Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

tayi itama tana kokuwa da nata hawayen dan kada su zubo da kyar tayi nasaran maida su sannan ta dago ni tana share min hawayen fuska ta tanayi wasu na kara zubowa.

Murmushi d'auke a fuskata ta take kallo na sannan ta fara magana " toh menene abin kuka anan kuma uhum? Yakin matan kenan muma haka aka rabo mu da gidajen zuwa inda bamu saba kuma muka d'auki hakuri da juriya muka saba kema hakuri zaki yi wata rana sai labari.

Aure bautan ubangiji ne a gare mu mata shine kuma mafi saukin hanyan shiga aljanna in min bi Allah kuma kika yiwa mijin ki biyayya kaman yanda Allah ya umarce da muyi toh tabbas zaki rabauta, miji a duk yanda kike tunani a musulunci ya wuce nan miji babban jigo ne a rayuwar 'ya mace tunda da zaran an kai mace d'akin mijin ta shikenan komai nata ya koma hannun shi ko iyayen ta basu da iko a kanta ko kad'an misali koda mutuwa akace nayi in yace ba zaki zo jana'iza ta ba dole ne kiyi hakuri ki zauna kiyiwa mijin ki biyayya...."

A razane na dago jajayen ido na da kuka ya rina ina kallon ta ina son yin magana amma na kasa sai baki na da yake ta karkarwa.

Gyad'a min Kai tayi tana mai cigaba da murmushin " irin wannan biyayyan ake son mace tayi a gidan mijin ta, nasan yanda kike ji na san abinda kike tunani amma ina mai baki shawara a matsayi na na mahaifiyar ki, ki cigaba da hakuri kiyiwa mahaifin ki biyayya insha Allah gaba ba mu ba ke da kan ki sai kinfi mu alfahari da wannan aure zan cigaba da yi muku addu'a insha Allah komai zai dai-dai ta .

Yanzu kiyi wanka ki fito ga masu miki kwalliya suna jiran ki a d'aki" tana fad'an haka ta wuce ta fita ta ja min kofa bata tsaya a ko ina ba sai bathroom din ta,ta fashe da kukan da take ta dannewa tun d'azu " ya Allah ka taimake ta ka kare ta kada ta fuskaci irin rayuwar da nayi a cikin gida na ya Allah ka sanyawa rayuwar auren ta albarka".

Haka ta cigaba da kukan ta tana sumbatu domin a kullum daurewa kawai take ace a aurar da 'yarka ga wanda baka san daga inda yake ba balle ayi bincike a san halin shi babban tashin hankalin ta shine bata da daman cewa komai akai saboda mahaifiyarta ta gargad'e ta tun farko, amma ba zata daina fad'awa Allah ba ya bani ribar biyayyan da nayi musu.

Da kyar ta rarrashi kan ta ta daina kukan ta fito jin hayaniya na kara yawa alamun mutane suna karuwa kenan.

Ko da ta fito sai ta aro jarumta ta daurawa wanda take dashi a baya ta cigaba gaggaisawa da yan uwa da abokan arziki amma taki yarda ta kalli gefen da Maa take balle su had'a ido ta fahinmci tayi kuka, sai dai bata sani ba ta makaro domin Maa ta riga da ta gane halin da take ciki, murmushi kawai tayi tana yaba jarumtar 'yar tata.

Bayan fitan Inna daga bayin sabon babin kuka na bud'e inayi ina mai tausayin kaina ta yaya zan iya yin biyyan nan da Inna take Fadi ga wannan azzalumin? Da kyar na rarrashi kaina na daina kukan na fara wankan sanadiyan takura ni dasu Maryam suka yi.

Koda na fito na kasa kallon kowa a d'akin sai kan stool na gaban mirror naja na zauna kai na a kasa ba dan komai ba sai dan bana son yawan magana, su kuma masu make-up suna ganin na fito suka iso dan yin aikin su, ban hana su ba kuma banyi musu gardama ba suka fara min sai dai yau light make up sukayi min amma duk da haka ba karamin kyau nayi ba, Maryam da jikin ta duk yayi sanyi ganin yanayi na ta d'auko musu trolley da aka saka kayan da zan saka yau da safe ta kawo musu.

Su suka taimaka min na shirya cinkin wata expensive lace fari sol dashi yasha diamond stones, ni dai tunda nake a rayuwata ko labarin irin lace din ban tab'a ji ba balle gani, headtie na wani yadi mai sheki suka nad'a min shima fari ne sai set na dan kunne da sarka harda zoben shi na pure diamond suka saka min.

Ba zan iya kwatanta muku yanda ni Zareefa nayi kyau a wannan rana ba just imagine it urself sai dai ko kad'an babu abinda ya burge ni a ciki in na tuna sabon rayuwan kunci da zan shiga ma sai inji kuka na neman kwace min.

Kawaye na suma sun fito cikin wani hadadden atamfa da sukayi anko kowacce sai zuba kamshi da haske suke zubawa ana jiran su angwaye su karaso dan karfe goma sha d'aya ne daurin auren.

A can gidan su Zafar suma haka suka tashi da shirye-shiryen gaske ba irin na jiya ba dan Baawa jiya bayan dawowar su daga gidan mu ta kai karan su Mom akan yaja musu kunne kada su zubar mishi da kima gidan surukai, aiko bata ji da dad'i ba wajan Abba dan sosai ya nuna mata b'acin ran shi sannan yaja mata kunne tayiwa 'yan uwanta magana kowacce ta kama kanta in ko ba zasu kama ba kofa a bud'e take duk su watse bayan son harkan k'ananan mutane, dole ta nuna tayi nadama a gaban shi da alkawarin babu wata b'araka da zata taso daga gare su sannan ya kyale ta ta koma ciki cike da tsana ta.

Sadeeq shine yazo ya tada Zafar daga bacci dan har tara saura yana kwance yana bacci cikin kwanciyar hankali abin shi, ya shirya tsaf cikin hadaddiyar shaddar shi ash color sai kamshi yake zubawa kaman shine angon,Koda ya farkan ma fad'a sukayi tayi shida Sadeeq din kan me yasa zai tashe shi yana cikin baccin shi mai dad'i.

Ganin yana son yaja hankali sauran abokanen su da suke parlour yasa shi yayi shiru yace toh yayi laifi kuma ya amsa ya tashi yayi wanka ya shirya ga Abba da sauran abokan su suna jiran shi su tafi wajan daurin auren.

Jin ya ambaci sunan Abba yasa ya mike Yana kumbure-kumbure kaman karamin yaro ya shige bathroom d'in shi dan yin wankan, dariya Sadeeq yayi sai da yayi Mai isar sa sannan ya ciro mishi kayan da aka tanada mishi domin d'aurin auren.

Sadeeq shiya taya shi shiryawa sunayi suna fad'a shi dai Sadeeq dariya yake ta mishi ganin yanda yake turo baki kaman wani karamin karamin yaro mai shagwab'a.

Farar dok ce mai matukar tsada yasa mai d'aukan ido yasha aikin hannu wato (gatau) hula takalmi duk farare ne wrist watch na hannun shi shima na pure diamond ne sai kamshi na musamman yake kana ganin shi kaga haddaen ango, suna gamawa suka fito parlour inda abokan sa suke jiran sa.

Yana fitowa ihu suka fara suna mishi kirari saura na tsokanan shi dan sake fuska yayi ya dan biye musu suka tab'a wasa sannan suka raka shi wajan Mom.

Tsakar gidan babu mutane sosai dan haka basu sha wahalan karasawa cikin ba , parlour Mom a cike yake ana ta hidima suna ganin shi wata mai murya ta saki wani irin gud'a da ya cika gidan nan da nan sukayi kan shi ana ta wasa da dariya da kyar ya samu ya karasa sama d'akin Mom, tana zaune cikin kawayen ta da 'yan uwan ta suna hira.

Ido ta zuba mishi har ya karaso ciki zuciyar ta kuwa kaman farar takarda yau Allah ya nuna mata auren tilon d'an ta.

Albarka suka yi ta saka mishi bayan ya suguna har kasa ya gaida su, Mom harda hawayen farinciki dan yau babbar rana ce mai babban tarihi a rayuwata.

Kiran da Abba yayi mishi ne yasa shi mikewa ya fita ya tarar da tawagar Abba har sun fara tafiya, ba b'ata lokaci shima ya shiga cikin abokan sa suka kama hanya.

Akwai wani babban masallacin juma'a a bakin layin mu kuma a nan ne za'a d'aura auren, so duk a can wajan layin sukayi parking wasu ma ko wajan parking din basu samu ba saboda yawan motocin dan haka wasu suka fara shigowa cikin layin namu Dan samun wajan parking.

Masallacin kan shi ma har yayiwa mutane kad'an wasu basu samu shiga ba ko ina ka duba taron al'umma ne, in wanda bai sani ba yazo yaga taron zai zata auren 'yar babban mai kud'i ake ba ko dan siyasa ba 'yar Mallam Hassan ba.

Baba yau in ka ganshi kaman yayi hauka saboda farinciki harda su governor a daurin auren 'yar shi harda manyan kusoshi na gomnati ,ba'a tsaya b'ata lokaci ba aka daura aure na da Zafar kan sadaki naira million 2.

Muryan maroki da ya fara shelan d'aurin auren har cikin gudan mu a lokacin ina tsakar gida cikin mutane dan Inna ta saka ni fitowa waje gaida 'yan uwan Baban mu, a take wajen ya kacame masu farinciki suka fara masu bakinciki ma nayi, ni kuwa ji nayi kaman an saka ni a cikin kankara haka naji jiki na yayi wani bala'in sanyi tare da zazzab'i mai zafin gaske ba shiri na nufi bangaren mu kamin na karasa d'aki na har na fara rawan sanyi ina shiga na kwanta na lullub'a da bargo ina hawaye a haka Aunty Batool tazo ta same ni cikin rarrashi tayi min nasiyan yadda da kaddara sannan ta bani magani na sha bata bar d'akin ba sai da taga bacci mai nauyi ya d'auke ni sannan taja min kofa ta fita.

Anan d'aura aure su Abban Zafar gaba daya suka wuce reception da Abba ya had'a a nan cikin gidan shi, su Zafar ma bayan shi suka bi duk yanda Sadeeq yayi dashi akan su tsaya ya d'anyi pics tare dani saboda tarihi yaki ya shiga mota suma suka rufa mishi baya.

Sai yamma naji d'an karfin jiki na aka kara canza min kwalliya zuwa walima cikin abaya da Inna ta siya min saboda walimar ba'a dad'e da farwa ba yan gidan su Zafar suka kawo lefe na da ya kusan haukata mutanen gidan mu dana anguwan baki d'aya, nima a yanda naji Maryam tana lissafowa ban tab'a jin labarin irin su ba.

Bayan an gama cece-kucen ganin lefen suma suka shiga cikin mu akayi walimar dasu inda Mallama Falmata Zanna ta wa'azantar kan biyayyan aure ko Inna ce tace tayi hakan oho, sai kusan magariba taro ya watse bayan anyi rabon manyan jakkuna masu d'auke da Al'quran ma daidaici sai sallaya da hijabi,nayi mamakin yaushe Inna ta shirya haka ko dan ban maida hankali ga bikin bane ban sani ba.

Basu bar ni nayi alwalan magriba sai da nayi wanka da ruwan turare sannan nayi alwala na fito nayi sallah ina kuka ganin cewa dai da gaske suke dan sai shirye-shiryen kai ni suke shirya ni sukayi cikin atampa super mai ratstsin silver a jiki , d'an kunne da sarka da suka saka min suma duk silver ne sannan suka nad'a min laffaya mai masifan kyau shima silver color aka fito dani wajan su Inna da yan uwan ta.

Nasiha suka fara min kan hakuri d'aya bayan d'aya Inna ta dai tana gefe tana kallon yanda nake kuka kaman raina ya fita, Maa ce ta katse ta tace itama tace wani abu mana.

Murmushi mai ciwo tayi muryar ta na rawa tace" me zancen Maa da ku baku fad'a ba, ni sai dai inyi mata addu'a Allah yaa...." Kukan da take rikewa ne ya kwace mata ta tashi cikin sauri tayi d'akin ta, kara kuka na nayi na mike zan bita suka rike ni ina musu magiya da roko amma basu saurare ni suka sada ni da d'akin Abba yana zaune shi kad'ai sai washe baki yake.

"Sai ku fita ku d'an bamu guri ni da 'yata ko" yace musu bayan sun zaunar dani a tsakiyar parlour shi, Aunty Batool har ta tsaya da nufin gasa mishi magana Aunty Fatima ta mata alama da ido da tayi shiru kawai su fita, ba dan ta so ba suka fita tana mitan wai dama ya san ni 'yar sace?

Suna fita ya juyo gaba daya gare ni yana kara washe baki yace " ke kuma in banda kuruciya menene abin kuka anan, Allah ya azurta ki da samun irin wannan mijin da babu kamar sa duk maiduguri yaushe kuka hadu dashi amma ga yanda ya sauya mana rayuwa baki d'ayan mu,

Wannan ai abin alfahari ne a gare mu ba ki saki baki kina kuka ba d'aurin auren ki har da gomna fa suka zo" ya karasa feeling very proud Yana gyara Zama.

"Abinda nake so dake shine kada kice zaki manta da gida dan kin samu daula ya kamata ki san yanda zaki rinka tatso wasu abubuwa daga gare shi kina aiko mana ai kin gane abinda nake nufi" ya karasa tare da zuba min ido gyad'a mishi kai nayi hawayen takaici na zubo min dan ni da yace su Aunty's dina su fita na zata zai min nasiya ko kuma ya rarrashe ni kan auren da ya d'aura min ashe shi tunanin shi daban, wai yaushe ne Baban mu zai canza?? Na jehowa kai na tambayan da babu mai bani amsa.

D'aga murya yayi ya kira su Aunty Fatima suka zo suka fita dani direct sai mota suka sakani suna ta zabga guda Aunty Fatima da Aunty Batool su suka sakani a tsakiya suna hirar su anan naji cewa wai Gwaggo Aisha da taji labarin taron d'aurin auren ta yanki jiki ta fad'i yanzu haka tana asbiti ba lafiya.

Har muka karasa gidan Zafar da ya amsa sunan shi gida ko ince Aljannar duniya dake can bolori lay out hawaye bai kara zubo min saboda mamakin halin Baban mu dana Gwaggo Aisha.

A maidaicin compound din gidan da fitilu da flowers suka ma ado drivern yayi parking ,Aunty Fatima dake zaune a gefe na dama ita ta fara fita sannan ta kama hannu na tace in fito da kafar dama, hakan kuwa nayi na fito kaina a kasa dan rabin fuskata a rufe yake tana rike da hannu na har entrance din parlour nan ma cewa tayi inyi Bismillah sannan in shiga da kafar dama.

Ni dai tafiya kawai nake ban san inda nake jefa kafa ta ba har naji mun shigo wani d'aki kuma naji an zaunar dani akan wani tattausan gado, sai a lokacin naji sabon kuka ya zo min na fara ina rike a jikin Aunty na, sauran yan rakiyan kuwa suka bazama duba gidan suna ta santi tare da yaba kayan d'aki da Inna ta min wanda ni ban san ma yaushe akayi su ba kasancewar naji Baba na cewa ba za'a min komai ba dan sun ce basa bukata komai daga gare mu.

Allah sarki Inna ta na san tayi hakan ne dan samo min martaba da Kuma daga gare su, bamu fi minti talatin da zuwa ba naga sun fara shirin tafiya dinner nima kara shirya ni sukayi cikin wani Indian material mai dan karan tsada da kyau, net suka saka min a tsakiyan kai suka kama da pin ana ganin kitson da aka min na gaba sai suka saka min sarkan kai wanda yazo min har goshi sarkan set ne da dan kunne da sarkan wuya da warwaro masu bada sauti mai dad'i.

Kamin su gama min duk sun tafi sai Maryam da wasu cousins dina 2 su suka tsaya Jira na da kuma Aunty Fatima har bakin wata arniyar mota da ko sunan ta ban sani ba suka rako ni tare da bud'e min kofa na shiga, ina jira inga ta shigo kaman dazu sai naga ta mayar da kofan ta rufe suka nufi wasu motoci guda 2 daya a gaban mu yake daya kuma a baya ya kasance sun saka mu a tsakiya.

Har motan ya fara tafiya naji motsi a gefe na a firgice na juya dan a zato na Ni kad'ai ce a cikin motan sai ganin mutum nayi a kishind'e kaman wani basarake yana latsa waya ko kallon inda nake baiyi ba, ni kuwa kasa d'auke ido nayi a kansa ganin sa cikin arniyar suit ko dan ban tab'a ganin ya saka bane sai naga ya masifan yi mishi kyau,

"Bana son kauyanci ki daina kallo na da wayan nan idanun naki" naji muryan shi ya katse ni.

Cike da jin haushin kaina na murkud'a mishi baki nace " da wani idon kasan ana kallon ka..." Ko rufe baki na banyi ba naji ya dalle min baki da yatsan shi a take naji hawaye sun cika min ido dan ba karya naji zafi sosai, a zuciya ta naja masa Allah ya isa cikin kwando na cigaba da murza lebe na can dai na kasa hakura dan abin na cizo na a rai ace kullum shi yake ha'in ta na ni bana ramawa.

Cike da tsiwa nima na bud'i baki zan rama naji mutumin da yake gaban motan yana ce mishi mun iso, bari yayiwa sauran magana su zo yace, kamin ma ya rufe baki su Sadeeq suka zagaye motan tare da bud'e mana, shi ya fara fitowa sannan ya zagaya ta bangare na ya kama hannu na ya fito dani yana wani murmushi kaman ba shine ya gama cin zalina yanzu ba.

"Come on wifey walk gently" yace min cikin wani murya da ban san shi da ita ba, a zuciya ta nace lalle wannan ya cika dan drama toh bai sani ba gidan ta yazo.

Cike da yanga da fari nima na amsa mishi da " yes husby".

A dan zabure ya juya ya kalle ni na second 5 ya d'auke kai yana murmushi, tafiya cikin hall din muka fara su Maryam suna watsa mana wasu abubuwa masu kyalli gefe daya kuma turaren wuta Hamra take bin mu da shi a baya.

Hannun mu sakale dana juna kaman masoyan gaske har muka karasa wajan zaman mu, tunda muka shigo mc ya saki wakan bikin da Ali jita ya rera mana mai taken Zareefa ta Zafar.

Sai da kowa ya zauna aka natsu sannan Mc ya fara gabatar da event cikin burgewa da wayewa, da aka nemi abokin ango ya bada tarihin ango Sadeeq ne ya fito ya bayar sannan Maryam ta bada nawa,daga nan aka bukaci mu fito mu yanka 🍰 kaman ince ba zan fito ba amma sanin duk abinda ya wakana anan zai je kunnen Inna yasa na fito muka tsaya a gaban tangamamen cake wanda ya kusan tsayin mu after d count of 3 muka yanka a tare, cikin wani salo ya gutsuro cake din ya saka min a baki da gangan na had'a da yatsun shi 2 na dalla mishi cizo wanda har ya saka shi saurin janye hannun shi yana yarfewa.

Dariya na tintsere dashi cikin tsananin farincikin nima na rama muguntan da yayi min, suma yan hall din dariya suke su a tunanin su wata salon soyayya ce haka.

Ina kallon shi sai harara ta yake ta kasan ido yana jiran in bashi shima ya rama bai san cewa na gama gano shi ba.

Maimakon in gutsuro cake din in bashi a baki sai lakato shi nayi a yatsana na shafa mishi a hanci nan ma dariyan yan hall din suka kwashe da shi ni kuwa ganin ya harzuka kaman ya shake ni yasa na juya da sauri zan bar wajan, har nayi step 2 naji anyi sama dani.

Tafi da ihu sosai ne ya cika hall din wanda ya ankarar da Zafar inda muke yayi saurin ajiye ni dan idon shi ya rufe burin shi ya min muguntan da nan gaba in muka had'a hanya da kaina zan gudu, lakace min hanci yayi yana yaken da yafi kuka ciwo, ni kuwa harda yi mishi gwalo muka koma wajan zaman mu raina fari tass yayin da shi kuma yake jin kaman ya had'iye zuciya ta mutu saboda haushi.

Ali jita shi ya baza basirar sa a wajan anyi rawa an cashe anyi barin nairori harda daloli , anci an sha sannan mun samu gift ba adadi zuwa 10 aka tashi kowa yayi inda ya fito, a mota daya muka dawo da kawaye na nayi musu karyan zai sallami abokan sa basu san guduwa nayi ba dan in na shiga mota daya dashi ban san kalan muguntan da zai min ba.

Muna zuwa gidan Aunty Batool ta had'a min ruwan turare ta sani a gaba nayi wanka ta shirya ni cikin wani dogon riga na material pink ta min light make-up ta zaunar da ni akan gado bayan ta min barin humra kala kala a jikina ta lulluba min katon gyale sannan ta zauna a gefe na ta kama hannu na duka 2 cikin nata tace;

"Toh Zareefa ni zan tafi sai gobe zamu dawo zan kara maimaita miki kiyi hakuri kiyi hakuri sannan...." Aunty dan Allah kadaki tafi ki bar ni mu kwana tare dan Allah Aunty" nace ina kokrin rushewa da sabon kuka.

"Kada ki kuskura hawayen nan su zubo shikenan naji zan kwana anan bari inje in rufo mana kofa sai mu kwanta ko" ta karasa cikin rarrashi.

Ajiyan zuciya mai nauyi na sauke ina gyad'a mata kai ta mike ta fita tare da bar min jakar ta a d'akin.

Toh fans yanzu aka fara wasan koyaya zaman ma'auratan nan zai kasance ??

Sai ku biyo ni a next page, sai kuna hakuri kwananan I'm so busy .
[6/16, 9:18 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*30&31*

Ina zaune da jakan Aunty sai baza ido nake in ga ta dawo amma shiru ko alaman motsi bana ji balle muryan mutum, gidan yayi wani irin shiru na ban mamaki, cike matsanacin tsoro da ya kamani lokaci guda na mike jiki na tsuma na nufi bakin kofa na bud'e na l'eko ina kyautata zaton parlour ne nan amma tashin hankali da nake ciki bai bar ni na tantance ba.

Muryata na rawa alaman kuka na iya kufce min a ko wani lokaci na bud'i baki na kwala mata, shiru kake ji babu wanda ya amsa ga dukkan yanayin gidan ma ni kad'ai ce a ciki, da gudu na koma d'akin da na fito na maida kofa na rufe harda murza key da na gani a
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment