Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yi
hakuni na san Ubang‘iji na sane da mu ba mancewa ya yi
da mu ba, kuma shi ya san yanda zai yi da mu, tashin
hankalina Saude a yanzu daya ne ' yanda zan tafi in bar ki
ban san a wane hali zan barki ba wace irin rayuwa ce za ki
fuskanta bayan bana nan, ban sani ba.”
Yasa hannu yana goge hawayensa kafin ya ce, ‘Dole zan
tafi', dole zan bar garin nan Saude ki yi hakuri ki rungumi
rayuwa a duk yanda ta zo miki kar ki yarda ki sabawa
Ubangiji a duk halin da kika tsinci kanki ciki, na dadi k0
kishiyar hakan. Na ‘ san insha Allahu Ubangiji ba zai bar
rayuwarki ta lalace ba." ‘
Yasa'hannu cikin aljihunsa ya ciro wasu kudi ‘yan, dari
biyar~biyar da alama kudin aikinsa ne ya
raba biyu ya miqa mata rabi yana fadar, “Ga. wannanki riqe
a hannunki kiyi amfani dasu insha Allahu zaki rinqa samun
aikena a duk inda na shiga a fadin
duniyar nan.”
Ya ajiye mata kudin saman jikinta ya mike yana fadar,
“Allah ya hada fuskokin mu da alheri."
Saude ta yi saurin miqewa ta riqe shi tana wani irin gunjin
kuka mai daga hankali.
“Don Allah kada ka tafi ka bar ni Yaya wallahi mutuwa zan
yi idan ka tafi Wayyo Yayana!” Ta qara fashewa da wani
gunjin kukan.
Rabi’u ya dafa ta yana kallon idanuwanta kafin ya ce, “Ki yi
haquri Saude ni kaina ba dan na so ba zan tafi inbarkiba,da
zaiyiwu da dole dake zantafi, amma ba yanda zan yi ne
tunda ke macece amma na
yi miki alkawarin duk inda make a duniya ina tare
da.... Ya kasa fadar abin da yake son fada saboda
kukan da ya kwace masa shi ma. Ya zame hannayenta
daga jikinsa yana fadar, “In har kina sona da gaske Saude
kada ki sake cewa komai ki juya ki koma gida ni na tafl sai
wata rana.”
Ya dauki jakar kayansa ya juya yana tafiya yana sharar
hawayen da ke zuba daga idanuwanshi kamar an kunna
famfo, Saude ta duka a gun tana wani irin gunjin kuka tun
iya karfinta. Rabi’u na jin ta amma bai waiwayo ba saboda
yanda yake jin zuciyarshi na
Barazanar tarwatsewa gaba dayanta ga shi a lokacin ba
jama’a da yawa a waje saboda safiya ce sosai. Tunda
Saude ta duka ba ta sake tashi a gun ba, tun tana kukanta
iya karfinta har muryarta ta disashe. ~
Rana ta soma mutane suka fara fitowa daga
gidajensu duk wanda zai wuce sai ya yi mata magana,
amma ba ta tashi ba, tana duke cikin Kasa tana' kuka, ba ta
ankara ba sai dai taji saukar duka ta ko ina’ tana dagowa ta
ga Inna Laure, ta mike ta ‘ kwasa da gudu ta nufi hanyar
gida, ita kuma ta raka ta da jifa. ' Tana shiga cikin gidan ma
nan ma Malam ya dora mata da na shi dukan yana zaginta
tare da yi mata mugun baki. Inna Laure ta shigo babu
alamun ' tausayawa“ a fuskarta ita ma ta hau zaginta tana
fadin
* “’Yar iskar ai ba yau suka fara ba, ai dole ta zauna
tana~ta aikinkuka karabata da jin dadinta munafuka.”
Ta hankade labule ta shiga daki ta dauko mata wasu
tsummokaran kayan ‘Yar Baba wadanda ta gama da su ta
watso mata tare da wando da tsumman dunzugu, ta gwada
mata yanda za ta sanya sannan ta ‘ dora mata tallar
wainar. Haka Saude ta dauki tallar ta tice daga gidan tana
matsar kwallah.
Haka ta je tallar ta dawo ba taci komai ba, sai kukan da
take ta faman yi. Haka ma da rana ta dauki
alala ta sake tafiya, ruwa kawai ta iya sha a wurin ranar
yau, duk inda ta gifta sai ta ga tamkar za ta ga Yayanta
amma k0 mai kama da shi bata gani ba haka ta karaci
yawon tallar ta ta dawo da yamma likis.
Ta samu Inna Laure da dillaliya suna tsakar gida saman
kujera ‘yar tsugunne taya ni gulma suna
hirarsu har da shewa. Tana shigowa Laure ta nuna ta da
baki tana fadar.
“Kin gan ta nan fa dillalliya, wan: ai aikatau ga wannan ai
tallar cc kawai ta dacc da ita.”
Dillaliya ta ce, “Haba dai a ganin ki dai, amma in da ni ce da
wannan wallahi Abuja zan tura ta kawai."
Saude ta qula ta gaishe da dillaliyar sannan ta mikawa Inna
Laure cinikinta ta mike ta wucc dakinta.
Tana jin Inna Laure na fadar, “Hmm! Dillaliya kenan ai ni
duk wanda ya ci tuwo da ni miya ya sha, to shi kuwa k0
miyar ma bai sha ba don in fada miki dama cike nake da shi
don har na fara tunanin in zuba masa shinkafar Bera a
abinci ‘ya ci kawai, sai dai a wayi gari ya yi mushe.
Ai in fada miki ina tashi. da Asuba na 'ga yarinyar jinin ya
zo mata, ai a take dabara ta fado mini, ni kaina sai da na
shiga daki na yi ta dariyar qeta yanda na ga Malam na
sharar ‘yar kwalla.”
I
Duka suka sa shewa suka tafa. Can Saude ta jiyo
diilaliya na fadin
“Ke wai ba zaki saro gyada ki soya mata ta rinqa zama
kofar gida ba na ga sabuwa ta fara shigowa wallahi ciniki za
ta yi ta rinKa zama nan kofar gida da daddare.”
Laure ta ce “Ai k0 kin kawo shawara bari gobe Talata inje
‘Yar Kutungu da kaina in siyo mai kyau
in zo in soya mata Ai shi yasa nake son ki kawata
Akwai ki da bada shawara mai kyau.
Saude ta lallaBa ta kwanta tana jin zuciyarta na tuquki
wasu zafafan hawaye suka rinka biyowa kuncinta ba ta da
mai lallashin ta yau dakin ya yi matA bakikkirin, saboda
rashin rabin jikinta, Yayanta a cikinsa
Sai yanzu ne ta gane marainiya ce ita marar gata, yanzu ta
yarda da maganar Yayanta da yake ce mata bata da. gata
a. duniya, ba su da kowa sai Allah. Ashe da gaskiyarsa. Ta
sake rushewa da wani sabon kukan lokacin da ta tuna da
lokacin da ya dawo daga aiki jiya ya kawo mata kayan
kwalliya. *
Ta tuna da irin yanda yake lallashinta idan ya ga ta shiga
damuwa duk ~ yanda zaiyi sai ya yi ya tsaida hawayen
nata, ga shi yanzu baya nan. Tabbas ta rasa gata a duniya
ta rasa jigon rayuwarta. don tana ji a jikinta da wuya. idan
za ‘
tasake ganinsa tunda shi kan shi baisan inda za shi ba
yanzu, wala ya mutu k0 ya yi rai. Shin k0 yana a wane hali
yanzun ma?
“Wai k0 ba da ke nake ba ne Saude kina ji ina ta faman
kiran ki?”
Saude ta jiyo muryar Laure, don haka ta zabura ta mike ta
goge hawayenta ta yo tsakar gidan a lokacin dillaliya ta tafi
Laure ta watsa mata harara kafin ta ce, “’Yar iska duk uban
me kike ina kiran ki kin yi min shiru?”
Saude ta yi shiru tana kallon yatsun qafarta hawayen da
suka taru a idanuwanta suna diga qasa, Laure ta ja tsaki
tana fadin.
“Ke dai kya kai su in kaya ne wuce ki ki dora mini sanwar
tuwo, idan kin dora ki zo ga kayan wankina can na jika ki
wanke mini su.”
Saude ta yi saurin dagowa ta kalle ta, Laure ta ce,
“Bakallona zakiba cewa zakiyi bazakiba kawai sai in san kin
isa.”
Saude ta juya ta wuce jikinta amace, saboda ita dai ba ta
taba yin wanki ba, don kayanta ma kale daya ne, duk wani
wankin gidan Rabi’u ne ke yinsa. To ta inn ma za ta fara?
Ba ta da zabin da ya wuce ta dora sanwar sannan
ta wuce bakin magudanar ruwa ta ci gaba da cuda kayan
Sai da ta yi da gaske sannan ta samu ta gama
aiyukanta saboda ciwon qirjinta da ya soma taso mata ga
mararta da ta kulle da bayanta, ta kwanta tana faman
numfarfashi.
Rayuwa ta dawowa Saude sabuwa gaba daya, al’amura sun
karasa damalmale mata, duk wata .wahala da dawainiyar
gidan gaba daya ita ke yin ta, ga yawan tallar datake yanzu
hartafi tada tayi ta safe, ta yi ta rana, ta yi ta dare.
Duk ta bi ta Kara lalacewa ta fige ta zama tamkar
kwarangwal, kazantar da take ciki har tafi ta da, ga alamun
girma na zuwar mata, amma kullum rayuwana Kara
dagulewa take tana Kara shiga cikin matsi da kunci. Kullum
a wurinta jiya ta fi yau.
Tun tafiyar Rabi’u bai sake dawowa ba, ba ta kuma Kara
samun labarinsa ba. Lokaci ya yi ta tafiya kusan shekara
biyu kenan da tafiyarsa kullum sai ta yi kukan rashinsa
wanda ba ta da kamar sa. Sai dai ta yi ta share hawayenta
ta kwanta ta yi barci, qunci da wahalhalun rayuwa sun yi
mata yawa har wani lokacin ta rinqa jin gara mutuwa da irin
rayuwar da take ciki.
Musamman abubuwan da ‘Yar Baba ke mata ya na
damunta, ko'dan ta ga ta fita girma ne duk da Saude a
lokacin tana da shekara sha shida, ita kuma ‘Yar Baba na
da shekara sha biyar, amma tafi Saude garin jiki, saboda ita
irin girman jikin nanne da ita gab-gab mai irin manyan
gaBoBin nan.
Don ita Saude ‘yar siririya ce sosai, kamar a hure ta 'ta fadi,
sai dai tsawo kamar an ja ta. Ita kuwa ‘Yar Baba gajeriya ce
mai Kiba sosai tana da manyan mazaune da wadatar na
shanu, ba laifi 'ita ma kyakkyawa ce tana da dogon hanci
da manyan idanuwa sai dai qaton baki ne kawai ya kware
ta mai cike da haqora kamar an watsa wake a miya.
‘Yar Baba har tafi mahaifiyarta wurin‘rashin mutunci da
rashin tausayi ga gadara da ' rashin kunya da tsinannan
surutu, kamar aku, ga shi' Inna Laure da Malam Bala sun
dauki son duniya sun dora mata, duk wani abin da suka
samu yana kanta.
Shi yasa ‘Yar Baba ta tashi da kwalliya ‘yar gayu ce sosai,
suttura komai tsadarta za ka ganta jikin ta, matsatstsu na
fitar hankali, kuma ba laifi tana yin kyau matuka, amma
idan ka kalli Saude to zaka iya cewa gara jiya da yau.
Yanzu haka Saude tafe take rungume da bokitin alala, tana
gab kawowa kofar gidansu ta hango wata qaramar mota
Joker ta yi fakin mai bakin gilas, ta qurawa motar ido a
lokacin da ta ga na cikin motar, dan iya saninta ba su da
wasu ‘yan uwa masu 'mashin' ma balle mota
Ta Kara gyara rungumar da ta yi wa bokitinta tana kallon
motar, ta zo daf da ita ne ta ga an bude an fito. ‘Yar Baba
ce da wani saurayi suka fito daga
gidan baya na motar hannunta na riqe da irin manyan
ledojin nan na shopping.
Ba ta ankara ba ta ji ta rafka tuntuBe har takalmin da ke
Kafarta ya tsinke dama sun sha duniya duk sun side ga su
daban-daban, wato wari da wari, wani ya fi wani. Hakan
yasa tasa reza ta ragewa babban tsawo, gaba daya
takalman duk sun sha faci da Leda.
Ta durkusa ta dauki takalminta ta wuce cikin gidan nasu
tana gyarawa, duka suka raka ta da kallo, tana jin saurayin
na fadar, ‘Wannan kuma wace ce?”
‘Yar Baba tabe fuska kafin ta ce “’Yar talla ce gidanmu take
tana yi wa Baba ta talla. Wani abu ne?”
Saurayin ya girgiza kai kafin ya ce “A’a, haka kawai amma
dai gaskiya kazama ce, wallahi bakijiba data wuceni
harzuciyata saida ta tashi. "
Daidai nan Saude ta shige cikin gidan tana jin zuciyarta na
mata wani irin kunci. Tana shiga cikin gidan ta ajiye bokitin
tallarta, ta miqama Laure kudin cinikinta sannan ta dauki
abincin dake ajiye bakin murhu babu k0 murfi sai kudaje ne
ke bi yabe
yaBe. Saude ta dauka ta nufi bakin qofar dakinsu ta zauna
ta soma cin dumaman tuwon.
‘Yar Baba ta shigo niki~niki da ledoji Inna Laure da ke
zaune gefen tabarma ta washe baki tana fadar.
“Oyoyo! Ga ‘yata, taho nan zauna, zo zauna mu ga me aka
farauto mana
‘Yar Baba ta cire takalmanta masu mugun tsini ta ajiye
ledojin saman tabarmar, ta cire dan karamin mayafinta mai
kamar matacin koko, saboda shara~ sharansa ta zauna,
gaban rigar nan an yanke shi sosai, maman nan nata ya yo
waje kadan ne kawai ke cikin rigar, Inna Laure na kallonta
k0 a jikinta ita ta ledojin ma kawai take.
Babu abin da ke cikin ledojin sai kayan makulashe kala-
kala, su sweet, cingam, biskit, choculate da sauran tarkace,
daya ledar kuma wasu hadaddun kayan shafawa ne irin na
manyan mata.
Bakin Laure ya Ki rufuwa‘ta dubi ,‘Yar Baba taha fadar,
“Wannan kuma ina ki ka same shi ‘Yar Baba, dan wane ne a
garin nan?”
‘Yar Babe ta tabe baki tana taunar cingam kafin tace,
“Wallahi ban san k0 dan waye ba, nima jiya na hadu da shi
na dawo daga makaranta.”
Laure ta rafka guda kafin ta ce, “Da kyau ‘yata tauraruwa
cikin taurari, mai farin jini, shi yasa. kullum nake Kara son ki
dan anan dai haihuwa ta yi rana, Ki dai tsaya ki nutsu ki
dage ki shake mana wuyan duk wanda ki
Kikeso in ja shi in zaga birni in ratsa Kauye nasa ai masa
daurin huhun goro
‘Yar Baba ta sa dariya tana fadar, “Kai shi yasa nake son ki
Laure.” ‘
Ta mike tsaye tana fadar, “Hmm! Gaskiya wani abu na ci
min tuwo a Kwarya, gaskiya Laure yarinyar can tana zubar
mini da aji a gaban samarina.”
Laure ta zaro ido “Wace yarinyar?”
‘Yar Baba ta yamutsa fuska kafin ta ce, ‘Yo wace ce in ban
da waccan Sauden banzar kullum tana cikin Kazanta
wallahi da ta wuce ki har wani wari za kijitanayi. Agaskiya
nibazan iyaba indaitaga ina zance ta koma ta samu dakali
ta zauna sai na gama, wallahi take ake yi mana daukar
matalauta.”
Laure ta ce, “Ai waccan mai kama da igiyar shanyar ni
kaina abun na damuna da ta tunkaro ki harwani Karni-Karni
za ki ji tana yi ita k0 warin jikinta ba ta ji.”
‘Yar Baba ta ja tsaki ta wuce daki tana faman juya mazaune
kamar mai rawar taBa-kaka.
Wani irin abu ya yiwa Saude tsaye a zuciya, wai harsu
sunada bakinda ’zasu kiratada kazama, alhalin sunfi kowa
sanin kayanta a duniya kala uku ne sumana Laure ne data
gaji da gurza tasakar mata, duk sun sha gamin baki. Daidai
da man shafawa bata da shi a gidan, to balle sabulun
wanka k0
na wanki, sai idan ita ce ta gaji da yawo da kazantar ta ta
siyo omo na goma cikin kudin tallarta idan ta dawo tayi
wanki tadiba aciki tayi wanka.
Idan ba zata manta ba rabon da fatar jikinta ta ga man
shafawa tun kayan kwalliyar da Yayanta ya siyo mata
shekaru uku kenan da suka wuce da ‘yan kwanaki. Ta
mayar da ‘yar kwallar da ta ciko mata ido ta ci gaba da cin
tuwon da ta keji tamkar dutse saboda yanda yake mata
tsaye a qahon zuciya.
Da rana Saude tana zaune saman bencin cikin tasha ta tasa
bokitin alalarta a gaba tana kallon jama’a na ta kai wa da
kawowa, can ta hango Garba Gurgu yana nufowa inda take
yana faman tsangala kafa da shanyayyan hannunsa guda
can gaban qirjin shi a makale yana kadawa irin na wanda
ya shanye
Saude ta Kara hade fuska dan a duniya idan akwai wanda
ta tsana, to bai wuce Garba Gurgu ba, ga shi dattijo dan a
Kalla ya kai shekara sittin, ga shegen iyayi kamar wani
qarami. Yaro
Garba ya qaraso har inda Saude take zaune yana
' faman watso hakora kamar an zana ABCD. Saude ta
daukc kanta ta ci gaba da kallon wani waje. Garba
ya cangala ya zauna saman dutsen da ke gaban ta. “sannu
da hutawa Hajiya Saude ya kasuwar?” Saude ta jiyo muryar
nan kamar an kunna injin
markade saboda girmanta, ta dago idanuwanta tana
Lol i relly feel unhappy for rabiu
[1/17, 7:54 AM] A A Dboy: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚
[1/19, 5:11 PM] I love my mum: *YAR TALLA*

*CHAPTER 12*

kallon shi sai faman sosa gemu yake wanda ke _ faman yi masa kaikayi duk ya yi wani quda~quda da alama ba za a rasa kwarkwata a cikin saba, saboda tsabar qazanta da kurar duniya da ya sha. Saude ta dame zuciyarta ta amsa masa don k0 kadan ba tajin za ta iya yi masa wulaqanci saboda girman shekarunsa dan ya yi jika da ita.
Garba ya Kara watso haqoran nan wadanda su kai kore fatau kamar gansa-kuka yana fadar, “Haba Saude na ga alamar kamar ba ki san magana dani, ki yi hakuri ni masoyinki ne ba makiyinki ba kuma ni aurenki zanyi bawai wasa zaikawoni wurinkiba yanzu haka idankika amince min mahaifinki kawai zan nema a yi magana.”
Saude ta watsa masa wani kallo mai kama da harara ta zumburo baki kafin ta ce, “Ni fa ba anre zan yi ba yanzu
Ya yaqe baki yana fadar, “Haba Saude ke yanzu idan bakiyi aureba saime zakiyi?idan ki ka amince: ki‘ka aure ni, killa ceki zan yi a‘gidana, kin gama zuwa talla idan ma kina tunanin matana hudu ne to a shirye nake dana saki daya daga cikinsu Ya kikacene Saude?” ’ Haushi ya kamata ta mike afusace tadauki bokitin tallarta ta yi gaba ta bar shi nan zaune
Garba Gurgu ya yi dariya yana girgiza kai yana fadar‘ “Yaro yaro ne.” Ya mike yana cangala qafa shi ma ya yi gaba abin sa.
Bayan Saude ta gama tallarta da yamma likis ta koma gida a gajiye ta samu ta ci abinci ta yi sallar Magariba, sannan ta dauki tallar dare ta fita kofar gida ta zauna da ‘yar fitilar aci-balbal.
Kamar daga sama ta hango shi tsangal-tsangal haushi ya cunkusheta ta bade fuska a zuciyarta ta kudiri aniyar idan ya sake ya zo inda take sai ta cire kunyarsa daga idanuwanta ta yi masa rashin kuunya tunda ta lura bai san girmansa ta gani ba ta daga masa kafa ba
Da mamakinta sai ta ga ya yi wa kofar gidansu tsinke, ta saki baki da idanuwa tana kallon shi, ta ga ya kira wani yaro ya tura shi cikin gidansu. Yaron bai jima ba ya fito tana kallon su can sai ta ga mahaifinta ya flto sun tsaya suna gaisawa, gabanta ya yi ’mata mummunar faduwa hankalinta ya yi masifar tashi ba dai Garba wurin mahaifinta ya zoba.
Wayyo Allah na shiga uku! Abin da ta iya fada kenan wasu zafafan hawaye suka shiga zarya a kuncinta tana kallon yanda mahaifinta ke ta faman
washe bakivyasa hannu ya karBi kudin da Garba Gurgu ya ba shi, sannan suka sake yin musabaha, sannan ya shiga gida shi kuma ya wuce abinsa ba
tare da ya kalli inda take ba. Saude ta ta kwashi kayan tallarta ta nufi cikin gida. A tsakar gida ta samu mahaifin nata na fadawa
“Laure kin ga wani abun murna k0 wai mutumin nan Garba Gurgu ke son Saude
Laure ta rangada kuda ta ce, “Kai amma abun ya yi min dadi wallahi, ka ga sai a hada su su duka da ‘Yar Baba. don ita ma ta ce yaron nan mai zuwa wurinta da jar motar nan ya ce zai turo ai maganar aure
Malam Bala ya ce, “Ai ko haka za ai dama ni na amsa masa, yanzu haka ya ce jibi za a kawo kayan nagani-inaso yanzu haka har kudi ya ba ni kin gansu dubu biyu. Kai gaskiya mutumin nan yana da mutunci.”
Laure ta ce“To, ai sai ka tsakuro mini nawa tunda ba kai kadai keda diyar ba
Malam ya ce, “Kefa tsiyarki ke nan duk abin ki ai kya bari' na mutu sannan ki rufe ni ai k0?”
Ya ja tsaki ya cimimiya kwarar dubu guda ya cilla mata ya juya zai tafi ya ga Saude tsaye rungume da kayan tallarta hawaye sun gama bata mata fuska.
Malam ya ce, “Ke kuma fa lafiya?”
Cikin muryar kuka Saude ta ce “Ka yi haquri Baba don Allah wallahi bana san shi ba zan iya aurensa ba, sabo...
Malam ya katse ta ta hanyar fadar, “Ke dalla Saurara mini kin jiki Ba kya son shi sai wa ki ke so?”
Saude ta yi shiru tana faman shashshekar kuka Malam ya sake fadar “Na ce idan ba kya son shi, sai ubanwa kike so?Munafukar Allah,nankikaso ki jibge mana kita zama kitsufa a tasha kina talla, tunda kebaki da tunani ko Allah yataimaka kemaya kawo miki dauki, tunda ki ka tashi akwai bakon takalmin da ya taBa zuwa wurin ki da sunan so, iye?
Amma shi ne har kina da bakin magana. Shekarar ki nawa yanzu a duniya? Kin zauna kin jibge babu mai taya ki kek0 kishin kanki ba kya yi, kina kallon ‘yar uwarki kullum wannan ya shiga wannan ya fita, harda masu motoci, amma saboda rashin kishin kai ba ki taba damuwa ba.” mts! Ya wuce yana fadar.
“Idankinada wandakikeso to saikituro shi ai lokaci bai qure miki ba daga nan har ranar daurin aurenki
Wani irin kuka ya Kara kwacewa Saude, ta aje kayan tallar ta yi dakinta da gudunta tana. wani irin kuka mai tsuma zuciya.
Laure ta ja tsaki tatattara kayanta tana fadar, “Ke
dai kya kai su idan kaya ne dan bakin ciki sai dai ya kashe ki don na gaba ya riga ya yi gaba har abada ba zaki iya kamo taba.”
Saude ta sha kukanta har ta godewa Allah bata . da mai lallashinta haka ta kwanta har bacci barawo ya sure ta. Haka ta farka yau idanuwanta duk sun ‘ kumbura sun yi jawur saboda kukan da ta sha jiya. Haka ta je tallanta ta dawo jikinta ba kuzari kana ganinta ka san tana cikin matsananciyar damuwa. Ta yi zaman daBaro kan sumuntin tsakar dakin, don
kuwa dakin bai da arzikin k0 qaramar tabarma
Saude ta jingina da bangon dakin ta rafka wani ; uban tagumi ko tunanin me take? Oho ‘Yar Baba ta dago labulen tana mata wani shakakken kallo kafin
ta ce
“Idan kin gama tagumin sai ki fito ga kayana na ki hado ki wanke mini. ‘
Saude ta dago da jajayen idanuwanta tana « kallonta, haushi da baKin ciki suka turnuqe mata zuciya, tuni dama batun yau ba take jin takaicin abin da ‘Yar Baba ke mata ba sai ka ce ita ce babbar, ita ma kuma ita ce karamar.
‘Yar Baba ta ce, “Ki ka tsaya kina kallona da wasu kananan idanuwanki can masu kama da na kwarkwata kixo ki min wanki na ce
Takaici ya kuma turnuke Saude cikin fusata ta ce, “Wai ‘Yar Baba me ki ka dauke ni ne jakar ki ko
kuma me? Karfa ki manta a girme na girme ki,amma ki rinka! yi min abu kamar wata yar da ki ka haifa. Ai ba ‘yar wanki ki ka aje ba, da ki ka
dama can da ina miki Inna ce ke sani, amma ke baki isakisani inmiki wanki ba” “
‘Yar Baba ta ce ‘Eh, lallai wuyanki ya isa yanka, har ni ki ke gayawa magana yau k0 Saude dan kin ga Laure ba ta nan lallai za ki san kin yi da diya ba shegiya ba, za ki gani.” Ta juya ta yi gaba.
Saude ta ja tsaki ta IaIIaBa ta kwanta ta ci gaba da nazarin abindayadameta. Bata ankaraba saidaita ji saukar kayan wanki a jikinta ta zbaura ta mike tana kallon mai wannan aikin.
0000000000
“Wato kenan har‘ yar iska ce har kin yi girman da ‘Yar Baba za ta sanya ki ki mata abu ki zage ta ki ce ba zakiyi ba.
‘ To yau sai na ga uban da ya ,tsaya miki ki dauke su maza ki je ki wanke mata, ki shanya ki zauna su *bushe ki linke ki kai mata daki, tantiriya marar kunya, ai na godewa Allah morewa ta dama na ga rayuwarki ta wulakanta, kuma na yi nasara, in dai ina numfashi kin auri Garba Gurgu kin gama, bankadaddiya yanda na ga bayan uwarki da wannan
takadarin ke ma sai na ga naki. ’
" Ta ja tsaki ta wuce tana fadar. “Munafukar banza!” .
Wasu irin hawaye masu dumi suka zubo daga idanuwan Saude tasa bayan hannunta ta goge sannan ta' shiga tattara kayan wankin ta wuce tsakar gidan,
Ta. wanke su gaba daya abun bakin cikinta har da bireziya da dan paint, saboda kawai tsabar raini da wulakanci. Rayuwa kenan.
Kamar yanda mahaifinta ya ce za a. kawo kayan nagani-inaso, haka kuwa aka yi Garba Gurku ya aiko mata da kaya cikin Gari ya yi zafi, dinkakkiyar atamfa ce ta roba riga da zani sai dakakkiyar abaya kwaya daya, sai takalmin roba shi ma guda daya da sinqin sabulu guda da Katuwar ’kwalbar mai dangwali-yaBa, sai naira dubu a sama.
Laure ta dauki naira duban sannan. ta mikawa Saude kayan don ba abin da ya yi mata a cikin kayan. Wasu irin hawaye masu zafi suka ziraro daga idanuwanta tasa hannu ta karBi kayan ta wuce daki ‘ da su.
Tana shiga ta wurgar da su tsakar dakin ta durkushe tana raira wani sabon kukan mai cin zuciya. Tabbas tana cikin halin da ya kamata a tausaya mata,Yayanta ya ringa yi mata gizo cikin idanuwanta ko wane hali yake yanzu? Saude ta sha kukanta ta gaji ta lallashi kanta ta yi shiru
Abu wasa-wasa lokaci ya ci gaba da tafiya, Garba Gurgu ya ci gaba da yi wa Saude hidima, idan abun kirki ne sai Laure ta rike, idan kuma ta gajam tagajan ne sannan za ta ba ta, ita k0 ba ta taba kallon kayan ba don yanda ta tsani mai kayan haka su ma kayan ta tsane su.
‘ Ranar: wata Laraba Saude ta dawo daga tallar safe, misalin qarfe daya na rana, Laure tace yau ba tallar rana ta je
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment