Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

gidan nan k0 kuma me?" Rabi‘u ya girgiza kai cike da kunar zuciya ya girgiza kai alamar a’a, ta hayayyako masa. “To gidan uban wa ta samu wadannan kayan?” Rabi‘u ya hadiye wani abu da ya tsaya masa a. zuciya kafin ya fada mata. yanda a kai ya samu kudin tun kafin ya karasa rufe baki ta sake dauke shi da wani gigitaccen mari cikin zafin zuciya take fadar. “Ni za ka dauka ‘yar iska ni zaka nunawa iyakata, Karya kake Rabi’u baka isa ba wallahi tallahi kaci karya ka kwana da yunwa baka isa kaja daniba,yandanaga bayan uwar data haifeku kuma bazaku gagareniba, don haka ka taka a sannu wallahi idan kai wasa sai na rufe babinka a duniyar nan k0 sunanka babu wanda zai sake ambata a garin nan.
. janyo Saude ta shiga cire mata kayan tana fadin. “Ban yi niyar ta sanya sababbin kaya ba, kuma kai baka isa ka sata sanya suba.”
Ta cire kayan gaba daya ta hankadar da ita gefe ta wuce daki tana. faman huci.
Rabi‘u ya runtse idanuwansa yana jin zuciyarsa kamar za ta fashe saboda baqin ciki da takaici
kukan Saude ya dame shi a zuciya ya tallabo ta a jikinsa ya wuce daki da ita, ya dauki kayanta masu datti ya saka mata ya ja ta a jikinsa ya rungume yana lallashinta.
“Ki yi hakuri ki daina kukan nan haka kinji ’ insha Allahu zan siyo miki wasu ki yi shiru kinji
' ban san yawan kuka
Da qyar ya samu ya lallashe ta ta yi shiru, har wani barci mai nauyi ya dauke ta sai ajiyar zuciya take saki akai akai, tausayinta ya dirar wa Rabi’u. Tabbas bacin ita da ta rage masa yana ga da ya gudu ya bar garin, to idan ya gudu bai san halin da gudar qanwar tasa zata shiga ba, a dole ya zauna, dole zai yi hakuri ya ci gaba da fuskantar rayuwar dake tunkarar su.
' Ya runtse idanuwansa wasu irin hawaye masu zafi suka shiga zubo masa a idanuwa suna sauka saman kan Saude wacce baccinta ya yi nisa sosai. yasa hannu yana goge hawayen da suka Bata. masa fuska.
Haka rayuwa ta ci gaba da taflya babu abin da da ya cansa sai ma abin da ya qaru, kullum da wahalar dake kunno kai. A tallar Saude kuwa sai ma abin da yayi gaba.
Wata rana da safe Sande ta dawo daga markade
Ta zauna bakin murhu' tana hadawa Laure wuta, Malam Bala ya fito riqe da hannun ‘Yar Baba tana
sanye da sababbin kayan makmantar boko, koran wando da farar riga da koran kallabi da farar abaya, ta sha takalminta sandal da farar safa, ta goya jakar: goyan ta.
Saude ta tsaya da hura wutar tana kallon su cike da sha’awa yanda ‘Yar Baba ta yi kyau cikin sababbin kayan, har bata san lokacin da ta mike ta soma bin su ba don kar ma su Bacewa ganin ta.
Tinqis-tinqis ta ringa bin su har suka iso makarantar ba ta tsaya aka ba ta labari ba hae: cikin oflshin Head Master ta bi su ta yi tsaye tana kallon su.
Malam Bala suka gaisa da Head Master sannan ya gabatar masa da ita matsayin sabuwar daliba, shugaban makaranta: ya riqo hannun ‘Yar Baba yana fadin
“Ai tuni wannan ta wuce shiga aji daya dan ta kai shekara goma zuwa sha daya, sai dai a kai ta aji uku idan ma ta maida hankali sosai maimakon ta shiga aji'shida sai ta wuce fom one kawai.”
Malam Bala ya shiga yi masa godiya, Head Master ya dubi Saude da ke tsaye tana zaro ido ya ce “Ke kuma fa lafiya, k0 tare ku ke” ‘
Malam Bala ya yi saurin juyawa yana kallon inda Saude take tsaye
Yasa sallallami ya mike yana fadin, “Yanzu biyo mu ki ka yi ‘yar jakar uba.” Ya fizgo ta yana rankwashi yana zagi.
Head Master ya yi saurin miqewa ya riko shi yana fadin, ‘Don Allah ka yi haKuri Malam ka kyaleta yarinta ce kawai.” _
Malam ya cw, “Haba, haba yanzu wace yarinta ce wurin wannan iskanci ne dai kawai.”
Head Master ya ce “A’a kar ka ce haka kila abin ne ya bata sha’awa hala ita ba ta makarantar neko?
Malam Bala ya cc, “Ba a sa ta ba ita talla take.”
Head Master ya ce, “Kai abin nan yana ci mana tuwo a kwarya wai yanzu yarinya kamar wannan a kashe ta a kashe rayuwarta da talla, kullum muna fadakar da iyayen yara a kan su kula da hakkin. ‘ya’yansu a kan su don kiwo ne a gare su Allah ya ba su amma ba sa ji.
Wallahi mafi yawanci ‘yanmata wurin talla nw suke lalacewa, don a wurin talla ne yarinya za ta saurari maganganun da ba su kamata ba. A wurin talla ne yarinya za ta ji batsar da tunda take a duniya bata taba jin taba. A wurin talla ne yarinya ke sanin abin da ke faruwa tsakanin namiji da mace, ba tare da shekarunta sun kai ta sani ba.
Malam idan na soma karanto maka illolin talla sai mu kwana anan ba mu idar ba, sai kun je inda matatarar maza suke ka iske mace ta kawo talla kaji
ikon Allah, daga nan sai ka fara ganin namiji ya ci abu ya ce ba zai biya ba yarinya na ta bin sa yaqi ya bayar, ka ga ta riko rigar shi sai ya ba ta ya kwace, ka ga yana gudu tana bin shi daga haka sai ka ga kokawa ta tashi, wata rana sai ka same su suna wasan banza da zabgegen saurayi da gandareriyar budurwa mts!” Mts! Ya ja tsaki cike da takaici yana fadin.
“Abin dai sai gyaran Allah.”
Jikin Malam ya yi sanyi ya yi wa Head Master sallama ya tisa Saude a gaba suka tafi yana jin wani abu na yi masa yawo a zuciya.
Yana yin sallama a gidan Laure ta yo kan su tana ' fadin, “Ina ka kamo wannan watsatstsiyar yarinyar? Tun dazu nake nemanta na karade gaba dayan gidan nan ba ta nan tun dazu na gama waina hatta sandare ina nemanta."
Ta fizgo Saude da ke gabanta tana faman kuka, “Ina ki ka je ‘yar iskar nan? Yawace-yawacen bin ' mazan ne naki ya fara k0 Allah ya baki sa,a, wadanda ma suka fiki basu ci riba ba ballantana ke ‘yar ‘ tatsutsuwa, daga ki hura mini wuta ki sa qafa ki fice har in gama wainar ta sandare sannan ki dawo
Malam yace, ‘Gaskiya Laure ki qarasa ido kan yarinyar nan don yanzu Malamin makarantarsu ‘Yar Baba ya rinka gaya mini irin abubuwan da yaran nan ke yi idan sun tafi wurin talla ki rinqa ja mata kunne
Wallahi kar taje ta dauko mana abun kunyar da ba zamu iya saukewa ba."
Laure: ta ja tsaki tana fadin, “Yo ‘yarinya Ma : ta sake ta kwaso abun kunyar ai sAi ta san inda ta nufa, don wallahi korarta za mu yi daga gidan sai dai ta nemi wasu iyayen."
Malam yace, “Gaya mata dai.” Yasa kai ya shige dakinsa.
Laure ta haure ta da qafa, “Tashi ki sauki tallar ki tafi muguwa kuma Batan sisi kikai min sai na ci ubanki cikin gidan nan kin dai san halina ba ni da kyau ba ni da dadl wallahi." ‘
Saude tana kuka ta duka ta dauki wainar ta fito tana sharar hawaye. A waje su kai karo da Rabi‘u yana ta bunzuma sauri yana ganinta ya nufo ta.
“Saude ina ki ka je ana ta neman ki ba inda ban jeba cikin unguwar har kin tada mini hankali.”
Saude tasa bayan hannunta tana goge hawayenta tace, “Ai Baba na bi zau kai ‘Yar Baba makarantar boko shi ne da muka dawo Inna Laure ta doke ni.”
Rabi’u yace, “To ke in ban da abin ki me ya: kaiki bin su Baban na dai san ba cewa ya yi ki raka shiba ko?
Taqara share hawaenta tana fadin “Eh, ai ni na bisu Yaya ina san makarantar in tafi can yanzu?
Rabi’u yace, “Haba Saude ya za ai ki tafi
kowa sanya shi ake baki ga ita ma Baba ya sanya taba?” ‘ Ta ce, “To, kai ma ka sanya ni yanzu.”
Ya dan yi shiru yana nazarin wasu al’amura, Saude ta riqo hannunshi tana girgiza shi, “Don Allah nima ka kai ni ka ji Yaya?”
Ya tsura mata ido yana kallonta zuciyar shi cike da al’amura masu yawa yasa hannu ya dafa kanta cike da tausayawa ya ce, “Ki yi haquri Saude insha Allahu za ki yi karatun boko, duk rintsi sai na ga kin yi ilimi dole zan cika burin mahaifiyarmu Saude kullum maganarta a kan karatunki ne insha Allahu zan cika mata wannan burin, dole zan nemi kudi k0 dan saboda kek0 dan saboda rayuwarki insha Allahu ba zan bari rayuwarki ta lalace ba, ki je tallar l
Ki dawo kin ji?”
Kai ta daga masa ya sake ta ta wuce sannan shima ya kama hanya ya yi gaba .
Al’ amarin ya damu Rabi’u matuqa a zuciya yana san Kanwar shi ta yi karatu k0 dan wata rana ta taimaki kanta da kanta, koda baya raye tunda Allah kadai ya san gawar fari. To wacce sana’a ma zai yi yanzu a duniya? Tunanin da ya fado masa kenan, in dai ba ya rinqa' sana’ar Baban Bola ba, sai dai ita wannan sana’ar dole sai kana da jari a hannu ka rinka tara naka kana siyan na wasu kana
hadawa. Ya ja numfashi sosai yana nazari, can abokinsa Halliru Maigini ya fado masa.
Tabbas shi ya kamata ya nema don yanzu ya tabbatar yana da qarfin da zai iya sana‘ar ginin, ya mike daga kwancen da yakw: ya fito ya yi gaba, yana jin Inna Laure na Kwala masa kira bai kula ta ba, don yanzu yanda yake jin zuciyarsa idan ta ci gaba da takurawa rayuwarsa gab yake da daukan mataki (Namiji kenan).
Cikin sa’a kuwa yana zuwa wurin abokinsa ya raka shi har “wajen mai gidansa ya amince ya karbe shi ya sanya shi cikin yaransa masu nazari da koyan aiki yace zai rinqa ba shi dari biyar duk safiya, amma ban da ranar da ba a fita aiki ba. Dadi da murna suka kama shi a ganinsa yanzu ya samu sana’ar da zai taimakawa rayuwar Kanwar tasa da ita, don haka har ya qagara gobe ta yi don ya fara . zuwa aikin shi ma ya ga yana rike naira dari biyar tashi ta kan shi. Mahaiflyarsa ta fado masa a rai, wayyo ina ma tana raye tabbas da ya zamo daya daga cikin ‘ya'ya masu kyautatawa iyayensu.
Kukan Saude ne ya dawo da shi daga duniyar tunanin da ya lula ya zabura da sauri ya yo waje, ya iske Inna Laure zaune ta dora qafafuwanta kan ta tana ta mintsini ta ko’ina ita kuma sai ihu take, tana roqonta.
Rabi’u ya jingina da bangon dakinsu yana kallon muguntar da take mata ‘yar Baba ta ruga ta dauko bakin wuta ta mikawa uwar tana fadin, “Karbi ki dake ta Laure.”
Rabi’u ya dauke idanuwansa ba zai iya kallon wannan muguntar ba. Sai da Laure ta tabbatar ta yi mata burdun-burdun da tabbuna sannan ta sake ta ta haure ta tana fadin
‘Tsinanniya ‘yar iska gobe ma idan halin ki ne ki sake Batar min da kudi.”
Saude ta kwaso da gudu ta fada jikin Rabi’u tana ihun kuka ya ja hannunta suka nufi dakinsu, ya zaunar da ita gaban shi yana lallashinta, yasa hannu yana goge mata hawayen, mur‘yarshi a sanyaye yake magana
“Kiyi haquri Saude kidaina kuka kinji insha Allahu komai ya kusa zuwa qarshe nan ba da jimawaba
komai zaizama tarihi,yanzu haka nasamu aiki gobe ma zan fara zuwa, share hawayenki nan ba da jimawa ba wadannan hawayen zasu daina zuba kinji?”
Ta daga masa yana gage mata hawayen ya ce, “To ki yi murmushi mana kobakiji dada bane?’
Dariya ta shiga qalqalawa tanayi kamar wata tababbiya shi kan shi har ta ba shi dariya ya dungure mata kai yana daria itama tace ala dole saita rama.

Lol kuma sance dani donjin yaddah laure da rabiu zasu kaya

Naku har kullum
Dboy
[1/12, 5:44 PM] I love my mum: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚
[1/15, 6:40 PM] I love my mum: *YAR TALLA*

*CHAPTER 8*

Rama ya rike hannuwanta duka da ta yunkuro zata dokeshi sai ya tura hannun ta daki kanta, ya yi tayi mata dariya.
Sun shagala sosai kuma kana ganin suka san suna cikin nishadi ba su ankara ba sai dai suka jiyo muryar Laure na fadin
“Sannun ku ‘yan iska watsatstsu, taBarar ceta motsa kenan shi yasa aka shiga daka k0 jin kira ba ayi dakyau aikana qoqari gara kayi amankaka lashe abin ka, ka ga tuwanka manka kenan. Kuyi iskancin ku san ranku babu mai hana ku, ai dama barewa ba tayivgudu danta ya yi rarrafe ba gado kuki ai dama abun, kun tsotsa,ne ku yi sha’aninku kun ji.” Ta = saki labulan ta juya ta yi gaba. Rabi’u ya girgiza kai yana jin tamkar zuciyarsa
Zata fashe saboda bakin ciki, idan akwai abin da ke
daga masa hankali duniya ya dungunzuma masa lissafi to bai wuce a tuna masa abin da ya faru a * baya ba, wanda ke daga masa hankali ya dagula masa lissaii duk wata annashuwa ta shi take take Bacewa Ya jingina da bango yana kallon Saude ya jirkita ta kwanta jikinta a sanyayc. ‘ Washe gari tunda safe Rabi’u ya yi jidar ruwansa gamida duk wasu aikace-aikace da ya san zai yi qarfe takwas daidai na safe ya sa kai ya fice abinsa b tare da ya fadawa kowa inda za shi ba.
Saude ta dauki taller wainarta ta tafi sarfiyar yau jikinta jinshi take babu dadi ko kadan da kyar ta samu ta iya saida wainar a hanya ma amai sau biyu tanayi harta samu ta iso gida da kyar, ta mikawa Inna Laure kudin tana neman faduwa, saboda juwar da ke
barazanar kayar da ita. Inna Laure ta zuba mata idanuwa cike da jin haushi kafin ta ce.
“Wannan lambon kuma na mene ne kl ke faman yi? Duk na kar ki dauki taller alalan ce k0 me?”
Saude ta girgiza mata kai alamar a’a tana nishi. Inna Laure ta ja tsaki tana fadin “To sai ki wuce ki dauka ga alalan can ta Murtala shida ce da goma
Saude ta langwaBe kai cike da jin jiki ta ce, “Ki yi hakuri don Allah Inna wallahi ban da lafiya bazan iya ba.”
Inna Laure ta waro ido waje tana fadin, “Uban me ki ka ce? Ni ki ke fadawa ba ki da lafiya Saude? To Allah yasa mutuwa ki kekina dawowa wallahi sai kin dauki tallar nan, ‘yar iska na lure kwanan nan wani tashan balagar tsuntsaye ce ke cin ki, kuma wallahi zan tatsiye miki ita tas za ki tafi ki dauka ki bani wuri k0 kuwa?”
Saude ta wuce tamkar wadda ta yi ciwon shekara goma ta dauka ta fice, tana tafiya tana hutawa k0 ta sule ba ta kai ga siyarwa ba ta zauna saman dakalin qofar wani gida tana faman kakarin amai numfashinta na fita sama-sma tun tana sanin inda
Har ya kai ta flta hayyacinta ta fadi can gefe sime.
Wani mutum da ke tahowa ta Iayin cikin shirin masallaci kasancewar yau Juma’a ce ya yo kanta a gigice ya jijjiga ta amma ba ta k0 motsi, kafin ka ceme mutane sun taru a kanta ana ta tambayar wanda ya san ta, amma babu saboda kullum dai ana ganinta
tana wucewa babu wanda zai ce ga daga unguwar da take tahowa, tun kafin a tafi masallaci har aka dawo sallar Juma’a, amma ba a samu wanda ya san unguwar su Saude ba.
Yamma liqis Rabi’u ya dawo daga wurin aikinsa ya yi dumu-dumu da yashi da suminti kana ganinsa kaga mai aikin Kasa, ya yi sallama ya shiga gidan. Laure da ke zaune a bakin rijiya ta dago tna kallonsa ya giftata zai wuce ta zabura ta mike ta cimimiyo rigarsa tana fadin
"Daga gidan uban wa ka ke dan iska tun safe ina gararin neman ka rumfa-rumfa ban gan ka ba daga ina kake?”
“Daga wurin aiki.” Ya ba ta amsa kai tsaye
Laure ta maimaita, ‘Aiki. Aiki fa ka ce? Eh lallai Wuyanka ya yi kwari wato harka san ka kakkare
Ka tafi wurin aiki, tabbas lallai wata rana sai ka
Shaqeni shi kenan jeka jeka kawai." Ta fada tana . murmushi
Rabi’u ya wuce dakin su kai tsaye ya cire rigar ya kwanta saboda gajiyardaya kwaso ga shi abinda ba ka sababa. A take bacci barawo ya sace shi, kiran salla ne ya farkar dashi
Ya tashi a gigice saboda rashin ganin Saude ya fita tsakar gidan amma batanan abinda batataBa ba yanufi kofar dakin laure ya duka daga bakin qofar muryarshi da alamun rudani yace, “Inna ko $aude tadawo?”
Laure ta watsa masa wani kallo kafin tace,“Ban saniba tana indata dawo da baka gantaba Ko kudice dazan Goyata?”
Gaban Rabi’u ya yi mummunar fad'uwa hankalinsa yayi masifar tashi.To inatake?
“Shin ba zaka tafi kanemota baneba zakatsaya kallon jama’a ne?” Muryar mahaifinsu ta katse masa dogon tunanin dayake ciki
Ya yunkura ya mike jikinsa asanyaye yafice.'shin ta inama zai fara neman nata ne? Wayyo Allah Ya Ubangiji kada kajarabeni da abinda bazan iya daukabaYaAllah kasa duk inda Saude take tana hannu nagari.
Abinda yake fada kenan azuciyarsa,yayanka yayi hanyar rewa
Tasha dukda yanada yaqinin zuwa yanxu an rufe tashar amman babu yaddah zaiyi yanashan kwanar layin nasu ya
Ci karo da jama’a wani na rungume da Saude wai za,a kaita gidan mai unguwa.
Hankalin Rabi'u ya yi masifar tashi ya tsare su yanavfadin qanwarsa ce su kai masa ‘yan tambayoyin da za su yi masa sannan suka ba shi ita ya nufo gida hankali tashe tun a hanya yake ta faman rusar kuka don shi duk a tunaninsa mutuwa ta yl.
, Yana shiga gidan ke Laure ta zabauro masa wai ina kayan tallarta, ita ta sana’aarta take ma. Wani_abu ya zowa Rabi’u iya wuya yanda ko kadan mahaifinsu bai damu da halin da Sauden ke ciki ba. Ya shimfideta a tsakar gida jikinsa na rawa ya nufi rijiya ya janyo ruwa ya shiga Sheqa mata, cikin ikon Allah ta farfado m har tana magana, ko motsin kirki ba ta yi, saidai sambatun datake tyi iri irin wanda ya zare hankali
Rabi’u yana kuka ya nufi dakin mahaifin nasu ya durqusa gabansa yana fadin, “Don Allah Baba ka ba ni kudi in kai ta asibiti ta farfado, amma ba ta motsi kada ta mutu.’
Malam Bala ya ce ‘Rabi’ u ta mutu mana, ai ranta ba a hannuna yake ba, ban da ikon sanyawa ta rayu haka kuma banda ikon hanata kaxo sai wani rawar jiki kake akan ciwon d bai taka kara ya karyba
Don nasan baxai wuce bugun iskaba da masassara
Ka je ka kira Malam Maidala yaxo ya yi mata rukiya ga naira hamsin ka siyo panado ka bata ta sha.‘ Ya wurga masa kudin.
“Tashi ka tafi.”
Rabi’u ya mike yana jujjuya kudin a hannunsa wani sabon kuka ya Kara kwace masa ya sa kai ya fita, kamar yanda ya ce haka ya je ya kira Malamin yazo ya dubeta shida kan'shi yace ba iskabane zafin zazza6i ne, don haka a kai ta asibiti. Ya dawo ya sanar da mahaifin nasu, a lokaicn har ya kwanta. _
Don haka a fusace ya tashi yana fadar, Wai menene zaka dame ni da zarya shin wai nina dora mata ciwon ne k0 k0 me?”
Rabi’ u yace, “Kayi hakuri Baba, Malam ya ce ciwonta na asibiti ne zazzaBi ne mai zafl.”
Yace ‘To shine har saika tadani ina baccina, tunda yafada maka zazzabine kaje katsinko ganyen dalbejiya kai mata surace mana, haba ban san matsawa wallahi.”
Rabi’u ya mike jiki a sanyaye hawaye na faman zarya a kuncinsa, tsanar mahaifin nasu ta qara mamaye masa zuciya gaba daya. A lokacin karfe sha daya na dare ne haka ya shiga dakin ya dauki Saude a kafada ya tafi chemist da ita.
A lokacin Bala mai allura‘ na' qoqarin rufe , chemist din nasa Rabi’u ya dube shi, ‘Don Allah
Malam Bala marar lafiya na kawo na ga kana kokarin tashi.’
Mal. Bala ya waigo yana kallonsa kafin ya ce, “Ashshal Waye ba shi da lafiyar?”
Ya ce ‘Wallahi Saude ce tun dazu zazzabi ya
kamata hadda su suma, yanzu haka k0 motsi bata ”yi
Bala mai chemist yace, “Ashsha! Ai kasan ni ban san sunansu na gaskiya ba, ‘Yar Baba k0 “Yar Tallar wacce cikinsu?”
Rabi’u ya' dan ja fasali kafin ya ce ‘Yar tallar dai’
Bala mai allura ya ce ‘Ikon Allah, saukota na ganta.’ Rabi’u ya sauko ta yana nuna masa har a lokacin sambatun ta kawai take.
Bala mai chemist ya ce “Ai wannan zafin zazzbine wallahi maleria, wato zazzaBin cizon sauro, gaskiya Rabi’u ku gaggauta kai ta asibiti don Wannan ciwon bana zama bane hadari ne babba dole ana buKatar likitoci. kamar biyu zuwa uku a kanta.’.
Hankalin Rabi’u ya Kara masifar tashi ga shi bai ajiye ba, bai ba wani ajiya ba, nairarsa dari biyar ta aikin yau, ita kadai yasan ya mallaka sai hamsin dinda Baba ya ba shi. Ya dubi Bala mai allura yana fadar.
“Don Allah Malam idan da akwai taimakon da zakamin ka taimaka min ai mata kafin zuwa safe na
ga abin da Allah zai yi, amma wallahi yanzu ban da halin tafiya asibiti ”
Bala mai allura ya ce‘Ai babu wani taimakon da zan iyayi yanzu anan nafada maka hatsarine a wurina na duba ta cikin wannan yanayi da take ciki.’
Rabi’u ya kifa kansa a ka Saude yasa wani irin kuka mai ban tausayi, ya zai yi da rayuwarsa tunda baidashi baidawada zai taimakamasa yana kallo rayuwar ‘yar uwarsa za ta salwanta, saboda kawai ba shi da shi... Kuka yake sosai.
Sosai kamar ransa zai fita

I will be back in no time

Via Dboy👍🏻
[1/15, 6:40 PM] I love my mum: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚
[12:17PM, 02/02/2017] 🙆🏼‍♂@lh@ji🙆🏼‍♂: [1/17, 7:43 AM] A A Dboy: *YAR TALLA*

*CHAPTER 9*

We miss 1page cours d page is damage I cnt c writting
clearly
Rabiu ya shiga mazaunin direba ya ja suka tafi. Kai tsaye
Federal Medical Center suka nufa a lokacin har shabiyu na
dare,ne da ‘yan mintuna.
Suna zuwa kuwa abin kada ma'aikacin wurin
cikin gaggawa aka wuce da ita Emagcncy Room da ita,
Malam Bala mai allura ya tsaya sai da ya kammala masa
duk wasu ‘yan shige da ficen daziayi masa sannan yayi
masa sallama ya tafl office don dama aikin dare yake.
Rabi’u ya dinga zabga masa godiya kamar zai kwanta
masa, abin har ya soma bashi kunya. ‘ A asibitin suka
kwana washe garida safe likitan daya dubata yaace yakoma
ya tawo da ‘yar uwarta mace ta kula da ita, hankalin Rabi’u
ya tashi ya ce, “Ai bata da ‘yar uwa.’ Likitan ya ceto gaskiya
ba zaiyiwu zamanka wurin jinyaba dole saika samu mace
yar uwarta koma wacece wadda zatayi jinyarta
A dole Rabi’u ya mike ya tafi zuciyarsa na faman suya, ya
nufi gida a qafa a lokacin karfe takwas 'na safe Yana isa
gidan ya samu Babansu a gidan ya duqa ya gaisheshi
yawaigo cikin Bacci yana kallonsa kafin ya ce
Rabi’u ka cika dan kanka yanzu gidan uwar wa ka kwana?” .
ya sassauta murya kafinn ya ce “Na kai
Saude Chemist ne daga nan mai Chemist din ya ce
yana taba ta yace wai dole sai an kai ta asibiti shine ya
daukemu yakaimu asibin acan:aka kwantarda ita,yanzu
haka ita tana can asibitin tama samu sauqi sosai, don har
tana iya gane wanda ke kanta‘. Yanxu likitanne ya ce in'zo
in taho da ‘yar uwarta mace, wadda za ta yi jinyarta.”
Kafin Malam yace wani inna laure ta hankado labule ta fito
tana fadar. “Ai k0 sai ka nemi ‘yar iskarda zata zauna
zaman jinyar badai laure ba donni hangar asibitinma banabi
ballantana in wuce ta gefensa, miyau wannan ban iya
hadiya cikin asibiti, don haka ma kar ku sake ku sani a
lissafi
Malam ya ja ihsali kafin ya ce ‘Ni duk ba ma wannan ba
Laure, shin kudin da za a biya a asibi'n ubanwa ya ajiye
zaibada nidai banidasu kuma ban ajiye ba, nan na ce kar ka
kai ta asibitin nan ammadayake kaibadan arzikibane shine
saida kakaita don kanunamini iyakata. Totundakai
dankankane basai kayi yaddakasoba,‘nidai kaga tafiya ta
kwandala ban maganinta.’ Yana gama fada ya juya ya fice
Laure ma ta hankada labule ta shige dakinta ta bar shi nan.
Rabi’u ya mike jikinsa amace ya rasa inda zai saka
Kansa haka yayita gararamba a gari data qarshe da yaga
vashi da mafita
Dole ya juya ya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment