Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank



Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241...



Juhud ba littafin kyauta bane ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241.....



*Oum Hairan*
[8/22, 8:04 PM] Oum Hairan: Da mugun gudu cikin fitar hayyaci Juhud ta fito daga dakin da take cikin gigita ta cacumi Rasheed dake shigowa idanunsa kamar garwashi ta jijjigashi tace “da gaske ko gizo kalamin Ya'isha sukemin Ya Kareem ya mutu....." Zubanta idanunsa yayi so yake yayi mata mgn ya kasa sai kawar dakai da yayi hawaye suna zubo masa yasa hannunsa ya janye nata, ganin yanda yake goge hawaye da tissue yasata zama a gurin dabar ta daura hannunta akanta ta rushe da kuka tana cewa Innanillahi wa Inna ilaihir raji'un" Ya Kareem kada ka mutu dom girman Allah ya kasance mafarki shudadde Wanda bazan qarayinsa ba har abada wlh na aminta da kai zan dawo gareka na qara Haifa maka qannen Muneefah nasan shin....shine burinka a duniya....." Dagota Mom tayi tace “kiyi hqr Meenah shirya mu tafi" Babu wani shiri ta sunkuci Muneefah da taketa bacci abinta baccin asara abin tausayi mota ta debesu gabadaya harda Alh Garbu suka nufi airport dake abin na manya ne nandanan suka Isa Nigeria kamar a qasar suka kwana goma na safe suka shiga Daura lkcn an gama shirya Kareem da Zahrah zaayi musu sallah mazan suka tsaya wajen jana'izar sukuma suka shige ciki.




Addah Abulle tana ganin Juhud ta miqe ta nufeta da sauri ta karbi Muneefah ta rungume ta qara rushewa da kuka tace “shikenan ya tafi Meenah yatafi yabar Mana duniyar Babu shi din Babu Zahra wayyoh Kareem dama inada dama Dana dawo dakai duniya nabarka da zabinka da yarka daya mafi soyuwa a ranka kullum kana fadamin bakajin dadin rayuwa baka tare da Muneefah ashe ita kadaice rabonka ita zaka tafi kabarni da ita Kareem wayyoh Ni Zainabu na cuci kaina na cuceka Kareem Allah na gde maka da bakabani saa ba lkcn da malam Mati yabani magani yace nabaki kici a waina da tuni Babu Aishatu da tuni Ni da kaina na kashe bayan dana kaicona Ni Zainabu Allah ya isa Dada Hanne da Hajiya Bilki kune kukayita dorani a keken bera ashe kaini zakuyi ku baro yau na rasa Kareem ban barshi ya rayu da farin ciki ba ya tafi da jin ciwon nice silar rabashi da matarsa mafi soyuwa a duniyarsa...."
Surutai taketayi kamar wacce ta zautu hakan yasa wasu mata daga cikin danginta sukazo suka kamata suka tafi da ita daki tana kuka tana kiran Meenah Kareem shikenan Kareem ya tafi yabarmim duniyar Ina nutsuwata da hankalina yayi na kasa gane nauyin qaddararsa?" Kowa ka gani a falon kuka yakeyi mutuwar Kareem tabar tambari ba iya Daura ko Katsina kadai ba hatta arewacin Nigeria baki daya duk Wanda yaji labarin mutuwar ko baisanshi ba sai yaji alhini a jikinsa duniya tayi rashin nagartaccen mutum me hqr da kawaici kunya da kara wannan dabi'ar tasa yake soyuwa a zuciyar duk wanda yayi mu'amala dashi ta kusa kota nesa ranar anyi yinin alhini Juhud kam zazzabi ne ya rufeta sosai bana wasaba hawaye yaqi tsayawa a idanunta tayi danasanin zabar Rasheed akan Kareem ta zabi Rasheed tabar Kareem Rasheed din ya tattarata yayi watsi da ita yaqi saurarenta.




Haka suka yini yinin koke² da dare kowa ya nemi guri ya kwanta itakam koda ta kwanta kasa rintsawa tayi rayuwarta da Kareem zamantakewarsu da yanayin salon qaunarsa me tsayawa a rai shudaddiya wacce bazata dawo ba tanayi mata yawo a kwanya saidai kawai lkc zuwa lkc ta dauke hawaye, wajen 10:30 taji ana taba qofar dakin data shiga ta kulle kanta ta miqe a wahalce ta bude ta dan ja da baya a tsorace ganin Rasheed ne jajayen idanunsa akanta ya miqa mata Muneefah da tayi bacci tasa hannu ta karbeta ta juya ta nufi cikin dakin taji muryarsa data shaqe da alamun yaci isasshen kuka yace “Duk da bansan irin radadin da kikeji a zuciyarki ba na rashin masoyinki uban yarki nasan kinajin fiye da abinda nakeji tabbas akwai daci daci mafi dacin daci rabuwa da abinda kakeso a lkcn da kake tsananin buqatarsa yaune kika farajin kwatankwacin abinda naji lkcn dana rasa hanyar dawowa gareki kwanyata ta daina fadamin daidai aka rinqa nunamin ke cikin wani yanayi dana kasa ganewa har yanzu and end aka nunamin ke wani mutum ya hankadaki cikin wani dogon rami Wanda na yanke shawarar binki mu mutu tare Meenah bayan na biki bansake sanin komai da hankali zai tuna ba sai bayan shekara bakwai dinnan Amma ko a cikin yanayin zautuwar qwaqwalwata ban mantaki ba duk wani furucina kece bansan ya ake tunani ba Amma idan na zauna kece kikemin gizo da siffofi mabambata"
Numfashi ya sauke ya juyo idanunsa na zubar hawaye yace “meye kike tunani ranar da Allah ya Amsa addu'ar masoyana ya dawo dani hayyaci na laluba naga bakinan na tambayi kina Ina akacemin kina matsayin matar wani waninma qanina Meenah taya zan iya yafewa kaina bata lkcn da nayi na nakasa rayuwata saboda ke? Nakasa yafewa kaina kema na kasa yafe miki girman cin amanar da nakeji a Raina kinyimin domin bana mantawa kintaba yimin alqawarin zamu rayu tare zamu mutu tare ya akayi tun Ina raye kika zabi rayuwa da wani bani ba?"




Duk da kalamansa sun kashe mata jiki Amma yanayin da take ciki yasata juyowa a fusace tace “qaddara Abdulrasheed dukkanmu akanta muke rayuwa Babu Wanda ya isa ya tayani dakon tawa kamar yanda Babu Wanda ya tayaka Babu Wanda ya taya Ya Kareem Allah madaukakin Sarki ya sardanta ku biyun daka kuna cikin qaddarata kaine kakeja da lamarin ubangiji ni bana jayayya Ya Kareem ma baitaba jayayya ba kullum nunamin yakeyi bayin kansa bane girman rabone da hukuncin Allah saiya Sanya Muneefah tsakaninmu Kuma na dade da sanin tun baya ma shine akan daidai kai kana rayuwa ne a doron son zuciya saboda haka Baffa'am tun da sauran mutuncinka a idanuna ka fice cikin rayuwata kafin na keta alfarmarka na shiga nayi fata² da qimarka Meenah daka sani a baya ba ita bace yanzu yanzun Aminatuh ce a gabanka me taqama da asali kyawun nasaba arziqi da ilimi kada ka manta bayan tafiyarka na samu shahadar zama Barrister Aminah Haroon Moddibo so nasan yancina banason kowa cikin rayuwata ta yanzu"




Shigewa tayi daki ta banko qofar ta murda mata key ta haye gado ta zubawa yarta ido tana mata tunanin rayuwarta ta gaba babu bangonta na farko kwanciya tayi bacci ya qauracewa idanunta kamar yanda ya qauracewa idanun Rasheed sosai yake jujjuya kalamanta ya rasa a ma'aunin dazai sanyasu ta fada masa kalamai masu wahalar gogewa a zuciya tabbas shima saida ne daga yanda ta watsar dashi da lamuransa na rayuwa yasan tabbas da gaske ba Meenan daya sani a baya bace, to Amma meye yasa ita ta kasa gane tayi masa laifi me girman daya dace duk hukunci ya dauka akanta?
Busar da iska yayi ya gyara kwanciyarsa tare da dauko takardar da Mai Martaba yabashi dazu dazai shigo bayan ya fito daga dakin Meenah yace Kareem ne yabashi yace abashi kafin ya rasu. Tashi yayi ya kunna haske zuciyarsa na bugawa ganin yanda takardar ta bushe da jini ya warwareta ya fara karantawa da larabci yayi rubutun fassararsa kamar haka.
_“Assalamu Alaika ya dan'uwa mai albarka na rubuta maka wannan takarda ne a lkcn da Raina yake tafiya ga ubangijin daya halicceshi, badon komai ba saidon inason na qara baka hqr akan laifin da kake tunanin nayi maka na auren matarka Allah yasani ban aureta don cin mutumci ko tozarci a gareka ba, Ni Abdulkareem Mahfuz na zabeka na mallaka maka amanar yata qwaya daya tilo ta zama taka dama nasan takan ce don Allah Abdulrasheed kada kabari Meenah da Muneefah suyi kukan rashina musamman Muneefah ita kadai gareni Kuma na mallaka maka ita halak malak"_




Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank



Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241...



Juhud ba littafin kyauta bane ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241.....



*Oum Hairan*
[8/23, 7:30 PM] Oum Hairan: Matse takardar yayi a tafin hannunsa jikinsa Yana tsuma zuciyarsa nayi masa wani zugi ya miqe a gadon ya rinqa zagaye dakin nasa a tsarinsa na gaskiya ji yakeyi kamar bazai iya sake zama da Meenah ba yanajin ciwon abubuwan da suka faru a baya so yanzu ya zaiyi da wannan nauyin da Kareem ya dora masa a halin yana gargarar mutuwa? Tambaya ce da yakasa amsawa kansa ita dole akwai sarqaqiya cikin wannan al'amari komawa yayi ya kwanta ya kasa bama kansa mafita sai zafi da zuciyarsa takeyi kawai.
Abu daya da yasan ya zame masa dole shine daukar amanar Muneefah da Kareem ya damqa masa to Amma ta yaya zai karbeta a gurin mahaifiyarta bayan yasani yanajin yanda shaquwa take tsakaninsu ko giyar wake Meenah tasha bazata bashi yarta ba, da wannan tunanin ya samu bacci ya dan daukesa da safe yana fita falo ya ishe kowa suka gaisa yanata raba idanun ganin Meenah Babu alamarta hakan ya tabbatar masa tana dakin daya isheta jiya yaja fasali ya dubi Amrah yace “shiga ki daukomin Muneefah" miqewa tayi ta nufi cikin dakin ta tarar Meenah tayima yarta wanka tanayi mata kwalliya ta zauna suka gaisa tace “Big Cele yace akawo masa Muneefah"
Bataso ba saidai batada ikon hanawa ta gama shiryata Amrah ta riqema yarinyar hanu suka fito ya dauketa suka fice daga falon Mom tana kallonsa batace masa komai ba, kwanaki bakwai din da Meenah sukayi suna karbar gaisuwa ta fahimci abubuwa da yawa sosai Addah Abulle tayi laushi batada aiki sai kuka tunda ta haifi Muneefah bazata iya cewa ga ranar da Addah ta dauki yarinyar ba sai cikin kwanakin nan da taketa nan nan da ita danma Rasheed ya hanata sakat akan yarinyar duk wani motsin da Muneefah zatayi tana gareshi.




Kwanaki goma da rasuwar su Kareem bayan komai ya fara nutsawa Meenah da Kumbo Hami suka fara Shirin tafiya Rasheed baisan me akeyi ba sai a daren da zasu tashi Mom ta kirasa lkcn bai dawo daga yawonsa ba kasancewar har yanzun bai koma bakin aiki ba yana hutune take sanar dashi su Muneefah zasu tafi, Saida yaji wata faduwar gaba yace “tafiya Kuma Mom na zaci sun dawo kenan?" Murmushi Mom tayi tace “basu dawo ba to yanzu haka ma Shirin kaisu airport mukeyi" tana Fadi masa haka ta kashe wayar ta dubi Meenah da hankalinta take kan Sarki junior da yaketa kukan sai yabita itama hawaye ta share tace “makarantarka junior kabari idan akayi hutu zanzo ko na turo a daukarmin kai kaji" daqyar ta rarrasheshi ta samu ta sulale ta shiga mota suka tafi abin mamaki wai harda Addah ayi musu rakiya ashe dama tunda suka rabu da Mai Martaba tayi aure batafi wata biyu ba ta kasoshi tanason Mai Martaba ya dawo da ita dakinta shikuma yaqi.
Ko a airport din daqyar aka karbi Muneefah a hannunta tanata kuka so take ta roqi alfarmar abata yarinyar take gani ko ta rinqa samun sauqi Amma tsoro ya hanata furtawa saboda ta fahimci suma dangin uwarta sunason kayarsu da hakadai jirgin su Meenah ya daga sukuma suka juya domin komawa inda sukafi wayo cike da kewar juna.
Wannan tafiya ta zamewa Rasheed tamkar famin tsohon miki a cikin zuciyarsa abubuwa sun fara dawo masa sabbi duk da cewa izza da dagawar da Meenah ta rinqayi masa ta girgizashi baitaba tunanin akwai juyin da duniya zatayi Meenah ta rinqa kallonsa watsi dashi kamar tunda Allah yayita batasan anyi ruwansa ba.




Wata biyu abubuwa suka zama tarihi akaci gaba da cudawa kamar yanda aka saba kowa yasa abinda yake gabansa a gaba Rasheed ya koma aikinsa gabadaya sun ajeshi guri guda a Lagos inda kullum tunaninsa zuciyarsa da ruhinsa yake Mali gashi tun a farkon da abubuwa suka lalace da Meenah ta rinqa kiransa yayi block na numberta itama tayi block nasa koya nemeta baya samunta wannan tasa dole ya nemi sabon layi dal saboda zuciyarsa taqi sabawa da rashin sauraro da jin abinda zuciyarsa take muradi saidai rashin saar da yayi daya Kira sai yaji layukan dukka a kashe girman kansa na masifa ya hanashi tambayar wani cikin yan'uwansa layinta yabari akan cewa idan ya koma yasan yanda zaiyi ya sata a wayar Mom.
Hakan kuwa akayi bai iya hqrn wata biyun da yayi niyyar yi a Lagos ba ya dauko hanya ya taho Daura bayan ya huta da dare suna hira da Mom a dakinta tanayi masa fadan zamansa haka yayi murmushi yace “mom kamar akanki nake duk kinbi kin damu nayi aure" jinjina kai tayi tace “to ai Rasheed nidai naga cikar kamalar mutum shine hade kansa da iyalansa guri guda kai Kuma na rasa inda kanka yake kunqi ku daidaita da yar'uwarka Meenah Kuma ka kasa samo madadi jiya ma Baffanmu yakirani yake tambayata akan lamarinka da Meenah ance mata aure tace karatu ance ta dawo hannunka tace har abada kaima ya tuntubeka kayi masa shiru wai meye yake faruwa ne"




Goge gumi yayi ya gyara zamansa yace “ni bawai Meenah ce bazan dawo da ita cikin rayuwata ba aa Mom abubuwa ne sun kasa gogewa a mind dina Kuma na fahimci kamar itama ba nine a gabanta ba yanzun" murmushi Mom tayi tace “hakane bakai ba aure ne ma bakidaya bashi gabanta so Amma idan kaje zaku iya daidaita kanku" shiru yayi yana nazartar kalaman Mom tace “zanji dadi idan hakan ta faru Rasheed Meenah tanasonka kanason Meenah ga yaranku guda biyu baikamata ku Bari shaidan ya raba kanku ba babu wanda ya isa cikinku ya canza wannan qaddarar kama godewa Allah da rabon Muneefah bai kasheka ba Rasheed rabon ya mace zafi gareshi shiyasa kullum yanada kyau karinqa yima kanka addu'ar Allah ya rabaka da auren mace me yayan wani a cikinta duk son da kake mata idan rabon nan ya yunquro to sai dayan biyun ta faru kodai a rabu ko Kuma a mutu"
Jinjina kai yayi jikinsa ya qara sanyi abinda Kareem yayita qoqarin fahimtar dashi kenan ya kasa fahimta yau kam ya gane Kuma ya fahimta wayar Mom ya dauka ya fice daga dakin nata ya shiga mota ya nufi gidansa ya shiga ciki Saida ya dangana da dakin baccinsa ya cire kayansa ya fada bathroom yayi wanka ya dawo ya kwanta gabadaya dakin manyan hotunansa ne shida Meenah saina yaransa Sarki da Muneefah ya zubawa hotunan idanu a fili yace “lkc yayi da yakamata da dawo da farin cikina" wayarsa ya dauka ya Kira Abokinsa Kamil suka gaisa yace masa “cikin satinnan kana free ne?" Amsawa yayi da “eh" yace “ok zamuje Mali ne jibi" bai boye masa komai ba khamil yayi dariya sosai yace “tsohuwar zuma kishin ya gushe kenan?" Ya lura tsiya ya shirya yi masa don haka ya kashe wayar ya dauki ta Mom yanabin contact din ya lalubo number ya danna kira lkcn tana sallar Isha Muneefah ce tana wasa da wayar ta danna tana gwarancinta yayi murmushi yace “daughter bakin yazo kenan?" Nan sukayita shirmensu da yarinyar bayan ta idar ta karbi wayar tunaninta ko Muntaz ne ko Urwat tace “surutu ke gareta Mamana bata rabo da rigima" ajiyar zuciya yaja a hankali taji ya sauke numfashi yace “hakan yanada kyau ba lallai tayi kamar na Mom dinta ba" qamewa tayi a gurin jin muryar da batayi zato ba nandanan ta rinqajin zuciya na ayyana mata ta kashe wayar tana Shirin gimtse layin taji yace “ranar juma'a idan Allah ya amince zan shigo qasar ki fara Shirin zama amarya domin bazan kwana a garin nan ba saidake matsayin matata kamar yanda yake rubuce a allon qudura duk wanda yayi karambanin shiga wannan gonar ma saiya fice da kansa ko Kuma dole ta fitar dashi"




Murmushi tayi tace “tunaninka ne yake baka hakan nikuma inajin a raina qaddarata tayiwa taka nisa Ya Rasheed so don Allah kada mu wahalar da shari'a kayi zamanka a inda Allah ya ajeka idanma matsuwa akayi nayi auren naji zan fitar da miji tsakanin yau da gobe Amma kaikam nagama aurenka" murmushi yayi yace “au haba da gaske Kuma kikeyi? To ai kin manta da Abu daya ni idan nayi niyyar aiwatarwa yuwuwa yakeyi Meenah badon kanki da kaina ba don rayuwar yaranmu nayi niyyar abinda na furta saboda haka kada ki manta gyarane kawai Amma kedin matata ce domin da igiyar aurena uku akanki aka jingine aka dauranki wani.... Oh God banaso nake tunawa fah ki share kawai sainazo".......
Daga haka ya gimtse wayarsa yabarta da sakin lebe lallai wannan yazo da izala mara gemu dole ta takansa birki don bataji a ranta wannan tatsunniyar zata yuwu ba.





Ranar kwana tayi tana jujjuya kalamansa da safe kuwa bata sanar da kowa ba ta shirya nata ya nata ta gudu gidansa Aunty Kharimatu batare da kowa yasan inda ta tafi ba Kumbo Hami ta riga tasan me ta gudarwa saboda sunyi waya da Mom a haukan ma da takeyi tuni magana taje ga kakanta ya Kuma amsa har anyi duk abinda zaayi an wucce gurin da sahalewar Mai Martaba.
Tana zuwa gdan Aunty Kharimatu suka lalace da hira har dare tayi kwanciyarta dake mijinta matafiyi ne washegari ma sukaci gaba da harkokinsu har magrib batada niyyar tafiya suna falo suna cin dambum nama sukaji sallamar Jabir gabanta ya Fadi ya shigo yanayi mata dariya yace “girman kujera aunty babba kinada baqi a waje fah" harara ta zabga masa tace “munafuki suwa kak debomin?....." Bata gama rufe bakinta ba sukayi sallama suka shigo idanunsa na kanta ta kuwa hadiye fara'arta ta hade rai ta miqe ta nufi wani daki suka dubi juna shida Khamil sukayi murmushi suka zauna Aunty Kharimatu nata zolayarsa fadi takeyi lallai ango kasha qamshi ashe da gaske kana tafe"
Shafa sumarsa yayi Yana cire hularsa yace “wlh Ina tafe nazo na dauke matata mu tafi nagaji da zaman gwaurontaka" harararsa tayi tace “aa kuwa baka isaba wannan abu Babu shiri nifa sai dazun Kumbo ke fadamin Shirin da akayi nace halan ma waccan uwar taurin kan bata sani ba don ko dazun Saida tace batada muradin wani aure" numfashi ya sauke yace “tasan komai ai dama barinta nayi ta huta saboda rayuwar batada tsayi Amma an fuskanci qalubale da suke buqatar dogon hutun brain"...........




Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank



Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241...



Juhud ba littafin kyauta baney ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241.....



*Oum Hairan*
[8/27, 9:03 PM] Oum Hairan: Dariya Aunty Kharimatu tayi tace "ah lallai to ubangiji ya kade fitina ya daidaitaku sai aje ayita hqr koda yake tsohuwar zuma ce Babu wani qalubale qalaunku zaku zauna wuyarta ku daidaita kanku......" Aunty Kharimatu bata gama rufe bakinta ba Juhud ta fito dauke da Muneefah da niyyar ficewa daga gdan Muneefah na ganin Rasheed ta fara zamewa a jikinta tana Kiran Dad sweet Dad biscuits...." Murmushin gefen baki yayi ya miqe ya nufi Meenah da takai bakin qofa yasa hannu zai karbe yarinyar ta juyo a fusace cikin bala'i tace “inada tabbacin bakada wata alaqa data wucce wan mahaifi gurin Muneefah domin kuwa qaddararta me qarfi ce itane ta sanya abubuwa da yawa suka faru a qarshe dai nida Kareem muka Samar da Muneefah saboda haka ikona ce"
Sakin yarinyar yayi yayi baya jikinsa na daukar sanyi yanajin saukar kalamanta na dukan zuciyarsa, batare da wata damuwa ba ta fice ta jefa yarinyar da keta kuka a mota ta shiga ta figi motar a mugun guje ta fice a harabar gdan tabarshi tsaye kamar dashe Yana qara maimata kalamanta, Khamil ne ya dafashi yace “nifa Ina mamakin yanda dangantaka tayi tsami haka tsakaninka da Meenah meye ya farune mutumin bakada dama ne fah qila Kaine ka tabo zuciyarta" janye hannunsa yayi yace “koma mene ban cancanci wadannan munanan kalaman akan yar qanina ba Amma zan gwada mata haihuwa ce tata nafita qarfin iko" Yana fadin haka ya fice Yana huci ran maza ya baci Jabir ne yazo yajasu suka nufi gda ganin motar da ta hau ta fito yasashi tabbatar da gidan ta dawo, bai shiga cikin ba ya nufi sashin baqin ya cire kayansa ya zauna yana fitar da iska me zafi zuciya na raya masa meye zaiyi ya rama wannan wulaqancin da Meenah tayi masa?



Ya jima bacci bai daukeshi ba sai juyi yakeyi da safe ya fiçe ya nufi cikin gdan Meenah bata tashi daga bacci ba a zahiri ba baccin takeyi ba kawai juyi takeyi, shiga yayi part din kumbo Hami suka gaisa ya wucce bangaren Alh Garbu suka gaisa yayi shiru na dogon lkc kamo hannunsa yayi yace “meye yake faruwa ne Dan Boko?" Qasa yayi da kainai Yana shafa sumarsa can Alh Garbu ya sake dubansa yace bai wucce kace kanason tafiya da matarka ba ko?" Jinjina kai yayi yace “hakane Alh inason jibi idan zan tafi mu tafi gabadaya saboda dawowa zatayimin wahala kusa" jinjina kai Alh Garbu yayi yace “shikenan zan fadawa kakar taku inyaso saisu fara Shirin abinne yazo Babu tsammani Amma fah akwai abinda bazan dauka ba cikin lamarin aurenku duk wani cin Kashi da akayi mawa Aminah a baya yanzu ko ita ta daukeshi ni bazan daukaba" ya jima yana kafa sharrudansa shidai Rasheed jinsa kawai yakeyi har ya gama ya tashi ya fice.




Lkcn da Kumbo Hami taji Shirin da Alh Garbu yayi taso tace aa Amma ya hanata katabus dole hakanan ta hqr tana jiran ranar zartaswa aikam ana samun Meenah da mgnr tayi tsalle ta dire tace batasan zance ba duk Wanda suke tunanin zai fada aji ya fada tayi kunnen uwar shegu Rasheed kam abokin gaba ya zama batako kallonsa bai wani damu ba saidai ya kalleta yayi murmushi ya barta tayi duk abinda yasan na dan lkc ne da lkcn ya wucce shikenan, ana gobe tafiyar da dare ya shiga har dakinta ya tarar da ita itada Aunty Kharimatu da Kumbo sai aikin rarrashinta sukeyi suna ganinsa suka miqe suka fita ya mayar da qofar ya rufe ya nufota ta miqe tsaye ya tsaya Yana murmushinsa na isa tare da zura hannunsa a aljihunsa ya harde qafarsa ya jingina jikin bango yace “banzo domin na baki hqr Kona rarrasheki ba saboda Ni nasan banyi miki laifi ba hasali ma nine nake tuhumarki so inada abinda yafi haka muhimmaci kin fadamin wata mgn ne da nakasa jureta shine nazo baki amsa Meenah yes na amince keda Kareem kuka Samar da Muneefah Amma kada ki manta kafin Kareem ya baki da nine na fara baki na farko kika zubarmin na biyu kika haifamin gashi ya zama saurayi so wannan kadai ya isa ya tabbatar miki ni na wucce kiyimin gatsali akan Muneefah Kuma ko kinaso ko bakiso dole kibarni da ita domin ba saboda ke nakejin yarinyar a Raina ba saboda mahaifinta yayimin kyautarta ne"




Shafa gemunsa yayi yayi murmushin gefen baki yace “shekarar Muneefah daya da rabi ki shirya karbar qaninta kowanne lkc daga yanzun ni bana wasa da dama amfani nakeyi da ita sosai" ficewa yayi daga dakin yabarta tsaye da zubar hawaye takaici kamar ya kasheta taja qwafa ta koma ta zauna.
Duk wani shiri da Kumbo Hami taso yi mata taqi bata hadin kai sai huci takeyi kamar ta kashe kowa haka takeji batasan meye yasa takejin haushin Rasheed ba ko ganinsa batason yi sauqinta daya dake tunda ta haihu Kumbo take hadata da magungunan da tasan bazasu cutar da itaba so data fahimci ba hadin kai zata bata ba saita tattara mata ta zuba mata cikin kayanta ta hade mata komai washegari kuwa da wuri suka dauki hanyar 9ja aikam anyi tafiyar kurame
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment