Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

23/10/2021, 08:34 - Messages and calls are end-to-end encrypted. No one outside of this chat, not even WhatsApp, can read or listen to them. Tap to learn more.
23/10/2021, 08:35 - ๐Ÿ‘๐Ÿป๐Ÿ‘๐Ÿป: *ALKIBLA*
_(THE BATTLE OF LOVE)_

*_HUGUMA_*

01


*_Da sunan Allah mai rahama mai jin ฦ™ai_*


*dukkan godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki daya bamu aron rai da lafiya,tsira da aminci su qara tabbata ga shugabanmu annabi muhammad S A W*


*_littafin ALฦ˜IBLA,labari ne dana qirqeshi mafi rinjaye kan soyayya,saidai kuma hausawa sukance ba'a rasa nono a ruga,akwai wani sashe na matsalolin da mafi yawan 'yammata ke fuskanta a wannan zamanin game da samarinsu,wanda kusan basu san daga inda matsalar take ba_*

_a wannan karon ina neman afuwan masu karatu,littafin alqibla bazai kai yawan littafin siradin rayuwa ko alqawarin Allah,saidai ina fatan zai nishadantar ya kuma qayatar daku in sha Allah,ASHA KARATU LAFIYA_

*ALLAH YAYI RUQO DA HANNAYENMU๐Ÿ™๐Ÿฝ๐Ÿ™๐Ÿฝ๐Ÿ™๐Ÿฝ*

โ˜๐Ÿพโ˜๐Ÿพ *KIJI TSORON ALLAH,KARKI TABA KAYAN DABA NAKI BA*โ˜๐Ÿพโ˜๐Ÿพโ˜๐Ÿพ

____________________________



*GOVERNMENT GIRLS UNITY COLLAGE KACHAKO*



Makekiyar harabar makarantar 'yammatan ta kwana dake garin kachako wato government girls unity collage cike take da dandazon al'umma,wanda mafi akasarinsu dalibanta ne,da kuma wasu daga cikin iyayen yaran dake ta faman qoqari dakai kawon kwashe yaransu zuwa gidajensu don gabatar da hutun zangon karatu na uku wato third semester.


Daga can gefe daya na harabar makarantar kana iya hangen yadda matashiyar ke tsaye goye da hannayenta sanye cikin wankakku kuma gogaggun unifoarm da suka amsheta sosai,ta zubawa harabar makarantar tasu idanu,kamar wadda aka baiwa aikin qididdige yawan al'ummar dake karakaina a wajen,kyakkyawar fuskarta babu alamun fara'a ko kadan.


Duk da cewa duka duka shekarunta ba zasu haura goma sha biyar ba,amma kana iya tantance kyan zubi diri gami da siffa da Allah ya bata.


Mai matsakaicin tsaho ce,ma'abociyar doguwar fuska da fata wadda bata cika haske ko duhu ba,ta yadda ba zaka iya kiranta da baqa ba,hakanan ba zaka kirata fara kai tsaye ba,tana da manyan idanu wanda ba'a fiya gane girmansu ba idan ba budesu tayi sosai ba duk sadda taso hakan,daga cikar girarta kawai zai gaya maka tana da yalwar gashin kai,Allah ya yi mata ado da dimple guda biyu a kumatunta hagu da dama,wadanda sukan bayyana duk sanda ta bude baki da niyyar magana,walau tayin ko bata yi ba.


Sake gyara tsaiwarta tayi idanunta na tara ruwan hawaye,duk da basu kai ga xuba ba amma duba daya zakayi mata ka gane hakan,iya damuwa ta damu ta kuma matsu,burinta kawai ta ganta a gida,Tana da burin son ganin mutane a rayuwarta da suke da gurbi na musamman a zuciyarta,duk da cewa ta rasa babban bango kuma jigo a rayuwarta,amma duk da haka bata rasa wasu daka iya xama makwafinsa ba bawai madadi ba.


Abinda ya qara mata zaquwa da son ficewa daga makarantar tunda wurwuri kamar sauran dalibai shine,komawar 'yar uwa kuma qawa a wajenta gida tun lokacin yin hutu da fitar dalibai baiyi ba,sakamakon lalura data sameta,wadda ta tilasta aka maidata gida,banda haka,bata da wata damuwa mai yawa kan jimawar tata.


"Fatima sa'id dabo,fatima sa'id dabo" daga bayanta taji ana kwarara kiran sunanta,a nutse ta waiwaya tana duban mai kiran nata,daya daga cikin 'yan ajinsu ce ladifa hamza,ci gaba tayi da dubanta har ta iso dab da ita
"Anzo daukarki,tun dazu 'yan gidanku ke nemanki" da mamaki ta maida dubanta farfajiyar da take tsayen sannan ta dawo da dubanta kan ladifa,tayi tsammanin inda ta tsaya din zata iya ganin shigowar motar da tazo daukar nata,bata tanka ba saita fara takawa kawai don barin wajen,ladifa ta rufa mata baya tana tsokanarta kan rashin kuzarinta,da yadda ta zama wani sukuku kamar ba ita ba tun tafiyar munira gida ta barta.


Tunga taja ta tsaya lokacin data kusa isa dab da motar da akace tazo daukarta din,mamaki bayyane qarara a fuskarta,wannan ba daya daga cikin motocin gidansu bane,duk wani ahali na gidansu yasan wannan motar waye,ya kuma san da zaman motar,yaushe yazo?,ya akayi ya yarda ya bada motar a daukota?,shine da kanshi?,saita girgiza kanta da sauri,bashi bane,don ko a mafarki tasan bazai taba zuwa daukar wani daga cikinsu ba.


Murfin motar da aka bude yasa ta maida hankalinta sosai ga motar,wani matashin saurayi ne ya fito,wanda dukka a qalla shekarun haihuwarsa ba zasu rufa ashirin da biyar zuwa da shida ba
"Ko baki shirya komawa gidan bane?" Ya dan daga murya yana fadi idanunsa a kanta,hakanan fuskarsa babu yabo ba fallasa,kai ta kada tana son tambayarsa da yaren kurame kan shi da waye sukazo?,saidai bata kai ga tambayar ba murfin sit din baya ya bude shima,wata matashiyar ta sake fitowa,wadda a qiyasce suna iya yin shekaru daya da ita,fuskarta washe da fara'a tana duban zahra dake tsaye.


"Suprise ko?" Matashiyar ta fada cikin sautin qyalqyala dariya,ba tare data shirya ba itama qaramar dariya mai qaramin sauti ya kubce mata,wadda hakan ya baiwa dimple din dake kumatunta damar bayyana,sa'annan kamar wadda aka qarawa qaimi ta doshi motar,tunda taga hafsat cikin motar ta tabbatar ba abinda take zargi bane
"Wallahi kun shammaceni,na farko na zaci daga gidan abban gwammaja za'azo daukana shi yasa na zauna jiran motar gidan,na biyu kuma saina ganku anan,ya akayi haka...?" Cikin dariya hafsat tace
"Shigo daga ciki kisha labari....dama naci alwashin koda gold akayi motar nan saina shigeta ai"
"Mayya....saida kika shiga din kuwa" zahra ta fada tana dariya
"Sarakan surutu...zaki kama mata sauran kayan ku shige mu tafi ko kuwa har sai lokacin da ya diba mana ya cika bamu koma ba?" Cewar daya matashin saurayin dake a mazaunin driver,cikin shadda dinkin zamani.


Leqensa zahra tayi ta window,saita fashe da dariya tana cewa
"Wai,congratumatur ya musty.....yaudai an dana,kaga ko yadda motar tama kyau kamar taka?,anya ba zakayi ratse ba kaje kadanyi shawagi ka dawo ba?" Murmushi mai kama da dariya shima ya saki yana cewa
"Bari kawai.....don dai kawai nasan yana sane da lokacin daya bamu ne,wallahi yau da sai na tsatse motar nan son raina...ke kinga yadda 'yammatan makarantar nan ke wani kallona....."
"Basusan duk bige bane baba" zahra ta fada tana qyalqyalewa da dariya gamida shigewa gidan baya,ya soma qoqarin tada motar bayan duk sun rufe murafun yana cewa
"Aina miki dare xakimin rana,tunda na kankaroki nazo daukarki a wannan dalleliyar motar ba"langabar dakai tayi ta koma kalar tausayi
"Haba ya musti,ni dakai fa bata baci,kada kasa 'yan uba suyi mana dariya"
"Dariya kuma ta nawa?" Wancan saurayin dake daya site din ya fada yana sake kwanciya sosai jikin kujerar motar
"Kaji ko?" Zahra ta fada tana bata fuska
"Rabu dashi,duka adawa ce,ba wanda zai ganmu a rana" mustapha ya fada yana harar shamsu dake gefansa zaune,wanda bai sake tankawa ba ya yamutsa fuska kawai gami da cewa
"Oho dai,maji ma gani".


Kusan wannan 'yar tsamar ba wani sabon abu bane a wajensu,sun riga da sun saba da hakan,wanda ba komai bane ya kawo haka ba face fahimtar juna da sabo dake tsakaninsu,duk da cewa akwai banbancin iyaye,duka sun fito daga mahaifa daban daban.


Saida suka hau titi sosai sannan ta gyara xama tana duban hafsat
"Wai ya akayi ne haka?" Dariya hafsat tayi kafin tace
"Wallahi ya hajja ce tace ya bada a daukoki,da yaqi ma tace to bari ta kira mas'udu ya bada tashi tunda shi ta isa dashi,to sai da yaji haka sannan ya bayar......zahra ma tana kusa sai data saka baki" tabe baki zahra tayi tana juyar da kanta xuwa window,tadan dubi titi kadan sannan ta dawo da dubanta ga hafsat
"Sai kace xai mani gafara motarma sai an roqeshi,ni wallahi ya hajja data sani bata roqa ba.....bama wannan ba,na dawo hutu da farinciki da burin samun sake,musha soyayyarmu nida hafiz,zuwansa nasan komai saiya rushe wallahi,babu wani sauran sake,bayan shi har gida ake biyoshi,ya kuma baje kolin soyayyarshi babu jin kunyar kowa,amma mu ya hanamu katabus babu gaira babu dalili,bayan yafi kowa sanin tsarin gidan,yanzu daka yi candy za'a zuba maka idanu ka kawo wanda zaka aura,idan babu ya zama jarraba,yanzun kuma kana tsaiwa dasu shiya hana ruwa gudu,haba" ta qarashe masifar dajan tsaki,dariya hafsat keyi abinta tana qarawa,kafin tace komai shamsu ya waiwayo yana dubanta
"Ke yarinyar nan da gaskene fa zaki qone tun kafin ki tafasa" hararar wasa ta jefa masa
"Saimu zauna ai ku jiqamu kusha,kunfi kowa daga murya idan bamu tsaida miji ba...."
"Meye a ciki,sadaka kawai zamu bada ku a masallacin malam ayuba" ya fada cikin shaqiyanci yana qyalqyalewa da dariya,wanda ya saka mustapha ya dara shima,baki ta tsuke ita kuwa kana tace
"Allah ya kiyaye ya sawwaqe,wuce nan wallahi".


Da ire iren wadan nan hirarrakin suka ci gaba da tafiya cikin motar,tana tambayar hafsat wasu abubuwa da bata nan akayi,da kuma wadanda ta tafi ta bari,shamsu dai bai gaji da tsokanarta ba ya sake cewa
"Sai tambaya kamar makahon daya warke daga makanta,kamar wadda aka sallamo daga gidan yari" fuska ta narke wanda da alamu lokaci zuwa lokaci tana da dabi'ar shagwaba wanda batasan ita kanta tana dashi ba,kusan a jininta abun yake
"To ya shamsu don Allah meye maraba,kowa an barshi yana jeka ka dawo amma ni an turani boarding saboda shawarar da wannan mutumin ya bada,kuma wai aka amince masa"
"To ya za'ayi sai haquri,kinsan shi,idan ya kafe akan abu,amma kuma da wuya idan ya kafe din a kasa ganin alfanun hakan" baki ta zumburo tana mita
"Kaidai kawai kana goyuwa da bayanshi ne a fakaice"
"Ko kadan,ke dince kin fiya qorafi a kan lamuransa,bayan dukka mun riga mun saba da halayyarsa"
"Ai shikenan" kawai ta fadi,don batason zancan yayi nisa,saita kamowa hafsat wani zancan suka shiga.


Tafiyar a qalla awa daya harda wasu mintuna masu dan dama a kai suka isa unguwar gadon qadon qaya dake qwaryar birnin kano,bakin wani gida mai manyan kagantu tsaho da kuma fadi suka tsaya,wanda kallo daya zaka masa tun daga waje kasan cewa ba mace ko mutum daya zuwa biyu bane kawai ke zaune cikin gidan.


Zaka sake gasgata hakan lokacin da gate din gidan ya bude motarsu ta kunnu xuwa ciki,sassane daban daban qunshe cikin gidan,a qalla akwai sashe hudu zuwa biyar,kowanne na mazaunin gida mai xaman kanshi.


Kamar mai jira,tun kafin ya kammala daidaita tsaiwar motar ta balle murfin motar ta kwasa da gudu tamkar qaramar yarinya ta nufi daya daga cikin gine ginen dake tsakiyar gidan,madaidaicin gini guda daya dake hannun dama.


Baki dukka suka sake suna dubanta,duk da cewa sun sani ba tun yau ba halin xahra din na daban ne,quruciya da rawar kai kamar bata qara komai cikin shekarunta.


Da sauri saurinta take kutsa kai zuwa sassan 'yar tsohuwar,burinta kawai ta cimmata,don ba qaramar kewarta tayi ba,sabo da shaquwa ne mai yawa tsakaninsu,wanda babu makamancin irin wannan tsakaninta da kowanne jika nata koma bayan zahrar.


'Yar kyakkyawar dattijuwa tsaye gaban freezer tana yunqurin ciro wani abu tana magana da wata matashiyar budurwa dake xaune kan daya daga cikin kujerun falon sanye da hijabi mai hannu kalar blueblack,kallo daya zaka mata kasan shekaru sun fara tura mata,saidai yanayin tsafta da son gayu irin nata ya qawata tsufan nata sosai,don kana iya hangen ragowar jan lalle dake qafarta wanda bai gama fita ba,da tajajjiyar sumarta dake cikin dankwali,wadda ke cike da furfura,saidai kuma awanke take fes cikin tsafta da tsari,sam bata lura da shigowar xahra cikin falon ba sai sautin muryarta daya karade ilahirin falon.


"Hajja!" ta fada cikin nuna zallar farinciki tana nufarta,kafin takai ga juyowa tuni zahran ta isa gareta,ta kuma cukuikuyeta gami da rungumeta tsam ta baya tana dan tsalle
"Yan makaranta....barka,barka" ta fada fuskarta na fadada da fara'a,wanda ke bayyana farincikin dake cikin zuciyarta,yake kuma alamta tarin qaunar dake tsakaninsu
"I miss you my hajja" zahran ya fada tana dariyar farinciki
"A'ah,sauya harshe dai,ni ba gane wannan surkullen naku nake ba,yanzu yayanku ya gama nashi ya fita" dariya zahran ta saki tana sakin tsohuwar,saidai sautin 'yar dariyar da taji daga gefanta yana hankalinta ya kuma hanata furta abinda tayi niyyar fada din,ta waiwaya tana duban sashen.


Kusan a tare suka sakarwa junansu murmushi
"Kicemin keda kishiyarki ne hajja......anty takwara ina yini" ta fada tana qarasawa inda matashiyar ke zaune,wadda fuskarta ke fadade da fara'a tana duban zahran gami da gyara mata wajen xama ta hanyar tattare hijabinta zuwa jikinta ta duban zahran itama
"Lafiya lau takwara.....ya makaranta?"
"Alhamdulillahi....gamu yau mun samu 'yanci"
"Aikuwa dai kam,gida akwai dadi" daga haka ta maida dubanta ga ya hajja wacce ta samu waje ta zauna
"Hajjata....me dame aka tanadarmin?" Tayi maganar a shagwabe kamar yadda ta saba
"Duk abinda takwarata keso" hajjan ta fada tana dariya,qaramin tsalle najin dadi ta doka ta fada saman kujera tana cewa
"Allah yabarmin hajjata"
"Eh qwarai,kafin ki shukamin wata tsiyar taki ba" da sauri zahra tadan bata rai tana wulqita idanu,kana ta maida dubanta ga hajjan
"Haba hajja....Allah yasa ba gaban 'yan adawa kika fada ba,da kin saka sunmin dariya,musamman su o'o" ta fada tana dan satar kallon zahra.


Sarai zahran ta fahimci wa take nufi,saita murmusa tana qunshe dariyarta gami da girgiza kai,kasancewarta mai sauqi da sanyin hali,marason yawan magana da rashin daukar al'amura da zafi
"Inna wuro....inna wuro rigima" ta ambaceta da sunan da yawanci akafi kiranta dashi cikin gidan,saita waiwaya tana duban zahran
"Eh ai nasan kin fahimta.....don nasan bakison laifinsa" ta fada tana sake bata fuska kamar wadda aka zaga,hakan ya sanya zahra yin dariya dole tana kada kai cikin jin nauyin ya hajja dake zaune a wajen.


"Sarkin neman magana,idan ya jiki kuma ya hukuntaki kice wani abu daban,shin kin shiga ma cikin gidan ma kin gaisa da mutane ko kuwa kkka zauna neman magana...." Kafin xahran ta baiwa hajja amsa hayaniyar 'yammatan gidan ta soma dosowa falon
"Tofa,Allahumma salli ala,aikin dawo,yanzu zaku taru ku dinga hanani sakat,sauqin abunma dodonku yana gari shima"
"Ni wallahi hajja ki dinga hanashi zuwa duk sanda zanzo hutu,tsakani da Allah fa hanani sakewa yake,hutun wata daya kacal din da nake samu saina qareshi cikin rashin jin dadi" baki hajjan ta kama tana dubanta,ta rasa wanne irin abune haka irin na zahran,qara kusantowar hayaniyar tasu alamun suna bakin falon yasa ta dauke kai ba tare da tace komai ba har suka qaraso cikin falon riqe da hannuwan jakankunan zahra guda biyu,wanda ta barsu a farfajiyar gidan bata samu daukosu ba saboda tsabar zumudi.


Kyawawan matasan 'yammata su biyar rigis sanye da unifoarm,wanda yafi kama da unifoarm din islamiyya,hudu daga cikinsu farare ne ba kamar kalar fatar zahran ba,yayin da daya ce kawai ta dauki kalar fatar zahra,dukkaninsu shekarunsu ba zasu wuce suma sha shida sha biyar din ba,saidai duk wadda ka kalla a cikinsu a ganin farko xaka tabbatar basu kama qafar zahra wajen kyau da zubi ba,duk da cewa babu mummuna duk cikinsu,kowacce da irin nata kyan,amma saiya zamana zahran ta zama zahara sosai a cikinsu.


Wani ihun murnar ganin juna suka saki kowacce na neman wajen zama
"Kai amma naji dadin dawowarkin nan wallahi,kinxo akan gaba" salma daya daga cikin 'yammatan ta fada,harara yusra ta jefa mata daya daga cikin fararen 'yammatan
"Eheen,kedai kin shiga uku wallahi"
"Ke kuma fa,tara kika shiga?" Salma ta fada itama tana maidawa yusra hararta duk da cewa mai kama da dariya dariya ce
"Kinga manta da ita,bani nasha ya akayi?"
"Bari mu saka labule tukunna saboda 'yan saka eyes....."
"Kunga ku tashi ku bani waje tun ban kira yayanku ba" hajja ta fada saboda sanin hali,ta sani sarai labarin nasu baya wuce na samarinsu shi yasa tayi musu haka,sosai suke wasan jika da kaka da ita,tun tana fada da fushi harta haqura ta qyalesu ta zubawa sarautar Allah idanu,harya zamana ma yanzu bata damuwa ya zame mata jiki,mutum daya ne tak da idan yana nan take samun salama,saboda dukkaninsu shakkarsa suke,kuma tsoron hukuncinsa suke.


"Idan wajen mama zaki don Allah ya zahra kice mata yanzu zan shigo na mata bayanin aiken" yusra ta fada tana duban zahra wadda ta miqe da wayarta a hannu tana murmushi
"Bafa can zata ba" hafsat wadda ta shigo daga qarshe ta fada
"Kema ai tunda kika ga ta miqe tana doka murmushi ai kinsan kwanan zancan" hafsat ta sake fada tana yin fuska,cikin dan jin kunya da nauyi zahra tace
"Kamar a kunnenshi kika fada" saita soma yin gaba cikin sauri sauri yayin da hafsat ta bita da magiyar ta tuba tayi haquri ta fice abinta tana dariya.


"Ni ina mamakin yadda soyayya ke gudana tsakanin yaya da yaa zahra"
"Ahto ai haka Allah ke lamarinsa,ku kuke masa wani kallo da bahagon hukunci,saboda ALฦ˜IBLARKU ta bambanta ta wajen ra'ayi,kowanne bawa komai irin halinsa akwai yadda Allah ya sallada wanda zai iya zama dashi ya kuma rayu dashi".


Tsam zahra ta miqe tana maida hijabin unifoarm din jikinta,wanda har yanzu bata kai ga cirewa ba tana cewa
"Bari na shiga ciki kan ku gama lacture din" don sam bata son irin wannan dogon sharhin na hajja,gani take koda yaushe aikinta shine bashi kariya dason wankeshi a idanunsu,bagan sun riga dasun gama sanin halayyarsa ciki da waje,kuma kowacce cikinsu ta kwana da sanin wannan,so tana ganin babu buqatar dagiya wajen bashi kariya da yima halayyarsa kwaskwarima a tsakaninsu.


Kamar hajjan zatayi magana sai kuma tayi shuru kawai ta bi zahran da kallo sanda take ficewa daga falon abinta ko a jikinta,har takai bakin qofa saita dakata
"Don Allah hajja wayata,tunda na dawo nake jina ba dai dai ba,na tabbata nuruddeen nacan yana nemana wallahi,tunda yasan yau zamu dawo" daquwa wannan karon ta watsa mata
"Qaniyarki,yanzu nake muku nasiha kika tashi kika barni zaune wajen,shine yanzu kikeso naje na dauko miki waya,idan kin damu ai kinsan mazaunarta kije ki dauko da kanki" dariya tayi cike da nishadi,ita da hajjan sun saba hakan,suyi tsiya suyi dadi,duk yadda suka kai ga shaquwa da juna amma indai akan irin wannan batunne sun saba haurawa,ita sam dole saita sanyata sun jitu da juna,ita kuma tana jin wannan shine abu na qarshe a rayuwarta da bazai taba yiwuwa ba,komai nasu yasha banbam,tun kan ta mallaki hankalin kanta yadda ya kamata ta fahimci alqiblarsu tasha banbam,hakan ya haifar da duk wani abu dake gudana a yanzu.


Kanta tsaye ta nufi dakin gadon ya hajjan,harta kusa sai kuma ta sauya akalarta zuwa kitchen dinta,inda take jin qamshin abinci na fitowa.


A nutse ta tura qofar tana wara idanu don ganin wace a kitchen,kamar kullum gaji ce,'yar aikin hajjan qwaya daya tilo data jima da ita,takun shigowarta ya sanyata waiwaya tana duban qofa,cikin fara'a da washe baki ta qarasa waiwayowa gaba daya
"A'ah,ashe kina hanya inna wuro.....marhaba da uwar dakina" murmushi zahra ta saki,saboda gaje ta wajenta ce sosai,yadda ya hajja ke ji da ita haka itama gaje ke ji da ita
"Yauwa inna gaje,na sameku lafiya"
"Lafiya qalau alhmdlh inna wuro,ya makaranta?"
"Mun gode Allah" zahra ta fada tana neman wajen zama saman kanta,kusa da wasu kwanuka data gani a rufe,hannu ta miqe tana shirin budewa gami da cewa
"Me aka tanadar mana haka yaketa zabga qamshi"
"Gasunan bude ki gani,duka naki ne hajja tace a yi miki" a nutse ta dinga budewa tana dubawa,sosai taji dadi har ranta,hakan kuma ya bayyana zuwa saman fuskarta,batun yau ba ta shaida da soyayyar da kakar tata ke mata,bata san me yasa ta fita daban cikin jikokinta ba,ko don sunanta taci?,ko kuma don ita din ita daya ce ta zama marainiya a cikin tarin jikokin hajjan?,saita ture wannan tunanin ta sanya hannu ta soma daukan abinda ke cikin kwanon tana sawa a bakinta.


Duk sai data gama dandanawa sannan ta fara lashe yatsunta tana cewa
"Ashe dai 'yar tsohuwar nan na sona haka,bari naje cikin gida na gaida mutane inna gaje na dawo" ta fada tana ficewa da dan sauri saurinta ba tare data saurari abinda inna gajen ke cewa ba.


Sai data fara biyawa ta dakin ya hajjan ta dauko wayartata hade da charger,ta shiga dakinta dake sassan ya hajjan ta jona chargy sannan ta fito.



*MAMUHGHEE* _UBAIDMALEEK_

*BILLYN ABDUL*
_MAKAUNIYAR QADDARA_

*HAFSAT RANO*_MABUDIN ZUCIYA_

*MISS XOXO*_DALAAL_

*HUGUMA*_ALฦ˜IBLA_


*ZAKU IYA BIYAN NAKU KUDIN TA WANNAN HANYAR*

ฦŠaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huษ—u____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

*_08085405215_*

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU๐Ÿ‘‡๐Ÿ‘‡

ย  0903ย 234ย 5899
23/10/2021, 08:35 - ๐Ÿ‘๐Ÿป๐Ÿ‘๐Ÿป: *KIJI TSORON ALLAH,KARKI TABA KAYAN DABA NAKI BANE,BA MALLAKARKI BANE*

02




Falon yanzu babu kowa duka sun yoye sai ya hajjan kawai,tana zaune tana gyara falle fallen littafin dala'ilu,da alama ta karantasu ne suka kuma hargitse mata take gyarawa,don ita din har tsufanta bai hanata bibiyar litattafan addini ba.


Ta baya ta rungumeta tana cewa
"Ashe dai har yanzu ana yi dani 'yar tsohuwa mai ran qarfe,bari naje na dawo na kwashi gara,Allah dai ya jiqan tsohon mijinki" daga haka ta juya cikin sassarfa tana barin falon.


Wannan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

1 Comments On ALKIBLA
avatar
halimat-6

8 months ago

Reply

Alkibla

Please Login or Register in order to submit comment