Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ciro manyan jakuna na shopping daya saba kawo mana ya mik'a min sannan ya kara da kud'i masu yawa yace in bawa Inna ince ta sayi carpet na tsakar d'aki dasu gado.



Cikin tsananin murna na dawo cikin gida da kaya niki-niki sannan na nunawa Inna kud'in daya bata tare da fad'a mata abinda yace tayi dasu.



Karb'a Inna tayi ta ajiye gefe ba tace komai ba dan yanzu zuciyar ta ta fara amincewa dashi sannan ta fara sabawa da lamarin sa.


Ni kuwa duk na k'ogu ta bud'e kayan domin na san duk tsaraba nane a ciki, tana bud'ewa kuwa sune ice cream da sauran kayan dad'i sai kaza gasassu biyu,ice cream na na d'auka na koma gefe na fara sha domin ni yafi min kaza sau dubu.



Da washe gari Inna ta sayo mana carpet d'in mu maroon mai d'an karan kyau harda katifan mu da sabon labule, murna a waje na ba'a magana muma munyi katifa kaman sauran 'yan gidan mu, a ranan da kyar Inna ta kirani waje domin tarewa nayi akan katifan.



A wannan rana mun ga hasada kiri-kiri a wajan matan gidan mu, Gwaggo Aisha tafi kowa shiga tashin hankali sai zage-zage take babu wanda ya kula ta sai 'yan koron tane suke taya ta.



Babu abinda zan cewa Allah sai Alhamdullilahi saboda rayuwar mu ta canza sosai yanzu muci mai kyau mu sha mai kyau mu kwanta a waje mai kyau hatta suturar da muke sakawa ya canza albarkacin Abdulbasit.



Mu muna nan zaune zuciya d'aya ashe bamu sani ba Gwaggo Aisha ta saka ana tayi mata bincike ta ina muke samun kud'i har rayuwar mu ta canza muka zama zara a cikin su.



Bata sha wahalan samun cewa wani saurayi mai kud'i ne yake taimaka mana ba, daga wannan rana ta saka ido sosai tana jiran zuwan shi,cikin ikon Allah duk lokacin da zai zo bata nan sai dai taji labarin yau yazo ya tafi.



A wannan lokacin Gwaggo Aisha duk yawon ta daina fita muka ga tayi a gida take wuni haka Hajara ma ta daina zuwa tallah kullum suna gida,ni na d'auka cewa sun daina tallah ne ashe wai ta gaji da kullum sai ta dawo daga gantalin ta taji cewa yazo har ya tafi shiyasa suka daina fita kullum hanya suke kallo suna jiran zuwan shi.



Sun kai kwana biyar da shiga kullen nasu Abdulbasit yazo yanzu mun saba sosai ni dashi dan har tambaya ta yake abubuwa da nake so, ni kuwa in kirgo mishi in zai dawo ya kawo min.



Ranan ma haka ya kawo min sautu da nayi mishi na kayan kwalliya shi kuma ya sayo min masu tsadan gaske kaman wata budurwa da kuma kayan makulashe daya zame masa jiki kullum zai zo sai ya kawo min, bayan ya gama zolaya ta na gama kuka na muka shirya na kwashi kayana na zan shiga ciki bayan nima na saba kullum in yazo sai na zolaye shi da in d'an b'uda murya ince," sannu da zuwa Yaya naaa".



Sai ya juyo a d'an razane yace," kin tsorata ni zaki sa in fita a guce" sai inyi ta kyalkyalan dariya.


A zaure na tarar da Hajara tana tsaye sai lek'e take ta sha kwalliyan ta na 'yan tallah fuska ya sha make up har yayi over.



Tana gani na ta had'a rai ta tsaya ni kuwa da hankali na na kuruciya ban kawo komai a raina ba nayi shigewa ta ciki, tana ganin na shiga ta fito da saurin ta zuwa wajan shi domin har ya shiga motan shi ya tayar saura yaja.



"Assalamu alaikum barka da war haka ya kyakkyawan d'an saurayi".



Fasa jan motan yayi ya tsaya kallon ta da wani irin fuska sannan ya ce," meke tafe dake?".



Juya ido tayi mishi irin na jan hankalin nan sannan ta ce," haba yanzu har sai nayi maka bayanin abinda yake tafe dani,me budurwa zata nema a wajan saurayi? Koda yake bari in fito in fad'a maka yanda zaka gane.


Naga kana wahalar da kanka akan wancan 'yar karamar yarinya, bayan gani na had'a duk abinda kake nema zan saka ka farinciki domin babu abinda zaka nema a waje na ka rasa" ta karasa tana kara matsowa jikin motan tana girgiza mishi kirji.




Kallon takaici da kyama ya bita dashi sannan ya ce," pls matsa min ka jikin mota kada kisa min k'azanta a jiki".



Kasa matsawa tayi ta tsaya da idanuwa a waje tana kallon shi dan tunda take ba'a tab'a ci mata mutunci haka ba duk yanda taci kwalliya nan yace wai zata shafawa motan shi k'azanta , a firgice ta koma baya jin ya fisgi motan da matukar gudu saura kad'an ya take mata k'afa ya tafi ya bar ta a wajan.



Da hawaye shame-shame ta shigo gida tun daga bakin kofa ta fara ihu tana magana," ni Gwaggo wallahi baki ga wulakaci......" Da hannu Gwaggo Aisha tayi mata alama da tayi shiru, kama hannun ta tayi suka shige d'aki.



A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu har munyi exam na third term muna hutu in mun koma kuma zamu shiga j.s.s 2.



Ranan nan muna wasa a k'ofar gida da kawaye na 'yan mak'otan mu naga Baban mu yana dawo wa gida ban kula ba dan shima ba kulanin yake ba kuma ya tsani in kula shi dan ma yanzu da sauki naga ya rage tsana da yake nuna min.



Bulala naga ya d'auka yayi kaina gadan-gadan zai zane ni bansan hawa ba ban san sauk'a ba, da gudu na kwasa nayi cikin gida ban tsaya a tsakar gidan ba na wuce d'akin mu sanin cewa baya tab'a biyo ni, Inna tana raba gasassun kaji da Abdulbasit ya kawo na fad'a d'akin ina haki.


Inna barin abinda take tayi ta kama min fad'an waye na tsokono zan fad'o mata d'aki haka?



"Inna wallahi ba tsokana nayi ba muna wasa ne sai naga Baban mu....." Had'iye sauran maganan nayi ganin Baban ya d'aga labule ya shigo, bani ba har Inna sai da ta zaro ido tana kallon shi da matukar mamaki.



"Ke yanzu Bintu haka ake tarbiyan 'ya mace yarinya ta fara girma amma ki bar ta tana wasa a waje sai kace namiji" yana maganan ne idon shi na yawo a d'akin har ya sauk'a kan kajin da suke gaban inna, mukut ya had'iye yawu tare da tsura musu ido shiri.



"Toh Mallam ayi hakuri insha Allah za'a kiyaye gaba" tana gama fad'an haka ta ture tiren da kajin suke ciki gefe tare da rufewa da wani tiren.





*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/8, 5:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*πŸ–Š
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ πŸ–Š *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Abin da ake fada idan za a yanka dabba, ko za a soke ta.*

بِسْمِ اللهِ ΩˆΨ§Ω„Ω„Ω‡Ω Ψ£ΩŽΩƒΩ’Ψ¨ΩŽΨ±Ω Ψ§Ω„Ω„ΩŽΩ‘Ω‡ΩΩ…ΩŽΩ‘ Ω…ΩΩ†Ω’ΩƒΩŽ ΩˆΩ„ΩŽΩƒΩŽ Ψ§Ω„Ω„ΩŽΩ‘Ω‡ΩΩ…ΩŽΩ‘ ΨͺΩŽΩ‚ΩŽΨ¨ΩŽΩ‘Ω„Ω’ Ω…ΩΩ†ΩΩ‘ΩŠ.

Bismil-lah wallahu akbar, allahumma minka walak, allahumma taqabbal minnee.

Da sunan Allah, kuma Allah ne Mafi Girma. Ya Allah! (wannan dabba) daga gare Ka take, kuma mallakarka ce. Ya Allah! Ka karba daga gare ni.


*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. πŸ‘‡


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu._


*8*


Karasa shigowa d'akin Baba yayi tare da yiwa kan shi masauki kan katifan mu yana kallon rufaffen tiren ya ce," haba Bintu yanzu iya abinda zaki ce kenan, Fateema ta fara girma sai da saka ido sosai fa".




Cike da mamakin furucin sa ta ce," naji Mallam za'a kiyaye gaba insha Allah" a zuciyar ta kuwa bata daina mamakin wannan sabon al'amarin ba domin ita dai tunda take a gidan bata tab'a ganin ya damu da 'ya'yan matan shi da yake so ba balle 'yar ta da kullum sai ya tsaya a tsakar gida yace ba son su yake ba



shiru ne ya biyo baya a d'akin,ni ina can bayan Inna ta saboda tsoron bulala duk da ya ajiye ta tuntuni naki fitowa, ita kuma Inna al'ajabin me ya zaunar dashi har yanzu a d'akin take gashi tana so ta gama rabon kazan in kaiwa wayan da take bawa kullum.




Mun kai minti kusan ashirin muna zaune shiru babu mai magana shi ya gaji da zaman kurame da muke ya d'an gyara zama yana kallon tiren ta gefen ido ya ce," naga kaman aiki kike Bintu dana shigo ko, toh ki karasa abin ki mana, in ta nine babu matsala Wallahi".



"Haba Mallam ba haka bane na riga da na gama ne shiyasa". Ta amsa mishi.



"Kin gama, me kika gama?" Ya tambaya tare da kafe tiren da ido.



"Rabo nake kuma na gama saura in bawa Zareefa ta kai" Inna ta amsa mishi cikin k'osawa da zaman nashi a d'akin.



"Toh su waye kuma zaki aikawa?"


"Maman Dije da Maa saboda sunyi yawa ga Zareefa ba ci take ba shiyasa nake aika musu".



"Ikon Allah amma Bintu kina da abin mamaki, ya za'ayi ki aikawa wasu alhalin ga 'yan gida nan, ko kin manta da nine?"




Cike da takaicin halin sa ta girgiza mishi kai sannan ta d'auko wani d'an gutsuri kad'an ta mika mishi jiki na rawa ya karb'a ya fara ci yana," kai amma Bintu baki da dama yanzu haka kike cin dad'i kuma ki manta uban 'yar ki?"



Ita yanzu inna halin nashi tsoro ya fara bata ya za'ayi kana magidanci mai iyali baka damu da ka samu ka kawo musu ba sai dai in ka gani a wajan su jiki na rawa ka karb'a, dubi yanda yanzu jiki na rawa yake neman a bashi kaza bai damu da tambayan a ina kika samu ba, sata ko maita ko karuwanci duk kiyi in dai zaki bashi to kece ma 'yar gaban goshin sa.




"Dama da yunwa na shigo kin ganni nan har wani juwa nake gani, Allah yasa da akwai abinci d'akin nan" yace yana faman tsid'e yatsu.



Girgiza kai Inna tayi sannan ta ce," babu abinci Mallam ba muyi girki ba sai...."



"Inna ki bashi nawa da kika ajiye min yaci dan ni nasha ice cream ba zan ci ba". Na katsewa Inna hanzari.



"Yauwa 'yar albarka, Allah sarki yarinya mai tausayin Baban ta" Abba yace cikin jin dad'i yana washe baki.



Inna tsuke fuska tayi tana jin kaman ta kamo ni tayi ta kirb'a sai yau ya san dasu a gidan a baya in ta aika mishi abinci kora ta yake hmmmm sai yau, ba dan taso ba ta tashi ta d'auko mishi hadaddiyar warmer sabuwa da ta sayo mana muke zuba abincin mu a ciki ta ajiye a gaban shi.



Cikin sauri Baba ya bud'e warmer, ba shiri ya lumshe ido saboda kamshi mai dad'i daya bugi hancin sa, yana bud'e ido sai da ya had'iye wani yawu ganin shinkafa da miyar kaza , ko ruwan wanke hannu bai nema ba ya tsoma hannu ya fara aikawa cikin sa hannu baka hannu kwarya.



Ni kuwa duk dad'i ya cika ni yau muma Baban mu ya shigo d'akin mu kaman sauran 'yan gida har yaci abincin mu tsab'anin Inna da duk zaman shi a d'akin namu ya takura ta saboda bata saba ba kuma ta san ba wai matsayin ta da yake kiran ta dashi a baya ba son ta yake bane ya canza a'a sai dan kwad'ayin abin hannun ta wanda ita kuwa ba zata so ya shiga jikin ta b sam..



Yana cikin cin abincin naje inda Inna take ajiye min juices da bobo
na d'auko mishi orange juice na ajiye a gaban shi.



"Ikon Allah shi kuma menene wannan 'yar albarka?" Ya tambaya cikin matukar farinciki.




"Lemon kwali ne Baba" na bashi amsa nima cikin jin dad'in sabon sunan da yake kira na dashi.



Balle murfin yayi ya kafa kai ya fara sha bai sauke ba sai da ya kusan shanyewa sannan ya ajiye yana tsid'e baki ya ce," wai..wai...wai.... Ikon Allah wai lemon kwali kika ce ko?" Ya kara tambaya bayan ya d'auko katon chicken breast a cikin abincin ya fara figa.



Ina dariya na amsa mishi da " eh Baba" Inna dai ko kallon mu batayi ta cika tayi fam jira kawo take ya fita tayi magani na.



Baba bai bar d'akin ba sai da ya gama cinye abincin harda lashe warmer sannan ya mike yana kallo na ya ce," 'yar albarka kada ki manta da Baban ki, ki rinka tunawa dani in kin samu kayan dad'i kinji ko?" Cikin jin dad'i na amsa mishi sannan yayiwa Inna sallama ya fita.



Yana fita muka ji muryan Gwaggo Aisha tana shewa ta ce," ahaiyye nanaye yau me nake gani jama'a kuzo ku tayani duba ko dai ido na ne yake min gizo?"



"Ba gizo idon ki yake miki ba nine nan Mallam Hassan kuma daga d'akin Bintu na fito ko kina da magana ne?" Baba ya b'ata amsa yana cire nama daya mak'ale mishi a hakori.




A yanzu yana dai-dai daya b'ata da kowa a gidan in dai akan Bintu ne, haba yaushe rabon daya ci kaza ko shinkafa da miya ita in banda aukin shinkafa da wake me take bawa mutum ko naira d'ari ko d'ari biyu amma ga Bintu kwanaki bashin dubu biyu ta biya mishi a take,gaskiya dole ne ma ya mak'ale a wajan ta.




Yana gama bata amsa yasa kai ya fice abinsa ya bar Gwaggo Aisha da ihu tana," aikin banza aikin wofi wato ta nan kika biyo dad'in abin kowa ya san dai sunan ki a gidan nan ba sonta nake ba, shine dai sunan ki".




Inna tana jinta bata tanka ba saima kamo ni da tayi zata daka akan abinda nayi Allah ya taimake ni ya jefo Maman Dije ta kwace ni tare da nuna mata kada tayi haka saboda koma ya yake ba'a tab'a canzawa tuwo suna ba, duk abinda zasuyi suyi tsakanin su amma kada ta sakani a ciki.



Da wannan nasihan Maman Dije na tsira ba'a jibge ni ba.



Tun daga wannan rana Baba ya maida d'akin mu wajan hiran sa duk da yanda Inna take tsuke fuska baya damun sa in dai zai shigo ya samu abin tab'awa, ni kuwa duk dad'i ya cika ni yanzu Baba na shigo mana kuma ya daina hantara ta saima sabon suna daya lika min wai 'yar albarka.



Inna kuwa duk rawan kafar da yake yi akan mu ba wani burge ta yake ba domin ta san dan abinda yake samu shiyasa har yake ihu da 'yar lelen shi wato Gwaggo Aisha, ta ina ma zata manta abubuwa da yayi mata na shekara da shekaru dad'in bakin sa na lokaci kad'an d'in nan ba zai tab'a goge tabo dake cikin zuciyar ta ba.



Abin takaici ma har yau bai tab'a yunkurin tambayan ina Inna ta ya take samun kud'i da har take wayan nan abubuwan ba, kuma wani ikon Allah bai tab'a had'uwa da Abdulbasit ba dan haka bai san daga inda muke samun kud'i ba.




Tsakani na da Abdulbasit kuwa wani shakuwa ne na ban mamaki ya shiga tsakanin mu ada yana kaiwa sati ko fiye kamin yazo gidan mu amma yanzu baya iyawa dan ana kwana 2 zai zo mu sha hiran mu yana sai dai mafi yawan hiran tsokana ta yake wai ya ganni da saurayi da sauran su ni kuwa insha kuka na in more daga baya kuma mu shirya abin mu ya tafi.




Rayuwa yanzu tayi mana dad'i sosai dan bamu da maraba da masu kud'i tunda duk abinda masu kud'in suke ci suke sha suke sakawa muma haka ni da Inna ta duk mun murmure harda d'an kumatu mukayi.



Gwaggo Aisha da Inna Asabe kuwa duk hankalin su a tashe yake ba ma kaman Gwaggo Aisha dan kiri-kiri ta rasa matsayin ta ya koma kan Inna tayi duk abubuwa da zatayi amma duk a banza dan gwara da yana d'an sauraron ta amma tunda ya shigo d'akin mu ranan ya tarar da Inna tana kirga kud'i sun kai kusan dubu hamsin a hannun ta tun daga wannan rana ya kara haukacewa kasancewar ko shi da yake d'a namiji bai tab'a rike irin wannan kud'i ba.




Ganin duk ya rikice yasa Inna ta bashi dubu biyar a ciki a ranan kaman yayi mata sujada haka ya kwantar da murya yana mata godiya.



Daga wannan ranan mulkin gidan ya koma hannun Inna ta dan Baban mu ya zama kaman wani bawan ta duk abinda tace baya musu balle ya karyata ta cin mutuncin kowa yake a gidan saboda mu.


.
Mun koma makaranta mun shiga jss 2 cikin farincikin sabon uniform da Abdulbasit ya d'inka min dasu sabon jaka da sauran kayan amfani na makaranta, tsab dani na koma kowa ma sai sha'awa ta yake masu tsokana ta da kuma yanzu sune suke bi na wai suna sona da k'awance.



Na biye musu nima duk abinda na kai makaranta na kayan kwalama ina basu ko in sun ce in saya musu wani abu bana kyashin saya musu amma fa ba wai na manta abinda suka min bane sai dai na barwa Allah ne.




A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu muna jss 3 komai na alamun girman 'ya mace duk sun bayyana a tare da ni kyawu na ya fito sosai, shakuwa da yake tsanani na da Yaya na ya rikid'e ya koma zallan soyayya, dan sosai yake nuna min abinda ke cikin zuciyar shi tun ina had'awa da kuruciya har ni da kaina na fahimci na fad'a son Yaya na sosai kullum zai zo mu sha hiran mu da kyar zai daure ya tafi, daya ga hakan ma ba zai wadatar dashi ba ya sayo min dankareriyar waya ta wanda kullum ya kasance muna cikin communicating.




Wannan waya da Yaya na ya saya min gaba d'aya ya d'agawa Gwaggo Aisha da Hajara hankali harda Jameela wacce take ganin sa'anni muke da ita.



Ban san ko ta yaya abin ya kasance ba sai dai gani nayi itama wani mai mota yana zuwa wajan ta hira, daga ranan da mai motan ya fara zuwa a ranan ta sallami duk sauran samarin ta dan dukan su babu mai mota a cikin su dama lallab'a su take.




Tun daga wannan rana su Gwaggo Aisha suka fara d'aga murya a gidan komin kankantar abinda ya kawo mata sai an fito tsakar gida ana maimaitawa ana yi mana iyayi a gida, mu dai ko a jikin mu amma Inna Asabe duk ta damu dan tana da 'ya Hasiya kuma sa'ar Hajara ce, Allah ya jarabce ta da bakin jini babu wanda ya tab'a zuwa wajan ta .




Yawanci Yaya na in zai zo wajena sai bayan la'asar yake zuwa kuma Baba baya zuwa gida a wannan lokacin amma a yau bayan azahar yazo saboda wai zaiyi tafiya amma ba dad'ewa zaiyi ba gobe zai dawo, muna cikin hira na hango Baba ya nufo gida sai gyara binjimar jikin sa yake, dum naji zuciya ta ta buga dan daga ni har Inna ta bama son Baba ya had'u da yaya na dan zai iya tafka abin kunya dan shi ba damuwar shi bane.




Motan yabi da ido ya gan mu tsaye a gefe kaina a kasa dan bana son yayi min magana amma banyi nasara ba.



Yana gani na ya nufo inda muke cikin sauri yana," a'a 'yar albarka kece anan?"



Kamin in bashi amsa Yaya na ya durkusa har kasa ya fara gaishe shi, cikin washe baki yake amsawa yana bin katuwar motan shi da kallo .




*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/17, 9:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚 🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*πŸ–Š
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ πŸ–Š *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*



*Addu'ar Wanda Ya ji Tsoron Faruwar Wani Abu Mummuna saboda Kambun Baka*

Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; "Idan dayanku ya ga wani abu da ya kayatar da shi ga dan uwansa, ko ga kansa, ko ga dukiyarsa, to ya roki Allah ya sanya albarka gare shi; domin kambun baka gaskiya ne.


*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. πŸ‘‡


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu._




*Kuyi hakuri kunji ni shiru kwana biyu kun san jiki da jini sai a hankali amma yanzu Alhmdllh naji sauki, wayan da suka kira da wayan da suka turo sakonni duk ina godiya da kulawar ku Allah ya bar kauna.

Nagode sosai*😘😘😘

*9*



"Lafiya lau yaro.... lafiya lau" Baba ya amsa yana had'iyar yawu yana kara karewa motan kallo, ni dai sanin zai kwafsa min yasa ko d'ago kaina na kasa yi bare mu had'a ido da shi.


Yayana kuwa yana gama gaishe shi bai d'ago daga tsugunen ba yayi kasa da kai yana jiran Baba ya bar wajan, Baba ba dan yaso ba yaja kafa zuwa cikin gida yaso ya samu wani abu wajan mai tsallen motan nan, amma ba komai bari yaje wajan Bintu zai ji ko wanene shi d'in.


Wata b'oyayyen ajiyan zuciya na sauke ganin ya wuce gida salin-alin ba tare da yayi wani abu daya tsinka ni ba, nabi bayan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment