Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

inyi biyayya in aure shi tunda ya biyo ta hannun Baba, baya ga haka in nace bana son shi waye nake dashi a yanzu, wanda na taso da son shi tun ban san kaina ba ya guje ni ya watsa min kasa a ido I don't have choice rather than accept this man domin na gama soyayya a rayuwata zuciya ta ta rufe kofa tayi ban kwana da soyayya harb abada.

Sanyi sosai Inna taji a ranta na ganin kalamanta sunyi tasiri a kaina har na daina kukan sai ajiyan zuciya da nake akai-akai, matsowa nayi jikin ta sosai tare da d'aura kaina a kan cinyar ta na saka hannaye na duka biyu na rungumo kwankwason ta, itama tasa hannu ta dama tana shafa min gashin kaina na fara magana a hankali kaman mai rad'a.

" Inna ku iyaye nane biyayya a gare ku ya zama wajibi a gare ni, kukan da kika ga inayi ba dan auren da Baba yace zai min bane kawai na tuna da Yaya nane" na karasa wasu sabbin hawayen na zubo min na tausayin kai na, na fad'i haka ne dan in kwantarwa Inna hankali ba wai da gaske ba.

Cikin jin dad'in kalamai na Inna ta kara rungumo ni jikin ta tana shafa kaina tare saka min albarka da addu'oin gamawa da duniya lafiya.

******************

A kwana a tashi babu wuya a wajan Rabbi Izzati, mun cinye wata d'aya cikin watanni 2 da aka saka na bikina kuma gini da Baban mu yake yayi nisa sa dan har an gamawa Inna bangaren ta,2 bedroom da babban parlour sai kitchen da store sosai ginin yayi kyau, yanzu bangaren Inna Asabe da Gwaggo Aisha ake yi.

Maryam ta dage sai rawan kai take akan bikin ni bata san haushi ma take bani ba, duk wasu frnds d'in mu na makaranta ta sanar dasu sai shirye-shiryen su suke ni dai na kawao na mujiya na zuba musu.

A bangaren Zafar ma hakan take dan shi cewa yayi babu wani biki da zaayi sai ranan da zai auri love of his life sannan zasu sha bukukuwa ba biki bama.

Sadiq ne yace bai isa ba dole ne su sha biki in ya tashi yin wancan yayi abinda ya ga dama, yaso yayi jayayya amma ganin yanda Abba da Mom suka dage suna shirye-shiryen auren yasa yaja bakin shi yayyi shiru tare da zuba musu ido ya san in har zai cigaba da nuna halin ko in kula asirin shi zai iya tonuwa.

Akwai wata mata daga sudan take ta kware wajan gyaran amare Inna ta nemo kuma wai dole sai kaje gidan ta da farko ta ganki sannan zata duba gyaran daya dace da fatar ki,sun gama magana da Inna saura wai ta tura ni ta ganni, ba dan naso ba Inna tasa na kira Maryam a waya kan tazo ta rakani.

Da washe gari kuwa tazo muka tafi gidan nata da yake can Shokari, koda muka je gidan ta cike yake da matan aure harda sabin amare ana tayi musu aiki dan harda 'yan mata masu taya ta tana biyan su.

Tarba na musamman akay mana a babban parlour ta inda take sauke bakin ta na musamman,bamu dad'e da zama ba tazo wajan mu bayan mun gaishe ta cikin girmamawa itama ta amsa mana cikin kulawa sannan ta fara aikin ta wato rubuta duk kayakin da zasu dace da fatana da kuma gashi na sannan ta sallame kan cewa sai next week zan fara zuwa, godiya mukayi mata muka fito zuwa gida.

A gajiye tibis muka dawo kasancewar Anguwan nata da nisa sosai da namu, mun shigo layin mu kenan wata had'add'iyar mota baka wuluk tazo zata fita mu Kuma muna shiga kaman ance min dago kanki ina d'agawa na tsaya cak tare da dafe kirji na da hannu biyu ina zaro ido waje duk at da same time bakina na rawa nace " YAYA NAAA..."
[1/26, 7:14 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*25&26*

Yanda ka san statue haka na tsaya ko motsi na kasa yi sai motan nabi da kallo da idanuwana kaman zasu zazzago kasa ga kuma zuciya ta na ta lugude kaman zai faso kirji na ya fito.

" What's wrong with you Zareefa daga ganin mota sai kice ga Yayan ki, ke duk wulakanci da mutumin nan yayi miki ashe baki cire shi a ranki ba har kina tunanin zai dawo gare ki Kuma ga dukkan alamu zaki karb'e shi da hannu bibbiyu kenan...."

"Maryam shi na gani fa ba imagination bane" na katse ta da muryar tausayi.

"What ever, zo muje ga Inna can da kaya a hannu zata shiga gida muje mu taimaka mata ba wannan surutu mara kan gado ba" tana magana ne tare da jan hannu na muka fara tafiya ina waiwayen baya ko zan ga motan zai dawo amma har muka shiga gida banga ko kalar motan ba, kamin mu karasa Inna har ta riga mu shiga gida.

A parlour muka iske ta zaune tana kallo babu lodin kaya da muka ga ta shigo dasu, zama mukayi muma anan Maryam tana yi mata bayqni akan zuwan mu gidan mai gyaran amma hankalin ta yana kai na ganin nayi shiru na zama wani iri ba kaman yanda muka fita ba.

"Ke kuma lafiyan ki kuwa ana magana kinyi wani zuru dake?" Kaina na mayar kasa ina kokuwa da hawayen da naji suna son zubowa, harara Maryam ta b'alla min tana muskudawa sannan ta bawa Inna amsa.

"Kyale ta Inna ni takaici ma ya hanani kula ta, muna shigowa layin nan wai kawai dan taga mota ya wuce kin ga yanda ta daskare waje d'aya wai taga wannan mayaudarin da kyar fa naja ta muka biyo bayan ki lokacin kina shiga gida ga kaya a hannun ki nace muzo mu taya ki".

"Ban san meyasa taki sakawa ranta dangana ba ko kin manta aure zakiyi, haka zaki je gida wani kina wanna shirmen da shashanci? Ki kama kanki daga irin haka na gaya miki" Inna take dad'in haka cikin fushi ba tare da ta bawa Maryam amsar tambayar ta ba, nima hakuri na shiga bata ina cewa na daina ba zan sake ba Maryam tana taya ni sai da muka ga ta sauko sannan muka bari.

Bayan mun huta mun ci abincin da Inna ta ajiye mana sannan Maryam ta wuce gida tare da cewa sai munyi waya.

Tun daga wannan rana suka kara kaimin shirye-shirye da suke Inna ta ta zama busy sosai these days sai fita sayayya suke da Maman Dije wata rana Kuma da Inna Asabe, Gwaggo Aisha ce dai ko kallo basu ishe ta saima yad'a habaice-habaice da take.

A haka satin da matan tace zan fara zuwa gyara ya zagayo na fara zuwa wajan gyaran a motan su Maryam wanda Mamanta ce ta d'auki nauyin hakan kullum driver zai zo ya d'auke ni in mun gama zuwa yamma kuma waya kawai zanyi yaje ya maido ni gida kasancewar tace ba'a son ina shiga rana saboda zai maida aikin baya.

***************

A gidan su Zafar suma ba karamin shiri suke ba abinka da masu kud'i an gyara mana gidan da zamu zauna duk da sabon gini ne sai da suka Kara da d'an gyare gyare,kayan da za'a saka na cikin wannan gida Abban Zafar ne yayi order su daga kasar waje haka ma kayan lefe na suma duk a kasar waje suka had'o su, shi dai yana gefe yana kallon su yana jin ina zai iya hana su ko kuma inama zai iya fad'a musu gaskiya cewa auren da zaiyi temporary ce ba permanent ba su daina kashe kud'in su amma hakan ba mai yiwuwa bane dan yayi Imani Abban shi yaji abinda ya shirya suna iya batawa na har abada.

Sadiq kuwa in ka ganshi zaka zata shine angon kan yanda ya kasa ya tsare komai yana tafiya daidai, baya ko neman shawaran Zafar yake abinsa shi kad'ai ko Kuma suyi da sauran friends d'in su saboda ko ya nema baram-baram suke rabuwa dan haka suma suka ajiye shi a gefe suke abinda ya dace.

Ana saura kwana goma bikin duk an gama komai a gidan nasu had'a dasu cards da kayan da zamu saka na duk event d'in sun kammala sai bikin kawai suke jira.

Da yamma Mom ta kira shi a waya kan ya same ta a part d'in su, amsawa yayi da toh dama ba wani abu yake ba dan haka ya mike ya fita zuwa amsa kiran nata.

A parlour ya iske su kusan su biyar da Aunty's d'insa wasu ta bangaren Mom wasu kuma ta bangaren Abba sun baza uban kaya a gaban su suna ta kallo.

Gaishe su yayi ya koma gefe ya zauna yana yan dane-dane da wayar shi.

"Ya kuma zaka zauna a nesa, oya come closer kayan amaryar ka ne zo ka duba in akwai abinda baiyi ba sai a canza ko" Mom tace mishi hakan.

" No Mom ba sai na duba ba duk abinda kukayi daidai ne" yace yana kara gyara zama alamun bashida niyyan motsawa bare tashi.

"Kema dai Yaya da son jan magana kike, wannan lefen nayi Imani ko gidan governor zamu iya kaiwa without fargaba balle Kuma wannan 'yar talakawan" cewar wata kanwar Mom da suke kira da Aunty Hauwa dama tana takaicin Zafar daya tashi aure bai nema a cikin 'yan uwa ba yaje ya jajib'o musu 'yar talakawa.

"Hmmmmm" Mom tace tana tabe baki alamun maganan yayi mata dad'i.

"Ai babu zancen duk abinda akayi dadidai ne kai kafi mu sanin matar ka da abinda take so da Kuma abinda zaiyi mata kyau dan haka kazo ka duba nace maka" Aunty Falmata ke fad'in haka babu alamun wasa kan fuskar ta.

Da yake ya san halin ta bata da sauki sam kusan halin su d'aya da Abban shi shiyasa yake matukar shakkar ta, ba musu ya taso yazo ya tsugunna gaban kayan ya fara dubawa kaman da gaske bayan kawai d'agawa yake yana ajiyewa ,su Kuma kannen Mom da ita kanta sai tab'e baki suke na jin takaicin wai sai ya duba.

Yana yi yana kallon ta ta gefen ido ganin hankalin ta baya kan shi ya mike ya dawo gabanta ya zauna cikin natsuwa yace " na duba su duk sunyi kyau sosai Baawa".

Murmushin jin dad'i tayi tana ajiye wayar ta a gefe sannan ta maido da hankalin ta gare shi ta fara magana tace" yanzu abinda ya rage ga kayan da zatayi amfani dasu a events na bikin ku naka da nata duk suna wajan mahaifiyar ka it's a small gift from me".

Mom da taji kaman tayi kuka dan haushi dama niyyan ta in har ba tayi magana ba ta tafi ba zata aika min su ba, cikin dauriya tace" eh gasu nan Son, zoka duba Baawar ka ta sayo muku latest designs na birgewa".

Karasawa yayi zuwa inda Mom take nuna mishi ya zauna ya bud'e had'add'un trollys d'in da wani cool suits mai d'an karan kyau ya fara arba wanda kana gani ba sai an fad'a maka kasan mai tsada ne, cikin farinciki ya cigaba da duba su d'aya bayan d'aya ko wani event da kayan da zai saka har zuwa ranar daurin aure kuma kowanne da takalmi da wrist watch d'in shi, godiya ya fara yi mata cikin jin dad'i dan kayan sun burge shi sosai.

"I'm glad u like it, sai dai ka manta baka duba na amarya ba" ta amsa mishi itama cikin farinciki, sai da ta fad'a ya tuna da wata amarya, bashi da wani zab'in illa kirkiro murmushi tare da bud'e first 1 dake kusa shi.

Sai da yaji numfashin shi ya d'an d'auke na second biyar da yayi arba da wata gown na Indian material sai walwali da d'aukan ido yake ya had'u har ya gaji da had'uwan, daurewa yayi ya cigaba da duba kayan Wanda gaba d'aya anko ne da nashi sai dai a tunanin shi wayan nan zasu fi nashi tsada tunda su kowanne ga jewelry da takalmi da jakan shi.

Tun yana kirkiro murmushi na kar a gane halin da yake ciki har zuciyar shi ta rinjaye shi fuskar shi ya nuna abinda ke cikin zuciyar shi, Baawa da hankalin ta yana kan shi tana jiran taga yayi ta murnan ganin irin kayan da ta hadawa amaryan shi sai taga tsab'anin haka fuskan duk a murtuke yake duba su.

Cikin sanyin jiki ta fara mishi magana" da alamu dai Zafar kayan amaryar nan basuyi maka ba ko?"

" Haba Baawa wad'an nan kayan ko makaho ya shafa su ya san sunyi matukar kyau, abinda yasa kika gan ni haka jikina ne yayi sanyi ban san wani kalamai zanyi amfani dasu ba wajan gode miki domin kayan sun burge ni sosai" yabata amsa yana gyara mood da kawata fuskar shi da yalwataccen murmushi.

"Menene a nan da har kake fad'in haka Son, ko ka manta kai d'in gudan jini nane?"

Girgiza mata kan sa da yake kasa yayi ya cigaba da murmushin dole.

"Good yanzu abinda nake so da ksi shine kada ka bar kayan anan ka kai su can bangaren ka ko zuwa dare sai ka kai mata ko?"

"Toh Aunty mun gode Allah ya saka da alkhairi" yace mata.

"Ameen my son Allah ya nuna mana ranan lafiya mu sha biki" tace tana d'an dariya 'yar uwar ta Hadiza na taya ta dan su Mom sun bar musu parlorn tuntuni.

Maida boxes d'in yayi ya rufe ya kira masu aiki suka taya shi d'auka yayi musu sallama ya fita, a parlour shi suka ajiye suka fita shi kuma ya nemi waje ya zauna yana ta jan tsaki dan shi raini ne baya so da girman shi da komai wai shi za'a aika wajan 'yar yarinyan ga Sadeeq ma jiya yazo mishi da rainin hankali wai shi zai kai mata invitation cards shi kuma yace in ba zai Kai da kan shi ba ya zubar dasu a bola shi Kuma ya watsar mishi akan gado yace ga bolan nan, da gudu ya bi shi ya fita yana mishi dariyan mugunta.

"D'an iska zamu had'u ai sai na koya mishi hankali" yace shi kad'ai kaman wani sabon kamu.

Ni kuma gyaran nan da akayi min na kwana 2 ya karamin masifan kyau kaman an canza min fata ta saboda yanda ya kara laushi da tsantsi ga kamshi na musamman da yake tashi jikina.

Da daddare bayan mun idar da sallah isha'i Inna ta kawo min wani had'i da akayi na madara tace in shanye in bata kofin ta, karb'a nayi na shanye na saboda ta zata auren gaskiya zanyi take b'ata kud'in ta bata san auren wata 2 ko uku bane.

Lafiyayyan abinci ta zubo min shima tace in cinye dan kwanakin nan abinci masu gina jiki take bani Kuma shine ya bada gudumuwar hana rama ta bayyana a idon mutane, ina cikin tsakurar abincin ina sauraron wa'azi da sheikh Aminu daurawa da yake akan rayuwa a tashan sunna tv,o sosai wa'azin ya saukar min da natsuwa domin kaman dani yake yi.

Sallaman yaron makocin mu da yayi yasa na dago da kai na tare da amsa mishi kasancewar ni. kad'ai ce a parlour Inna tana kitchen.

"Wai ana kiran ki inji wani mai mota a waje".

Rasss shine sautin da naji zuciyata ya bada, na kasa bashi amsa saima zuciya ta daya tafi tunani waye zai kasance kenan,Yaya na ko d'an rainin hankali nan ne?

Koma wanene ina daidai da shi, kamin in samu amsan da zan bashi naji muryan Inna a kaina tana " baki ji bane ana kiran ki kikayiwa mutane shiru ko duk salon wulakanci ne haka, wato duk maganganun dana gaya miki ta bayan kunne suke wucewa ko?"

Kamin in bata amsa ta cewa yaron yaje yace tana zuwa, shi kuwa ya amsa da toh ya fita abinsa.

Itama kitchen ta koma ba tare da ta kara kallon inda nake ba, hannu nasa na goge hawayen da suka zubo min sannnan na mike na d'auki hijabi na dake kan kujera na saka na kama hanyan fita nima.

Har na kai hannu zan bud'e kofa naji muryan Inna a bayana tace" ki tabbatar kin shigo dashi parlour baki na Baban ku kada ki bar shi a waje kuma in kun shigo ki zo ki kai mishi ruwa".

Da toh na amsa na fita, ina jan kafa har na fita waje na tsaya a kofar gidan mu da yanzu ya koma gate, na kusan minti uku tsaye a wajan ina kallon motan banida niyyan karasawa, shima kuma ko fitowa bai da niyyan yi balle in saka ran zai fito.

Tunawa da yanda naga Inna ta b'ata ran ta d'azu yasa na fara takawa a hankali kaman mai tsoron kasan har na isa jikin motan na tsaya.

Sauke glass d'in motan yayi yana min kallon up nd down fuskar shi d'auke da wannan shu'umin murmushin sa na gefen baki " 'yar Mallam Ni kike jira in je in same ki kenan, baki san cewa duk zuwan da zaki ga nayi nan dalili yake kawo Ni ba wai dan kin isa ba...."

"Kaman yanda nima dalili ne yake sakani fitowa ba dan kana gaba na" na katse shi nima ba tare da na bari ya gama ba.

"Really!!! I like ur courage, ki cigaba but ki rike a ran ki cewa zaki gane kuskuren ki when we are together under the same roof" yace har yana wani cize lebe.

Kaina na kawar gefe ina son bashi amsa amma abinda nake hangowa a nesa damu kuma cikin d'an duhu shiya d'auke min hankali har na kasa kula shi, shima ganin hankalin na baya tare dani yasa ya fito tare da sauke kayan da ya kawo ya kira yara da suke wasan su a gefe yace su shigar min dashi cikin gida.

Shiga motan shi yayi ya tayar yayi revise, karan motan shi da naji shiya da na mayar da hankali na kan motan ba tare da ya kara ko kallon inda nake ba yaja motan shi ya tafi na raka shi da ido, sai da ya kusan b'ace min sannan na dawo da ido na wajan dana d'auke sai dai Kuma yanzun naga wayam babu kowa a wajan sai duhu da ya kara mamaye wajan.

Dafe Kai na nayi da naji yana juya min saboda tsananin ciwo da yake min , da kyar naja kafafu na da suka min nauyi na nufi gida ina mai mamakin ya akayi Inga mutum kuma lokaci d'aya kuma ya b'ace, ko dan na kasa cire shi a raina shiyasa yake min gizo.
[6/16, 9:15 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*26&27*

Haka na shigo ciki hannuna dafe da kaina, ragwajab na zube akan kujera ina lumshe ido ba tare da na lura da kayan da aka shigo da su ba Inna ta saka su a gaba tana aikin kallo.

"Ban san yaushe kika samo wannan halin na rashin ji ba Zareefa, yanzu duk maganan da na gaya miki amma babu wanda kika d'auka kika bar bawan Allah nan a waje ko balle ki kai mishi ruwan sha?"

Ban iya bata amsa ba sai goge hawaye da suka ki tsayawa nake dan na san ba lalle ne ta amince da abin da zan fad'a ba kasancewar bata san komai akai ba, nima kallon kayan da ban san daga ina suka zo ba nake domin ko za'a yanka ni ba zan iya cewa shi ne ya kawo su ba.

"Kai jama'a wannan lodin kaya daya kawo su kuma na menene, uhum harda su gwalagwalai kuma da alamu na fitan biki ne ko?" Na tsinkayi muryar Inna ta katse min zancen zucin da nake.

Bani da mafitar da ta wuce na amsa mata da " eh " tunda yanzu na fahimci daga ina kayan suka fito.

"Toh Masha Allah amma hidiman nasu yayi yawa bana so gaskiya ki gaya mishi su rage hakan nan kinji?" Nan ma dai gyad'a mata kan nayi ina mamakin dukiya da aka narkar wajan sayan kayan nan.

Nan na kwanta kan kujera duk abin duniya ya ishe ni na rasa ya zanyi da rayuwata, ban tab'a kawowa a raina zan shiga cikin irin tashin hankalin makamancin wannan ba

A kwana a tashi babu wuya wajan Allah dan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment