Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

mala mala akasan wajen, daga Omari yayi yana sharemai hawaye ya rungume shi yana kallon maman tasu dake nan kaman mara rai, Tsugunnawa tsohuwar tayi akanta tace "subhannallah metayi ta galabaita haka jini ya tsinke mata?" ahankali yace "gudu mukayi" girgiza kai tayi tace "assha ku matsa daga tachan inga mezan iya mata Allah bani sa'a" jan hanun Omari yayi yana rike da Abdallah suka koma chan daga dan nesa basa ganin su, rungume Abdallah yayi yana bubbuga bayanshi danyay bacci shikuma Omari ya daura kanshi akan kafadarshi ya rikeshi duk sunyi zuru zuru gawata uwar yunwa dake cinsu tun asuba suke gudu gashi har yamma tayi da kyar Abdallah yay bacci dan yunwa yakeji, sunkai kusan awa uku zaune sanan matan tazo inda suke rike da dan kwalin Maman su tana share hanunta dake da jini sosai idanunta sunyi wani iri tace "kuzo Maman ku na kiran ku" da sauri Omari ya mike tsaye shima tashi yayi rike da Abdallah dayay bacci gabanshi na faduwa sosai yarike kanin nashi sukai wajen, akwance sukaga Maman nasu inda suka barta ga jaririyan data haifa acikin wani mayafin ta baki an nannadeta, dago kai maman nasu tayi da kyar ta kallesu da gudu Omari na kuka ya tsugunna agabanta ya daura kanshi akan hanunta yana kuka, murmushi tayi ta shafa kanshi kafin ta daga hanunta ahankali ta mikama Marwan dake tsaye goye da Abdallah dake bacci abaya, ahankali yataka kafa yawani irin tsugunna agabanta idanunshi sunyi ja yana kallon fuskar Maman tasu yanda tai fari sosai tai wani irin haske kaman mara jini, dago jaririyan tayi ta mikamai hakan yasa ya sauko da Abdallah ya mikama Omari shi ya karbi yarinyan yana kallon fuskanta very cute baby girl ga gashi kanta bakin kirin har goshi tana bacci, dayan hanunshi ta kama hakan yasa ya kalleta ahankali ta mikama Omari hannu hakan yasa ya riketa shima yana kallonta cikin kuka murmushi tamusu da kyar cikin harshen larabci tace "Marwan" dago kai yayi ya kalleta yama kasa magana tsabagen yanda yakeji ahankali tace "ga sister kunan nasa mata suna Rahma da babban ku kafin ya rasu yace inhar nahaifi mace sunan dazamu samata kenan, Marwan ka kula da kaninka kaji, duk runtsi duk wahala karka sake ka rabu dasu ko ka nisan cesu, Omari" takira sunanshi tana kallon fuskarshi asanyaye, daga mata kai yayi cikin kuka yakasa magana, ahankali tace "kubi yayan ku kaji, kome yace shizakuyi, karku saba mai ko sau daya, kuhada kanku kuso junanku, farin cikin dayan ku ya zamto na dukan ku, bakin cikin dayan ku ya zamto na dukan ku, karku sake ku koma gida dan zasu kashe ku kaman yanda suka kashe mahaifin ku, Marwan" takira shi ahankali tanadan nishi, cikin wani irin raunanniyar murya yace "Umm" ahankali ta daga hanunta dake rawa ta mika zata daura akan kan jaririyan dake hanunshi takasa sabida yanda hanunta ke rawa hakan yasa ya kamo hanunta ya daura akan yarinya murmushi tayi wasu hawaye suka gangaro ta gefen idanunta da kyar ta iya magana tace "ina so bayan na rasu kutafi motherless home achan za'a kula daku zasu tayaku rainon Rahma kanajina" gyada mata kai yayi daidai lokacin Abdallah yatashi da kuka sauka yayi daga jikin Omari yafada jikin maman tasu yace "Momma are you sick?" cikin kuka, rungumeshi tayi sosai tafashe da kuka sosai danya karya mata zuciya, hannu tamikama Omari dake kuka shima harda majina yafada jikinta ta rungume su biyu tana lallashin su tana kallon Marwan da idanunshi sukai jajir yana kallonsu, dagasu tayi ta kalli Marwan tana murmushi takamo hanunshi da kyar hawaye nafita ta gefen idanunta tace "my strong brave boy, the only Man damuke dashi, haka nakeson ka da jarumta, karkai kuka okay dan aduniyan nan kaikadai ne gatan kaninka, inaso ka rage zuciyan nan naka, wanan hot temper dinan ka rageshi kaji Marwan, ga kanwarku nan ka kulanmin da ita, mace ce ka tsaremin ita ka kare mutuncin ta, katuna abinda Abban ku yafada akan idan har mace na haifa? Gyada mata kai yayi ahankali, tai murmushi tace "Masha Allah, karka manta da hakan, Omari karku manta kota girma bata yardaba ku fada mata abinda iyayenta sukace ce kuma suke so, inaso ku kula da junanku kuso junan ku, ku hada kanku ku dawo daya, karku sake ku raba kanku, ku tuna kuku dinan kune ku, kuna gatan kanku, Allah ya muku albarka ya tsaremin ku, ya karemin ku, ya kulanmin da ku, i love you so much yarana" sosai Abdallah da Omari ke kuka ahankali ta zare hanunta daga kan macen idanunta na kukkulewa ta mika hanunta tanaso ta shafa kan Abdallah wani irin jini ya balle mata paaa da sauri tsohuwar da matsar dasu Abdallah tana salati ta tsugunna tana cema Marwan ya matsa tashi tsaye yayi yana kallon maman nasu rike da jaririyan su Omari da Abdallah suka wani irin rungumeshi suna kuka sosai suna kallon maman nasu da jikinta ke rawa, kafe maman nasu yayi da ido ko kyaftawa bayayi tun yana ganin alamun numfashi ajikinta har yadena gani ya lumshe ido zuciyarshi na wani irin rawa ya tsugunna ahankali ya kankame kaninshi yana sauke ajiyan zuciya da sauri da sauri, mayafinta tsohuwar ta cire ta lullube ta tajuyo ta kalli yaran dataji sun bata tausayi sosai tace "bari naje nakira jama'a amata sutura" fita tayi tabarsu awajen daidai lokacin jaririyan ta tsala ihu tashi yayi ya shiga jijjigata yana kallon fuskarta sai ihu takeyi gasu Omari na kuka suma hakan yasa ya sakamata yatsarshi abaki ta dinga tsotsa tana bacci hawaye yacika idanunshi ahaka bacci yasake dauke ta gaba daya ya zare yatsar yasake rungumeta yana kallon gawan Umm dake lullube.


Ba'a wani jimaba tsohuwar tadawo da mutane kusan 20 mata da maza da jarkokin ruwa a hannun su nan dai aka kebance wajen mata suka mata wanka ana gamawa aka shiryata suka sallaceta aka kaita makwancinta Abdallah Omari sai kuka suke yana lallashin su, tsohuwar da mutanen ne suka tasasu agaba suna tambaya basu da yan uwa da kyar ya iya girgiza kai yace "basu dashi kuma baban su yarasu" hakan yasa tsohuwan tace to azo aje akaisu motherless home kaman yanda mahaifiyar su tafada kodan wanan jaririyan nan akula da ita achan, cikin mutanen wani dayazo da machine ya kwashe su aka kaisu motherless home din dake garin nan fa aka karbesu ga yara da dama agidan, aka karbi jaririyan da ya yarda ya bayar da kyar aka mata wanka aka bata madara aka saka mata kaya za'a kwantar da ita akan gadon jarirai ya karbeta ya rungumeta tsam hakan yasa suka barshi da ita, Abdallah dake zazzabi sosai aka bashi magani aka basu abinci sukaci banda shi daketa kallon yarinyar su Omari na gamawa sukai bacci akan gadajen su shiko yana zaune da jaririyan yana kallonta yanda take bacci abinta.




Ahaka rayuwan tacigaba ana kula dasu sosai a motherless home din, ma'aikatan wajen nada kirki har an sansu dan kullun tare zaka gansu su uku wuri daya babbban yadau jaririyan da ayanzu har yama iya mata wanka yaro dan 12 years yanama jaririya wanka yabata abinci ya shiryata yariketa, basa wasa da sauran yaran koda yaushe suna tare a manne suna jikin wansu.

Jaririyan na kimanin wata biyu wata rana suna zaune a compound din motherless home din suna zaune a simenti a karkashin bishiya yana rike da Rahma da idanunshi biyu tana rike da yatsarshi gam tana kallon sama, Abdallah yay bacci ya daura kanshi akafarshi shikuma Omari ya jingina da bayanshi yana wasa da duwatsu yaga an bude gate din gidan wasu manyan motoci hudu sun shigo an rufe gate din, wacce ake kira da Ameera dake in charge of the motherless home tafito tana murmushi aka bude kofa wani babban Alhaji dayasa kayan yan Nigeria malum malum dawani balarabe dayasa farin jallabiya da rawani ne suka fito, tunda yafito yake kallon su Marwan har hada ido sukayi da Marwan daya kafesu da ido shima yakasa dena kallon yaran, Ameera ce ta nunasu ganin yanda yake kallonsu tace "wayan chan marayu ne maman su tamutu tabar kanwar su mace jaririya watan ta biyu yanzu, muje office Alhaji wanan karan adopting kazoyi ko siya kazoyi? Dan gaskiya kudi yakaru" wucewa sukayi sukai ciki office dinta Alhajin na kallon yaran.
Motherless home din abinda gwamnatin garin basu saniba shine suna sayar da yara kuma wanan Alhajin suke saida mawa duk bayan wata biyar yake zuwa saya, nan Alhaji ya nuna yana sonsu mazan yabiya miliyoyi akansu ya shiga mota shida abokin shi balarabe yacema Ameera da daddare insunyi bacci zai turo adauke su gyadamai kai tayi tana murmushi dan tunda yake siya bai taba biyanta irin kudin wanan karan ba, aranan da daddare duk suna bacci shidai Marwan sama sama yake bacci dan tun ranan dasuka fara dira gidan marayun yaji hankalin shi bai natsu ba baya iya bacci saisa bini bini yake tashi ya kalli kaninshi sanan yakara kwanciya yana rungume Rahma da kyau, lekowa Ameera tayi dakin tawani irin huro wani hoda, strange wari dayaji yasa yabude ido yana kokarin laluban touch light yaduba Rahma dasu Abdallah amma kafin ya farga kawai yay passing out, shigowa wasu kattai sukayi suka kama Marwan, Abdallah da Omari suka fita dasu aka sakasu awani bus a sussume akabar motherless home din dasu. Wani irin ihu Rahma dake kan gado ta sandara da sauri Ameera data taushe hanci ta shigo ta dauketa tana jinjigata tafito sanan ta saki hanci tace "sorry baby anbiyani da kyaune saisa na saida brothers dinki kema karki damu in kinada luck wani zaizo yasiyeki in baki dashi haka zaki girma ahannuna yarinya".
[9/13, 11:52 PM] Lady: *don't read in baka biyaba*




*Maman Abd Shakur*


Gyada mata kai yayi yace "okay" zare safan yayi daga hanunshi tawani irin kafe hanun da kallo ganin hannu fari fat kaman na bature kafin ahankali yana kallonta ya zare na dayan hannun ya ijiye safan akan table din wurin, ahankali ya sauko da jakan dayake goye a bayanshi ya ijiye kan table yana kallonta, hanunshi ya daga sama ahankali ya kwantar da hulan hoodie dake kanshi baya, hanunshi yakai kan fuskar nashi slowly yana kallonta, sosai kirjinta ke wani irin bugawa da kana ganinta ma zaka gane hakan, saukar da hanun yayi zuwa wuyanshi kafin ahankali ya juya mata baya, cire black mask din yayi gabaki daya ya ijiye kan table batare daya juyoba, tundaga keyanshi har molon kanshi take kallo da babu gashi ko daya kan saiko dashi, ahankali yace "are you ready" gyadamai kai tayi kaman yana ganinta ta kasa magana tsabagen yanda kirjinta ke bugawa, wani irin juyowa yayi ya fuskance ta, ihu tayi sosai ta diro daga kan kujeran tai hanyar fita daga kitchen din da sauri sakamakon wani irin fuska data gani mai kama dana dodo, fuskan babu gashin gira gashi wasu irin kuraje kuraje da wani irin dabbare dabbare baki baki kaman fuskan aljani a fuskan, bakinshi baki kirin, wani irin gudu tayi amugun tsorace zata fita daga kitchen din kamota yayi hakan yasa ta saki ihu ta kankame jikinta ta kulle idanunta gam, ahankali ya jawota jinkinshi yajuyo da ita yahada jikinshi da nata yadanyi dariya dashi kanshi yamanta rabonshi dayay dariya haka, hanunshi ya daura akan habarta yana kallon yanda ta kankame idonta yace "open your eyes" makemai kafada tayi murya chan kasa dake rawa sosai tace "am scareddd" bakinshi yakai saitin kunenta yace "of me?" gyadamai kai tayi tana tabe bakin shirin kuka jikinta na rawa sosai kafin ahankali ta bude idanun ta daurasu akanshi wani irin nishi tayi uhmmmmm tana kallon fuskar shima ita yake kallo kurii batare dayayi ko motsi ba, cikin rawan muryan na mutum dake cikin tsananin tsoro tace "what happen to your face?" shiru yayi bai bata amsaba hakan yasa ta fashe da kuka sosai dan wani irin tausayi yabata murya chan kasa tace "sorry yanama zafi?" tai maganan tana kuka, ahankali yadaura hanunshi akan fuskarta ya share mata hawayen kafin ya dagata ya zaunar da ita akan kujeran datake kai da ya tsaya agabanta yana kallonta, juyawa yayi yasa hannu ya cire face mask din kurajen ya ijiye akan table, bin mask din tayi da kallo kafin ta dago kai tabi bayanshi tayi da kallo, tundaga bayan wuyanshi take kallo wani irin fari tass tass ne skin dinshi dake wani irin glowing sanan ga gashin kanshi baki kirin maidan tsawo a kwance sun wani irin yin curls kana ganin gashin kasan ba gashin dan Nigeria bane kaman gashin balarabe kaman gashin ba indiye, sosai gabanta ke fadi fin na dazu ma tarasa kuma maisa hakan ke faruwa da ita, yakai kusan 2min kafin ahankali ya juyo irin juyowan nan kaman wani boss, tundaga kanshi take kallonshi yanda gashin kanshi maidan tsawo suka kwanta sukai curls, wani irin farin mutum ne da fari irin na larabawan nan gareshi, kwayar idon shi ash color ne saikuma farin idon fari fat yanada dogon hanci sosai gashi ya tsaya akan fuskan nashi dass saiwani irin pinkish lip pink sosai kaman lip din bature karami, yanada saje maidan yawa da fadi gashin baki sidik kwantancen gashi mai walkiya sanan yanada dan gemu daya kwanta amma baiwani sakko yay tsawo sosai ba, tunda take bata taba ganin kyaykyawan namiji hakaba Ya Muhsin da Ya Ahmad kyawawa ne, sanan wanan mutumin data taba bugewa a super market shima kyaykyawa ne amma duk basukai wanan ba, kyaykyawa ne ajin farko naban mamaki ma, kasa jure kallonshi tayi hakan yasa ta saukar da kanta kasa kirjinta na bugawa sosai kaman zatai fitsari, ahankali ta diro daga kan kujeran jikinta na rawa sosai tazo zata wuce ta gefenshi tafice daga kitchen din, hanunta ya rike gam ya juyo da ita ta dawo gabanshi, hanunshi are very soft kaman natamace, yadaura akan fuskanta murya chan kasa yace "Hey! U asked me to unmask myself i did dat and u want to walk away, why?" yay maganan ahankali yana dago fuskarta murya chan kasa yace "look up?" dago dara daran idanunta tayi ta zubasu akan fuskarshi, dan lumshe idanunshi dataji sun mata wani iri ajiki yayi ya budesu, ahankali ya zuba akanta yace "why?" girgiza mai kai tayi jikinta na rawa sosai dan wani irin cika mata ido yayi bana wasaba muryanta na rawa sosai tace "am scared" janyota jikinshi yayi ya daura kanta akan kirjinshi ya kankameta yadan fuzar da iska yace "of me?" gyadamai kai tayi batare datai magana ba, dago kanta yasake yi ya kalleta dauke idanunta tayi tai wani irin atishawa tana kallon wuyanshi wani bakin layi data gani babba haka yasa ta daga hanunta dake rawa sosai ta daura akan layin, atishawa yayi yay hamdala ahankali yanajin wani iri sabida hanunta dayaji akan wuyanshi, ahankali yakai hanunshi ya rike hanun nata batare data kalleshiba tana kokarin fizge hanunta tace "wat scar is that?" daukanta yayi hakan yasa ta tsorata sosai ahankali yajuya yafita daga kitchen din da ita wani irin faduwa gabanta keyi yahau staircase da ita hannu daya yasa yabude kofar dakinshi ya shiga da ita ya maida kofan ya rufe yay wurin gado da ita, kwantar da ita yayi akan gadon shima ya kwanta a gefenta yasata ajikinshi sosai, fashewa tayi da kuka sosai jikinta na rawa sosai wani irin tsoro takeji dan yanda yasata ajikinshi a kwance yasa ta tuna da Abba, ahankali ya kama lips dinta da yatsunshi yace "shiiiii" hadiye kukan tayi batare data kalleshiba, murya chan kasa yace "how old are you" yay maganan yana sakin lips dinta yana kallonta, bakinta na rawa sosai cikin shirin yin kuka tace "22" murmushi yayi dake lobar da dimple dinshi na both side, murya chan kasa yace "look at me" kallonshi tayi tana sauke ajiyan zuciya dan sosai yake cika mata ido kyanshi yama idanunta yawa, wani cool look yake mata ahankali dawani irin murya da dagashi sai ita zasu iyaji yace "you're 22 u are not dat small but why do you like crying and acting like a baby" so take ta lumshe ido dan kallonshi wani irin cika mata ido yake yanasa tana shakkar shi tana kumajin wani iri da kyar adan tsorace tace "am the last born" ahankali shima yace "and d only gurl in d house right?" gyadamai kai tayi wasu hawayen nabin gefen idonta suna gangarawa kasa, cikin tsananin fargaba da tsoro tace "yaushe za...zaka...zaka kaini gun Mumy na? I...i don't like here am d only one in dis h..ou...house" ta karashe maganan d kuka sosai, hanunshi yakai kan soft face dinta yace "Hey! Stop crying for me" gyadamai kai tayi tana hadiye kukan, matso da kanshi yayi sosai saitin fuskarta danhar tanajin saukan numfashin shi da sauri ta runtse ido kirjinta na bugawa kaman zai fashe sabida tsoro murya chan kasa yace "look at me" bude idanunta tayi ta kalleshi tana danne kukan tsoron dake cinta, hanunta daya yakama yahada da nashi ya rike gam yana kallonsu kafin ya kalli fuskarta yace "you are not d only one akwai brothers dina agidan i was d one dat told them karsu bari ki gansu, u want to be seeing them?" da sauri ta gyadamai kai hawaye na gangaro wa daga idanunta, murmushi yamata daya lobar da gefen fuskanshi, numfashin ta yakusa daukewa yace "okay you will see them tommorow okay, Omari and Abdallah sunan su" gyadamai kai tayi wasu hawayen na gangaro mata jikinta ko ina na bari, kafeta yay da ido itama kallonshi take amma kana ganin kallon kasan dan yayi forcing dinta ne, sunkai kusan 10min ahaka sanan yace "do you have friends in school?" gyadamai kai tayi murya chan kasa yace "a guy or a lady?" cikin rawan murya tace "lady, Fauzy" gyada mata kai yayi tareda sa hannu ya zare hulan kanta long kalaban ta suka bayyana yabisu da kallo kafin ya kalleta yace "ask me too" shiru tayi kirjinta na bugawa sosai takasa magana, ahankali ya shafo lips dinta yace "am listening ask me" cikeda tsoro bakinta na rawa sosai tace "are...are you d one danagani a hospital dinmu dat day?" gyada mata kai yayi yace "yes har aka kaiki police station akaina ko" gyada mai kai tayi kaman yarinya, shiru yayi yana wani irin kallonta kafin ahankali ya kwantar da kanshi kan filon da kanta yake kai ya juyo da fuskanta tareda hada forehead dinsu suna facing juna, atishawa tayi shima yay atishawan sosai jikinta ke rawa cikin kuka sosai tace "sanyi nakeji" dan lumshe ido yayi yabude su ya daura akanta yace "me too" atishawa yakara yi itama tayi da sauri ya karayi itama tayi, ahankali yajawota yahadata da jikinshi tsamtsam yay wani atishawan itama tayi tana rawan sanyi, hannayen shi biyu ya daura akan fuskanta yana wani irin kallon pink lips dinta dake fizgarshi sosai ya kafe da ido dan rawan kuka suke, fashewa tai da kuka tsoronshi yahanata tai ko motsin kirki, murya chan kasa yace "shiiiii" hadiye kukan tayi tana sauke ajiyan zuciya da sauri da sauri, daura forehead dinshi yayi akan nata yay cupping face dinta yana kallonta tana wani irin sauke ajiyan zuciya da sauri da sauri dake sauka akan fuskarshi, ahankali slowly ya saukar da bakinshi kan bakinta yabata light kiss mai kara ya janye kanshi yana kallonta yanda ta lumshe ido kamkam kirjinta na bugawa, tunda yake bai taba kissing mace ba and wamam dayayi really feels good, kasa hakura yayi yasake mata another light kiss mai kara batare daya janye bakinshi daga kan nataba yana numfashi da sauri da sauri shi kanshi baisan yayayiba gani kawai yayi ya shiga tsotsan bakinta yafara kissing dinta passionately kaman zai cire mata lips dinta.
[9/13, 11:52 PM] Lady: *idan kika karanta baki biyaba keda Allah*



*Maman Abd Shakur*


Fashewa tai da kuka sosai tana so ta fizge bakinta amma yaki sakinta yakai kusan 20min yana kissing dinta kafin ahankali ya janye bakinshi daga nata idanunshi sun kankance sunyi lup lup dasu lips dinshi sunyi jajir yana wani irin kallonta, duko dakai yayi saitin fuskarta kafin ahankali yasa hannu ya goge hawayen datake yi cikin dishashiyar muryan shi yace "stop crying for me" gyadamai kai tayi jikinta narawa sosai tahadiye kukan, ahankali yasake rungumeta tsam tsam yana shafa bayanta saida yaji kirjinta yadena bugawa sanan yadago kanshi ya kalleta har lokacin ta kankame ido, kaman mai rada yace "open your eyes" bude idanunta tayi ahankali cikeda tsoro ta daura akanshi tana shirin yin kuka, hannayenshi biyu ya chusa ta karkashin kanta ya dago da kanta sosai har hancinsu na gogan juna, ajiyan zuciya ta sauke tana wani irin kallonshi kaman taga dodo, goga hancin shi yayi akan soft wet lips dinta kafin yahade forehead dinsu ya kwanto da fuskarshi kan nata sosai dan har lips dinsu na gogan juna cikin wani irin murya dake sanya natsuwa yace "wat have you done to me? Why am i like this" yana maganan lips dinshi na gogan nata, girgiza mai kai tayi a tsorace tana kokarin kawad da kanta amma yaki bata daman hakan, murya chan kasa yace "answer ur husband" wani irin nishi tayi dayasa ya runtse ido da sauri sabida yanda hucin zafin yamai wani irin tsir tsir ajiki da kyar muryanta na rawa sosai tace "p..pl..leas stop am..m..scared" tafashe mai da kuka girgiza mata kai yayi yace "stop crying" gyadamai kai tayi ta hadiye kukan tana sauke ajiyan zuciya tashi yayi ya zauna ya dagata zaune ya nuna kayan jikinta ahankali yace "girls sleep with this?" shiru tayi dan bata gane kan tambayan ba ahankali ya sauko daga kan gadon ya mika mata hannu alamun tazo saukar da kanta tayi kasa dan bazata iya jure kallonshi ba taki bashi hanun, murmushi yayi ya kamo hanunta ya sauko da ita daga kan gadon yana rike da ita sukai hanyar bayi kofa ya bude musu suka shiga agaban closet ya tsayar da ita ya bude saiga kaya nan daya sa su Omari suka siyo da yawa juyowa yayi ya kalleta yace "change" kallon kayan tayi kafin ta share dan guntun hawayen daya zubo mata da sauri wani dogon gown sky blue na bacci ta zaro wanda zai iya tsaya mata a gwuiwa ahankali batare data kalleshiba ba tabude kofa ta shiga bathroom binta yayi da kallo kafin ya zauna akan kujeran dake wajen yana dan lumshe idanu yana ganin fuskarta takai kusan 10min cikin bayin danhar saida tai wanka sanan tasaka rigan yamata kyau sosai rigan mutunci ne ta bacci iya gwuiwa yamata kyau sosai ajiki saida ta jinginar da kanta jikin kofa shiru dataji yasa taji dadi alamun babu mutum da sauri ta bude kofa ido da ido sukayi yana zaune akan kujeran ya kafe kofan bathroom dim da kallo saida kirjinta ya buga kai wanan mutumi yacika kwarjini da sauri harda dan gudunta ta bude kofa tafice dakin har tana neman faduwa fadawa tayi kan gado taja bargo ta lullube kanta jikinta na rawa sosai tafashe dawani irin kuka kasa kasa tana kiran Mum tun tana sauraran fitowan shi har bacci yay gaba da ita. Yakai kusan 20min abayin yafito kan gadon yahau yana kallon dan fuskarta yanda yay fayau tana sauke ajiyan zuciya ahankali ahankali, ahankali ya yaye bargon ya shige kafin yadagata ya kwantar da ita akan jikinshi matseta yayi yana sauke ajiyan zuciya da kyar bacci da baitaba mai dadi irinshi ba yay awon gaba dashi.



Wuraren takwas nasafe Abba ya shigo gidan parking yayi a parking space ya sauko daga motan ya shigo part dinsu, zaune yaga Mum afalo taci uban gayu na manya mata tai kyau sosai tana kallon tv kana ganinta kaga tsantsan damuwa akan fuskarta dan bama tagane me ake fadi a tv, sallama yayi ciki ciki hakan yasa ta dago kai ta kalleshi dauke kai yayi yawuce ciki yana kallon kofan dakin Nadeera kaman ya bude ya ganta haka yakeji, bude kofar dakinshi yayi ya shiga yay bedroom dinshi direct kafin ya shiga bayi ya sakinma kanshi ruwa ya mikar da hannayen shi ya dafa bango yana tunani, ko duka duniyan nan ya mallaka zai iya bayarwa inhar zaigano inda princess take d biggest problem in trying to track down her location according to abinda commissioner yace is because bata tare da
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment