Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

zauna a saman kafet. Dr. Ya wurgar da
jaridar kan kujera tare da gyara zama ~sosai ya harde
yatsun hannunsa guri guda sannan ya kira sunanta.
‘ “Saudat, kiyi hakuri da takura ki da nake ki daure ki ba ni
labarin ki ina san in ji labarin ki na damu da in san wace ce
ke kuma me ye dalilin kawo ki aikatau maimakon a inganta
rayuwarki da ilimi k0 dan ke ma ki amfanar da wasu a
gaba?”
Saude ta yi shiru tana tunanin dan abin data sani a cikin
rayuwarta, idonta ya ciko da kwalla-ta dago tana kallon shi
da sarqaqkiyar muryarta ta ce
“YallaBai babu komai a cikin rayuwaba sai duhu, . babu abu
guda na haske a cikinta, idan ma na samu
to ya suBuce mini. ban san komai a cikin rayuwata
ba sai wahala da. Qaskanci, haka rayuwar tawa ke tafiya...
‘ Kukan da take riqewa ya soma kwace mata, ta sa
hannu tana goge hawayen kafin ta ci gaba ‘ “Ni dai nasan
ance an haifeni ne a gafin Katsina, kuma na bude idona a
cikinta, don haka na
ci gaba da rayuwa a yanda tazo mini a ciki, "tunda nayi
wayo na ganni a: gabana Yayana Rabi’u sai mahaifina
Malam Bala, sai kishiyar mahaifiyata Inna Laure da yarta
iKilima wadda ake ce mata ‘Yar Baba.’ » A nan ta Iabarta
masa gaba dayan labarin rayuwarta har ya zuwa yanzu.
Tana gamawa ta kifa kanta a saman cinyarta tana kuka.
Tausayinta ya qara kama Dr Ahmad wanda yake jin tamkar
ya". zubar mata da hawaye, ya tausayawa halin da ta ’
tsinci rayuwarta tun tana yar karamarta har girma ta
mallaki hankalinta, amma Inna Laure ba za ta bar ta haka
ba wannan wace irin macece? ‘ ; Ya kira sunan ta cike da
damuwa ya ce.“Ki yi hakuri Saudat insha Allahu sai kin
yi,alfahari da rayuwarki ni zan maye miki gurbin Yaya
Rabi’u da kuma Hamid in dai ina numfashi. Saudat sai kin yi
‘ dariya da farin ciki kamar kowace mace, ki kwantar”da
hankalin ki ki daina kuka haka kinji?” ‘ _ Kai kawai ta daga
masa alamar eh ya zaro ~ hankicif cikin aljihunsa ya mika
mata ta karBa ta’ share hawayenta sannan ta mika masa ya
karba kafin yace, “Yanzu ki tafi kije Ki kwanta daga masa
alamar eh? Ya ce to shi kenan,‘kidab bani lokaci zan danyi
tunani a kan matsalarki kafin. in “ samar miki mafita da
fatan‘dai ba zaki yi fushi da;
Duk abinda rayuwa ta sake baki ba zaki karba da hannu
biyu
Saude ta daga masa kai alamar eh yace to allah ya kaimu
Jin yayi shiru yasa ta miqe ta nufi hanyar fita har takai
bakin korar taji ya kira sunanta ta waigo tana kallonsa yace
ki kawomin coffe yau da daddare kai kawai ta daga masa ta
juya ta fice abinta koda ta koma bangarenta ruwa kawai ta
watsa ta koma ta kwanta a binta wani barci ya dauketa ba
ita ta farkaba saida wayarta ta dameta da qara tasa hannu
ta dauka cikin magagin barci jin muryar hamid yasata
saurin watstsakewa daga baccin suka shiga hira sunfi awa
biyu a haka sannan sukai sallama da niyyar zai qara kira
zuwa anjima misalin qarfe goma daidai saude ta fito daga
bangarenta ta fita kai tsaye kichin ta nufa ta dauko flasks
din coffe da qananun kofinan da yakesha dasu ta nufi
bangarensa dasu saidai tun kafin ta qarisa ta hango
bangaren nasa dun dum babu alamar hasken wuta tsoro ya
kamata gashi bata taho da wayartaba ballentana ta haska
kuma babu damar ta koma
Wayyo allah taji tamkar ta fashe da kuka
Taja ta tsaya cak tana tunanin abinyi tun kafin ta
Qarasa nazarin taji wani haske mai Karfi ya taso da saukar
ruwan sama mai Karfi ai bata san lokacin data kwasa da
gudu ba ta yi Bangaren nasa, ba ga shi duk ta jike Tamkar
daga sama ta ji ta yi tuntuBe da wani abu ta fasa wata
uwar qara ta saki kayan ta kwasa a guje, karaf sukai kicibis
ta da mutum, ta sake kwala wani qara mai qarfi cikin
dabara ya rungume ta sosai a jikinsa yasa hannu ya kunna
wutar falon. Amma har a lokacin ‘ ihu take tana, zullon
kwacewa, hannu yasa ya
tallabo qeyarta ya juyo da fuskarta saitin tasa su kai
ido hudu. Sai Alokacin ta tsaya da ihun ta saki wata _
. ' nannauyar ajiyar zuciya cikin muryar kuka ta ce ‘Wallahi
ka tsorata ni na zata, na zata... ’sai kuma tayi
Shiru Yanda take maganar a shagWaBe ya barge shi har bai
san lakacin da ya saki wani murmushi ba yasa dan
yatsunsa ya lakace mata hanci yan fadar, . “You ar so
beautiful Ya lumshe idanuwansa tare da mata wani
murmushi,wadda ta tsaya iya makoshinsa kawai
' Sai a lokacin Saude ta lura da irin rikon da ya yi mata ta yi
saurin zame jikinta da na shi a kunya ce saboda yanda
ruwan. ya jika kayanta duk suka mammanne a jikinta
tamkar ba ta sa komai ba ta juya da gudunta ta bar falon
tana ji yana kiranta amma ba ta tsaya ba, haka ta koma
sashin nata cikin ruwan. '
Tana shiga ta hada kanta da bangon falon tana jin tamkar
qasa ta tsage ta shige ciki, saboda kunya da nauyi. Ai k0
ba za ta sake yarda su hadu ,ba duk rintsi kai dole ma in
bar gidan. nan, wannan abun " kunya har ina, musamman
idan‘ matar gidan ta samu labari ai ita ta san ta kade har
ganyen ta. Kunya ta isheta tarinqa jin tamkar tarusheda
kuka.
Ta samu ta yi ta maza ta cire kayan ta dauko tsohon
zaninta ta yi daurin Kirji da shi ta haye kan ‘ gadonta ta ja
bargo ta kwanta. Amma sai me? Da ta rufe ido sai ta ga
tamkar ga Dr. Ahmad nan zai rungume ta, ta zabura ta
tashi zaune tana muzurai, ga qamshin turarensa da ya
mamaye ta, ta yi wani gajeran murmushi tare da komawa
ta ‘kwanta: ta runtse idanuwanta a haka bacci mai nauyi ya
dauke ta. Washe gari tunda ta farka take zaune tana san
zuwa wurin aikin nata, amma kunya ta hana ta, ji ‘ take ba
za ta iya sake hada ido da shi ba, don haka ta
gidan.
Ita kanta ba ta san ta dan lokaci ba sai da ta soma jin
cikinta na kukan yunwa, ta daga kanta ta kalli agogo. Sha
daya da mintina, tana shirin tashi zaune ta ji an turo Kofa
an shigo. Ta yi saurin tashi tana fadar, “Sannu Aunty.".
Ta amsa da “Yauwa Saudat laflyadai ki kek0?” Saude ta ce
“To da sauqi dai kaina neke dan ”ciwo.” ‘ .
Ta ce, ‘Ayya, Allah Sarki kije Hajiya na neman ki tana falo.”
Gaban Saude ya yi wata mummunar faduwa, ta ce, ‘Lafiya
dai k0 Aunty? Allah yasa ba wani laifl na yi ba.
‘ Aunty ta ce “To laflya, YallaBai ne ya aiko kiranki.’ _
Hankalin Saude ya Kara tashi alamun tsoro ya . bayyana
karara a fuskarta, ta mike jiki amace tana fadar, “Ga ni nan
zuwa.”
Cikin sanyin jiki ta canza kayan jikinta sannan ta fito
zuciyarta na faman bugun dardari. harta qarasa .falon ta
hango’Asma, tsaye riqe da Kugu, tana sanye da wasu
riga‘da siket sari tare da 'mayafinsu tamkar wata
.Ba’indiya, takalmin nan mai shegen tsini a qafarta.
A danyi nesa da ita Saude ta tsaye ta durkusa tare ‘ da
fadar, ‘Ina kwana Haj iya.” .
Asma ta watso mata wani razanannan kallo kafin ta ce
‘Shut up ke nan har marar kunya ce wace ce ke? Uban
waye uban ki a garin nan da har za kiqi zuwa aiki saboda jin
dadi har Dr. ya aiko kiran ki, me ki ke ji da shi a cikin gidan
nan? Me ki ka taka'?
, Banza sakarya jaka‘ yar qauye.
Yau k0 rashin lafiya ki ke dole za ki sanar in ba daibakisan
inda kankiyake ba, tunda an ajiye miki wayar tarho da za ki
iya kira da ita ki sanar, amma ke isasshiya kin yi shiru abin
ki wato idan ana so a neme kito ki -sani wannan shi ne
laifinki na biyu cikin manyan laifukan da ki ka aikata a gidan
nan duk ran daki kikai na uku,kisani aranar”zakikarbi
takardar sallamar ki kinji na fada miki” Tana gama fada ta
juya ta haye sama a zafafe
Jikin Saude ya yi sanyi matuqa, ta lallaba ta mike ta fice
zuciyarta a cunkushe da baKin cikin yanda aka wulaqanta
ta ba tare da an saurari uzurinta ba.
Rayuwa kenan ,
Haka ta sa kai ta shiga falon tare da sallamar’ta, tsaye yake
tsakiyar falon ya goya hannayensa a baya yana jin
sallamarta ya yi saurin waigowa ya nufo ta da hanzarinsa
Lafiya Saudat me ya same ki? Ba dai ruwan jiya
, neya saki zazzaBi ba?”
Saude ta girgiza kai alamar a’ a, sannan ta durkusa tana
gaishe shi, bai iya amsawa ba ‘ ya sake jefo mata wata
tambayar
‘Ban yarda ba Saudat idan lafiyarki qalau me yasa yau ba ki
zoba?"
Saudat ta Kara dukar da kanta qasa tare da fadar, ‘kaina ne
yake ciwo kadan shi ya sanya.’
Dr. ya ce ni dai na sani, :nasan baki da da lfy Saudat bari in
kira likita ya duba ki, kin ci abinci ' ‘ kuwa? .
Da sauri ta ce ai na warke.
Dr ya. girgiza mata kai a’a Saudat ban san wasa da lafiya,
taso ki ci abincin kafin yaz0.
Ganin yana shirin riko hannunta yasa tayi saurin tashi da
kanta ta bi shi ya nuna mata tsakiyar kafet ta' zauna sannan
ya nufi dining ya dauko kayan abincin ya kawo mata, yau da
kan shi ya zuzzuba mata ya tura mata a gabanta tare da
fadar. ,
‘Don Allah ki daure ki ci.”
Kai kawai ta daga masa, sannan ya wuce ya dauki wayarsa
ya kira likitansa. Yana cikin wayar ne Asma ta sawo kai
falon tana wani taku sai ka ce wadda take filin. gasar iya
taflya, Dr. ya zuba mata idanuwansa cike da tuhuma. ‘
Karaf idonta ya sauka kan Saude wadda tuni hanjin cikinta
ya shiga juyawa saboda tsananin
firgita da tashin hankali, Asma ta ja ta tsaya tana ,fadar.
“Me nake gani haka Dr? ‘Yar aikin ce kecin abinci a faod
flask dinka, kam babban ....... ’
Kai jama,a akwai rikici fa sai kunjini agaba donjin yaddah
zataci gaba da kayawa naku har kullum admin Dboy🤔
[1/25, 10:39 AM] A A Dboy: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚
[12:17PM, 02/02/2017] 🙆🏼‍♂@lh@ji🙆🏼‍♂: [1/27, 10:11 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*

*CHAPTER 19*

“Me nake gani haka Dr? ‘Yar aikin ce ke cin abinci a food
flask dinka, kam babban ....... ’
Ya watsa mata wani kallo lokacin da ya kashe wayar ya ce
“To k0 rai ya yi baki ne? Ai dai anawa take ci ba a baki ba
k0? Ya yi mata tambayar cike da ‘ isa da gadara. _
“ Asma ta qara shaqa kafin ta ce ‘Hmm! Dr. kenan amma
dai .ka san wannan ba qaramin kaskanci bane da zubdawa
kai girma ka yi bak0? A. Zo a iske yar aikin ka na cin abinci
a kwanan ka,
‘yar aikin ma ‘yar Kauye, jaka dakikiya, wadda talauci ya yi
masu daurin .....
Dr. yayi saurin daga mata hannu ‘ya isa haka Asma, kin
sanni sarai ban san cin fuska don Allah tunda ban aika miki
da katin gayyata ba ki bar nan, banasan ciwon kai.’
' Takaici ya kashe Asma, ta matsa daf da shi tare da
sassauta mur'ya ta ce ‘Yanzu Dr saboda ‘yar aikin ka ka ke
cimin fuska haka?” ‘ Ya ce ‘Amma kin sani Sarai ba a gaya
mini yanda zan yi ko?’ Haushi ya kama ta ta juya a zafafe ta
bar masa falon, ya taBe baki ya juya wurin Saude wadda “
lomar abinci ta yi wa tsaye a maqogaro tun dazu ta gaza
hadiyewa, saboda tsabar firgici da tsoratar da ta
Dr. ya zauna bakin kujerar dake fuskantar ta yana fadar.
“Ki nutsu ki ci abincin ki sosai ga likita nan zuwa.’
Hawayen da suka taru a kwarin idanuwan ta suka gangaro
cikin kuka ta ce, ‘Wayyo Allah na ka ja mini Allah kadai ya
san abin da za ta yi mini yau na
banu na lalace! ’
Dr. yace ‘Kuka kuma Saudat? Yanzu nan har an yi abin
kuka? Lallai ashe kina da kukan jini nan gaba. ’
Saude ta Kara rushewa da kuka, ‘Wallahi gida zan tafi”
Dariya ta kama Dr. ya ce, ‘Ashe matsoraciya ceke lallai
Saudat na tabbata da Asma ta ji haushin ki da k0 sama da
qasa za ta hade anan ba za ta kyale ki ba, ta riga ta san
halina ne sarai don haka ba ta damu da ke ba ta kaina za ta
dauki matakin don haka ki ma kwantar da hankalin ki ki ci
abincin ki ’
Saude ta ture abincin tare da fadar, ‘Na qoshi.’
“Me? Ai wannan ne baki isa ba k0 ki dauka ki cinyc shi ko
yanzun nan in kira ta ince kin cetazo ta kwashe kwanukan
kin gama.’
Saudc ta yi saurin waro ido waje tare da janyo
abincin da saurinta ta ci gaba da ci, ya yi dariya a ,
zuciyarsa sosai ya ce matsoraciya.
Tun kafin ta gama cin abincin likitan yazo ya duba ta sosai
tare da rubuta mata wasu magunguna, ya kira direba yasa
ya je ya siyo mata su, ya dinga lallashinta yana rokon ta a
kan ta rinka shan magungunan, sannan ya ba ta ta tafi
Cikin tsoro ta shiga sashin nasu don gani take Asma na nan
na jiranta. ' .
Tana shiga sashinta ta maida qofa ta rufe ta ajiye
magungunan ta haye kan gado ta janyo wayarta da .taketa
faman ruri tun dazu ta ci gaba da wayarta.
Washe gari da yamma tana zaune a bangaren Dr.
tana aiki, zuciyarta sai faman sake-saken neman mafita
take saboda wayar da su kai da Hamid jiya da
daddare
Dr. ya sauko daga samansa yana sanye. da qananan kaya
irin na hutawar turawa, ya tsaya daga gefen kujera yana
kallon Saude wadda ke durkushe tana 'goge goge
‘ . Jikinta ya ba ta tamkar ana kallonta, don haka ta yi
‘saurin waiwayawa, tsaye ta gan shi a gabanta ya harde
hannuwansa a kirji tamkarmai nazarin wani abu. Saude ta
yi saurin durkushewa tana masa sannu
da fltowa, bai amsa mata. ’ba‘ sai ma ya sake gyara
tsayuwarsa. “Me yasa baki san hutawa?”
Saude ta dan kalle shi kadan kafin ta ce ‘Ai aikina ne shi
yasa.’
Dr. yadan dauke kai kafin yace, ‘Ai kin kusa barinsa, saki
wannan aikin ma taho mu fita mu sha iska.”
Bai jira abin da za ta ce ba ya yi gaba abinsa,
Saude ta raka shi da idanuwanta. To me yake nufi da ita?
Ba dai korarta za su yi ba? Da sauri ta zabura ta bi
bayansa.
. Hadaddan wurinn shakatawa ne wanda aka kashewa
dubban nerori wurin Kawata shi, don an zuba abubuwan ban
sha’awa da debe kewa. Saude ta . koma jikin wani dodon
roba, tana kallon Dr. wanda ke wasa da dan biri, can ya
dago ya yafito ta da hannu alamar ta zo duk da tsoron da
ya cika mata zuciya haka ta dake ta tafi inda yake, ta tsaya
daga gefe tana kallon su, ba ta ankara ba ta ji ya fizgo
hannunta ya hada da na birin, yana wa birin magana cikin
harshen turanci.
Mutuwar tsaye ta yi don tana bala’in tsoron sa sosai, don
ma yana dan Karami, sai ta ga ya ’fadi' Kasa alarnar
gaisuwa. Dr. ya yi dariya yana kallonta ya ce “Ana gaishe
kifa?” Kallonsu kawai take bata ‘ iya yin magana ba, birin ya
mike yana ta faman zazzagaya ta yana tsalle-tsallen
murna. ' ,
Dr. ya janyo hannunta suka nufi wani.‘ qaton lilo
na roba mai matattakala ya dan kalle ta da murmushi a
fuskarsa ya ce “In hau za ki jujjuya ni’?’ ‘Duk da
haushin riKon da ya yi mata ya kama ta sai da ta yi dariya
saboda yanda ya yi maganar.
Ya ce, ‘Okoy, dariya ma na baki to bari in dora ki in jujjuya
ki.’ Tun kafin ta yi wani yunkuri ta ji ya sure ta ok ya dora
saman lilon.
Saude ta fasa wata uwar kara saboda razana, don ita gaba
daya ma lilon tsoron shi take yi, dariya ta bawa Dr. sosai na
kauyancin nata, don haka yana dariya yana jujjuyawa da
ita, mutuwar zaune ta yi ta . runtse idanuwanta tana
sauraren ikon Allah, shi kuwa dariya kawai yake mata, yana
zolayarta ganin ba shi .da niyar daina juya ta yasa ta bude
idanuwanta tana shirin kuka, ta hau rokonsa.
‘Don Allah don Annabi ka sauko da ni.’
Dr. ya tsaya da lilan ya matsa yana fadar, ‘To sauko tunda
ba kya so.’
Saude ta waro idanuwa don ta san ko da kudi aka bata
bazata iya saukowa ba, ya yi murmushi tare da mika mata
hannunsa ta rike sannan ya sauko da ita, yana mata dariya
yace matsoraciya duba ki ga aku na .kallon ki. ’
Saude ta yi saurin juyawa, caraf ya riKo hannunta ya ja ta
da saurinsa. Haushi ya kama ta yanda ya maida ita kamar
Karamar yarinya. Saman wasu kujerun roba ya zaunar da
ita shi ma ya zauna, suka
sa zagayayyan tebur din a tsakiya. Saude ta bi abin . da aka
dora' saman tebur din da kallo, wanda a kai ‘
‘ rafin din shi gwanin burgewa. Dr. ya miKa hannu ya dauko
ya mika mata ta tsaya tana kallon shi ya miqa mata tare da
fadar.
“Karba mana.’
Ta mika hannu ta karba,tana kokarin bude rafin leda din.
Dr. ya yi saurin tsaida ita yana fadar, ‘tsaya tsaya waya
fada miki idan aka bawa mutum gift budewa yake'a take
bakauyiya ai bari ake sai an tafl.’ Yana maganar cike da
zolaya. .
Saude ta zumBuro baki" jin ya kira ta da bakauyiya, dariya
ta kama shi ya ce, ‘A’a ‘yanmata ashe kin iya fushi irin
haka?”
Ta dauke kanta ba tare da tace Kala ba. Ya ce, ' ‘Wai fushin
ki keyi da gaske am so sorry, tuba nake -kaina bisa
wuyana.’
Dariya ta kubce mata yanda ya yi maganar a ladafce sai
kace ba YallaBai din da ta sani ba, ganin dariyarta yasa ya
mikc yana fadar
“Taso muje kin ji ana ta kiran sallah a_ masallaci.’ ‘
Saudeta tashi ta mika masa gift din da ya bata, ‘ya dan
zuba mata idanuwansa babu alamun wasa a fuskarsa ya ce
‘Da shi za ki tafi kyauta ce daga gare‘ ni.’ Yana gama fada
ya juya ya yi. gaba abinsa, ba tare da ya saurare abin da za
tace ba.
Tsabar mamaki da kaduwa su suka hana Saude furta
komai, har sai da ya kusa bacewa ganinta
saunan ta iya wage murya tana fadar, “Na gode kwarai.’
Hannu kawai ya daga mata ba tare da ya juyo ba
ya Bace abinsa, ita ma ta yi gaba cike da zullumin
abin da aka nannade haka. Tana .shiga dakinta ta fada kan
gadonta ta yi zaman dirshan ta shiga bude kyautar, ta ciro
wani
kyakkyawan kwali mai kyan gaske da zanen waya waya a
jikinsa. Saude ta bi hoton wayar da kallo kai da gani ka san
ta yi tsadar gaske, a zuciyarta ta furta ‘Allahumma
arzuquni" tasa hannunta ta bude kwalin.
Gabanta ya yi wata mummunar faduwa ta yi ‘ masifar firgita
ganin sabuwar wayar kwance cikin kwallin, ta ciro ta tana
jujjuyawa, touch screen mai shegen kyau, wadda ta san ko
da kudl aka hada ta ba za ta iya kunnata ba.
Saude ta riqe wayar tare da dafe kai, yau na shiga uku ni
Saude, wai me ke shirin faruwa da nine? Wasu irin hawaye
suka ziraro daga idanuwanta ta lura mutumin nan so yake
ya jaza mata bala’in da ba zata iya dauka ba, yanzu
tsautsayi yasa Hajiya ta samu labari ya kenan?
Motsin taflyar da ta ji ne ya sa ta zabura ta maida
wayar cikin kwalinta ta tura a qarkashin filonta, tana
faman‘muzurai. Aunty ce ta shigo da sallamarta suka
gaisa sannan ta ajiye mata wata leda Saude ta mika hannu
ta janyo ledar tana duddubawa.
Sabulan wanka ne dana wanki tare da kayan shafawa da
mayuka, ta ajiye‘ leadar gefe ta koma ta kwanta tana fatan
gari ya waye ta je ta maida
masa wayarsa, don ba zata yarda ba ya jaza mata tashin
hankali da bala’in da ba za ta iya dauka. Ba
Dole nema ta runtse ido ta fada masa‘ ya fita daga
rayuwarta ita dai ba kowan kowa bace hakan kuma ba yana
nufin ba ta san mutuncin kanta bane da wannan tunanin
bacci barawo ya sace ta.
Washe gari da safe Saude ta tafl Bangaren Dr. Ahmad babu
kowa a falon nasa don haka ta zage ta shiga aikace-
aikacenta qarfe goma daidai ya sauko daga samansa yana
sanye da jallabiya sabuwa ruwan toka mai hade da hularta
Suna hada ido da Saude ya yi saurin qarasa saukowa daga
matattakalar yana fadar, “Zo. nan Saudat." *
A hankali ta dago ta kalle shi tare da gaishe shi cikin
girmamawa kamar yanda ta saba. Ya amsa' a tsanake
sannan ya jefo mata tambayar da ta sanya ta saurin
dagowa tana kallonsa, ya qara‘gyara tsayuwarsa tare da
maimaita mata tambayar.
“Na ce laflya ba ki bude kyautar da nayi miki ba
Ko baki iya bane?” Ya karasa maganar cike da tuhuma. ;
Saude ta dukar da kanta tana kallon kafet din dakin cikin
nutsuwa ta soma magana.
“Kayi haquri Yallabai ba wai ban yaba ba ne kawai dai na
ga kyautar ba ta cancanta dani bane shine yasa nayi'
tunanin maido maka, amma ka yi hakuri
Dr. Yayi wani takaitaccen murmushi tare da zama saman
hannun kujera ya zauna yana kallonta a nutse kafin ya ce
‘Dama ita kyauta cancanta ce ke sawa ayita idan kuwa
cancanta ce to ke kuw kin ' wuce wadda a kai miki kinfi
qarfin hakan.
Kuma idanma ba ki sani ba ina so yau ki sani dangantakata
dake tamkar hannu da ido ne yanzu sannu a hankali zan
shafe hawayen da ke kwaranya daga idanuwanki insha
Allahu sai na wanzar da dariya a idanuwan dake ta zubar
hawaye, kin fahimta?”
Saude ta girgiza masa kai tana fadar, ‘A’a Yallabai yin
hakan yana nufin zaka tsamo ni daga rijiya ka jefa ni kogi
ne Yallabai ka yi tunani zan iya shiga matsala wajen Hajiya,
na tabbatar idan ta samu labarin kudirin da kake nufo ni da
shi zata dauki kowane irin mataki a kaina,
Dr Ahmad ya kada mata kai yana fadar, 'Ko
kusa Saudat babu wandu ya isu ya yi wu mutum ”abinda
Allah bai masa ba haushin me Asmu za ta ji
don kawai ina kokarin taimaka miki meye abin da zai
tunzura ta a ciki? Ni ban ganshi ba, kuma koma
akwai ba zai dame ni ba, zan yi Kokari har sai na sauke
alkawarin da na dauka.”
Idon Saude ya ciko da hawaye cikin muryar kuka ta ce, ‘Na
san ba zai dame ka ba YallaBai amma ni zai dame ni, wata
qila ma ya zamo silar barina duniyar gaba daya. ’
Dr. Ahmad ya ce, ‘Hakan ma ba za ta kasancewa ba Saudat
ki daina ma fada.’
Saude ta ce, ‘Idan ya kasance fa?”
Shiru ya yi yana kallonta Saude ta yunkura ta mike
hawayen da suka ciko daga idanuwanta suka samu damar
zubowa cikin kuka ta ce, ‘Zan bar gidan nan dole zan bar
shi, dan ina tsoron abin da zuciyata ke hangowa ina jiyewa
kaina, dan idan ma wani abu ya same ni babu wanda Zai yi
kukan rashina, babu ba ni da shi.... Kuka ya ci Karfinta
sosai.
Dr. Ahmad ya yunkura ya zagayo ta gabanta yana kallonta
cikin sanyayyar muryar shi ya soma magana.
‘Duk inda ki ka nufa a fadin duniyarnan sai na nemo ki, babu
inda za ki shiga ki layance min. Ina tare da ke Saudat har:
sai na ga kin yi dariya sai na ga rayuwarki ta inganta kin
samu farin ciki mai dorewa
na yi wa kaina wannan alkawarin kuma zan cika shi ko da
hakan yana nufin rasa komai na a rayuwata.’
Saude ta yi saurin juyawa tana kallonsa ya daga’ mata kai
yana fadar, "Tabbas kisa ido kiyi
kalio.’ ‘Ya juya a sukwane ya fICe daga falon ya bar ta
nan tana kallon qofar da ya fita. Wani irin kuka ya zo mata,
tsoronta daya a duniyar nan matarsa Asma; don ta san ba
lallai bane ta yi musu kyakkyawar .zargi ba, tana tsoron ta
yi musu mummunan zargin da zai‘sa ta yanke mata hukunci
daidai da zarginta. Saude ta Kara rushewa da kuka don har
ta hango irin bala” in da za ta iya fuskanta Haka ta karasa
aikinta tas ta bro Bangaren nasa, yinin yau haka ta yi sa a
kwance. Da daddare kuma Hamid ya kira ta ya Kara caza
mata Kwakwalwa. “Wai Saudat me ke damun ki ne shin k0
kin mance da yau saura sati uku auren ki? Na lura hankalin
ki kwance yake tun yaushe nake fama da ke kina gocewa.
Saudat idan harkin soma san Garba ne ki fad'a mini in fidda
raina kawai, amma don me za ‘ki ta yi min yawo da hankali
ki ce yau ki ce goba, idan kin san ba zaki iya fitowa daga
gidan ba ki 'fad'a mini ni in zo da kaina in dauke‘ki.’ 'Saudat
ta ja numfashi ba ta taba tunanin ya iya bude wuta haka ba,
ta ma rasa ta indaza ta fara, don . haka ta kwantar da
murya ta ba shi hakuri tare da yin .
masa alkawarin duk rintsi gobe za ta gudu ta bare ‘ Abujar.
» ,
Abun duniya duk ya ishi Saude tunaninta daya yanzu
hanyar da za ta bi ta bar. gidan ga YallaBai yana nema ya
taso ta gaba tsoronta daya ma yanzu kar ya ruguza mata
al’amuran ta, wannan tunanin ne ya hana Saude barci da
wuri sai kusan biyu da wani abu na dare ta kwanta, don sai
da ta harhada kayanta tsab na barin garin. .
Sallar Asuba ma da kyar ta iya yin ta saboda baccin da yaci
qarfinta. A kan sallayar ma wani sabon baccin ya sake
dauke ta. Ba ita ta farka ba sai qarfe sha daya da mintina.
Ita kanta ta yi mamakin tsawon lokacin da ta dauka tana
bacci, don haka ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment