Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank



Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241...



Juhud ba littafin kyauta bane kada ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241.....



*Oum Hairan*
[8/8, 9:07 PM] Oum Hairan: *0032* Sallama sukayi ya rakashi ya hau motarsa tare da karbar magunguna bai koma gdan ba shima ya shiga tasa motar Yana duba agogo 8:30pm ya jinjina kai ya fice a gdan kai tsaye wani restaurant ya nufa yayi musu siyayyar abinda zasuci ya juya ya koma gdan ya kulle ko Ina ya nufi saman Saida ya shiga dakinsa yayi wanka ya sanya kayan baccinsa ya fito ya bude nata dakin tana zaune inda ya barta har yanzu kukan takeyi gabadaya lamarinta ya tsinka masa lakar jiki da gaske take jin damuwar a cikin ruhinta.
Aje ledar dake hannunsa yayi ya tsugunna a gabanta ya kamo hannunta ta fuzge ya zauna sosai a gabanta ya dafe kuncinsa da hannayensa biyu ya zuba mata manyan idanunsa da a baya suke firgitata da sanyata shiga taitayinta baiji a ransa ko yace ta tashi suyi nafila zatayi ba shiyasa ya janyo ledar yace “Ya'isha tace tun shekaran jiya bakici abinci ba ko meye dalili?" Shiru tayi masa yaja fasali ya furzar da iska ya bude ledar ya fara yaga mata Naman yanda zataji dadin ci ya dauko yakai mata bakinta ta kawar dakai yayi murmushi yace.
“Lamarinki abun mamaki ne Meenah sai naga kamar kina jayayya da hukuncin ubangiji ne ya kamata ace rayuwarki kadai ta ishenki darasin da duk wani abu da Allah yayi zaki tarbeshi hannu biyu wlh duk da nakasance me qulafuci da addu'ar idan kedin Alkhairi ce gareni ki zama gatana ki zama mallakina bantaba furtawa wani burina a kanki ba na fawwalawa ubangiji na yarda duk abinda yayi daidai ne so Kuma sama taka cikin lkcn da ban tsammata ba kiran Mai Martaba ya shigomin yana fadamin na tanadi sadaki a hannuna daga dubu hamsin zuwa abinda Allah ya horemin nazo masallacin Fada yana nemana bansan meye zai faru ba hakanan na tafi Ina zuwa naga dogare sun budamin na shiga kamar yanda baa nemi izininki ba nima baa nemi nawa ba wlh kudin aljihuna kawai Mai Martaba ya karba dubu tamanin yabada umarnin a daura nidai na nemi guri na zauna Ina jiran naji auren waye zaa daura kawai naji ance yace shi a matsayin waliyinki ya bada aurenki gareni akan sadaki naira dubu tamanin bisa sharadin zanyi miki lefe kamar yanda al'ada ta tsara"



Shiru yayi yana mayar da numfashi sannan yaci gaba da cewa to meye laifina cikin lamarin nan Meenah?" A qufule ta dago tace “meyesa bakace bakaso ba?" Murmushi yayi yace “ko bake bace zan karba balle Kuma ya kasance dadaddiyar addu'ata ce ubangiji ya amsamin tare da tabbatarmin da ita kamar mafarki so ni a tsarina bana jayayya da duk abinda nasan ba ikona bane, Meenah a baya kema haka kike saboda kedin dalubata ce bansan meye ya sauyaki ba kinga inada maganganu da yawa da nakeso mu tattauna da zasu zame mana mafita Amma farko don girman Allah badon halin Abdulkareem kici abinci muyi sallah wlh ko Isha banyi ba saimu zauna"
Yanayin magiyar tasa tasata dole ta dauki Naman takai bakinta yaji dadin hakan sosai ya miqe ya shiga bathroom ya dauro alwala lkcn daya fito ta gama ya tattare ya fita da kayan ya dawo ya isheta a bayi tana brush da alwala, abin sallar ya shimfida yajasu sukayi Isha sukayi nafila raka'a biyu ya sanya hannunsa ya dafa kanta ta zame zata miqe ya miqe ya riqeta tare da matseta a jikin bango ya fara karanto addu'o'insa cikin larabcinsa me Sanyaya jiki sunkai 10 minutes a haka sannan ya saketa yana binta da kallo har zuwa lkcn bata daina dauke hawaye a idonta ba miqewa yayi ya dagata ya zare mata alqyabbar jikinta ya sake ware lafayar jikinta tana tureshi tana komai ta durqushe da sauri yayi dariya wai kunyarsa takeji Meenah da lkcn data fara period shine mutum na farko daya fara sani shima a lambu ya isheta tanata kuka wai taji ciwo daqyar ta fada masa yayi mata bayani.
Sautin dariyarsa ce tasata dagowa ya zauna tare da daganta gira yace “ashe kinajin kunyata Meenah yaushe kika farajin kunyana?" Harara ta galla masa yace “ko a jikina ki kwana kinayi yanzun dai Bari na barki ki kwanta ki huta abinki Saida safe" ficewa yayi yaja mata qofa tabisa da kallo tare da miqewa tayiwa dakin key ta haye gadon tayi kwanciyarta badon tayi bacci ba saidon tabawa zuciyarta damar tunanin abinda yake damunta.




Batasan lkcn da bacci ya dauketa ba a sama ta rinqajin ana taba qofar ta miqe tana miqa tare da yin salati tace “wayene?" Cikin sanyin yanayinsa na dabi'a yace “kinyi sallah ne?" Bata bashi Amsa ba ta nufi bathroom ta watsa ruwa ta dauro alwala ta fito ta sanya doguwar riga ta tayar da sallar bayan ta idar tayi azkhar ta sake zubewa a gurin duk da ba wata hidima tayi a bikin ba tanajin gajiya a jikinta sosai, bacci ne ya sake dauketa bata farka ba sai 10:30pm shima din wayarta ce taji tana ring baqon layine ta Kara a kunnenta yace “barka da safiya ki fito kinyi baqi"
Miqewa tayi tasa rigarta ta bude qofar ta fito Sarki ya rugo da mugun gudu ya rungumeta ta dagashi daqyar tana dariya yaron yace “Mom jiya nayita kuka daban ganki ba ashe gdan Uncle kika dawo nima na dawo nan" murmushi tayi tace “surutu dai kazo ka dameni ko" tsuke fuska yayi zaiyi kuka Kareem ya matso ya karbeshi yace “ba tun jiyan nace kazo mu taho ba kace kai bazaka tafi kabar Mom dinka ba to yanzun fah zaka taho ko shima aa?" Da sauri ya daga kai yace “eh" Mom dake tsaye tayi dariya tace “aikam baka isaba yaro muna tare aurena dakai mutu ka raba" kuka ya saka Yana cewa “nin...Ni Mom banasonki kinmin tsufa ni gurin Mom dina da uncle zan dawo"




Dariya sukayi dukkansu ta nemi guri ta zauna Hamida tace “jikin yayi sauqi kenan tunda na tafi nakasa sukuni dake na kwana a raina" sunkuyar dakai tayi ya miqe yace Mom me zaa kawo muku gdan namu bai gama tsaruwa ba Hajiyan sai yanzu ta fito" kiransa Mom tayi tace “kazo kayi zamanka bama buqatar komai tun jiya da sukaje suka sanar dani halin da ake ciki na kasa sukuni shiyasa nazo naganku yanayin Alhmdllh komai zai wucce insha Allahu Meenah hqr zakiyi da abinda Allah ya hukunta, Aminatuh nice na haifi Rasheed Amma bazanyi shaidarsa kamar yanda zanbada shaida akan Kareem ba kin samu miji na nunawa saa daya tamkar da dubu idan kin kwantar da hankalinki insha Allahu komai zaizo qarshe ita rayuwa kowa da irin tasa jarrabawar Babu me taya wani dakon kayan da ubangiji ya qulla masa dole shine zaiyi dakon kayansa rabon dake tsakaninku me qarfine Allah ne kawai yasan adadinsa saboda haka kuyi hqr da jarrabawarku"
Kallon kallo sukeyi kowa da abinda keyi masa yawo a ransa Mom ta miqe tace “Inason mgn dake Meenah miqewa tayi tabita suka haura saman dakin baccinta suka shiga Mom ta zauna a gefen gadon ta kama kunnenta tace “ki kiyayi shiga haqqin Kareem kawaicinsa da kararsa ta game kowa zai iya zubanki ido akan duk abinda yaga baki da raayi koda kuwa shi zai cutu hqrnsa abin jinjinawa ne shiyasa yake wahala idan ciwo ya ganshi don Allah kada ki zama silar wargatsa masa rayuwa kinji"




Kwantar da kanta tayi a cinyar Mom tana shassheqar kuka ta dauko wasu turaruka masu qamshin gaske na humra da na wuta tace muje a jerasu a show glass din fita sukayi suka jera ta fito da wani garin magani ta dauko danyen nonon raqumi ta barbada a ciki ta miqa mata tace “shine yayi saura da jiya kikaqi sha duk yanda kike tunanin fitinar Rasheed Kareem yafisa saboda akan hakan har so akayi a raba aurensa da Zahrah kwanakinsa bai qare ba yanzu Kuma gashi zaki zauna ke daya da sunyi hqr ma sun barta ta dawo da kin samu sauqin wani abun don Allah banda rowa Meenah shidai abinnan in kin hanashi ma ba ado zakiyi dashi ba Kuma ba kwanaki zaa qara masa ba idan wa'adinki yayi shima nasa yayi please a kula don Allah" sosai Mom ta rinqa bata shawari a fakaice saida taga ta dan sake sannan sukayi musu sallama suka tafi shima ya fice a gdan ta shiga bathroom tana wanka ta jiyo wayarta tana ring batabi takanta ba Saida ta gama shirinta tsaf sannan ta dauka number Ya'isha ce tabi suka gaisa tace “ya amarci jiya tsohuwar zuma ta motsa Ya Kareem an kwana ana zikiri" dariya mgnr tabata tace “waiku don Allah meye yasa kuka bawa abinnan muhimmaci ne haka"
Dariya Ya'isha tayi tace “mahadin rayuwa kenan gulma nazo yi miki" gyara zama tayi tace “aike dama indai anga kiranki to gulma ke cinki meye zaki fadamin" gwauron numfashi ta sauke tace “wato bantaba sanin Addah Abulle jahila bace sai jiya iliminta baya mata jagora kamar yanda yakeyiwa danta jiya Mai Martaba Yana zagaye bayan an taho kawoki ya nufi bayan gda ya isheta ita da Dada Hanne suna qusqus Dada Hanne nabata shawarar kawai tunda duk bugunsu yaqi tasiri akanki to su dora miki jinya yanda shi Kareem din zai gaji ya koreki sannan su sanyawa kowa qiyayyar ki a zuciyarsa ta yanda ko kin dawo gdannan Babu me karbarki Ina kaiki sun gama tattaunawar nan suna daga ido sukaga Mai Martaba da Ya Muntaz shine Mai Martaba yayi musu wani warning mai kama da daukar rai har yana fada musu daganan zuwa shekara goma idan kikayi ciwon kai saiya hanasu kwanciyar hankali ke sosai fah akayi rikici qarshe dai Addah Abulle tace da Mai Martaba tunda har ya nuna mata ita ba kowa bace akan danta to saidai ya zaba ko ita ko ke shikuma yace ya zabi zabin dansa aikuwa tace saiya saketa anso hanashi yaqi ji qarshe yayi mata daya me kyau sannan yace da Kareem yabashi damar rabuwa da Zahrah tunda abin nasu iskanci ne aikuwa tuni ya yankawa Zahrah ticket itama Kinga sai tafi samun sukunin zaman gida"




Zuciyar Imani ta Meenah duk sai jikinta yayi sanyi tace “Innanillahi wa Inna ilaihir raji'un Ya'isha wannan ba labarin badawa bane Allah fa shine ya halatta saki Amma bayasonsa nikam banji dadi ba idan Addah bataci arziqin komai ba yakamata taci na yayanta wlh wannan sakin bala'i Mai Martaba ya qara jefani sannan ita Zahrah meye laifinta a ciki najifa ance iyayenta ne suka dauketa bataso tanason mijinta Kuma ko jiya da yazo dakina naga ta kikkirashi bai dagaba haba don girman Allah wannan ba adalci bane bai kamata ba"
Tabe baki Ya'isha tayi tace “saiki fada mawa Mai Martaban tunda kinfishi hangen nesa nikam naji dadin hakan ko banza sayi hankali susan ba ko Ina ake shimfida a zauna ba" kashe wayar tayi ta zabga tagumi wannan wacce irin masifa ce daga wannan sai wannan?
Bataji tsayuwar motarsa ba saiji tayi ya zare hannunta a kuncinta ya tsugunna a gabanta ya shafa habarta ya dago kanta taja numfashi tace “Hasbunallahu wa ni'imal wakil" Babu alamun bacin rai a tattare dashi yace “meye kuma?" Kafin ya rufe bakinsa yaga ta balle da kuka tayo qasa ta dora hannunta a cinyarsa gwiwarta na gugar nasa tace “kayimin wannan alfarmar ko ita daya ce a rayuwa don Allah Ya Kareem" da rashin fahimta ya dubeta tayi qasa da kanta tace “ka dawo da matarka dakinta domin Allah.




Miqewa yayi yace “ok kinyi sallar Isha?" Girgiza masa kai tayi yace “ki dafamin coffee ki kawomin dakina" ficewa yayi daga dakin ta bishi da kallo wani takaici ya tokareta waishi miji gashi babu damar yin musu yau izzar yakeji sosai batada zabi sai nufar kitchen din da tayi ta fara hada masa coffee din ta gama ta nufi dakinta tayi wanka ta Sanya kayan baccinta ta zura hijjab ta nufi dakin nasa ta qwanqwasa yabata izinin shiga ta bude ta shiga gabanta na faduwa ta kawar dakai tunda take bata taba ganinsa a tube ba sai yau cikar zatinsa kawai abin ka tsaya ka nazarta ne qirarsa ta hutun gaske fatarsa lufluf su ta lura kamar sign na Fam dinsu ne gargasar jiki daga mazansu har matansu.
Sunkuyawa tayi ta aje masa ta miqe zata fice ya Kira sunanta ya nuna mata guri ta zauna Saida ya gama abinda yakeyi sannan ya miqe ya nufi wardrobe ya dauki riga yasa yajasu sukayi sallar ya dauki coffee din yanasha Yana kallonta ita Kuma na kallon qasa ganin yanda duk ta takura yasashi cewa “jeki Saida safe" kamar me jiran umarni ta miqe tayi zuruf ta fice ya girgiza kai yana murmushi yace “Meenah kenan"




Ya jima zaune Yana tunanin hanyar da zaibi ya samo kanta bai kwanta ba sai 12:00am koda ya kwanta din baiyi bacci ba yanason kasancewa da matarsa Yana tsoron takurawa rayuwarta ko kadan baison shiga rayuwar dan' Adam balle Meenah da take da muhimmaci cikin rayuwarsa hakanan ya kwana Yana juyi shikam bacci me sunan bacci baiyishi ba da safe ta rigasa fitowa ta gyara part din nata ta sauka qasa ta gyara ta koma ciki tayi kwanciyarta fitowa yayi cikin shirinsa na fita yaga ta gyara ko Ina ya girgiza kai ya bude dakin nata tana kwance tana chat ta kallesa ta kawar dakai yace mata “barka da safiya" aje wayar tayi ta miqe tace “ina kwana" shafa sumarsa yayi yace “na tashi lfy Visa dinmu zan karbo gobe da safe zamu tafi nayima Sarki passport Mai Martaba ya hanani shi bansan meye yasa ba" itadai batace masa komai ba ya miqe yace “kina burgeni salonki yana sanyani nishadi nabarki kiyi iyakar abinda zaki iya kafin ki shigo hannuna"
Ficewa yayi ta tabe baki ta koma tayi kwance abinta bata tashi ba sai azahar da yunwa ta fafaketa ta shiga kitchen ta samawa kanta abinci ta dawo ta zauna a falon qasa tana zaune taji an bude qofar an shigo ta daga kanta suka hada idanu da Amrah da Zahrah ta miqe tana cewa dasu “Lahh Amrah sannunku da zuwa ku iso mana" wani mugun kallo suka watsa mata Zahrah tace “tun Ranar dana fara ganinki matsayin tsohuwar budurwar mijina naji zuciyata bata karbeki ba ashe kedin masifa ce Kuma bala'i cikin rayuwata Aminah kin kashemin Zainab nikuma nayi alqawarin kashe taki rayuwar sai kinyi nadamar shigo da kanki cikin rayuwar gidana"..........…...





Juhud is not free read... regular 300 VIP 600 via👉🏼 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank



Then you show ur evidence via WhatsApp 09013718241...



Juhud ba littafin kyauta bane kada ki biya 300 regular VIP 600 kafin ki karanta ta wannan account din 0255526235 Fauziyya Tasiu Umar GTbank ko katin MTN pls ban buqatar vtu hoton katin ko digit number ta WhatsApp number 09013718241.....



*Oum Hairan*
[8/9, 7:14 PM] Oum Hairan: Sun jima suna zazzaga mata rashin mutumci banda kallonsu da hawaye Babu abinda takeyi ita qwarin gwiwar ayi mata ta rama ma ba ko yaushe takedashi ba tana tsaye suka juya suka fice Amrah tana cewa banza liqaqqiya ai baki fara kuka ba tunda kika nace Saida kika auri yayanmu muna murna Allah yarabamu da qaya ashe kina manne zaki gane bakida wayo shashasha dake kawai" suna fita ta koma ta zauna ta zuba uban tagumi tana kukanta me cin rai bata ganin laifinsu kanta take dorawa laifi data maqale musu da tayi wani yunquri na samawa kanta yanci da yanzu ba wannan zancen akeyi ba itadai batasan tsayin lkcn data bata ba kawai dai taji tsayuwar motarsa ne ta miqe ta dauke abincin data faraci dazun ta nufi kitchen din ya shigo yabi bayanta da kallo bata juyo ba hakanan yaji ransa bai kwanta da shirun nata a kitchen ba yabi bayanta.
Tsaye ya tarar da ita ta kifa kanta a cabinet tanata kukanta me karya zuciya gabansa ya fadi ya fita yabarta qlau ya dawo ya tarar da ita cikin damuwa, matsawa yayi bayanta ya hade tazarar dake tsakaninsu qamshin turarensa ya daki hancinta taja ajiyar zuciya ya sanya hannunsa biyu ya dagota ya juyota ta sunkuyar da kanta ya matsa sosai kanta ya hade da qirjinsa yaja numfashi ya dafa kanta yace “meye ya faru bayan fitata naji a jikina wani yazo gdannan" dagowa tayi ta dubeshi ko fushi Kareem yake fuskarsa a washe take yace “fadamin waye don Allah" kawar dakai tayi ta tureshi ta juya zata fita ya riqo hannunta ya janyota ta shige qirjinsa ya Sanya hannunsa ya matseta Yana sauke ajiyar zuciya me sanyi yace “kiyi hqr don Allah duk da kinqi fadamin meye ya kawo kukan"





Sake janyewa tayi zata bar gurin ya riqota ya dagata cak bai direta ko inaba sai dakinsa ya sauketa a gadon ya kulle qofar ya shige bathroom ya jima ya fito daure da towel yana tsane jikinsa har zuwa lkcn kanta na qasa tana wasa da yatsunta bayan ya gama shiryawa ya zauna a gefenta ya riqo hannunta Yana qarewa lallen hannunta kallo yace “yayimin kyau sosai am su Amrah da sukazo Basu bar miki saqo kibani ba?" Girgiza kai tayi yaja numfashi yace “ita dawa sukazo?" Cikin rawar murya tace “da Zahrah" nandanan annurin fuskarsa ya dauke yace “ok sai sukace miki me da har yasaki kuka?" Kallonsa tayi da idanunta da suka kada sukayi jawur yace “uhum inajinki" kawar dakai tayi yasan bazatace komai ba ya dauki wayarsa ya fice batasan me yayi ba ya dawo tana zaune inda yabarta yace “kiyi hqr komai zai wucce insha Allahu"
Ganin taqi daina tsiyayar hawayen yasashi kashe wutar dakin ya nufota gabanta ya yanke ya Fadi ta miqe da sauri taja baya ya tsaya tare dayin murmushi yace “kina tsoron mijinki akan me?" Bata ganinsa sosai hakan yabashi damar cafkarta ya cillata gadon ta miqe yabita da sauri ya danneta ya dora harshensa a kuncinta yana tsotse hawayen nata sanyi da qamshin iskar bakinsa na saukar mata da wata kasala me qarfi shikuma yaci gaba da yawo ds harshensa tsakanin kuncinta da wuyanta gabadaya ya saukar mata da wani yanayi wanda bata tanajin irinsa ba ta lumshe idonta tana sauke numfashi a jere hakan yasashi fahimtar rauninta ashema sauqin kamuwa gareta ya tsaya Yana wahalar da kansa.




Saida ya sake kashenta jiki sannan ya kamo bakinta ya hade da nasa yana tsotsar lips dinta da salo me kwantar da hankali a wannan yanayin ya mantar da ita komai daki daki ya rinqa binta harya isar da hannunsa ga qirjinta tayi saurin riqe hannunsa ya dago kansa dake tsakanin qirjinnata cikin muryarsa me sanyi data hade da kasala yace “na daina bakyaso?" Da sauri ta daga masa hannu yayi ajiyar zuciya tare da janyewa ya koma gefe ya kwanta yana matse cinyoyinsa tare da lumshe idonsa yayi alqawarin iya wahalar da zaisha bazai takurata ba yafiso ta kawo masa kanta ta yanda bazataji ya wahal da ita ba tunda yasan kansa yana jinjina haduwarsu, ji yayi ta shige jikinsa ta Kira sunansa da wata murya data sanya tsigar jikinsa miqewa gabadaya ta rikice jikinta sai rawa yakeyi ita kanta yanayin yabata tsoro bata taba rinskar kanta a mugun feeling irin na yau ba ji takeyi kamar bazata iya kaiwa gobe ba indai baa sosata ba bai zataba bai tsammata ba yaji harshenta a saman nipples dinsa yaja wata wawuyar ajiyar zuciya ya dafe kanta yace “ahhhhh Meenah!!!"
Harshenta ta rinqa karkadawa a saman nipples dinsa Yana sauke numfashi tare da sakin ajiyar zuciya Yana matseta ta sake shigewa jikinsa a hankali ta janye tare da dora kanta a qirjinsa tana shafa gashin dake kwance tace “bamuyi sallar Isha ba....." kulle mata baki yayi da nasa yana Shan yawunta yana sakin nishi jikinsa na rawa yace “kin riga kin canzamin move bazan iya komi ba yanzu Meenah ki barni nasha daga gareki zanji dadi zanyi alfahari da hakan kinji don Allah kice kin amince bana burin yimiki dole" kawar da kanta tayi ya janye jikinsa ya miqe yana layi ya nufi bayi baikai ga qarasawa ba ya zauna saman bedside drower yana mayar da numfashi daqyar shi kadai yasan yanayin da yakeji mararsa ds twins dinsa ciwo sukeyi masa sosai yanason ya fitar da ruwan daya taru masa Meenah taqi bashi dama bangaren zuciyarsa daya na bashi shawarar ya karbi haqqinsa kota wanne hali wani sashin na cewa dashi aa yabita a hankali.




Miqewa yayi Yana Shirin shiga bathroom din yaji ta riqeshi ta baya yaja numfashi ya juyo ya dago kanta idanunta suka kawo ruwa tace “ni....sai nakega kamar bai dace....." Hannunsa ya dora saman bakinta yace “meye bai dace ba Meenah kina nufin kinfi ubangiji sanin abinda ya dace?" Saurin girgiza masa kai tayi yace “to shine ya halattamin ke Kuma yabani damar nayi komi dake batare da komai ba Meenah shi lamarin aure da gadon mamaci Allah ne ya tsara abinsa dakansa koda Rasheed yana tsakankaninmu yana rayuwa idan Allah ya qarar da rabonsa a jikinki hakanan ko yanaso ko baiso zaiji baya buqatar zama dake koda laifi ko babu ya rabu dake ni Kuma na dauka saboda Allah ya hukunta Mana kedin ba matar mutum daya bace a cikinmu so banso don Allah ki daina qoqarin haramtamin abinda Allah ya halattamin ko zamanin samartaka bantabaci daga haramtacciyar itaciya ba"
Yana fadin haka ya juya ya shige bathroom din a bakin qofar ya tsaya yace “bazan hanaki abinda kikayi niyya ba bakuma zanyi miki dole ba Amma kisani duk da cewa tun aihuwata an haifeni da sign na ciwon zuciya bata taba qarfin da take neman kaini Ramin kabari ba saita dalilinki Aminah idan kika wayi gari babuni kada ki zargi kowa kece abar zargi" turo qofar yayi ta tura da qarfi tana wani irin kuka me kashe jiki ta durqushe a gabansa tace “kayi amfani da qarfinka ka qwaci haqqinka yafimin sauqi dakace kabarni da Allah Ya Kareem da wanne zanji da ciwon rashin galihu koda na sharrin Maitar da aka liqamin ko Kuma da batan mij......"




Rufe mata baki yayi jikinsa na rawa yace “karki qara Aminah karki qara hada kanki dashi keba matarsa bace yanzun kada ki Kuma danganta kanki da wani namiji madamar bani bane" yanda ya harqitse mata lkc guda abin ya bata tsoro bata taba ganinsa cikin wannan yanayin ba ashe akwai abinda yake sosa zuciyarsa haka lallai kishinsa babba ne, kama hannunta yayi ya fitar da ita daga bayin ya koma ya watsa ruwan daqyar ya gama saboda zafin da zuciyarsa takeyi masa ya fito har lkcn tana tsaye a inda ya barta ya kalleta yace kije kiyi wanka zakiji dadi sosai" batayi masa musu ba ta nufi qofar fita daga dakin yabita da kallo harta fice tana fita tayi wankan tayi sallar Isha tayi shafa'i da wuturi ta zauna tana lazumi sai 11:00pm ta miqe tasa kayan baccinta ta shafe jikinta da turaruka masu qamshin gaske ta kwanta.
Hakanan takejin zuciyarta bata aminta da rashin jin motsinsa ba ta miqe ta fito daga dakin nata taja baya da sauri ganinsa tsaye a falon yana kaiwa da komowa cikin yanayi na mutuwar jiki ta matsa bayansa batare da yasan ta fito ba tace “Ya Kareem" tsayawa yayi batare daya juyo ba ta zagaya gabansa yayi saurin sanya hannunsa ya goge hawayen daya tsiyayo masa ta zaro ido waje tace “mene yayi zafi?" Murmushi ya qaqalo yayi mata ya lakace mata kunci yace “meye ya hanaki bacci?" Rausayar dakai tayi tace “kai meye ya hanaka?" Iska ya furzar yace “Feeling Meenah" kallonsa tayi da sauri ya lumshe idonsa tare da budewa a kanta yace “kwanaki 34 ga lafiyayyen namiji kamata babu mace ba kwanakine masu sauqi ba ko a baya lkcn da baki gama sanin wayece kedin ba kinsha tambayata meyesa nake yawan azumi nasha fada miki zaki fahimci hakan daga ranar da liman ya saqala igiyar aure tsakanina dake Aminah Ina wahaltuwa haqiqa cikin kwanakin nan kinqi tausayamin"




Daga hannunta tayi sama idanunta a lumshe tace “nabaka dama
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment