Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

da lantana da yake can jejin Goshe ko tsoro basa ji na yanda hanyoyin maiduguri suka lalace, sunyi sa'a sun same shi ya basu magani amma yace a abinci za'a zuba mishi na kwana 3 in dai har yaci abincin toh zai min wani irin tsana da bashi da iyaka ya min koran kare a gidan shi.

Wani kullin maganin ya Kara miko musu yace shi wannan kuma a turare zasu saka Hajara ta rinka shafawa a duk lokacin da zata je kusa da shi , in har ya shaki kamshin toh shikenan an wuce gurin zata zama itace mace kad'ai a rayuwar shi ko uwar shi ba zai kara tuna ta ba.

Cikin tsananin farincikin samun nasara ta dawo gida ta labartawa Hajara yanda sukayi da boka, nan kuwa ta hau murna kaman da gaske harda su rawanta wai ta kusa samun miji balarabe.

***************

Kaman yanda ya saba kullum sai yaje ya gaida iyayen nashi yauma ya isa gidan nasu akan lokaci domin ya samu Abban shi a gida bai fita ba, cikin girmamawa ya isa gare shi ya zauna wajan kafafun shi sannan ya gaishe shi yana daura kan shi kan kafar Abba.

Cike da so da kaunar tilon d'an nashi ya amsa yana mai shafa gashin kan shi, dan yanzu sosai suke shiri ba kaman da ba da kullum suke cikin rigima kan hallayyar shi ganin yayi auren yasa yake ganin ya natsu sosai.

"Ina 'yata tana lafiya ko?" Abba ya tambaya bayan ya amsa gaisuwan nashi.

"Tana nan lafiya Abba tace ma in gaishe ku" ya bashi amsa yana wani tsunne Kai kaman da gaske.

"A'a ni gaisuwan nan ta ishe ni hakan nan tunda taki zuwa mu ganta koda yake bata da laifi kai ne kake mana rowan ta ko Hajiya?" Ya karasa yana maida hankalin sa kan Mom da take saukowa yanzu.

Sai da ta tab'e baki ganin dukkan su basa kallon ta sannan ta kirkiro murmushi tare da karasawa gare su ta zauna kusa da Abban tana mai cewa " babu batun rowa ririta amaryar sa yake" ta karasa tana dariya kaman da gaske.

Dariyan suma sukayi suka cigaba da hiran su har zuwa wani lokaci sannan ya mike yace zai tafi

"Ya maganan da mukayi da kai sai yaushe zaka fara fitowa office?" Abba ya dakatar da shi.

"Sai nan da 2 months" yace yana sosa keya, dariya suka mishi Abba yana " ja'iri wata 2 ai kaman kwana 2 ne yanzu zai zo ya wuce, amma ka tabbatar ka kawo min 'yata mun gaisa".

Mom da duk haushi ya cika ta na me yasa Abba yake son gani na ta bud'i baki zatayi magana yayi saurin dakatar da ita wajan daga mata hannu ba dan taso ba tayi shiru tana gani har Zafar din ya fice zuciyar shi fari tass dama abinda yasa yace sai bayan wata 2 zai fara aiki kamin nan ya gama da chapter na ya Zama free man zaiyi abinda yake so.

Ni kuwa bayan wannan incident daya faru tsakanin mu wanda ya kasa barin kwakwalwata bamu kara zama waje daya dashi ba sai dai da naji motsin shi zan l'eko in kare mishi kallo sometimes yana cin abinci sometimes kuma yana wannan danne- dannen shi a laptop, ni dai har yau ban san me yasa bana gajia da kallon shi ba.

Yau tunda na tashi na gama aiki na zauna ina duba wani littafin Hadisi cikin litattafai na islamiya, wannan mayen kamshin nashi shi ya fara min sallama, wani irin zillo zuciya ta yayi kaman zai fad'o kasa jin wannan sassayan muryan yana cewa " ki shirya anjima da daddare zamu je ki gaida su Abba, nd saura in muka je kada ki kama kan ki kije kiyi ta musu kauyanci ki da kika saba kiga yanda zan tsaba miki ".

Maimakon inji haushi ni dariya ma ya bani dan haka ban san lokacin da na saki wani kayataccen murmushi ba, wai nice zanyi mishi kauyanci ko ce mishi akayi daga kauye nake oho.

Cike da takaici yake kallon yanda na sunkuyar da kai kasa ina murmushi, shifa wannan sabon dabi'a da na samu haushi yake bashi da duk abinda zaiyi min ko ya fad'a min baya bani haushi balle in nuna ko inyi kuka, in ya ganni ina kuka wani dad'i yake ji na musamman amma da yanzu bana nuna jin haushi sai yaji duk haushi ya kara cika shi.

Cike da tsana ta ya hamb'are ya fice yana" duk abinda za'a mata sai ta zauna tanawa mutane dariya, mayya kawai ni dai ba zaki cinye ni ba" yana magana yana mai ficewa daga parlourn.

Tashi nayi na karkad'e jikina still murmushin bai bar fuskata ba wai nice mayya hmmmm.

Tunda yace zamu je gaida iyayen shi duk sai na kasa zaune na kasa tsaye ina tunanin me zan kai musu da zan burge su, abinka da masu kud'in nan ba komai zaka musu kayi gwanin ta ba.

Duk tunani na ya tsaya ne kan girki, toh in banda girkin me nake dashi da zan kai musu, kitchen na shiga nayi tsaye ina tunanin what should I cook? Wai meye nawa da zan takura kai na kan sai na musu gwanin ta kwana 2 nan mantawa da nake cewa auren temporary nake zai iya sallama ta at any time tunda yanzu mun bawa wata d'aya baya, saurin kawar da wannan tunanin nayi saboda yanzu na tsani in tuno da hakan a cikin raina.

Tunani na ya tsaya ne kan inyi musu abincin gargajiya maybe zasu fi son ci, ina da garin ndalayi da aka had'o min cikin gara ban tab'a amfani da shi ba,yau shi na d'auko na daura tukunya mai dan girma da ruwa dai-dai yanda nake so.

Kamin ruwan ya tafasa na gyara kayan miyana na daura miyan a gefe, miyar kubewa danya da yaji zallar naman rago sannan na tuka tuwo bayan na wadata ruwan daya tafasa da man gyad'a, sabuwar warmers da ban tab'a amfani da su ba na ciro na zuba abincin a ciki bayan nayi malmala masu kyau sannan na Kara bin man su da man shanu na rufe.

Ganin akwai sauran time yasa nayi samosa da meat 🥧 suma nayi package din su a wasu containers masu kyau, duk na jera su a cikin yalwataccen basket sannan na lullub'e saman da tumakasa mai kyau na fito da shi kan dinning sannan na wuce dan shiryawa.

Cikin atamfa super fari tas da adon flowers blue na shirya kaina na zauna na dan yi make-up dina sama-sama harda kashe d'auri duk da Ina jin ana kiraye-kirayen sallah magarib ban dakata ba saboda ina fashin sallah, jewelries da na saka duka pure gold ne hakan sai ya kara haskani nayi kyau sosai abina .

Sai da na gama kwalliya na sannan na tuna ashe ban ci abincin ba, fitowa nayi kitchen na zuba rabo na a plate shima na zuba mishi komai da nayi harda su snacks din dan a tunani na ba lalle bane yaci abincin gargajiyan da na girka.

Ina cikin cin abinci na naji motsin ya shigo Kuma na tabbata yana dinning yana kwasan gara sai dai shegen girman kan shi yasa ba zai tab'a admitting cewa yana ci ba sai dai yace masu gadi yake bawa.

Muryan shi ne ya katse ni yana in fito mu tafi, sai da na kara shafe jikina da humra mai dad'in kamshi na yafa mayafi blue mai dan girma na saka takalmi flat shima blue da poss din sa wanda wayata ce kawai a ciki sannan na fito hannu na dayan d'auke da plate din da na gama cin abinci, a tsaye na same shi shima ya shirya cikin kananan kaya riga ash color da wandon jeans fari sol.

Ta gefen ido na kalli kan table din ga mamaki na tass ya cinye abincin ko tab'a su snacks din baiyi ba, fasa shiga kitchen din nayi na tsaya na tattara kan table din na wuce dasu Ina kallon shi ta gefen ido dariya na cina ganin yanda ya wani tsare gida wai shi ala dole ba shine yaci ba.

Naso in tsaya in wanke plates da muka bata sai dai gudun masifan shi yasa na bari kan sai mun dawo, koda na fito shi har ya fice nima ban tsaya b'ata lokaci ba na d'auki basket da na jera abincin a ciki nabi bayan shi, a dan tsorace na isa ga motan da yake ciki duk da kasan zuciya ta cike yake da farincikin yau zan fita in ga gari dan tunda aka shigo dani cikin gidan nan ko bakin gate ban tab'a lekawa ba.

Koda na iso bakin motan sai nayi tsaye na rasa ya zanyi in shiga kada in shiga baya yace na maida shi driver sannan ina gudun shiga gaba yace na raina shi, shahada nayi na bude gidan gaban na shiga ganin ko inda nake bai kalla ba saima mayar da kan shi da yayi yana duba wani abu a cikin locker, sai da na zauna sannan na mayar da murfin na rufe tare da neman inda zan ajiye basket d'in.

Basket d'in hannu nawa yabi da kallo kaman zaiyi magana ko me ya tuna oho naga kuma ya mayar da kanshi gefe tare da jan motan muka fita a gidan ba tare da ya Kara kallo na ba.

Shiru cikin motan kaman babu mutane a ciki har muka iso wani tangamemen gida wanda ko ta waje kasan masu gidan sun jiku da naira, horn d'aya kawai yayi sai ga mai gadi ya taho da gudu ya zuge mana gate muka kutsa kai cikin hadadden gidan, baki sake nake bin gidan da kallo ashe da gaskiyan shi da yake cewa kada na mishi kyauyanci.

Talle min baki dana sake yayi da yatsa yana harara ta yace" wato baki yarda da abinda na gaya miki ba ko?" Yace yana jefa min mugun kallo, b'ata fuska nayi ina shafa baki na dan ba karya naji zafi sosai.

Bai bi ta kaina ba saima bud'e motan da yayi ya fita abin shi, shiri na saita natsuwa ta na bud'e murfin motan nabi bayan shi ganin yana son bace min, tun kamin mu karasa ma'aikatan gidan nasu suke ta durkusawa har kasa suna kawo mana gaisuwa amma maimakon ya tsaya ya amsa gaisuwan cikin mutunci sai dai kawai inga ya daga musu hannu ya wuce abinshi a zuciya ta nace wato shi ko ina yake sai ya nuna wannan girman kan nashi.

Wata mata ce ta karaso gaba na cikin sauri zata karb'i basket din hannu na nace mata ta bar shi amma ta nace sai na bata,ni kuwa ganin zata kusan sa'a da Inna ta yasa naki sake mata, dago kan da zanyi naga ashe bai shiga ba ni yake jira wani mugun kallo ya watsa min mai kama da warning yasa na sake mata basket d'in babu shiri na karaso inda yake jira na.

Hannayen mu ya tsarke waje d'aya sannan yayi sallama muka shiga cikin parlorn ,ashe abin kallon na ciki banga komai ba, ban san yanda zan kwatanta muku ba amma gidan yafi gaban had'uwa da kyar na shanye kauyanci na wannan karon na daina kalle-kalle na kalli gaba na, a can tsakiyan parlour Abba ne da Mom zaune kan wani lallausan rug sun saka warmers a gaba da alamu abinci suke shirin ci muka zo.

Abba fuskar shi d'auke da fara'a ta musamman yake amsa sallaman yayin da Mom Kuma baka gane yanayin da take ciki gata nan dai fuskan nan nata ba yabo ba fallasa, sau d'aya kawai na dago daga nan ban kara gigin d'agawa ba saboda kunya duk ya gama lullub'e ni yanda muka shigo hannun mu sarke nayi ta kiciniyan kwacewa amma bai bani daman hakan ba.

Kusa da Mom matan nan ta duka har kasa ta ajiye basket din sannan ta fice, sai da muka zo tsakiyan parlorn sannan ya sake min hannu ya karasa kusa da Abban shi ya zauna yana zuba musu shagwaba kaman karamin yaro suna biye mishi.

Ni dai daga dan nesa dasu na tsugunna Kai na a kasa na fara gaishe su, cike da kulawa Abba ya amsa yana in karaso kusa Mom in zauna mana ya zan zauna a nesa sai kace wata bakuwa,cike da jin nauyin su na matso na zauna ina Kara gaishe ta ganin bata wani amsa min ba.

Sama-sama ta amsa min tana kokarin fara serving din mijin ta amma sai ya dakatar da ita yana mai cewa " dakata mana da zuba abincin nan, ga surkuwar mu ta kawo mana kayan dad'i shi ya kamata muci yau ki maida naki gefe sai wata rana" ya karasa suna dariya shida Zafar ni dai murmushi kawai nayi na kasa dago da kai.

Yake kawai Mum tayi tare da maida warmers din ta rufe zuciyar ta na kuna ta yaya zata kwashi lokaci tayi mishi girki amma wai dan yaga nawa yace ba zai ci ba, bata musa shi ba ta jawo basket din ta fara cire warmers da suke ciki , tana bud'ewa kuwa kamshi duk ya cika parlorn na girkin dana man shanu.

Ranta duk babu dad'i haka ta zuba mishi abincin ta ajiye a gaban shi tana shirin rufe su yace mata " ya zaki rufe baki diba ba?"

" Zan diba ba rufewa nake ba" ta bashi amsa ta jawo plate gaban ta ta zuba malmala kwaya d'aya tak ta zuba miya kaman bata so ko mai kyankyamin abincin ta kai baki a ba zata sai da ta lumshe ido, dan abincin yayi mata wani irin dad'i domin batayi tsammanin zata ji abincin haka a tunanin ta tunda ni 'yar talakawa ce ban iya komai ba.

Zafar da yake kallon duk drama dake faruwa ya saki murmushi domin shi shaida ne in ta girki ne bani da ta 2, Abba sai santi yake ta zubawa wai ya akayi na san yana son abincin gargajiya, ashe wai dole su daina ganin Zafar wajan neman abinci a gida bayan cika baki da yayi ta musu a baya ko mata 4 be dashi abincin Mom d'in shi kad'ai zai ci.

Mom tana ji bata ce uffan ba koda suka gama Abba cewa a ajiye mishi snacks din nashi ne shi kad'ai, Mom sai tabe baki take tare da jin haushi Abba yana tsinka su a gaban wannan jinjirar yana abu kaman bai tab'a cin abinci mai dadi ba, ni kuwa duk farincikin ya lullube ni ganin yanda Abba yake ta yabon girki na dan ni nayi ne kawai banyi zaton zasu ci ba balle in samu irin wannan yabon.

Tattare kayan Mom ta fara Nima nayi saurin mikewa dan in taimaka mata amma cikin tsare gida tace in bar su, duk sai naji jiki na yayi wani irin sanyi na kasa komawa in zaunan, muryan Abba naji yana min magana yace " zo nan ki zauna daughter akwai hirar mu ta musamman dake" ya karasa yana nuna min gefen sa da hannu.

Da kyar na ja kafafu na zauna a inda ya nuna min yayi kasa da murya yace " kyale uwar nan taku haka take bata son in tana aikin mijin ta wani ya saka hannu wai ladan ta zai ragu shiyasa bata barin masu aiki suyi sai ita da kan ta" ban san lokacin da murmushi ya kwace min ba dan salon da yayi maganan dole ne yasa mutum dariya.

Zafar dake d'ayan gefen shima dariyan yayi dan ko shi baiji dad'in abinda Mom din nashi tayi ba amma yanzu daya ga Abba yana min barkwanci sai yaji hankalin shi ya kwanta kuma yaji dadi har cikin ran shi.

Wani envelope mai dan girma da yake kan kujeran bayan shi ya d'auko ya miko min yace " ga wannan tukuici ne daga gare ni kan yanda kika bada gudumawa wannan stubborned son nawa ya koma gentle boy".

Kasa karb'a nayi sai bin foldern nake da ido ina imagining what could be inside? Zafaar da yake sauraron mu ya b'ata fuska cikin shagwaba yace" Abba pls mana".

"Kwarai hakane my daughter ki karb'a Mana" yace ganin na kasa karb'a, hannu na rawa na saka na amsa tare da cewa " nagode Abba Allah ya kara girma da daukaka" Ameen my daughter" ya amsa min cikin jin dad'in addu'an da nayi mishi.

Muna cikin haka Mom ta dawo ta zauna hankalin ta da imanin ta duk suna kan abinda ke hannu na wondering ya akayi yazo hannu na, ganin irin kallon da take min yasa Abba ya maimaita mata abinda ya faru tare da ce mata " saura kema ya kamata ki kawo taki gudumawar"

Dama ance in talaka ya rabe ka in ba kayi sa'a ba toh kaima sai ka talauce, if not ya zaayî ya d'auko takardun company shi na buga ledodi dugurungum ya bada kyautan shi ma yar mitsitsiyar yarinya? Duk a cikin zuciyar ta take wannan maganan amma a zahiri kuma sai ta kirkiro murmushi tace" lalle Alhaji kana ji da wannan surkuwar tamu sai dai ai ko ni ban kara komai ba nakan ma ya wadatar kyautan company fa ai ya wuce wasa" ta karasa zuciyar ta na suya.

"Company? Ni Zareefa aka bawa kyautan company?" Na tambayi kaina da kaina hawaye na kokarin zubo min amma na shanye ina kara kasa da kai.

" Ga complimentary card dina daughter duk private numbers dina suna jiki a duk lokacin da yayi miki ba daidai ba ko kina bukatan wani abu kada kiji nauyi ki Kira ni Kai tsaye ki fad'a min kinji ko?"

Yanzu Kam sai da hawayen yayi nasaran zubo min nayi saurin saka gefen gyale na goge na saka hannu na amsa kamin in samu bakin magana naji muryan Mom da ta kasa hakuri tace " kaima dai Alhaji sai kace kaga wani alamun rashin zaman lafiya a tare dasu ko Kuma wacce bata da iya..."

Wani kallon ki shiga hankalin ki da Abba yayi mata yasa ta had'iye sauran zancen nata tare da kawar da kai gefe, saida ya maye fuskar shi da murmushi sannan yace " ta riga da ta shigo wannan family dan haka muma iyayen tane ko kin manta ita zata haifo mana magajin gidan nan a gaba?"

A razane take kallon Abban Jin wannan furucin da yayi me yake nufi kenan, duk shekarun da ta b'ata tare da shi ya tashi a tutan babu? Lallai ko sai ta kara tsayawa da kafafun ta ko ayi mata tsakiyar da ba ruwa. Amma a zahiri sai ta gyara fuskarta da nemo aron murmushi da ya tsaya mata a iya leb'e tace " hakane Alhaji Allah ya kara bud'i".

Gaba d'ayan su suka amsa da "Ameen " daga nan Abba da Zafar ne kad'ai suka cigaba da hiran su game da business daya yake taya shi a gida ,zuwa kusan karfe 10 Zafar yace zamu tafi Abba yana ta saka mana albarka ita kuma Mom cewa kawai mu gaida da gida.

Ga mamaki na har muka shiga mota bai kara hantara ta ba saima murmushi da yake ta faman sakewa shi kad'ai yana tukin sa cikin kwanciyar hankali ni kuma zuciya ta tana wani waje daban Ina rike da complementary card din Abba ina ayyana abubuwa da yawa a raina.
[6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*INNALILLAHI Wa INNA ILAIHI RAJI'UN
Muna taya 'yar uwar mu PRINCESS FATIMA MAZADU na babban rashi da tayi wato yayan ta HRH. ALH ABUBAKAR MUHAMMAD KWAIRANGA ( SARKIN FUNAKAYE) UBANGIJI ALLAH ya jikan shi da rahama yasa mutuwa hutu ce a gare shi AMEEEN*


✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.


*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.



Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.



*Bismillahir Rahmanir Raheem*



*41&42*


Bakomai ne yake raina ba sai yanda zan rama zalunci da yayi min, domin na yarda da maganan Yesmin da take fada min na cewa yana matukar tsoron Abban shi saboda nima gauce yanzu ba jiyau ba, ya wani natsu sai abubuwan mutanen kirki yake alhali kuwa mugu ne na bugawa a jarida.

Har muka karaso gida ko ci kan ki bai kara ce min ba nima na share shi na wuce d'aki na, kayan jiki na na fara ragewa sannan na shiga na watsa ruwa na fito nayi shirin bacci na kwanta amma sai na kasa samun baccin, tunanin wannan company da Abba ya bani shi ya fad'o min a rai toh ni ya zanyi da companyn nan? kawai bari in bari in an kwana 2 sai in fad'awa Inna inji me zata ce.

Lumshe ido nayi da niyyan bacci haka kawai Yaya na ya fad'o min a rai, ko a wni hali yake ciki, ko meyasa ya guje ni??

Tunanin hakan da nayi yasa na fara hawaye sosai harda shasshek'a dan ji nayi abin ya dawo min sabo fil zuciya ta sai kuna yake, duk halin da nake ciki a yanzu shine sila da bai guje ni ba da wannan mugun ko kallo na ba zai samu daman yi ba balle har in shigo gidan shi.


A wannan dare da kyar na samu bacci ya d'auke ni mai cike da mafarkai kala-kala.

Ko dana farka da safiyan nan sai naji duk raina a cunkushe yake fuskata babu walwala sam, iya d'aki da parlor na kawai na share nayi kwaciya ta ko kitchen banida niyyan lekawa balle inyi batun girki.

Zuwa kaman karfe 10 naji yunwa na neman hallaka ni dole yasa na fito main parlour na had'a tea mai kauri akan dining na d'auki mug d'ina da niyyan komawa d'aki naga mutum a zaune yana waya ko kallon inda yake banyi ba nayi wucewa ta na bar shi baki bud'e cike da mamakin abinda nayi yake bi na da kallo har na shige.

"Toh wai me ya hau kan yarinyan nan yau? Zaman da nayi anan ya kusa 1 hr ina jiran inga ta girka wani abu in samu inyi breakfast in fita shine taki yin komai saima tea da ta had'a ta wuce ko gaishe ni batayi ba, ko dai ta gane bana iya cin abincin kowa yanzu sai nata?" Zafar kenan shi kad'ai yana sumbatun sa a cikin ran shi.

Zuruf ya mike yana cewa naga kwana 2 yana d'an sake min shiyasa na fara kawo mishi raini bari ya shiga ya gyara min zama, yana maganan ne tare da nufan d'aki na.

Hankali kwance nake sipping tea na naga mutum ya shigo min babu sallama sai wani had'a fuska yake wai shi ala
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment