Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

so abune dai da bakada yanda zakayi dashi Mom gsky a dauki mataki akan lamarin nan wlh idan aka barsu a gdannan zasu dorawa baiwar Allah hawan jini a banza ita gata mijinta ba mazauni ba balle yake rarrashinta" miqar da ita Mom tayi ta kama hannunta suka fito wani abun mamaki duk inda sukabi sai suga bayin gidanma suna darewa suna barmusu gurin lamarin daya qara tashin hankalin su.




Zama tayi a parlour tanaci gaba da kukanta da iyakar rarrrashin mutum bataji a ranta zai iya fada mata kalmar da zata iya kwantar mata da hankali ba, sai yanzu mom ta magantu da cewa “duk wani abu da zai faru ko Kuma yake faruwa Aminatuh kiyi watsi dashi ki durfafi rayuwarki ta gaba kisa mijinki da yayan da zaki Haifa masa a gaba shine komai zaizamo miki me sauqi Amma indai kika sake mutane suka jefa miki qulli a ranki to zaki samu matsala kinsani babu wani abu daya gagari Allah wlh Meenah banida ikon hana wannan mgnr fita da tun farko ban Bari ta fita ba balle tazo ta damemu hqrn dai shine zakici gaba dayi domin shine ya kamaki tsarin gdannan mijinki ya taka shiyasa komai ya dada lalacewa Kuma nasan komai akanki zai kware"
Har Mom ta gama mgnrta Meenah kallonta kawai takeyi daidai lkcn wayar Mom din ta dauki ruri ta duba taga number Rasheed ce gabanta ya fadi tayi kamar bazata dagaba ya sake Kira tadai sanyawa kanta nutsuwa ta daga suka gaisa yace “meye yake faruwa da Meenah ne na Kira wayarta yakai sau goma bata dagaba" cikin daburcewa tace “eh wlh batajin dadine tunda muka iso kasan yanayi na me qaramin ciki dan gwajab² din hanyar nan yasa mata zazzabi Amma dai Alhmdllh yanzu ta samu bacci, ya aikin?"




Aje numfashi yayi yace “alhmdllh hankalina yaqi kwanciya ne da zaman Meenah a gidannan Mom inajin tsoron kada a Dora mata damuwa ba iya ramawa zatayi ba sanyinta yayi yawa ni kadai ne Meenah bata bari Amma Urwat ma idan yayi mata qyaleshi zatayi" “nasan da hakan Rasheed babu abinda zai faru insha Allahu ka kwantar da hankalinka ai bama dadewa zakayi ba ko?" Gyara kwanciyarsa yayi yace “wata uku zanyi saidai fah banjin zan iyashi ni kadai tun jiya nasa a gyaramin gda a barreck idan naga yanayin garin Daltan Babu matsala zanzo ko na turo a tafi da ita"
Fatan Alkhairi Mom tayi masa sukayi sallama ta dubi Meenah tace “ko ya Kira kada ki daga kinsan halinsa idan yasan abinda ya faru bazatai kyau ba ki taimaka wajen boye koma mene daqyar nasamu na dsidaitashi da Mai Martaba mijinki akwai kafiya kamar kafirin farko don Allah Meenah kiyi hqr ga yar'uwarki nan ko kowa yaqiki naji a jikina jinina bazasu gujeki ba su kansu yayyenku sun gamu da kaidin matane musamman Arman saidai addu'a"
Juyawa Mom tayi ta fice Ya'isha ta zauna tana qara bata baki harsaida ta Dan saki jikinta suka qara gyara abinda baiyi musu ba tayi hamma Ya'isha tace “yadai da miqa ko a Kira Big Cele ne?" Murmushi tayi tana shafa cikinta tace “nazama jaka wlh bana jure yunwa Kuma da naci zanji an yasheni kamar wacce mukeci da wani kiga fah jikina har rawa yakeyi" dariya Ya'isha tayi tace “tab kice Big Cele ya qara daure dammara da saqale bindiga" duka takai mata sukayi dariya tace “hankali ne baa kwance ba bari na Kira Mom ta turo a kawo Mana abinci" sallama tayi tace “unborn din danki ne yakejin yunwa Yana neman wahalarmin da yar'uwa" dadi sosai Mom taji dajin ta saki jikinta tace “ok Bari na turo kausar ta kawo muku abinci tun dazu na hada wani abune ya daukemin hankali"




Suna nan sunata hirarsu gabadaya hirar akan bikinsu Ya'isha ne Kausar ta shigo ta aje musu abincin ta fice Ya'isha ta dauko abincin ta zubansu abincin sunaci suna hirarsu ya sake Kiran wayarta ta dauka ta manna a kunnenta tace “girman kujerarka duniyata" ajiyar zuciya yayi yace “har naji dadi nakasa aikata komai banji lfyr rayuwata da babyna ba hope dai qalau kuke?"
Murmushi tayi tace “ni qalau nake saidai ko kai naji yanayinka a kasalce" qasa yayi da murya yace “meye yake faruwa a gdannan ne jikina na bani ba lfy ba kamar akwai abinda ya faru" shiru tayi tanajin bugun zuciyarta na qaruwa Ya'isha ta zungureta tayi firgigit kamar wacce ta tashi a bacci yace “akwai abinda yake faruwa din kenan ko?" Saurin girgiza kai tayi tace “babu komai kawai dai naji Babu dadine dazun Amma yanzun na warke" bawai yarda yayi ba domin a muryarta kadai ya fahimci akwai damuwa so baison takurawa da tambayar hakan yasa yace “shikenan lkcn la'asar yayi ki huta My Meenah Baffa'am dinki Yana kewa dama shekaran jiya baki baniba Kinga sai kumburamin wando qawanki takeyi" dariya tayi shikam baijin kunyar kalaminsa tace “idan ka zaneta zata nutsu fah....." “Wht?" Ya furta da qarfi tasa dariya shima yayi dariya suka aje wayar tare ta juya zatayima Ya'isha mgn batanan ta miqe ta kulle barayinta tayi sallah ta qara gyaggyarawa shiru tana jiran Ya'isha har dare tama hqr tayi kwanciyarta a falon tana kallon wani Korian series tana latsa wayarta lkc zuwa lkc tana duba agogo sai goma ta miqe ta bude sashin da dakunan baccinsu suke ta shiga ta watsa ruwa ta haye gado ta qudundune yanayinta yasa batada wuyar bacci nandanan bacci ya dauketa sai asuba ta farka shima tashinta yayi a waya tayi sallah ta shiga harkokin gyaran gdanta duk da akwai masu gyarawa tafiji a ranta tayi abinta domin ta fahimci mijinta ba Maison a rinqa dafdala a sashinsa bane.





Goma ta gama tayi karinta ta sako hijjab dinta har qas ta fito tare da kulle sashin ta nufi cikin gdan domin gaishe da surukanta abin mamaki yau dinma duk inda tabi sai taga jama'ar gurin sun miqe zunbur sun watse wani sanyin jiki ya kamata itan da a baya idan ta fito kowa yakeson yaga tayi masa mgn yanzu itace wai bayin gidan ma suke gudarwa hawaye ya ciko idanunta tayi qarfin halin shanyewa taci gaba da tafiyarta harta Isa qofar shiga bangaren matan gidan ta murda qofar ta shiga falon tare da sallama Mom Addah Amrah sai Urwat sune kadai a falon sai Mai Martaba dake duba jarida a gefe.
Ta nemi guri a qasa nesa da Mom cikin ladabinta da alkunya ta fara gaishe da Mai Martaba ya amsa da sakin fuska yace “Aminatuh baiwar Allah an fito to ya nauyin jikin?" Kunyace ta kamata yayi murmushi yace “kunyar nanan dai to madallah Allah yayi albarka" amsawa Mom tayi da Amin suka gaisa da Mom itama cikin kulawa take amsawa ta juya ga Addah Abulle ta gaisheta ta amsa mata Babu yabo Babu fallasa bata damu ba domin tayi alqawarin jure komai domin mijinta ta dubi Amrah dake kwance tana latsa waya tace “sister ba mgn...." Da sauri tayi jifa da wayar tace “wace sister taki ta ina muka hadu Allah ya kiyaye irin gidannan Babu yanlasan wlh saidai a kwasosu a kwashe² kamar yanda aka kwaso Mana ke ak......"
Wata qara ta saki tare da dagowa ga mamakinta sai taga Kareem ne ya sake kai mata duka Addah ta janyeta yace “na dade Ina fada miki ki rinqa saita kalamanki banason ku rinqa shigar da kanku abinda babu ruwanku kunqi ko to waima Ina ruwanku da lamarin Aminah ne kuke neman hana masa mata sakat a gidannan nine dai zakuce kuna tayawa jin haushi Kuma bada ita kuke ba da ubangiji kuke domin shine yayi alqawarin bazai taba bayar da rabon wani ga wani ba Aminatuh bata yaudareni ba tasoni tabani kulawa ta shirya rayuwarta dani qaddarar baa kaina take ba akan Ya Rasheed take matarsa ce rabonsa ce da iya wuya saita isa gareshi ni na yarda waman qaddarallahu haqqan qadarihi Babu wani ruwa dazai kwaranye zanen qaddararmu ta son Abu daya nida dan uwana Kuma dama duk inda mutum biyu sukayi tarayya akan son Abu day to dolene daya yayi nasara daya ya fadi"




Yana fadin haka ya juya ya fara takawa cikin tafiyarsa ta isa har yakai bakin qofar fita ya tsaya ya juyo idanunsa taf da hawaye yace “Meenah!" Yanda ya Kira sunanta hatta Mai Martaba Saida ya dago idanunsa suna tsiyayar da hawaye yace “kada komai ya dameki bakiyimin komai ba qaddarar so ce a haka har gaban abada ke nakeso Amma bazan taba goyon bayan ki bijirewa mijinki ba domin nasan kema kinasona Meenah (Fa Inna maal usri yusra) ba zance na bane zancen Allah ne kiji haka a ranki"
Da sauri ya fice fit daga falon yabarsu zaune da sanyin jiki itakam Meenah gabadaya kalamansa tsinka mata jijiyoyin jikinta sukayi ta kasa koda miqa wuyanta miqewa Amrah tayi tana taunar dabino tace “aikin banza Harbin daurarre dama tunda an cinye maka zuciya Ina zakaga laifinta baqar munafuka wlh bantaba tsanarta irin wannan lkcn ba" daquwa Mai Martaba ya watsa mata yace “dake da tsanar na hada na dakaku a turmi naci kan uwarku ja'ira me qirar yar tsana" sumsum tabar gurin tana haarar Meenah Mom ce tace da ita Aminatuh tashi ki shiga ciki ki kwanta naga kamar sanyi kikeji ko?" Miqewa tayi ta nufi sashin Mom ta bude ta shiga ta ishe Ya'isha na guga ta karba tana tayata suna hirarsu itadai qarfin hali kawai takeyi da taji ma bazata iyaba sake mata gugarta tayi ta koma ta kwanta nandanan zazzabi ya rufeta wasa kamar wasa Abu ya rinqa qarfi hardai a qarshe Saida aka Kira likita ya daura mata ruwa da magunguna.




Kwananta biyu tanajin jiki sannan taji dama sabon laulayi yasata a gaba batada aiki sai cin gurji shi dayane abincinta aikuwa nandanan ta zuqe kowa yazo ya dubata a gidan Amma Banda Aliya da Nana matan yayyen mijinta itakam Addah cewa tayi haqqin dantane da tun ranar daya zabgawa Amrah Mari yake kwance ciwon zuciyarsa ya tashi yanata Aman jini duk ya fice daga hayyaci sunan matar yayan nasa kawai yake kira a qarshe dai dole Mai Martaba ya daukeshi yabar qasar dashi.
Itakam tama manta da babinsa ta kanta takeyi da lfyrta gabadaya ta zuqe ta rame saboda tsangwamar da take fuskanta a gidan batada wani sauqi a gidan saina bangaren surukarta da kullum take rarrashinta da bata baki shikam Rasheed baisan meye akeyi ba kasancewar daga Dalta Enugu aka turasa wayarsa ma ba samuwa takeyi sosai ba a haka dai har bikinsu Ya'isha ya qaraso aka shiga hidimar biki ka'in da na'in dake bikin yazo mata a wani yanayi batama fiye shiga mutane ba warin jikinsu amai yake sanyata.





Ana jibi daurin auren yan uwan Mom sukazo daga Mali ranar Juhud yini tayi a daka Babu lau tana kwance taji an shigo part din batada qarfin miqewa ma shiyasa ta sake bin katifa ta lafe ya bude dakin ya shigo cikin dokin ganinta da shauqi ya tsaya jikin qofar dakin yace “Uhmmm qaddarar so! Kenake so!! So habo ya zabaran yayi naso!!! Yadda nakeyin nazarin so habone!! Ni inajinsa arai tuntubene!!! Dan Adam shikuwa Mai kuskurene!!! Afuwa ki agaran nayi zaune!!! Ban iyawa da rabon qaddarar so!!!!!
Wani tsalle tayi ta saki ihun murna ta rungumeshi tana kissing dinsa ta ko Ina shima kissing dinta yakeyi suka zube a gurin ta hade bakinsu cike da shauqin qaunarsa sun jima a haka ta janye ta shafa kansa zuwa qirjinsa tace “miss ur My life...." Miqewa tayi da sauri hawaye suka zubo mata ya miqe ya riqota yasa harshensa ya lashe hawayen yace “ina tsananin buqatar matata wlh nasha wahala a wata ukun bantaba gwadawa ba......" Hannun takai ta shafo mararsa zuwa qasa ta dago tayi masa murmushi tace “burina kenan Abba Aanam ya kasance me kiyaye kansa hakan shine farin cikina" harararta yayi ya riqe kunnenta yace “bakijin tausayin babynki?" Tasan meye yake nufi ta riqe hannunsa tace “asalin tausayi ma kuwa duk da ajiyarta ya hanani sakat Amma zan bata kulawa bakin gwargwado da haka ta samu ya tashi ta hadamai ruwan wanka yaqi Wai saidai tayi masa batason qamshin sabulum hakanan ta daure ta tayashi suna gamawa ya kulle dakin ya janyota jikinsa ya fara lalubeta ta sakensa jiki sosai sukayi qara'in watanni sun gurji juna kuwa son ransu ita kanta ta yarda sunyi missing junansu bayan komai ya nutsa ne ya dubeta itama shi take kallo ya lumshe ido yace “da kewarki da qaunarki zan mutu Meenah kowanne motsina kene na yarda so Yana canza mutum wlh tunda na tafi naji bana sha'awar kowacce mace bayan ke ko nayi qoqarin nema idan na tuna dake sai naji na qoshi nake nakeson ci.........




*JH013 littafina na kudine idan kinsan baki siya ba don Allah kada ki karanta, bansanki ba bare na yafe miki haqqina dake kanki*

*Regular group 300 VIP 600 via bank Account 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank or card for This number 09013718241 only WhatsApp or vtu only for dis 09031307566*
*Ga yan Niger da suke son wannan littafi basusan ya zasuyi ba ga number da zasu tuntuba 94775574 zasu tura katinsu daidai da kudin littafin sai suyimin mgn na gde*







*Oum Hairan*
[8/1, 8:43 PM] Oum Hairan: *0025* Sake shigewa tayi jikinsa tana sunsunar qamshin turarensa cikin wata murya me kashe jiki tace “inasonka My world" matseta yayi Yana shafa cikinta na watanni hudu yace “inasonki fiye da yanda nakeson komai a duniyata ki zama amanata tawa Ni kadai kinji" murmushi tayi masa ya sake mirginawa kanta ta lumshe ido ya dora bakinsa saman idanun nata Yana lasar eyeslashers dinta tare da matse nononta a qirjinsa yana matsata yanda yaga dama wannan Rana an kurbi zumar qauna yanda ya kamata.
Sunaji ana buga musu qofar sukayi likimo abinsu fir ya hanata fita wai yau lkcnsa ne bazaa yimasa ojoro ba hatta abinci Saida dare ya fita yaje ya siyo musu ya dawo suka qara bajewa suna tsinkar furensu da dare aka kwanta akaci gaba da bawa qauna haqqinta tun Juhud na jurewa har ta fara gajiyawa abinka dame yaron ciki shikuma dadinta ya hanashi qyaleta, da safe Mom da kanta tayo tattaki tazo barayin nasu domin babu wanda yasan ya dawo sai Muntaz daya daukoshi a airport.
Ta jima tana bugu daqyar ya saki Juhud daya maqale ya fito parlourn yana tambayar waye? Jin muryarsa yasa Mom cewa ”haba nidai naji shirun tayi yawa Rasheedu ashe ka dawo?" Bude mata qofar yayi ya kwantar da kansa a kafadarta wannan tsohuwar al'adarsu ce yace “wlh tun jiya da yamma na dawo" murmushi tayi tace “babu Kuma ko nemanmu saima hanamin yata fitowa anata hada² a cikin gida tun jiya wayarta a kashe" sosa qeyarsa yayi ya zauna lkcn da Juhud din take fitowa ganin mom yasa taji kamar ta nutse ta rusuna a kunyace ta gaisheta tayi dariya tace “yar jaka ba ko sisi waike dadi miji mijinki ya dawo kin manta dani ko zai tafi yabarni dake ai muga qaryar rashin kunya"




Dariya sukayi dukkansu Ya'isha da Amrah suka shigo da Khadija da Zahrah matar da zaa aurawa Kareem Ya'isha ce kawai ta kalli Juhud tace “ai dama Saida na kawo haka a Raina nace duk yanda akayi Babban ogane ya dawo kika manta damu" murmushi tayi tace “yo mi zanyi muku duniyata ta dawo gareni" dukkansu kallonta sukayi ta matsa jikinsa lkcn da Mom take fita tana cewa “aifa baki ya bude da alamun shima unborn din babansa yake buqata naga yau jiki ya wartsake ya samu abinda yakeso"
Gaisheshi sukayi ya Amsa hankalinsa nakan Meenah ya miqa mata hannu ta kama ya dagota jikinsa ya zaunar da ita suka kalli juna Ya'isha tace “baba Aminu ne yace mu kawo maka Aunty Khadija ku gaisa Wai kun dade baku hadu ba" shafa qirjinsa yayi yace “wlh fah tun rasuwar mijinki halan kin gama idda ne?" Wani farr tayi da idanu tace “kayyy soja ai tun lkcn mutuwar Aunty Zulaihat ma nayi iddah" tabe baki yayi yace “ok to ai saiki fidda miji kiyi aure kada kice zakici gaba da shashancin da kika rinqayi a baya yaja miki aure da qananun shekaru" murmushi tayi tace “ai nama fitar Yaya Soja" bai bawa hirar muhimmaci ba ya kalli Zahrah yace “wannan itace dayar amaryan ance amaren ukune halan ya jikin Kareem din hope Yana samun sauqi?" Tabe baki Amrah tayi tana wani yatsina tace “to bama dolenshi ya warke ba wannan auren gayya da zaayi masa da yar asali me cikakkiyar nasaba" kallonta yayi batare daya fahimci meye takeso tace ba ya miqe yace “Life help me breakfast kin yasheni jiya fah" Saida taso ta nutse dan kunyar qannen mijin nata hakana ta miqe Khadija na harararta ta nufi kitchen cikin yan mintuna ta sama masa abinda zaici ta dauka ta nufi dakinsa ta aje masa zata fita ya riqota yace saurin na meyene?"




Zama tayi tana hada masa tea din tana cewa “mom tace idan na gama naje mu gaisa da baqin Mali sunzo tun jiya sunata buga sashin nan ka Hana a budensu" yasan da hakan shiyasa baice komai ba ya rinqa janta da hira Saida ya gama yayi wanka sannan suka fito tare sunsha kyau na ban mamaki suna fitowa da ango Kareem suka fara kicibis sukayi musabaha ya tambayesa aiki shikuma ya tambayesa jiki itadai gaba tayi saboda zuwa lkcn wani haushin Kareem din takeji yanda yake nacin kallonta.
Ta rigashi shiga tana shiga parlourn Hajiya Bilki da su Nana da sauran mutanen suka fara watsewa ta tsaya sake da baki kawai sai tajiyo a bayanta wata mata na cewa “ai wannan kina ganinta kyaun dan maciji baqar annoba kenan yanzu kina cika wargi zaki tsinci kanki a Ramin kabari ta tsotse bargo ta lashe kurwa"
Juyawa tayi ta zubawa me mgnr ido hawaye wani nabin wani shiyasa jiya taqi fitowa saboda gudun abinda zatayi gamo dashi a wannan taron bikin, ji tayi an saqalo qugunta taja ajiyar zuciya tare da share hawayenta da gefen mayafinta ya zagayo gabanta yace “dame Kuma kika gamu daga fitowarki" murmushi tayi tayi gaba ya riqo hannunta yace “wlh bazaki shigaba saikin fadamin uban waye ya tabaki?" Tana Shirin mgn Ya'isha tace “wato Ya Rasheed yau zaayi kutmar uba a gidannan....." Fuuuuuu tayi gaba tana zuwa ta dauke Hajiya Bilki da Mari ta kama qunduma mata ashar abinka da bakatsina yau jini ya motsa bala'i takeyi tana dara nandanan gurin ya kacame taron biki ya koma taron fada shidai Rasheed baisan meye yake faruwa ba Saida yaji tana cewa “aikin banza aikin wofi har wasu kune zaku dubi Meenah ku rinqa jifanta da miyagun kalamai dama ai na dade Ina jiran damar cin bura uban kowannen shege a gdannan idan kuna taqamar ance muku itan mayya ce to ai gara ita ansan wacece ita ku waye yasan asalinku yayan bayi kawai Wanda tsiya da munafurci ta Haifa ta goya ta shayar Bilki kibi a sannu halwa ce dake gaba da baya Kuma mata ba maza ba aure Big Cele yace bayaso bazai auro irin masifa irin jaraba ba wlh dadai auren halwarki gara auren mayyah so million indai msita irinta Meenah ce Kuma Meenah ta zame muku ciwon ido a gdannan kowanne dan iska saidai yaganta yabarta idan da meja Kuma yaja shima ya wullah barzahu kamar yanda Zulaihat data dage saita shiga tsakanin rabo ta fece, yan iskan banza munafukan wofi"





Tunda yaji dalilin rikicin jikinsa ke tsuma ran maza ya baci idanunsa suka kada sukayi jawur ya dubi Juhud data durqushe a qasa taketa aikin kuka me cin zuciya ya juya ya dubi mutanen kowa jikinsa ya hau karkari baice komai ba baiwa kowa mgn ba ya figi hannunta da qarfi suka fice daga falon gurin Mom din da baajeba kenan ya mayar da ita sashinsu ya kulle ya zauna yanata huci ya miqe ya zauna yafi sau ashirin sannan Kiran Mai Martaba ya shigo yayi jifa da wayar ta tarwatse ya tashi ya shiga dakinsa batasan me yayi ba ya fito dauke da jakankuna manya guda biyu ya fice ya jefa a mota daidai lkcn da yake Sanya kayan a mota Mai Martaba ya iso gurin yace “ya subhanallah meye Kuma hakan Ina zaka?" Juyowa yayi idanunsa sun kada sunyi jawur ya dubeshi ya kawar dakai Alh Aminu ne ya matso shima lkcn Rasheed din ya koma cikin gdan ya figo hannun Meenah ko dankwali Babu akanta Mai Martaba daya fahimci barin gidan yake niyyar yi yace “wai ba mgn nakeyi maka bane" a fusace ya juyo yace “banaji Mai Martaba banji abinda kaceba ka kauce kabani guri yau kam ko baku koreni ba na gama zaman gdan sarautar nan akan matata zan iya hqr da komai....."
Muryarsa ce ta sarqe ya jefata a mota ya kulle har yanzu kuka takeyi yama kasa rarrashinta ya sake kallon Alh Aminu ya nunasa da yatsa yace “ka sanar da munafukar matarka ni Abdulrasheed nafi qarfin yayanta a aure kun bani Zulaihat banaso na karba Allah ya dubeni ya kasheta kun bani Hidaya na sakar muku kayarku shine yanzu zaku liqamin bazawara kwancen wasu saboda kun Mai dani jani talau waima ni kadaine da namiji ne a gidannan Ina Salman Ina Arman Ina Kareem Ina Muntaz hatta Urwat kukayiwa aure zama zaiyi da matarsa saini akanme zaku sanyawa rayuwata idanu ne banaso na fada muku banaso wlh tallahi zanci mutumcin duk ubanda ya qara tunkarata da mgnr aure auren banza auren wofi da har zaku sanyawa matata tsura akansa aiba ita ta hanani ba nine naga batada tamka bare mahadi, Abu na qarshe ka fadawa Bilki ta kiyayi dawowata gdannan Kuma ta shirya Amsa Kira kotu saita fadamin uban wa matata ta kashe da take fadawa duniya cewa in mutum ya cika rabar Meenah saidai yajishi a Ramin kabari?....."




Sosai Mai Martaba ya girgiza da yanayin Rasheed din yasan tabbas yau yakai qarshe akwai gagarumar matsala idan yabarshi yabar gidan dama Meenah ce zatake kawoshi tunda shi dama asalinsa bayada ra'ayin zaman gdan sarautar to ya dauke abarsa meye Kuma zaisa suganshi? Mai martaba na Shirin mgn Mom ta iso gurin ita da wasu mata su uku dole tasashi yin shiru ta kama hannun Rasheed tajashi gefe sun jima suna bugawa kafin ta shawo kan kayanta Yana kuka kamar wani yaron goye daqyar ta lallabashi ya yarda zaibar Meenah a gidan sarautar Amma da angama biki da ita zai tafi.
Zuwa tayi ta fito da ita a mota ta janye mata sumar data rufe mata fuska tana ganin Mom din ta fada jikinta ta sake rushewa da kuka itama hawaye ta share tana tausayawa rayuwar Meenah Babu uwa Babu uba babu shaqiqin dan'uwan da zata zanta dashi taji dadi ga rayuwar taqi mata dadi wata murya taji ta bayansu tace “kiyi hqr Aminatuh komai yayi tsanani sauqi na zuwa hakanan Allah yake jarabta bayinsa zababbu domin ya gwada imaninsu ba sonki ne bayayi ba qaunace ta kawo miki hakan bantaba ganin Wanda akayiwa irin wannan qazafin ya qare rayuwa a wulaqance ba ko baizama wani ba zai samu yardar Allah"
Juyawa tayi ta zubawa matar idanu gabanta ya yanke yabada wani rass ta janye jikin Mom da sauri tana qara kallon matar tare da langwabar dakai a rayuwarta nata taba ganin kamar tsagin Kara irin wannan ba kama haske da jiki inda kasan innatun ta a hankali ta sauke ajiyar zuciya tace “mom wannan fah?"




Dadine ya cika mom ganin ta fara warewa tace “Wannan Kharimatu kenan qanwata ce babanmu daya daga Mali suke ita da Mamanta Hamida kinganta can" juyawa tayi ta kalli dattijuwar matar da tayi tsufan jin dadi fatar nan kamar a matsa a tatsi jini tana sanye ds farin tabarau tayi mata murmushi ta bude mata hannu ta fada jikin matar hakanan takejin wata nutsuwa na ratsata da kwanciya a jikin Kumbo Hami Kumbo Hami ta shafa kanta tace “kiyi hqr jikata zakiga ribatai a gaba munci wannan baqin cikin nida babbar yata Aysho tana jaririya a tsumman goyo aka koremu daga gdan babansu Aishatu surukarki......" Kuka ne ya qwacewa Kumbo Hami ta share qwallarta tace “saboda qin jini da yanayin qabila wannan abu yake bibiyarmu kamar garin Bodde wani babban
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment