Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ki wuce tasa hannu zata amsa hannunta na rawa ya hada hannun da kudin ya riqe yana dariyar mugunta
Meye sunanki yan mata?
Ta janye hannunta jikinta na rawa tabar wurin a hanzarce har tana tafka tuntube wani dan kamasho da yawo giftawa ta wurin ya tintsire da daria yana fadin dan baba kabar iya shege kabi Allah kaji
Ya miqe yana fadin kai garba mufa duniya gaba muka bata ba baya ba
Garba yace shegen sama kura taga biri
Allah ya kauda abin kunya
Yace ba aminba mu abin kunya binta muke tana guduwa Allah ka hadamu da abin kunya duk inda yake
Duk wurin sukasa ihu ana sai oga allah yabar mana kai
Ikon allah mai tsaida wando ba zariya saude dai bata sake bi ta kansu ba ta nufi inda danladi ke zaune saman teburin cikin tasha tace kaika aika a kawo maka alala ko?
Yace eh zubomin ta murtala biyu
Dadi ya kama saude don tasan daga wannan ta siyar tana murna ta zuba masa tasa masa mai da yaji
Ya zauna ya harde gamida lashe alalannen tas yana lashe baki
Saude na zaune tana kallonsa yana gamawa ya dubeta
Kinada canjin naira dubu?
Saude ta waro ido ita tunda takema bata taba riqe naira dubunba ballentana harta samo canjinta
Ta girgiza masa kai alamar a,a
Yace to ya za,ai kenan ko kuma xo muje na samo canjin saina baki kudinki
Ta mike ta tattara kayan ta bishi
Suka soma tafiya ganin suna shirin fita daga tashar yasa ta dubeshi tace
Ina kuma zamuje?
Yace ban gane ina zamujeba canji zan nema in baki kudinki
Saude tadanyi shiru maganar yayanta ya dinga dawo mata cikin kunne tamkar yanxu yake gaya mata
Saude ki kula banda aje tallah ki tafi samo canji banda kuma kibar mutum ya tafi samun canji shi kadai
Kuma karki sake ki yarda wani ya jaki zuwa wani guri koda kuwa nan da canne
Saude ta dubeshi a,a gaskia nidai kazo muje cikin tashar a samu canjin kaban kudina don yayana ya hanani bin wani
Ya hade rai jini da yar iskan yarinya sai kuma akacemiki kowa dan iskane. To karki bini ki karbi kudinki zauna
Ya wuce zai tafi hankalin saude ya tashi tasan kan kudinnan yau inna laure kashetane kawai ba zatayi ba tayi saurin riqo rigarsa tasa kuka
Nidai wlh saika bani kudina
Ya juya a fusace ya danna mata wani mugun zaki ke dan ubanki bazaki sakeniba? Ta qara cacimo rigarsa nidai wlh saika bani kudina idan naje gida a haka dukana za,ayi
Haushi ya kama danladi yasa hannu ya dauketa da wani wawan marin dayasa saidata kife. Ya juya zai wuce wani magidanci ya kwaso a guje yana kiran
Tsaya nan danladi karka sake ka matsa mugu mai kai mata?
Yayi saurin juyowa jin muryar ogansa
Gabansa ya fadi yai saurin juyowa yace wlh oga yar iskan yarinyace wai dan uwar yarinyarnan waini zata tsare nace
Nace taje ta samo canjin dubu tace babu nace muje na samo na bata taqi yarda toya takeso nayi da itane oga ?
Ya tallabo saude gamida fadin yanxu don rashin imani wannan yar qaramar yarinyar zakaima irin wannan marin?
Yanxu wannan yarinyar fisabilillahi meta sani?
Ya zaburo cikin irin muryar yan shaye shayennan yace oga zaginafa tayi yace idan ta zageka kai yanxu zagi nawa kai mata a gabana ko kunyata bakajiba
Yi hakuri yarinya kinji allah ya saka miki bani dubun na canja muku
Yadan sosa qeya a,a ai gurin ilu zan amso dubun na samo canjin mutumin ya girgiza kai yana fadin allah ya shiryeka ya zaro kudi cikin aljihu ya kalli saude. Kudin naki har nawane?
Cikin muryar kuka tace murtala biyu da goma ne
Ya girgiza kai ya bata sannan ya kalleshi na ranta maka ka samo canjin ka kawomin kudina
Dan ladi ya turo baki yana dan harare harare ya wuce kamar zaikai duka
Mutumin ya dubi saude yace wuce ki tafi kinji allah zai saka miki yace ai harda laifin iyayenku mata dake turoku tallah cikin maza basu san da irin mazan da zaku hadu ba don ko cikin masallaci zakukai tallah sbd tsoron allah sai an samu mutanen banza ballentana cikin tasha inda yayan banza ke taruwa wadanda daman can lalatattu ne ya za,ai ace bazai,ai barnaba fisabilillahi balle ke yarinya qarama
Wuce kije allah yayi miki sakayyah
Haka saude ta wuce gida jiki na rawa da yamma lis don tuni rana ta fadi a lungun gidansu ta hadu da rabiu cikin taron jama,a wai ana duban wata
Saude ta lallaba ta janyo hannun rigarsa yayi saurin juyowa yana kallonta yayi murmushi tana fadar
Tun daga nesa na hangoka duk ka keresu tsawo
Rabiu ya dungureta yana daria yace ke kuma sarkin sharri ko?
Daria itama tayi tana fadin anga watanne yaya?
Yace a,a munadai dubawane amman munasaran za,a ganshi kedai ki zauna da niyyar azumi gobe
Tace ai nima tsayawa xanyi yaya ka dagani inga watan
Yayi murmushi yana fadin so kike yau inna laure tayi kujera dake kenan ko? Ya riqo hannunta
Yace wuce mu tafi kinga har yara su fara tsokanarki
Saude ta juya taga dandazon yaran daketa tsalle suna waqa
Yar tallah qazama yar tallah bata wanka yar tallah bata wanki yar tallah bata sallah yar tallah saidai yawon tallah
Ta dago idonta cike da kwalla ta kalli yayanta tace aidai yaya ina sallah ko?
Kai kawai ya daga mata sbd yaddah abin ke sukarsa a zuciya ya daura hannunsa saman kuncinta inda shatin yatsu suka kwanta wurin yayi jajir abinka da jar fata
Muryarsa na rawa yace waya mareki haka saude?
Muryarta na rawa ta shafa wurin tace wanine ya mareni a tasha yaya wai don naqi binsa ya samo canJi
Rabiu yaja numfashi ai gara dabaki bishiba saude shida allah
Sai a lokacin ya lura da jinin daya kwanta a idonta yAja hannunta suka tafi yanajin zuciyarsa na suya fiye da radadin marin da taji
Suna shiga cikin gidan inna laure dake duqe bakin rariya tana tsane gero ta dago ganin kwanikan duk sun baci da qasa
Jar ubannan kai badai barin alalar kikaimin yauba ?
Saude tace a,a na saida wanine ya mareni harna fadi waidon naqi binsa ya samo canji
Inna laure ta daka mata tsawa ke gafara can munafuka tantiriya idan yace ki bishi ya samo canji to sai meye ?
Koyana iskanci dai ai bazaiyi da keba a balla qashi ko,a karya qafa bani kudina ni ki wuce
Saude ta warwaro kudin a habar zani ta miqa mata. Ta karba gamida kirgawa taga sun cika cas ta ninkesu ta soke akai
Rabiu ya dubeta dauki gora kije kiyi alwala kiyi sallah
Inna laure ta zaburo bazatayi
Maza ga kudi kije ki siyo icce ki daura sanwar tuwo kai kuma ka tattara kayan tallar ka wanke
Idon saude ya ciko da kwalla ta kafama yayan nata ido
Laure ta zaburo mata to yar iska gama kallon nasa kixo ki amshi kudin
Ko ubankima bai isa ya hanaki yin tuwonnan ba ballentana wani banza jaki can zakizo ki karba kokuwa sai naxo nayi miki dukan kawo wuqa?????
[1/8, 4:43 PM] I love my mum: πŸ“šπŸ“šDAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100πŸ“šπŸ“š
[12:17PM, 02/02/2017] πŸ™†πŸΌβ€β™‚@lh@jiπŸ™†πŸΌβ€β™‚: [1/8, 4:44 PM] I love my mum: *YAR TALLA*

*CHAPTER 5*

Tace to yar iska gama kallon nasa kixo ki amshi kudin don ko ubanki bai isa ya hana kiyi tuwonnan ba ballentana wani banza jaki can zakizo ki karba ko kuwa?
Anan muka tsaya
Rabiu ya turata alamar taje ta karba
Laure ta maka mata rankwashi akai wanda yasata fasa wata uwar qara sbd azaba
Ta wurga mata kudin tana fadin munafuka nafa alamar watarana sai kin nemi kifi karfina a cikin gidannan
Dole saina gyara miki zama ta haureta da qafa
Zaki tashi ko sainaxo na casaki? Yar iska kawai lau yayyar banza kawai
Saude ta yinkura ta tashi gamida ficewa tana kuka
Rabiu ya rakata da idanu yana tausayin kansa rayuwarsu na bashi tausayi
A ganinshi babu yaran da suka taba samun kansu cikin halin kunci kaman yanda shi da qanwarsa ke ciki yanxu. Yace ya allah gamu gareka
Laure ta wurga masa murfin kwano ya zabura gamida dawowa hayyacinsa yayi gaba yana tattara kwanukan
Laure tace daka barta ta tafi kaita tunani ai gara ka bita can kuyita
Kwakwale kwakwalenku dan iskan banza da wofi kawai
Maganar ta soki rabiu yai saurin wuceta sbd yaddah maganar ta daki zuciyarsa matuqa ji yake kamar bata taba masa abinda ya qona masa zuciya irin na yau din ba
Saude ta dawo daga siyo iccen ta zauna ta hura wuta gamida daura ruwan tuwo a lokacin har ta fara sarewa da wahala a jikin murhun ta soma jinyar qafafuwanta ta samu daqar ta kammala tuwon da miyar kuka a bakin murhun taci tata ta miqe tayi alwala ta shige dan akurkin dakinsu domin jero sallolin da batayiba
Washegari aka tashi da azumi don haka saude ta samu sauqin wahalar sosai
Dukda aikace aikacen gidan da tayi itada yayanta bata wata sha wahala ba
Saida azahar inna laure tasata dauki markaden tiya uku aka kai markade aka markado shi ta sake daukoshi akai ji take tamkar wuyanta zai karye sbd nauyi
Data kawo markadenma qin sauke mata tayi ta barta dashi akai
Saude tasa kuka don allah kiyi haquri ki saukemin inna kaina zai karye
Laure dake zaune tana kwadon zogale ta dubeta a harzuqe kin fara ko? Wato nabar kwadon zogalen naxo na sauke miki sbd inajin tsoronki ko?
Ta maida kai taci gaba da kwadonta tana fadin bankadaddiyar yarinya masifaffiya
Iklima dake kwance gefenta tace laure bani ruwa insha karya azuminnan zanyi bazan iya kai azuminnan ba
Laure tace a,a ko aike kikasa kanki tuntuni nake fadin ki ajiye ki ajiye kikaqi waike sai kinyi.
Ta miqe gamida dibo mata ruwan cikin randa mai sanyi ta kawo mata ta miqe tasha iya shanta tayi wurgi da modar
Laure tace a!a mai makon ki bani in mayar sai kiyi wurgi da ita
Iklima tayi tsaki ta janyo kwanon kwadon dake gabanta ta soma ci
Laure taja kwafa sannan ta miqe ta dauko modar ta mayar sai a lokacin ta nufi saude data dafe wuyanta da takeji tamkar zai karye
Laure tace shin zaki tace ko na tace? Donna lura wuyanki ya isa yanka
Saude ta wuce ta nufi rijiya sannan ta dibo ruwan ta taceshi tas tana
Tana gamawa rabiu ya dawo daga markaden qosai
Da alamar shima a gajiye yake
Laure ta dubi saude maxa ki hadamin wuta ki hadamin kaskon suya ki hadamin murfi biyu dayan murhun kuma ki dora ruwan koko
Ba yaddah ta iya haka taci gaba da hada hadar hada wuta babu ko tausayawa
Laure ta soya kosai sannan ta sheqa koko cikin bokiti
Qarfe shida tace su dauka sukai makarantar malam hadi tasan almajirai zasu siya
Rabiu ya dauki kokon ita kuma
Saude ya dora mata kosan
Laure ta kwala musu kira suka dawo
Tace kuma ban yarda da ku daukarmin ko kayan sile ba kuje ku dawo kayan buda bakinku nanan zan ajiye muku suka amsa da to sannan suka fice
Cikin ikon allah kuwa suna zuwa ana kiran sallah
Alhaji bashir wani tsohon mai kudine a cikin layin yaxo zai shiga masallaci ya tsaya wurinsu ya zaro dari biyar ya miqawa rabiu yace ya kirga kosan da kokon ya bada sadaka,,,dadi ya cikasu shi kuma ya shige masallaci abinsa
Rabiu ya kirga kayan gaba daya na dari hudu da hamsinne
Yayima almajiran wurin sadaka da koko da qosan
Ana gama sallar alhajin ya fito rabiu ya fada masa ko kayan nawane yace tosu riqe canjin
Sannan yace musu kullun su rinqayin sadaka da koko da qosan zai rinqa biya
Ya zaro wata dari biyar din ya basu rabiu ya amsa cikin ladabi suka cika da murna
Alhaji bashir din yace kuma ku dinga diba kunaci kunji?suka amsa da to sannan ya wuce abinsa
Suma suka wuce gida rabiu ya canja kudin ya dauki canjin yankan da suka rage yaba laure sauran kudinta dadi ya cikata za,a ringa siyan kayana kenan kaga babu bandaro (kwantai) kenan ta dubi
Saude jiki maza ki dauko muku koko suka tsugunna a tsakiyar gidan tamkar almajirai sukasha sannan saude ta miqe ta dauko musu sanwar dimamen daya rage tun na sahur sukaci suka koshi duk da kuwa miyar kukar tayi tsami ta lalace amman a haka suka cinye tuwon tas. Gaskiane da hausawa sukace da babu kwara ba dadi
Sun gamaci suka tafi sallar asham a masallaci suna dawowa su duka suka kwanta a gajiye kamar matattu
Qarfe uku na dare laure ta tashesu wai su tashi susa sanwar tuwon saidawa na asuba
Saude tasa kuka saboda bacci da gajiya dake cinta
Laure ta haskata da cocila au kukama kika tsayayi kenan ni inanan ina jiranki?
To malam zoka gani da idonka saude na zagina
Malam bala ya zaburo tamkar shayayye
Zagi kuma laure wani irin zagi ba dadin ji?ya hankade labulen dakin ke ba magana ake miki ba yar jakar ubannan shine kika zauna kinama mutane kuka
Idanda uwarkice ta dawo daga lahira ta sanyaki aikin ai bazakiyi kukanba ko?
Fitonan inji wanda kike zagi
Saude tahau rantse rantse abinka da yarinta kuma ta rikice sai fadi take wallahi baba karya take ban zageta ba na rantse da allah ban zageta ba
Malam yace shin zaki fito ko saina shigo dakin?
Rabiu yace kayi haquri don allah baba wallahi bata zageta ba
Malam yace au karya tayi mata kenan?
Ta zabura ta boye bayan rabiu tana kuka tana bashi haQuri amman bai sauraretaba yasa hannu ya fisgota daga bayan nasa ya jata a qasa kiyyyyyyyy
Har waje ya janyo igiyar guga ya shiga laftarta ta ko ina bugu bana hankali ba baya ko duban inda zai doka sai ihu take tana roqonsa
Rabiu ya duqar da kansa qasa baya ko iya motsi hawayene kawai masu zafi dake diga daga idanunsa
Saida yayi mata dukan bala,I ya farfasa mata jiki sannan kuma ya tabbar da ko motsi batayi sannan ya kyaleta harya wuce ya dawo ganin alamun kamar ta suma yasa ya janyo ruwa cikin guga ya sheqa mata ta sauke nannauyen numfashi yace sannan ki tashi maza ki dora tuwon siyarwan don lokacin sahur ya gabato
[1/8, 4:44 PM] I love my mum: πŸ“šπŸ“šDAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100πŸ“šπŸ“š
[1/9, 9:55 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*

*CHAPTER 6*

Saida yayi mata dukan bala,I ya farfasa mata jiki sannan
kuma ya tabbar da ko motsi batayi sannan ya kyaleta harya
wuce ya dawo ganin alamun kamar ta suma yasa ya janyo
ruwa cikin guga ya sheqa mata ta sauke nannauyen
numfashi yace sannan ki tashi maza ki dora tuwon
siyarwan don lokacin sahur ya gabato
Anan muka tsaya
Rabiu ya miqe ya rarrafa wajenta gamida jawota jikinsa
yana sharar hawaye baisan sanda wani irin kuka maiban
tausayi ya kubce masa ba saida yai mai isarsa sannan
Ya janyeta ya tafi hura wutan tuwon don daman ya iya
tuwon duk da ba sosai ba don tun yana yaronsa inna laure
ke sanyashi kafin saude tayi kwari amman abinda ba
aikinkaba har saude data girma daga baya taxo ta fishi
iyawa
Saidai yau haka ya zage bakin kokarinsa yayi tuwon da
miya laure ta murmula musu naira biyar biyar ta zuba
tuwon a baho miyar a bokiti gamida basu fitila
Rabiu ya dauki kwanon tuwon akai kana ya dauki na miyan
a hannu yace saude ta koma ta kwanta shi zaije ya siyar
har bakin tasha yaje dukda rashin kyan hanyar ya samu
wuri ya zauna inda yan garuwa direbobi da matasa ke zama
Acan yayi sahur dinsa daida akai sallar asuba sannan ya
dawo saidai bai saida duka ba
Laure tahau fada tsohon munafuki ai daman don mugunta
kaqi tafiya da sauden don kaje ka dawomin dashi
Inda kun tafi tare ganinta ai wanda baiyi niyyar siyabama
sai ya siya tunda yana ganin mace amman shine kai ka
kwasa ka tafi
Zan gani duk uban daya daure muku gindi a garinnan yau
zan ganshi don sahur din da za,ai na gobe da ita zakaje
Munafikin bazan da wofi wanda yayi gadon baqin hali insha
allahu qarshenku bazaiyi kyau ba
Yaddah uwarku ta mace a wulaqance kuma haka zaku bita
daya bayan daya
Rabiu ya ajiye mata bahon ya wuce zuciyarsa na faman
suya da tuquqi mai ciwo
Wasu irin hawaye suka dinga zarya a saman kumatunsa
Yana isa dakin tun kafin ya zauna ta zaburo ta nufo dakin
ta hankade labule saika fito munafukin allah kaxo ka jido
mana ruwa ka tashi wannan yar iskan taxo ta fara aikin
gida ita kuma aiba wani kuka ajeba da zaku kwanta kuyi
barci shikuma yai muku aikin gida maza ku taso
Rabiu ya goge hawayensa sannan ya tayar da ita zazzabine
fal a jikinta tausayinta ya kamashi ya kamata suka fito yana
nashi aikin yana nata har suka gama basu suka zaunaba
saida rana ta haske gari gaba daya
Sannan suka kwanta hakanma badon tasoba saidon babu
sauran ayyukan da zasuyi matanne amman da bata barsu
sun kwantan ba
Sun samu barci yakai na awa biyu kafin masifaffiyar ta
tashesu ta turasu markade daganan basu sake samun
zamaba har dare
Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin kunci da takura har
azumi yakai ashirin da tara kowa nasaran gobe sallah duk
inda ka gifta anata yankan kaji
Wasu natakai markaden abincin sallah inda su rabiu da
saude ke tsugunne kan dakalin dakinsu duk sun zubawa
inna laure ido wacce ke zaune a bakin murhu saman kujera
sai faman suyan naman shanu take
Iklima yar baba (sunan da take kiranta dashi kenan)sai
faman kaiwa da komowa take tana miqa faranti ana tsomo
mata
Suna tsugunne harta kammala suyar ta zuba cikin babban
langa ta juye man tayi daki tabar iklima zaune waje tana
yagar nama
Malam bala yai sallama niqi niqi da laidoji a hannunsa
Rabiu ya tarbeshi da sannu da zuwa ya miqa hannu zai
karbi kayan dake hannun nasa ya noqe yana fadin
A,a barshi kawai gyaramin tabirma kawai na zauna a bakin
dakina
Rabiu ya kwasa da hanzari ya gyara masa tabarman ya
zauna
Sannan shima ya koma wurinsa kamar daxun inna laure ta
fito daga daki tana fadin
A,a malam sannu da zuwa ya amsa yauwa laure sannu da
gida taja ta zauna kusa dashi
Mu muka samu kuma malam?
Ya watsa hakorannan kaman an watsa wake miya kamin
yace kayankune na amso muku daga wajen tela sannan na
qara biyawa ta kasuwa na qara hado muku sauran
kayayyaki wasu kudine nai sa,a wallahi akaimin biyan
bashinsu yanxunnan
Inna laure taja ledar tana fadin sannunka kuwa malam bari
mu gani
Ta janyo ledojin tana zazzagewa
Atamface soso yar yayi aka dinka mata ita da yarta kala
bibbiyu sai takalmi danko kowa guda guda sai tsakiya ta
wuya data hannu kowa da nashi sai gyale kowa da nashi
Dadi ya cika laure aiko saita rangada guda aiyiriri wallahi
tallahi malam ka biyamu allah ya qara budi kaji
Shi kuwa sai ji yake kansa na qara fashewa ji yake dada
akwai saura cikin aljihunsa daya qara zazzage mata
saboda yaddah ta kodashi
Laure ta yafito iklima dake zaune tanacin namanta
Iklima ta kwaso da sauri cikin doki ta zauna tsakiyarsu tana
daddaga kayan
Dadi ya cikata ta miqe tana gwargwadawa tana tsallen
murna
Saude dake zaune ta daga kai ta kalli yayanta idonta cike
da hawaye yaya ni ina nawa kayan?
Rabiu ya kalleta cike da tausayawa yace kiyi haquri kema
anjima zan siyo miki naki kinji?
Kai kawai ta daga masa hawayen da suka taru idonta suka
gangaro yasa hannu yana goge mata
Inna laure ta miqe ta tattara kayan ta shige dasu daki
shikuma malam ya dauki buta yai bandaki
Rabiu ya dubi saude murya qasa qasa yace bari inje in siyo
miki naki kinji?
Kai kawai ta daga masa ya miqe ya shiga dakin nasu ya
bude kayan qyaure ya ciro kudin da yake tarawa yan
hamsin hamsin din da alhaji bashir ya dinga bar musu ta
cikon koko da kosai
Tun farkon azumi har zuwa yau ya fito ya fice abinsa
Kai tsaye kasuwa ya wuce ya zaga sosai ya samo mata yan
kanti doguwar riga da wandonta naira dari bakwai sannan
ya siyo mata yar qaramar abayarnan mai hade da kyale
waddah akema laqabi da gemun shaidan lol ya siyo mata
wannan naira dari biyu da hamsin
Sannan yasai mata takalmin dari biyar
Daman kudin dubu dayane da dari hudu ya tara kuma ko
naira bai dawo da itaba don saima da aka biyoshi bashin
naira hamsin
Yayi sa,a daya dawo ba kowa a tsakar gidan don haka ya
wuce dakinsu kai tsaye
Saude na kwance tayi rigingine tana kallon sama daka
ganta zakasan tana cikin damuwa ya zauna gefenta yana
fadin tashi saude ga kayan na siyo miki
Ta tashi cikin doki ya zazzage mata kayan ta daddaga tana
gama gani ta fada jikinsa domin murna shima ya rungumeta
yanajin wani sanyin dadi na ratsa zuciyarsa
Ganin farin cikin qanwar tasa ya fiye masa komai a duniya
Washe gari itace ta kasance ranar qaramar sallah idan ka
duba jama,a sai hada hada ake kowa yana cikin murna da
farin ciki yara da manya
Kowa yana cikin sababbin kaya cikin tsabta da kamshi
Haka gidan malam bala shida matarsa da yarsa suna cikin
wadanda suka raya wannan rana sunsha kwalliya cikin
sabuwar sutura amman banda
Rabiu da saude
Don tunda garin allah ya waye suketa faman aiyukan gida
suna gama aiyukan kuma saude tahau kai abinci gidaje
yara sai tsokanarta suke qazama qazama yau abin ko
kadan bai dametaba sbd itama tasan yau zatayi tsabtar
kamar kowa itama zatayi kwalliyar da take ganin iklima nayi
ta shafa jan baki tayi kwalliya a fuska tana gama rabon
abincin ta zura guga a rijiya cikin rawar jiki don itama tayi
kwalliyarta tayi yawon sallah
Yan matan unguwar tasu sukai sallama da yawansu don
aqallah zasukai goma duk sunsha kwalliya ji take babu na
biyunta
Saude ta amsa musu sallamar dasuketa rerawa
Yar baba nanan?suka tambaya saude tace tananan a daki
suka wuceta suka shige ita kuma taci gaba dajan ruwanta
tana shirin wankane suka fito suna labarin zuwa masallaci
daganan su wuce yawon barka da sallah
Saude tace dan allah larai nima ku tsaya nayi wanka mu
wuce tare
Larai ta watsa mata wani kallo tabdijam waye zaije yawo
dake yar tallah duk nanma wacece qawarki? Tayi shiru tana
kallonsu
Salame tace ai sunanki ta kira kinga kenan kece qawarta
Larai tayi saurin fadar allah ya sauwaqe saidai ko yar
gidansu takebi yar baba yar uwarta yar baba ta turo baki
allah ya sauwaqe niba yar uwata bace yar tallar gidanmuce
yarinyama tace zata bini ba sai inci uwartaba
Lantana tace to a ware kowa ya ware muga wanda zatabi
kowa ya ware ya daddaure fuska
Saude ta hadiye kukan dake neman kubce mata tace ai
nima yara yanxu zanyi wankana insa sababbin kayan da
yayana ya siyo min inyi kyau
Yar baba tace ke matsa can kyan gidan ubanwa zakiyi
kullum sai qazanta jibeta da wani hancinta can sai kace
kajeren wando duk sukasa daria harda tafawa sannan suka
fice
Saude ta dauki ruwanta ta nufi ban daki tana fadin aidai
allah ne ya bani
Tayi wankanta ba soso ba sabulu don dama ta saba ta fito
ta shiga dakinsu batada ko man shafawa ballentana kayan
kwalliya
Don haka kayan kawai ta dauka ta sanya ta saka sabon
takalminta
Da gyalenta tayita juyawa dukda ba kallon kanta takeba
amman ji take tamkar babu wanda ya kaita haduwa
Rabiu ya riqe labule dariya ta kwace masa yaddah yaga
tanata faman juye juye sai kace mai rawa tayi saurin
juyowa
Tace yauwa shigo yaya wai don allah nayi kyau?
Rabiu yai murmushi mai hade da daria kamin yace aike
daman kyakkyawace qanwata ba kayanne zasu fito da
kyankiba kyankine zai fito da kayan kisha kuruminki insha
allahu indai ina raye saina fito da boyayyen kyanki a idanun
duniya dauko kusar can kixo in kwance miki kanki duk shi
ya bata kwalliyar
Saude tayi saurin dauko masa ya zauna ya kwance mata
tas ya sharce mata yasa tsumma ya daure mata shi ya
lulluba mata gyalen ta miqe zata fita
Sai kuma ina?
Tadanyi jim kafin tace waje zani yace to bari inci abinci sai
in sameki kofar me gari zan daukeki muje kiyi kallon sallar
Dadi ya kamata harda tsalle. Ta fice
Inna laure na zaune saman kujera tanacin soyayyen nama
wanda ko qashi batabamasu saudenba ballentana susa ran
tsoka
Cikin rudu da kidima laure ta dauki sallallami laila ha
illallahu muhammadur rasulillahi
Mezan gani yau ni laure saude zonan dan qashin ubanki
Ta zaburo ta shaqurota ta maqure uban waye ya baki
kayannan?
Yar iska kudina kike sata a gidannan ban saniba,,,
Ta dauketa da mari da qarfinta kokuwa maza kika farabi
iye?
Saude ta fara ihu tana kakari sbd shaqar da tayi mata
Laure ta hankadar da ita har kanta ya bugu da bango ta
shiga kwalama
Rabiu kira wanda tundata soma dukan nata yakejin kamar
ya hadiyi zuciya ya mutu sbd baqin ciki ya fito daga dakin
ya nufota yana fadin gani
Laure ta daukeshi da wani mahaukacin mari wanda ya
sashi dafe kunci ta nunashi da dan yatsa cikin bala,I bakinta
har kumfa yakeyi
Gidan ubanwa aka samu wannan kayan sata kukemin a
gidannan ban saniba?
Aiko sai laure tasa ihu yau na shiga uku na lalace abinda
nakeji a waje yau ya shigo cikin gidana ashe da yan fashi
nake zaune ban saniba
Lol
Su laure manya
[1/9, 9:55 AM] A A Dboy: πŸ“šπŸ“šDAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100πŸ“šπŸ“š
[12:17PM, 02/02/2017] πŸ™†πŸΌβ€β™‚@lh@jiπŸ™†πŸΌβ€β™‚: [1/12, 5:44 PM] I love my mum: *YAR TALLA*

*CHAPTER 7*

Laure ta dauke shi da wani mahaukacin mari wanda ya sa shi dafe kunci, ta nuna shi da dan yatsa cikin bala,i
β€œGidan uban wa aka samu wannan kayan sata: kuke min a
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment