na mishi ina murmushi Abba yace" da fatan kin tashi lafiya my daughter"


Kara kwantar da murya nayi sannan na amsa mishi da" yau na tashi da jiri da amai da zazzab'i Abba ko tashi bana iya yi shine na nemi alfarman ba zan iya shiga kitchen ba yau amma yake ta min fad'a"


"Mene! Yana ina, ki bashi wayar in yana kusa" Abba ya karasa a d'an zafaffe.

Ina kif-kifta ido kaman da gaske nace " gashi nan Abba" tare da mika mishi wayan, sai a lokacin ya dawo hayyacin sa ya saka hannu ya karb'a yana min mugun kallo, ni kuwa ko a jikina saima murmushin mugunta dana bi shi da ita.

"Assalamu alaikum Abba barka da safiya" yace cikin sanyin murya.

" Wa'alaikum salam son me nake ji haka kada ka kasance cikin mazan da basa kyautatawa iyalin su mana kayi koyi da manzan Allah dan ya kasance mai kyautatawa iyalan sa,ko kaga haka muke da Momyn ka?" Bai iya bude ya bashi amsa sai girgiza kai da yayi kaman yana gaban Abban.

"Kada in kuma jin irin haka try to be a good husband ok, nd get something for her tayi breakfast". Insha Allah Abba" ya amsa cikin sanyin murya sannan ya katse kiran.

Ina jira inga ko zai hau kaina da wannan masifan nashi amma ga mamamki na sai ajiye min wayan yayi ba tare da yace komai ba ya fita daga dakin, murmushin nasara nayi tare da gyra kwanciya ta kan kujera na d'auko wayata na shiga watsApp.


Bayan fitan shi kaman da minti 30 sai gashi ya kara shigowa da sallama da wasu shopping bags a hannun shi ya ajiye min harda na pharmacy a ciki da alamu magani ya sayo.

"Ga breakfast dinki da drugs ki sha bayan kin gama nd pls next time in baki da lafiya let me know" yana gama magana ya fita, ni abin ma sai naji shi wani bambarakwai wai yau Zafar ne yake min magana a nitse babu tsawa harda wani pls? Hmmm tab na yarda da maganan Yasmin da tace yana bala'in tsoron Abban shi daga waya sau 1 har ya sauya.

But sai nake jin kaman ban kyauta ba da na had'a shi da mahaifin shi har yayi mishi fad'a, wani bangare na zuciya ta na kara ingizani cewa sai me ai shima lokacin da yake takura ni bai tausaya min ba.

Bud'e ledan eatary nayi naga manyan package na take away guda 2 na farko cike da chips da kwai sai na biyun kuma cike yake da pepped chicken sai kamshi suke ba b'ata lokaci na d'iba na fara ci ina zuba santi,sai da nayi nak sannan na tattara sauran na kai kitchen ban gan shi a parlorn ba ban kuma bi ta kan shi ba nazo na cigaba da charting na.


******************

Washe garin ranan da suka dawo daga wajan boka Gwaggo Aisha tasa Hajara wanka da sassafe ta shirya wai ta taho gida na su fara aiwatar da kudurin su tunda wuri, bata musa mata ba ta shirya tsab tayi kwalliyar ta cikin doguwar rigar ta na atampa daya amshe ta sosai,tana bari tayi breakfast kamin ta fita amma ta hana ta tace in azo nan gidana taci.

Haka ta fito wajan 8 da wani abu ba tayi nisa da gidan namu ba ta samu kwata ta jefa maganin a ciki tayi wucewar ta, bata son zuwa gidan da sassafe haka ta san duk yanda akayi kila ko farkawa daga bacci bamuyi ba, tunda ta shigo anguwan da nake ta fara jan kafa dan bata san kowa a anguwan ba da ta shiga ta dan ja lokaci har sai Zafar din ya fita kamin ta shigo.


Dole haka ta karaso kofar gidan tayi knocking mai gadi yazo ya bud'e mata kofan ta shigo daga ciki sannan ta gaishe shi cikin girmamawa da yake ya dan manyan ta, amsa mata yayi cikin kulawa kasancewar yaji dad'in yanda ta gaida shin.

"Dan Allah Baba masu gidan sun tashi kuwa?" Ta tambaya shi lokacin yana shirin komawa dakin shi.

"Gaskiya bana jin sun tashi dan sai kusan goma sannan muke kin motsin farkawan su" ya amsa mata.

" Toh dan Allah zan zauna a nan kamin su farka" tace tana nuna mishi wasu kujerun roba da suke can gefe cikin furanni.

"Toh toh shikenan ki zauna sai sun fito" yace yana shigewa dakin shi, karasawa tayi ga kujerun ta zauna tana ajiyar zuciya samun relief ta ciro wayar ta daga cikin jaka ta fara game dan ya rage mata zaman kad'aici, ya ko taimaka matan dan bata san lokacin da taja a wajan zaune ba hankalin ta duk yana kan wayan taji saukan ruwa kaman daga sama a jiki ta, a firgice ta mike tana " innalillahi wa Inna ilaihi raji'un" a masifance ta juyo da niyyan ciwa wanda yayi mata wannan danyen aikin mutunci sai dai tana jiyowa idanun su suka sarke dana juna shima ya taho da niyyan bata hakuri saboda sam bai kula cewa da mutum a zaune a wajan ba domin kullum yazo haka zaiyi aikin shi ya koma ba tare da yaga wani na gidan ba gwara shi Zafar din sukan had'u wasu lokutan.


Da kyar ya samu bakin bata hakuri cikin sanyin muryan shi da ya zame masa jiki, sai a lokacin Hajaran ta dawo hayyacin ta ta janye idon ta akan shi a kunyace tare da ce mishi babu komai.


Ajiye tiwon hannun shi da yake bawa flowers ruwa dashi yayi cikin sauri ya koma can inda ya ajiye kayan shi wajan Baba mai gadi ya d'auko wani babban handkie ya dawo duk tana tsaye tana bin shi da ido yazo ya goge mata ruwan da ya jika kujera da take kai sannan ya dube ta wannan karon fuskar shi d'auke da murmushi yace " ki zauna Hajiya kiyi hakuri wallahi ban lura da mutum a wajan bane d z an kullum Ina zuwa aiki ban tab'a cin karo da wani a nan zaune ba shiyasa".


Zama tayi a hankali itama fuskar ta d'auke da murmushin tace " kada ka damu na san ba da gangan kayi ba, nima na zauna a nan ne kamin masu gidan su farka daga bacci, ba matsala ka cigaba da aikin ka nagode".

" Toh Hajiya nima nagode" yace yana komawa kan aikin shi sai dai tunda ya fara hankalin shi gaba daya yana kan ta haka itama ta kasa natsuwa hankalin ta kacokan yana kan shi sai kallon shi take ta kasan ido dan ba laifi shima kyakkyawa ne gashi da hasken sa dan yafi ta haske sosai.


Suna had'a ido sai su sakarwa juna murmushi a haka har ya kammala aikin shi ya dawo wajan ta yana ko ya taya ta zama ne tunda har yanzu da sauran lokaci, bata musa ba ta bashi dama ya zauna sai gashi suna hira kaman sun dad'e da sanin juna kamin Zafar ya fita har sunyi exchange na phone number tsakanin su.


Zafar ya fito zuwa gaishe da iyayen shi kaman yanda ya saba ya shiga mota ya wuce su sun ga fitowan shi Amma shi sam hankalin shi bai Kai kan su ba yaja motan shi ya fita bayan mai gadi ya bud'e mishi gate.


Koda Zafar ya fita sai da suka kara kusan minti 20 tare kamin su rabu ta samu daman shigowa cikin gidan a lokacin ni kuma na gama breakfast nazo nayi kwanciya ta naji salkamar ta, cikin ihun murna na fito na rungume ta zan iya cewa bayan yinin bakwai da akayi sai yau wani nawa yazo min dan haka cike da farincikin na tarbe ta ina tambayan ta Inna ta da mutanen gida tace min duk suna lafiya.


Bayan gama gaishe-gaishe na gabatar mata da sauran abincin da na rage ta fara ci muna hira cikin tsananin farincikin da kewar juna.


Shi kuwa Zafar tunda ya tafi gidan su hankalin shi na kaina dan ya kasa sakin jiki suyi hira kaman yanda suka saba, bini-bini sai kallon agogo yake har Abban shi ya gano shi yace" ya kamata ka tashi ka koma gida son dan my daughter tana bukatan kulawar ka musamman a halin da take ciki yanzu".


"Wani hali take ciki kuma?" Mom da tundazu taki saka baki a hiran nasu ta tambaya a d'an rikice.


"Ke kuwa ai zaki fimu sanin halin da take ciki tunda ke macece, yau ta tashi bata da lafiya wai tana fama da jiri da ciwon kai kinga alamun ciki sun bayyana a tare da ita amma fa a nawa hasasshen kenan ko kunje asibiti?" Abba ya amsa mata da wadatattacen murmushi saman fuskar shi yana kallon Zafar daya duke kai shima yana murmushin tare da girgizawa Abba kan shi.

"Ja'iri ji wani murmushi dan Allah Hajiya yaran yanzu da shegen son 'ya'ya suke" ya karasa yana dungure mishi Kai.

Mom da tayi suman zaune ko jin abinda yake fad'a ba tayi ba har yayi musu sallama ya fita ya bar ta baki bud'e.

Anan Kuma nida 'yar uwata sai hira muke zubawa yanda tun daga kofar shigowa zaka ji hayaniyar mu ba dan komai ba sai na labarin sabon saurayi da tayi na gidan mu take tana yayi mata amma tana gudun kada yaji ta tab'a aure da haihuwa ya guje ta...


Ni kuwa ina kara karfafa mata giwan cewa babu wanda zai kalle ta yace ta tab'a aure balle har ace ta haihu, muna cikin haka Zafar ya dawo gidan jiki a sanyaye amma tunda ya fara jiyo murya ta cike da nishadi muna hira yasa ya shigo da karfin shi, sallama yayi ya tsaya daga bakin kofa fuskar shi d'auke da tsantsan farincikin samu na a haka da yayi, bude min hannuwa yayi alamun inzo gare shi har zan watsa masa harara na tuna cewa ashe fa in a gaban mutane ne drama muke yi hakan yasa banyi musu ba na taso cikin wani yauki da ban san na iya shi ba na nufe shi tare da kashe da wani sexy smile.


Kafe ni yayi da ido ko kiftawa ba yayi yi har na iso gaban shi kaman zan shiga jikin shi sai na zille ina dariya nace" ga Yaya ta nan ku gaisa"

Shafa suman kan shi yayi da hannnu daya dayan hannun kuma yasa ya rike min hannu sannan ya kai duban shi ga Hajara da duk kunyan abinda ke faruwa ya rufe ta yace " babbar Yaya barka da zuwa" har da d'an risinawa kaman da gaske, cikin jin nauyi Hajara ta amsa suka gaisa duk yana rike da hannu na.

"Zo muje ki had'a min ruwan wanka wifey" yace yana kokarin jan hannu na zuwa parlor, tirjewa na fara kokarin yi tare da nuna mishi nayi bakuwa zan zauna wajan ta ya tafi kawai banyi aune ba naji ya d'aga ni cak in a bridal style yayi waje dani.

" Naji dadi sosai da nazo na same ki cikin koshin lafiya" yace yana bin ko ina na jiki na da kallo ,muna karasa fitowa parlorn na watsa mishi harara tare da kokarin sauka a jikin shi nace " Mallam kana over acting fa sauke ni dan Allah sai kace da wanda yake ganin mu a nan".

Cikin wani yanayi na sanyin jiki ya sauke ni kamin yace min wani abu na bar shi nan tsaye na shige kitchen nemawa Yaya ta abinda zata ci da rana , jiki a mace ya koma ya zauna tare da dafa kan shi tsakanin jiya da yau din nan bai san me yake damun shi he feels a different person.
[6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*




✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.


*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.



Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.



*Bismillahir Rahmanir Raheem*



*43&44*



A wannan rana a nan parlourn ya yini kaman an dasa shi yana zaune sai kurb'an ruwa yake duk inda zan wuce kuwa sai yayi ta bina da ido kaman ya samu tv, ni dai ko kallo bai ishe ni ba dan yau wani tashen rashin mutunci nake ji dashi.


Sallah azahar kad'ai naga ya fita yayi a masallaci ya dawo a lokacin ni Kuma fitowa ta kenan daga kitchen hannu na d'auke da wani tray mai d'an girma da na d'aura kayan dad'i dana girkawa 'yar uwata, wuce shi nayi zuwa parlona inda na bar Hajara zaune tana kallo,nan tsakiyar parlour na ajiye na fita na had'o drinks masu sanyi a fridge na kara wucewa ta.

Ya d'an jima zaune wai ko zan dawo in kawo mishi rabon shi yaji shiru, murmushi yayi kawai tare da kad'a kai ya d'auki makullin mota ya fita ba jimawa sai gashi nan ya dawo da kaya niki-niki a hannu leda d'aya tak ya ajiye a parlorn ya wuce da sauran parlona ya same mu mun fara cin abincin muna hiran mu, ajiye kayan hannun sa yayi ya d'an kalle ni yace " pls ga kada ki manta da drugs d'in ki in kin gama cin abincin ki sha sannan ga fruits suma ki sha zaki ji dad'in bakin ki" gyad'a mishi kai kawai nayi ya juya ya fita yana waiwaye na.


"Zareefa gaskiya kinyi dacen miji nagari a wannan zamani da maza ba abinda suka iya sai wulakanta matan auren su, amma ki ga yanda yake tarairayen ki" cewar Hajara kenan, murmushi kawai nayi mata ba tere da na bata amsa ba na fara bud'e ledan fruits d'in a raina ina baki san waye shi bane har kike yabon sa.

A can main parlour kuwa Zafar zaune ya saka fried rice nd chicken daya sayo dan yaci amma ya kasa kwata-kwata bai fi spoon 3 yayi ba yaji abincin ya fita ran shi, tsaki yaja yana hararan inda muke bai san ya akayi haka ta faru ba daya saba da cin abinci na har baya iya cin wani abincin wani.

Kara kallon abincin yayi gashi dai so color full ya sha veggies amma sam bai ji wani taste ba a bakin shi,tattre su yayi ya ajiye a gefe ya sha fruits d'in daga baya duk ya kwashe su ya mikawa Baba mai gadi.


Har kusan la'asar muna tare da Hajara sannan tace zata koma amma zatayi kwana 2 a jere tana zuwa saboda akwai wani waje da Gwaggo Aisha take Aiken ta ita kuma bata son zuwa shiyasa zata rinka zuwa nan as ta tafi inda ta aike ta, ni kuwa cikin murna da jin dad'in zan samu mai taya ni hira har na kwana 2 na amsa mata da ina jiranta tazo da wuri.


Duk sauran kayan ciye-ciye da Zafar ya kawo ita na tarawa nace ta kaiwa su Ibrahim, ta amsa tana ta godiya na rako ta har bakin kofan main parlorn ta tafi.


Tana zuwa gida ta tarar da Gwaggo Aisha a tsakar gida tana jiran ta, ganin ta da manyan ledoji yasa ta fara washe baki domin taga alamun nasara a aikin bokan ta.

"Ya kika dad'e haka Hajara, kin gan ni nan tun d'azu nake zaman jiran ki" ta fad'a cikin d'aga murya yanda sauran 'yan gidan zasu ji.

Cikin kara fad'ad'a farar ta ta karaso gaban ta tare da ajiye kayan hannun ta murya kasa-kasa tace" gashi nan yace in kawo gida yana gaishe ki".

Wani irin shewa Gwaggo Aisha ta saka tana dariya tace" wannan duka yace ki kawo min lalle sirkin nawa ba wasa" murmushi kawai Hajara tayi ta shige ciki ta bar ta a nan sai bud'e su take d'aya bayan d'aya tana kara bud'a murya tana yabon kayan tare da yad'a habaici.

Dare nayi suna zaune suna hira da Gwaggo Aishan wayan ta ya fara ringing ganin number sabon saurayin ta ne yasa ta d'aga tana murmushi bayan sun gaisa yake ce mata bata ma tambayi sunan shi ba, nan itama tace ai ba sai ta tambaya ba shi ya kamata ya fad'a mata nan yace mata sunan shi Amadu.


Tashi tayi zuwa bedroom d'in su ganin Gwaggo Aisha ta ishe ta da waye ya kira ko Zafar ne? Da kai kawai ta amsa mata ta karasa shigewa daki ta barta tana ta murna.

*****************************

Da daddarem ma kin girkin girka komai nayi na kwanta Ina kallon wani series da nake matukar so a zee world ya shigo min da sallama na amsa mishi ciki-ciki kaman yanda shima ya min, tsaye yayi kaman me son cewa wani abu ko me neman wani abu ni dai bance mishi kala ba na mayar da hankali na kan tv.


"Ya jikin naki?" Naji muryan sa kaman daga sama.

" Na warke" na bashi amsa ba tare da na kalli inda yake ba.

Bai kara cewa komai ba ya fita nabi bayan shi da harara, a raina ina wa zai kara kula ka kaci zalin shi ko ka mishi mugunta da ka saba.

Shirin bacci na nayi bayan na gama kallon, na sha bacci cikin kwanciyar hankali sab'anin Zafar daya kwana cikin wani yanayi da shi kan shi ba zai ce ga inda ya dosa ba shi dai kawai so yake ya zauna kusa da ni ko kuma inda zai samu yayi ta kallo na, tun yana d'aukan abin da sauki har ya fara jin haushin kanshi wai me yasa ya damu da wani lamura nane? in ya kalle ni uban me zan bashi illa ma in b'ata mishi rai da sabon rashin kunya da na samo, bayan wannan ma tun lokacin da ya d'auke ni ya fito dani parlor jiki na da nashi da ya had'u yake kewar d'umin jiki na tare da kamshin jikina mai sanyi da tsayawa a rai sai dai dole ya matse gudun kada raini ya shiga tsakanin mu.

Ya san bakomai yasa ya damu da lamurana ba maybe tausayi na da ya fara jine kawai dan yaji bani da lafiya, " hakane ma" ya furta a sarari yana mai kara bawa kanshi karfin guiwa da kyar dai ya samu bacci yayi nasaran sace shi a wannan daren.


Da washe gari na tashi da sauki dan wannan nauyin da zuciya ta yayi jiya yayi sauki hakan ne ya bani daman fara aiyuka na kaman yanda na saba, bayan na gama share ko ina tass na gyara sannan na shiga wanka ban dad'e ba na fito light make-up nayiwa fuskata na shirya kaina cikin English wears riga da skirt pink color anyi mishi ado da flowers blue hakan yasa na yane kai na da blue vail, kayan bai wani matse ni ba amma ya zauna das a jikina ya min kyau sosai.


Zagewa nayi ina girki sanin cewa Hajara zata iya zuwa at any moment,kayan dad'i nake dafawa dan haka gidan ya cika da kamshi masu dad'in shaka,kamshin nan shi ya fito da Zafar daga d'akin shi sai bud'e hanci yake yana lumshe ido tsohon yunwar shi ta jiya na dawowa sabo fil.


Kofar kitchen d'in yazo ya tsaya yana kallon yanda nake aiki gaba daya hankalina yana kan aiki ban san ma da zuwan shi ba,shi kuma controlling d'in kan shi yake akan abinda zuciyar shi take ingiza shi ya aikata dan ji yake kaman yaje ya rungume ni yaji wannan d'umin jikin nawa da wannan daddadan kamshin mai sanyaya zuciya amma ya daure yayi gyaran murya Wanda ya d'an firgitani na juyo a d'an razane na ganshi tsaye cikin kayan baccin sa farare kal da alamu tashin sa kenan ko wanka baiyi ba.


Kaman ana min dole nace mishi" Ina kwana" saboda ganin babu wasa a fuskar shi, maimakon ya amsa min sai cewa yayi " ki tabbata kinyi da rabon masu aiki tunda kin samu lafiya" sai da na turo baki sannan na bashi amsa da cewa " ni bada su nayi ba dan Hajara zata zone shiyasa nayi girkin".


Kara had'a fuska yayi yace" try anything stupid and see"Yana gama fada ya juya ya fita ba tare da ya jira amsa ta ba, " zaka gani kuwa ai ka daina cin abinci na a gidan nan tunda kai d'an wulakanci ne"nace ina cigaba da aiki na.


Bayan kaman 30 minutes na kammala komai na jera su kan try na fito na wuce parlour na ba tare da nabi ta kan shi da na gan shi zaune a main parlour ba, shirya su nayi anan tsakiyar parlour na tare da kara saka turaren wuta na dawo inda na shirya kayan abincin kenan sai gashi nan ya shigo da fuska kaman an aiko mishi da sakon mutuwa.


"Ina na masu aikin da na gaya miki?"
"Banyi dasu ba na amsa mishi ina kara gyara zamana a gaban warmers d'in, bai saurare ni ba direct kai tsaye ya karasa shigowa da niyyan zai d'auke warmer d'aya, cikin azama na kai hannaye na duka biyu na rungume su a kirjina tare da turo baki ina " ni wallahi ka bar min kayana".

Bai saurare ni ba yana zuwa yasa hannu ya d'agani cid'ak kaman wata karamar yarinya zai ajiye ni a gefe na rike shi gam ina "wallahi ba zaka d'auka min ba
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment