Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zasu kawo DJ tun shekaran jiya suke zancen Ina ga shi d'in ne suka kawo" Dije ta bani amsa.



"Taso muje mu gani...taso muje" cewar Dije tana jan hannun na .



Muna zuwa kofar gida muka ga Amarya da kawayen ta suna ta rawa, jan hannu na Dije ta fara wai muma mu shiga nace mata ta shiga ina zuwa.



Ina daga gefe ina kallo kawai naga mutane sun rufu a kai na suna min liki, maza da mata amma mazan sun fi yawa na rasa ta ina ma suka zo dan ni dai ban san su ba.



Neman shiga gida nake amma sun tare ko Ina ba hanyan wucewa daga cikin matan naji wata tana ", ke Hindu ki zo ga Amarya nan kiyi mata liki"



Da mamaki na d'ago na kalle ta na ce", ni fa kanwar Amaryar ce ga Amaryan can" na karasa ina nuna musu inda Hajara da kawayen ta sukayi sororo suna kallon mu.



"Eh ga Amaryar can wannan kanwar ta ce " wata kanwar Gwaggo Aisha ta fad'a tana harara ta.



Jiki a tsabule suka juya ga Amaryan su suna kallon ta har taji ta muzan ta, ni dai ban san ya suka kare ba na shige cikin gida na bar su.





Da daddare bayan an kai Amarya gidan ta Dije tazo d'akin mu a lokacin ina kwance ina chatting da Yaya na.



"Zo...zo...zo muje ki sha labari zo muje" ta ce tana jan hannu na ina ta tsaya in ajiye waya amma ina haka taja ni muka tafi bangaren su.



"Mijin Hajara da ake cewa mai kud'i ne ashe karya ne,kin ga gidan nata gidan yawa mutane sun fi shida a ciki ga d'akin nata ya yiwa kayan ta kad'an ke abun b dad'in gani wallahi.


Ina matar da ta zo tace ita 'yar uwar sa ce tayi magana a kan an fasa dinner ashe gidan haya ce ta had'a su".


*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*
[10/10, 7:42 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._



_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_


_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*


*_BA SONTA NAKE BA_*



*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*πŸ–Š
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ πŸ–Š *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*


*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*


_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. πŸ‘‡


https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp


_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu._


*12*



Bangane ba Hajara me kike nufi wai?" Na tambayi Hajara cike da rud'u.


Kamo hannu na tayi muka zauna a bakin k'ofar d'akin su sannan ta fara magana," hmmmm duk abinda Alhaji Khalid mai gidan gona ya fad'a a gidan nan ashe zuki ta malle ne sunan shi haladu kuma sana'ar sa kuma bawa dabbobi abinci a gidan gonan Alhaji Mukhtar dake Sabon layi".



Samun kaina nayi da matukar jin haushin sa sannan ga tausayin 'yar uwata daya rufe ni lokaci guda,cikin wani irin yanayi nace", amma Allah ya isan Hajara makaryaci kawai in bashi da kud'in menene amfanin shirga mata wannan karyan? Allah sarki Hajara ko wani halin take ciki yanzu?"



"Lalle Zareefa kin bani mamaki meye naki na wani zakewa haka, wallahi kada ma kiji tausayin ta ita ta jawowa kan ta ko ince su suka jawo dan harda uwar ta su ala dole dake zasu yi gasa, chab ni wallahi ko kad'an bata bani tausayi ba hasali ma dariya ta nayi ta sha, a mota ina ta tunanin yanda Gwaggo Aisha zatayi in taji wanga batu" ta karasa cikin shekiyanci tana dariya.



Girgiza kai na nayi hawaye na taruwa a ido na, na ce mata," Dije kenan taya ba zan tausaya mata ba ko kin manta cewa 'yar uwata ce jini d'aya yake yawo a cikin jikin mu"



"Na sani mana amma ba kya ganin yanda suka saka ki a gaba su da iyayen su sun hana ki sakat ke da mahaifiyar ki tun muna kanana har zuwa girman mu"



"Koma menene Dije su d'in 'yan uwa na ne, jini d'aya yake yawo a jikin mu daurewa kawai nake ina share su amma ina kaunar su har cikin raina ina kuma sha'awa in ga mun had'a kan mu kaman sauran 'yan uwa"



Hawayen da ya zubo min na share na mike na kama hanyan bangaren mu itama Dije ko motsi kasawa tayi dan maganganu na sun kashe mata jiki,ko da na shiga d'akin mu na samu Inna zaune gefen gado ta rafka tagumi da alamu itama taji zancen kenan.



"Tun d'azu ake kiran wayan ki" ta ce min ba tare da ta sauke tagumin ba saboda wannan al'amari ya bata mamaki da tsoro samarin yanzu mayaudara ne kuma macuta ne, in banda cuta kazo da wata siffa da suna dan a baka mata me yasa ba zai zo a yanda yake ba? Ko da yake Maman Dije ta ce wai sun riga sun nunawa duniya cewa in ba mai kud'i ba akai kasuwa shine yasa shi zuwa da wannan siffa.



Ajiyar zuciya ta sauke wanda sai da na juya na kalle ta dama rply na tex nake rubutawa 'yar ajin mu a islamiya ta kira bana kusa shine ta min tex tana min tuni kan abubuwa da muka shirya na walimar mu.


"Inna lafiya kuwa na gan ki haka?" Na tambaya.



"Hmmmm ba komai je ki wanke min hijabi na da da yake cikin bukiti a waje" da toh na amsa na fita wankin.


Ina fara wankin naga Gwaggo Aisha sun shigo da kannen ta 2 duk sunyi wujiga-wujiga ko kallon inda nake ba suyi ba suka wuce, a zuciya ta na ce," chab Gwaggo Aisha ana cikin tashin hankali tunda bata harare ni ko ta tsaya ta zage ni ba, lalle yau tana cikin matsala, d'aki suka shige suna neman mafita.



Har gari ya waye ba'a cimma abu d'aya ba sai shige da fice suke, sun samu Baban mu da maganan yace toh me zai mata, ta riga da ta fita a hannun sa lafiya dan haka sauran ya rage musu ita da mijin ta.



Gwaggo Aisha takaici ya hana ta sauran sauran bayanin nashi tayi ficewar ta, ta rasa ina zata kai kukan ta a share mata hawaye, babban burin ta shine a raba auren domin jiya da daddare ita da kannen ta daga gidan Hajaran suke suka ja mata kunnen kada ta yarda ta bashi kan ta duk rintsi duk wuya dan gobe-goben za'a raba auren nasu sai gashi har sha biyu ta kusa babu alamun nasara ko kad'an.




Gwaggo Aisha bata gama shiga tashin hankali ba sai da d'ayan kanwar ta da ta tura gidan Hajara dan a dubo mata lafiyr ta ta dawo da mummunan labarin cewa Haladu yayi nasaran kusantan Hajara jina-jina suka same ta abun babu kyan gani ko taimaka mata bai tsaya ba ya tsallake ta yayi tafiyar shi.




"Yanzu fisabillilahi duk fad'an da muka yi mata sai da ta sakewa wannan mayaudarin jiki ya gama da ita?" Gwaggo Aisha ke tambaya tana goge hawaye da gefe zanin ta.


"Ba laifin ta ba ne shi mijin ne tantiri, ta bamu labarin komai cewa da ta fara mishi taurin kai shine d'aure ta a jikin gado yayi abinda ya ga dama da ita wai bata isa ta hana shi more kud'in sa ba" 'yar uwar ta ta bata amsa.




"Amma wannan yaro anyi tsinanne Allah ya isa tsakani da shi, ina zan shiga da wannan abin kunyan, kayyah " yanzu kam kuka Gwaggo Aisha take tsakani da Allah tana tunanin tayaya zata kalli idon 'yan gidan bayan duk abubuwa da tayi musu wai ita 'yar ta zata auri mai mota.



"Mama kada ki tada hankalin ki domin nayi miki alkawarin saka ki farinciki, ba zan tab'a kula kowa ba kuma ba zan auri talaka ba sai mai kud'i" Jamila ke fad'an haka da take sauraron su tun d'azu ba tare da sun sani ba,d UK kallon juna suka tsaya yi babu wanda ya iya bata amsa sai dai ita Gwaggo Aisha ido ta zuba mata tana nazari tare da hasko yiwuwa da nasara a cikin abinda ta fad'a domin Jameela tafi Hajara kyau da tsarin jiki nesa ba kusa ba.



Haka akayi wannan wunin a tsaye babu wanda ya lek'a gidan Amarya wasu ma saboda bakinciki a ranan suka koma inda suka fito shiyasa gidan namu ya zama shiru kaman ba biki ake ba.



Bayan kwana 2 da bikin Hajara Yaya na yazo da rana bayan azahar cikin kananan kaya wandon kaman na sojoji sai bakin t shirt da bakin glass sosai yayi kyau, muna hira a kofar gidan mu yana tambaya ta me da me nake bukata a walimar saukar mu? Ni kuma ina ce mishi bana bukatan komai duk abinda ake bukata mun gama shirya su.



A wannan lokacin ashe Baba yana gida ya dawo saboda wata bukatar shi lokacin da yazo Yaya na bai zo ba yana ciki ya zo dan haka bai san da zuwan shi ba,yana d'aki Gwaggo Aisha tabi shi tana magiya akan yayi wani abu akan al'amarin Hajara a raba auren domin muddin tana raye ba zata tab'a barin auran nan ya dad'e ba.



Bata san duk haushi ya cika shi ba tazo ta ishe shi da surutu alhalin shi in ya tuna tsoro ya hana shi gaisawa da Yaya na da yanzu yana cikin kud'i yanzu gashi bashi da kud'i a hannu, tsaki yaja yana bin ta da mugun kallo ya ce," ke Aisha wai wace irin mace ce ke da zaran kin ga mutum ya shigo gida sai ki bi shi da korafin ki na banza da na wofi yarinya tana gidan mijin ta shine kike neman wai ni uban ta inje in fito da ita wannan wani irin rashin kan gado ne, toh ba dani ba wallahi kije can ki gama haukan ki kada ki kara tunkara ta da wannan iya shegen ko kuma ranki yayi mugun b'aci". Yana gama maganan shi ya mike a fusace zai fita ya juyo ya ce," ba sai kin kara gani na a gidan ba balle ki zo ki takura ni"



Fita yayi rai a b'ace yana ta masifa shi yasa kai zai fita da sauri ya koma baya yana tunanin anya idon shi dai-dai ya nuna mishi kuwa?



Kara lek'a kan shi waje yayi yaga dai da gaske ne Yaya na ya gani fuska a murtuke wai shi ala dole yayi fushi me yasa ban fad'a mishi maganan saukar namu ya d'auki nauyin komai na ba nayi da kai na.



"Innalillahi wa inna ilahi rajiun wai shi wannan yaro banda bala'i irin nasu na sojoji meya kawo shi da rana tsaka yana muzurai sai kace anyi mishi dole" Baba ke fad'in haka bayan ya koma cikin zaure ya manne da bango wai duk dan kada Yaya na ya gan shi.



Da kyar na shawo kan sa ya daina fushin muka ci gaba da hiran mu cikin annashuwa da shaukin soyayya, abinda bamu sani ba ashe Baba yana nan mak'ale a zaure yana jiran tafiyan Yaya na ya samu shima ya tafi majalisa, yaki komawa cikin gida kuma saboda rigimar su da Gwaggo Aisha kada taga ya koma ta mishi dariya.



A takaice mun kai good 1 hour sannan mukayi sallama ya wuce ni kuma na shigo gida cikin farinciki hannu na d'auke da sayayyar da yayi min.



Ina shigowa zaure saura kad'an in zubar da kayan hannu na saboda firgita ganin mutum manne a jikin bango yana goge zufa, sai da na tabbatar Baban mu ne sannan na samu natsuwa amma kuma mamaki da tambaya fal cikin zuciya ta me kuma yau Baba yake a nan ?



Hanyan fita ya nufa yana masifa kallon inda nake bai yi ba hakan ko ya kara saka ni cikin konkonto, a yanda nasan Baba da son dad'i amma yau ko kulanin baiyi ba bayan ga shopping bags a hannu na, juyawa nayi da niyyan shiga gida naji muryan Baban mu yana," wallahi Allah yau yaron nan ya cuce ni, in banda ina gudun abin kunya cikin anguwa kada a ce ga Mallam Hassan can yana fad'a da sirikin sa ba Allah da na nuna mishi ko ni waye, Aikin banza wa zai yiwa barazana har kofar gida har da wani sako kayan sojoji toh sai me...?"




Dariya na tintsire da shi har da dukawa sai yanzu na gane me Baba yake a zaure, da kyar na tashi na kwashi kayana zuwa cikin gida.




Bayan kwana 2 akayi bikin saukar mu a islamiyar mu wanda ya tara duban jama'a ciki kuwa har da Yaya na sai dangin Inna a 'yan gidan mu Inna Asabe ce kad'ai ta tafi dan Gwaggo Aisha cewa tayi karatun karuwanci dama nake shine yau kuma za'a je party toh ba da ita ba.



Bajintar da Yaya na yayi ba a cewa komai kayan rabo kala-kala ya kawo aka raba harda na malamai suma nasu daban ga gifts nima daya kwaso min ba zasu lissafi ba duk da haka cewa yake komai ya min gani yake bai yi ba saboda sauke Al' Qurani mai girma ba abin wasa bane.



A islamiyar ma na samu kyauta daban-daban saboda hazaka ta daga karshe taro ya watse bayan mun sha pics saboda tarihi.





*************************



Wato ka mai da ni mutuniyar banza a gidan nan saboda ban isa in fada kaji ba ko, fisabillilahi ka kyauwa kan ka kenan?"cewar wata 'yar dattijuwa mai kamala da kyau da haiba wacce ba zata haura shekaru hamsin ba.


Wani kyakkyawan saurayi ne zaune a gaban ta shi take takewa fad'a amma shiru yayi kan shi a kasa yana kallon lallausan rug da yake malale a katafaren parlour nasu wanda kallo daya zaka mishi ka kira shi da aljannan duniya domin babu ne kawai babu a ciki, just ku hasaso shi a cikin zuciyar ku domin in nace zan tsaya zayyano muku tsari da kyan gidan sai mu kusan cika novel din bamu gama ba



Duk da kan shi a kasa yake bai hana ni hango dogon hancin sa ba ga sajen sa baki wuluk na lallausan gashin sa sun kewaye fuskar shi, gashin kan sa kuwa kaman na larabawa saboda laushi da tsantsi sai dai yayi mata wani aski wanda an kwashe daga gefe-gefe da keya sai tsakiya da ta gaba ne da gashi kana ganin gashin ka san ya sha gyara da kulawa wajan mai shi.



"Zafar... Wai ba da kai nake magana ba ka min shiru" wannan kyakkyawar dattijuwar ta fad'a cikin tsawa.



Wanda ta kira da Zafar ya d'ago kai masha Allah ashe da kan sa yake kasa ban ga komai ba sai yanzu.



Zafar fari tas irin farin nan mai yellow yana da dogon hanci wanda ya kawata kyakkyawan fuskan shi ga maidaicin bakin sa mai d'auke da jajayen lips sun kara fiddo ainihin kyan fuskar sa, idon sa kuma kaman mai jin bacci suke a takaice Zafar ya had'u iya had'uwa sai dai ya kasance d'an shan minti ne kasancewar shi d'a tilo ga multi millionaire.




A shagwab'e ya d'ago da kai yana d'an tale baki kaman d'an karamin yaro alhalin ya kai shekaru ashirin da takwas yana kallon mahaifiyar tashi da lumsassun idon shi da baturai sukewa lak'abi da sexy eyes ya ce," wai ya kuke so inyi ne Mom for god sake ni komai nayi kice bai yi ba, look at dis " yace yana nuna mata gashin kan sa sannan ya cigaba.



"Wats wrong with it nayi wancan kunce baiyi ba nayi wannan ma kice baiyi ba then which 1 do u want me to do?" Ya karasa yana watsa hannayen sa cikin iska.



Wacce ya kira da Mom ido kawai ta zuba mishi ta kasa cewa komai domin lamarin tilon dan nata ya fara bata tsoro a ce d'an da ka haifa shi zai rink'a mayar maka da magana haka, babu wanda yake shaka a gidan sai Abban shi, sanin haka yasa ta cewa," ok haka kace ko? Kaje kayi duk abinda kake so amma kafin ka fita inayi maka albishir da gobe Abban ka zai taso daga Portugal zuwa gida sai ka tanadi bayanin da zakayi mishi in ya ga askin naka".


A rikice ya dawo kusa da ita, da ya kai har tsakiyan parlour da niyyan komawa part d'in shi yana zuwa ya zauna a gaban ta tare da d'aura hannayen shi duka 2 kan guiwoyin ta ya ce," na san ko Abba ya dawo my sweet Mom zata kare ni kaman yanda ta saba ko Mommy naaaa just once daga wannan shikenan ba zan kara ba I promise shima wannan dan zamu yi bachelor's eve na Musaddiq ne shiyasa".




Murmushi tayi tana shafa gashin kan nashi ta ce," promise.. promise dai wanda ban san sau nawa aka yi min su ba remember jiya me kace?"



Dafe goshin sa yayi yana d'an tuno yanda yake mata in taki yi mishi abu, zai fara yi mata ta dakatar dashi tana," bana son wannan shagwab'an naka jeka let me think about it"



"Yesss.... dats my sweet Mom" yace yana d'an tsalle a gaban ta sannan ya fita da gudu yana dariya, itama dariyan take a zuciyar ta kuwa tana blaming kan ta da duk abinda Zafar yake itace sila domin a koda yaushe itace mai kare shi wajan Abban sa in yayi wani laifi, ita da kan ta bata jin dad'in abinda take wasu lokutan amma ya zata yi shine fa kad'ai kwan ta a duniya dan ma Allah ya tsare baya wasu mugayen dabi'un na 'yan zamani shi dai bar shi da zuwa parties da kula 'yan mata sai kuma son swagger.








*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[1/26, 7:04 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

*13*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*wΜΆΜΆΡ” Ξ±rΜΆΜΆΡ” Π²Ρ”Ξ±rΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆ'sΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ sΜΆΜΆΟƒ gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ*
*wΜΆΜΆΡ” wΜΆΜΆrΜΆΜΆΓ­tΜΆΜΆΡ” Ξ±sΜΆΜΆsΜΆΜΆΓ­dΜΆΜΆΓ­ΟƒuΜΆΜΆsΜΆΜΆlΜΆΜΆΡ‡ pΜΆΜΆΡ”rΜΆΜΆcΜΆΜΆΡ”Γ­vΜΆΜΆΡ” nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ,*
*sΜΆΜΆΟƒ mΜΆΜΆΞ±gΜΆΜΆΓ­cΜΆΜΆΞ±lΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ cΜΆΜΆrΜΆΜΆΡ”Ξ±tΜΆΜΆΓ­vΜΆΜΆΡ” gΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆΜΆ* ✍ *,Π²Ρ”hΜΆΜΆΟƒlΜΆΜΆdΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ.Ξ± pΜΆΜΆrΜΆΜΆΟƒdΜΆΜΆuΜΆΜΆcΜΆΜΆtΜΆΜΆ ΟƒfΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ pΜΆΜΆΡ”nΜΆ*ΜΆ *,sΜΆΜΆΞ±vΜΆΜΆΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ ΟƒuΜΆΜΆrΜΆΜΆ wΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆdΜΆΜΆsΜΆΜΆ, fΜΆΜΆΟƒrΜΆΜΆ Γ­tΜΆΜΆ wΜΆΜΆΓ­lΜΆΜΆlΜΆΜΆ* *cΜΆΜΆΞ±uΜΆΜΆsΜΆΜΆΡ” Ρ‡ΟƒuΜΆΜΆ nΜΆΜΆΟƒ pΜΆΜΆΞ±Γ­nΜΆΜΆ.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buΖ™ata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana Ζ™ara mana Ζ™arfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*13*

Yana fitowa daga parlourn Mommy shi fara'an fuskar sa ta d'auke lokaci daya dif kaman wutan NEPA sai ma wani shan kamshi da yake wanda ya kara fiddo da kyan sa, a nan na fahimci wato babu mai ganin wannan fara'ar tashi sai mahaifiyar sa.

Wani haΙ—aΙ—Ι—en madaidaicin flat house ne dake gefensa na mahaifan sa, ya nufa ko kula masu aiki da suke gaida shi baiyi ba ya shige abin sa.

"Dude ka san I have been waiting for you amma ka wani shanya ni, tun dazun su Sabeer suka dame ni da waya wai kowa ya hallara sai mu ake jira" cewar wani guy dake zaune kan sofa shima kana ganin shi kaga classic guy saidai ko rabin kyan Zafar bai kai ba.

Ko inda yake Zafar bai kalla ba ya wuce bedroom d'in sa da yaji royal bed fari kal,komai na d'akin farare ne hatta da curtains tsab'a parlour kuma komai na ciki royal blue ne, bai tsaya cikin bedroom d'in ba ya fad'a bathroom domin yin wanka.

Girgiza kai Sadiq yayi ganin Zafar yaki kula shi ya wuce ciki in da sabo yaci a ce ya saba kam duk da cikin abokan sa jinin su yafi had'uwa da Sadiq d'in kuma tare suka taso tun suna kanana har zuwa girman su babu abinda ya tab'a raba su ko a makaranta.

Baban Sadiq yana da wadata shima amma ko rabin kudin su Zafar bashi dashi, saboda aminitar dake tsakanin su 2 yasa iyayen su maza da mata kulla zumunci sannan Baban Zafar shi yake biya Sadiq kud'in makaranta ganin cewa shine farincikin d'an su.

Zafar yana da fara'a sosai da wasa da dariya amma fa sai ga Mommy sa dan ko shi Sadiq da suke tare shekara da shekaru bai cika ganin dariyar sa ba sai jifa-jifa wanda shima in mutum ya bibiya toh yaga abin mugunta ya sami shi Sadiq d'in anan zaki ga dariyar sa harda rike ciki.

Zafar yana da wani hali ko kuma ince buri, ya raina 'yan matan mu na gida kwata-kwata basa burge shi a cewar sa bai ga abin so ba a tare dasu ba, 'ya'yan masu kud'i da masu fad'a aji na cikin kasar nan babu wacce bata kawo mishi kokon barar soyayyar ta ba duk yayi watsi dasu dan ko kallo basu ishe shi ba,sai dai in zasu tafi party wanda sai da chick ake zuwa toh shine zai kula ki shima da ya fito shikenan amfanin ki ya kare amma hakan ma farinciki wacce ta samu wannan daman take ko ba komai ta samu na canza status kenan tana sham kamshi cikin kawayen ta.

Wannan halin nashi yasa mutane da yawa suke mishi kallon mai neman mata alhalin ba haka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On BA SONTA NAKE BA
avatar
maryam-4

1 year ago

Reply

How to download it

avatar
daiy

1 year ago

Reply

replying to @maryam-4 you must sign in in order to download

Please Login or Register in order to submit comment