Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

waya da an iya anyi tracking down location dinta sharp sharp, gashi bai samu yaga inda koda hanyar gidansu ba balle yabada any clue dazaisa agano inda take easily, inda ace yasan sace princess wanan mugun zaiyi daya shanye koma me yake damun shi aranan yahakura, gashinan duk binta dinan dayayi ne yaja wani banza chan ya aureta, runtse ido yayi da karfi ya daki bango yana cikin zafin rai yana fata dakuma rokon Allah akan karya bashi daman tabamai princess harsai angano inda take tadawo gida araba dan iskan aurenta dayayi. Yabata kusan one hour abayi tunanin yanda zaiga princess yake sanan ya kashe shower yabude kofa yafito daga bayin Mum yagani zaune abakin gado hakan yasa ya dauke kai yay gaban wardrobe wani goggagen shadda gizna brown ya ciro ya shiga sakawa ahankali Mum tace "a ina ka kwana jiya Alhaji?" ko kallonta baiyiba saima karasa zira riganshi yayi yay gaban madubi yadau mai yana shafawa tasowa tayi tazo wajen tana binshi da kallo tace "ina kaje Alhaji, a ina ka kwana?" ko kallonta baiyiba danji yayi yanxu koson ganinta bayayi daukan turaren shi mai shegen dadi yayi zai fesa Mum ta fizge cikin fushi ta jefar akasa yafashe tace "nizaka maida mahaukaciya nace ina kaje?" wani irin mugun kallo yamata kafin yay controlling kanshi yace "naje neman abin sona, yata Nadeera, my princess, the apple of my eye, My love" cikin wani irin kunan rai Mum tace "Alhaji wai dan Allah lafiyan ka lau kuwa kokuma you are posses ne nakira malamai ama ruqiya, this isn't you" wani kallon rainin wayo yamata kafin ya dauko wani sabon turare zai fesa takara fizgewa cikin kunan rai tace "Alhaji talk to me wai menama ne? Dan Allah kabar wanan wasan dakake min i know you are joking ko dakace zaka auri Nadeera, nasan nama laifuffuka da dama, jiya nakasa bacci tunanin abubuwan danake ma nayi and nai concluding maybe zakai punishing dina ne you want me to realize my mistakes shine kake cewa u wanna marry princess, Alhaji yanzu kamin bayanin auren dakace kamata da gangster din dakace musan yanda zamuyi mu kwatota because i know wasa kakemin da xancen sonta kake xaka aureta ko Alhajina?" wani irin kallo yamata from head to toe kafin yaja tsaki yace "ina ganin too much business da tafiye tafiye yafara affecting yanda kike tunani ko Hajara, now bari namiki bayani daki daki kiji ki fahimta, zauna kiga" ya wani irin ingiza Mum kan gado ta zauna ya tsaya agabanta ya nuna kanshi yace "ni dai ni dinan uban yayan ki Muhsin da Ahmadu Alhaji Naseer Aluminum Son yarmu Nadeera nake, dazaran an ganta kinajina? Zan shigar da kara kotu zan raba auren inje masallaci a aura mini ita mubar muku kasar Spain zamu, jibi Hajara inama Princess so dakoke dakina budurwa ban miki irinshi ba, ke ina gaya miki princess yar baiwa ce, wato Allah yay hallita ne awurin nan, tafimini ke sau miliyan kan miliyan, Allah yay kira, yay zubi awajen nan, yatace idan na aureta sai yanda nayi da ita dama gata dajin magana very innocent girl wlh ba irinki ba dakika nunama duniya kinfi karfina, bari kiji kin riga kin shani na warke raras, auren Princess zanyi ke bakiga yanda muka dace bane jibifa sunayen mu Naseer da Nadeera wayyo Allah na" yay maganan yana wani irin shafa kirji yana kallon sama yana wani irin murmushi daya bayyana fine set of teeth dinshi, salati kawai Mum take aranta dan gani take kaman tabin hankali Abba yasamu, kallonshi tayi tace "Alhajina kodai tsufa ne yafara kamaka muje asibiti ne?" wani irin ihu Abba yamata kaman zai daketa yace "ni kike cema tsoho? Kibari mufara aure nida princess ta haifamin twins kafin kice nai tsufa, kinma tunamin lemme call commissioner yace dama nabashi yau da gobe lemme call him inji how far about princess dina, in sha Allah sai an ganta in sha Allahu saikinga aurena da princess, banyi baccin dareba jiya Allah naketa kaima kukana da yardan ubangijin al'arshi princess zata bayyana zakiga aurena da Princess hajara, agaban ki direba sai tuka mota yakaimu airport mu barmuku garin, nama mata order Lamborghini duk randa tadawo shi zan bata as gift i really really miss my baby girl" cikin Wani irin mugun kishi da gushewan tunani Mum tace "in sha Allah, da yardan Allah baza aganta ba, indai niyyarka kenan da yardan ubangiji bazaka sake saka princess a idanun nan nakaba in sha Allah kagama ganin Princess aduniyan n..." wani irin mugun mari Abba ya dauke ta dashi dayasa tasaki wani irin wawan ihu dan ya mugun shiganta, Muhsin da Ahmad dasuka shigo dan gaida Mum sukaji ihun ta shigowa dakin sukayi da gudu, tsayawa sukayi suna kallon Mum data dafe kuncin ta tana kuka sosai tana kallon Abba, ga Abba tsaye akanta yana huci kaman zaki yana ganin su ya nunasu da yatsa kafin ya nuna Mum yace "kuma maman ku magana tafita daga idona, ta kiyaye ni inhar tanason aurenta and you Muhsin" yanuna Muhsin da idanunshi sukai jajir yana sanye da black suit hanunshi rike da necktie yace "yes, yes, yes, I know kunsan komi by now kunga komi kunga komi ta CCTV footage, dat is why kuka tsaneni haka ko gaisuwa bani samu daga wurin ku kuma nagode da hakan bakomi yasani aikata hakan ba uwarku ce tajamin ita tajefani halaka amma yanzu nasan maganin matsalata, Muhsin start with divorce proceedings wanan dan daban daya dauke Nadeera shiyasa akazo har gida shekaran jiya aka daukeni yasa nabashi aure Nadeera aka daura auren akan sadaki 200k, yanzu kwamisona yace nabashi yau da gobe Nadeera zata fito, once sun ganota tadawo gida zamu maka dan shegiyan dan ta'addan a kotu mu raba auren nasu na aureta, kufada ma mahaifiyar ku tun wuri tai karatun ta natsu dan wlh aurena da princess babu fashi, and duk randa tasake maganan banza akan Princess dita wlh abakin aurenta, i can fight the whole world for my babygirl inhar war ne am ready kota gabas kota kudu kota yamma kota arewa zanyi fighting, me and my princess mutu karaba takalmin chicken" kuri Muhsin yayi yana kallon mahaifin nashi tun yana gane meyake cewa haryaji zuciyarshi ta tsaya chak ko kadan baya ganin kowa sai duhu, daga Abba dake ta bambamim bala'i dabayaji yanadai ganin bakinshi na motsi sai Mum dake zaune kan gado da Ahmad dake kallon Abba yanaji kaman ya tsireshi basu lura da Muhsin ba kawai karan fadin abu sukaji da sauri kowananesu ya kalli inda yaji karan atare dukan su sukace "Muhsin" gabaki daya idanunshi sun kafe yana kallon sama baya numfashi ko digi.
[9/13, 11:52 PM] Lady: *this book na kudine if you are interested chat me 07012181461*



Wani irin mugun sanyi jikin Mum yayi, kukan datake yi yakasa tsayawa, ahankali ta rufe bakinta da hanunta tana kallon Abba dayake huci kaman kumurci kafin ta janye hanun daga bakin tace "Alhaji Nadeeran? Yar da muka raina tun tana 3months old a duniyan nan shine kakeso a matsayin mahaifinta fa kake?" nuna mata yatsa Abba yayi cikin zafi da bala'in masifa yace "ki dena kirana mahaifinta aini ba ubanta bane, Nadeera halaliyata ce ba haramiya ba, akwai aure tsakanina da ita, danna raineta tun tana 3months doesn't make me her father so aurenta zanyi" chakumo shi Mum tayi cikin fushi dawani irin kishi tace "wlh bazaka auri Princess ba, baka isa ka aureta ba saidai in bana numfashi a duniyan nan, wlh bazaka auri Princess yarinyar danake so, na raineta a matsayin tawa kawani bijiromin da zancen nan ni zaka hada kishi da princess? Wlh Alhaji daka aureta gwara ka auro wasu mata dari daga waje zaimin ciwo amma zan iya jure wanan bana princess ba, wani irin concoction kakeso kayiwai ma? bazaka taba auren princess ba wlh saidai in bana numfashi a doron kasan nan na rantse maka" wani irin kallo Abba yamata da tunda ta aureshi bai taba matashi ba yace "cikani, wlh karki bari zuciya ta dibeni namiki abinda bamu tabayiba tsawon shekaru talatin da daya da auren mu, ki cikani hajara" kin sakinshi Mum tayi takara chakumo shi tace "wlh bazan sakeka ba saika janye maganan auren princess, kamayi tunanin tayaya zamu kawo mata zancen bamune iyayenta ba, wlh wlh bazaka auri princess ba" wani irin tunkude Mum Abba yayi tafadi akasa hartana bige gado yace "wlh auren princess kaman nayi nagama, nine ubanta kuma dole tabini kotaki kotaso dole tamin biyayya saina aureta watch and see, saidai ki mutu amma princess saina aureta nasha zumanta ta haifamin cute twins girl, see bama a Nigeria zamu zauna ba garin zan barmuku dan bazan iya tolerating wani cikinku ya batamata rai ba, and wlh inzaki kawomin nonsense am ready na sakeki dama darajan yarana maza kikeci wlh da kike tafiye tafiyen ki batare dakin tambayi izinina ba just because kafin aurenmu parents dinki sunce zan barki kiyi business doesn't mean you can go anytime without my permission, be very careful marriage dinki na rawa Hajara" tsallaketa yayi inda take zaune yay gaban wardrobe wani dogon wandon shaddan shi ya dauko ya sharce ya saka cikin fushi ya saukar da jallabiyar shi yadau car key da wayarshi ya bude kofan dakin nashi ya fuce cikin fushi Mum tabi kofar da kallo, sosai take wani irin kuka wanan wani irin fitina ne tazo ta tarar daga dawowan ta, wanan wani irin kaddara ne da musiba "innalillahi wa innailaihi raji'un, na shiga uku" tayi kuka fin na awa biyu kafin ta tashi ta kakkabe jikinta ta ficemai daga dakinshi ta shiga nata dakin, zama tayi abakin gado tai tagumi tana tunani saikuma tasake fashewa da kuka sosai tafi minti talatin ahaka kafin ta tashi ta shiga bayi alwala ta dauro tadawo ta kabbarta salla, itace jiran Abba shiru shiru har sha biyun dare bakaramin damuwa tayiba dan tana son mijinta sosai Abba is such a sweet kindhearted loving husband and father, ahankali ta tashi ta dawo falo ta zauna akan dogon kujera tana kallon agogo ahaka bacci yay gaba da ita a dogon kujera.


***
Kuka tayi bana wasaba yau ko kadan bata sashi a idoba, rabonta dashi tun jiya bayan sun dawo daga side din Abba, tun safe saidai ayi knocking wani kuku da farin uniform ya shigo ya ijiye mata abinci batare daya kalletaba ya fice haka har dare, bayan magrib ma kuka taci tai baccinta akan dadduma sai wuraren karfe daya na dare ta farka cikin bacci da sauri ta tashi tsaye tana sanye cikin wani pink plain t-shirt na mata daya dan kamata sai wani dogon black straight skirt, juyawa tayi tana sosa ido ta shiga bayi ta dauro alwala tafito tana goge hawaye tahau kan dadduma tasaka hijabi tai salla takafe kofar da kallo zuciyar ta na raya mata ta gudu, ahankali ta mike tsaye silifas ta zira tazo wajen kofan jikinta na rawa ahankali ta bude kofan ta leka babu kowa a wurin sai hasken wuta koina yay shiru fes fes karasa bude kofan tayi ta fito tana kallon ko ina kafin tasa kafa tafito cikin sanda tai wajen stairs tana sauka da gudu tana waigen bayanta cikin tsoro fadawa tayi jikin mutum atsorace ta dago kai ta kalleshi yana sanye da bakaken kaya da bakin mask yasaka hulan hoodie akanshi ya goya wani bakin jaka abayan shi kaman mai shirin fita, da sauri ta juya jikinta na rawa zata gudu fizgo hijab dinta yayi ta dawo da baya ta fada jikinshi wani irin atishawa tayi ahankali ya kulla hanunshi acikinta shima yay atishawa yana kara kankameta bakaramin kewanta yayiba, sosai yadinga fada dakanshi tsawon jiya zuwa yau yanaso yanuna ma kanshi ba sonta yakeba saisa yahana kanshi ganinta amma kasa tabuka komi yayi, hanunta tadaura adan tsorace kan hanunshi kaman zatai kuka tana kokarin kwancewa ta cirw daga cikinta, murya chan kasa yace "where are you going" girgiza mai kai tayi tana shirin yin kuka tana kokarin kwance hanunshi daga cikinta takasa, wani irin juyo da ita yayi da karfi ya kulle hanunshi ta bayanta, atare dukansu sukai atishawa kowanen au najin wani irin sanyi matseta yayi da hannu daya yasa dayan hannun ya dago habarta, kallonshi tayi saikuma ta kawad takai ta kalli falon bindigogi tagani da sunkai kusan takwas manya dogaye ga bullet zube akan kujeran da wayanda ke cikin kwali dake bude da wayanda kw ajiye akan kujeran juyo da fuskarta yayi hakan yasa ta kalleshi a tsorace saikuma ta sake janye idanunta tana kallon bindigogin juyo da kanta yayi yana kara matseta, ahankali adan tsorace tace "me kake yi da alot of guns?" shiru yayi yana kallonta ta cikin mask yana kallon yanda small pink lips dinta ke wani irin shining dake fizgarshi, dan ajiyan zuciya ya fuzar jikinshi namai wani iri kafin chan kasa ahankali yace "operation zani" yay maganan yana sata jikinshi gabaki daya kaman zai rungumeta, kokarin janye kanta takeyi daga jikinshi amma yaki bata daman hakan adan rude tace "wani irin operation kai Doctor ne?" girgiza mata kai yayi batare dayay magana ba sai chan murya chan kasa yace "ina zaki?" raurau tai da ido tace "water zan sha" daukanta kawai yayi unexpectedly ta ware baki zatai ihu, lips dinta ya kama da yatsunshi ya rike yace "don't scream" gyadamai kai tayi adan tsorace tana wani irin kallonshi cikeda tsoro, ahankali ya juya da ita batare daya dena kallonta ba ya fara sauka yay daga stair case din da sauri ta kankame riganshi jikinta na rawa, sauka yayi daga stairs din yay hanyar babban kitchen dinsu da ita zaunar da ita yayi akan wani dogon kujera dake kitchen din ya juya yay wajen fridge binshi take da kallo kirjinta na bugawa sosai, dauko cold Eva water yayi ya rufe fridge din ya juyo yadawo inda take ya tsaya a gabanta, bude ruwan yayi ya mika mata batare da yay magana ba hanunta har rawa yake takai zata karba ahankali ta daura hanun kan goran hakan yasa ya sakan mata ta karba tana kallon fuskarshi wondering wai waye wanan boyayyen mutun din, wani irin atishawa tayi dayasata sakin goran ruwan daga hanunta ya zube akan hijabinta dan ihun sanyi tayi da sauri ya dauke goran ya ijiye agefe hannunshi ya daura kan hijabin yacire mata hijabin kai tsaye ya ijiye kan table da sauri ta dukar dakai tana wasa da yatsun ta dan jitake kaman zata saki fitsari sabida tsoro ahankali yadau ragowan ruwan ya bata karba tayi takai bakinta kadan tasha tacire daga bakinta dan dama ba kishi takeji ba, karba yayi ya ijiye agefe sanan ya dago kai ya kalleta, ahankali yatako yazo gabanta sosai wani irin nishi tafara dan sosai ya cika mata ido, cikin wani irin murya yace "karki kara yunkurin guduwa is not worth trying, u cannot escape okay" gyadamai kai tayi da sauri hawaye na taruwa a idanunta lips dinta ya shafa yace "Hey! Don't cry" sake gyadamai kai tayi hawayen na shirin gangarowa da sauri ta share, bakinta na rawa sosai tace "p..please ka kaini gidanmu wurin Mum, i..i..wan.." saita kasa karashe maganan tafashe da kuka mara kara sosai sabida tsoro, ahankali ya sakala hanunshi ta waist dinta ya dauresu abayanta adan firgice cikin kuka ta kalleshi, girgiza mata kai yayi murya chan kasa yace "stop crying" gyadamai kai tayi tasa bayan hannu ta goge hawayen dasukaki dena zuba sai gogesu take da bayan hannu, janye dayan hanunshi yayi daga bayanta ya kai kan fuskarta ya saukar da hanun kasa batare daya sakiba ya rike gam yace "you want wat?" bakinta na rawa tace "i...w..ant to go back to school, nacigaba da practical dina, i want to go and stay with my Mum" shiru yayi yana kallonta saikuma ya girgiza kai ahankali yace "u are my wife i can't release you again, bazaki kara komawa dat house ba da mijinki zaki zauna" shi kanshi baisan yay maganan ba hakan yasa yay shiru yana kallonta yanda take goge kwalla dago kai tayi ta kalleshi tace "da gaske ne dama Abba yamana aure, ni matar aure ce?" gyada mata kai yayi yay shiru yana kallon fuskarta saikuma chan yace "ke matata ce" share wasu sababbin hawayen tayi cikin kuka datake so ta danne tace "how? Tayaya zan auri wanda bansan shiba, maisa Abbana ya auramin kai? I don't know you, bansan kaba fa, kai Boyayyen Mutun ne, bansan kaba" hanunshi ya daura akan fuskarta ya share hawayen datakeyi kafin ahankali ya duko da kanshi yahada goshin shi da nata murya chan chan kasa kaman mai whispering yace "kina so kiga fuskan mijinki?" sosai kirjinta kewani irin bugawa jin kanshi hade da nata kamshin dayake yana wani irin shiga hancinta hakan yasa tawani irin ja numfashi kafin ta saki da karfi adan tsorace tace "e..eh" ahankali ya janye kanshi daga nata ya mike tsaye agabanta yadan tattare hanun hoodie dinshi sama ya daura hannunshi daya akan safan hanunshi na dama ya dago kai ya kalleta yace "are you ready?" wani irin bugawa kirjinta yafara tana kallonshi kaman taga tv ta gyadamai kai tace "y..yes".
[9/14, 7:07 AM] Lady: *Maman Abd Shakur*




Sosai take gudu akan keken, kutsawa cikin dajin kawai takeyi batare datasan inda ta dosaba, tai tafiya kusan na minti goma taji kafafunta sun sage da tukin keken hakan yasa ta rage gudu tana goge zufan goshinta wani dandamali keken yaci karo dashi hakan yasa da ita da keken suka wani irin juyi tadinga tumble tumble tana gangarawa dan slope din har takai wani bishiya ta wani irin buge da bishiyan ta sume awajen jini nabin kafafunta da gefen goshinta.

Yakai kusan 15min abayi sanan yafito, shirya wa yayi a closet tsaf wani black hoodie da dogon wando yasaka da talkami yasa face mask dinshi dana hannu dan akwai inda zashi, feshe kanshi yayi da turare sanan yakoma gaban bayi yadau wet dogon riganta dake kasa ya bude bayin yasa a washing machine sanan yafito ya bude kofa yafito dakin, sosai gabanshi ya fadi ganin gadon empty babu kowa akai, ahankali ya juya yabi ko ina na dakin da kallo ganin wayam babu ita yasa da sauri yay wurin kofa ya bude yafita yana waigen waige yana kwala a kaninshi kira. "Abdallah, Omari, Omari!" sauka kasa yayi da gudunshi yana kallon ko ina, yay kitchen da sauri, babu kowa a wajen yafito yana wani irin kwalama kanin nashi kira "Abdallah, Abdallah Omari!" yawani irin daka ihu azafafe "Abdallah!" da gudu Abdallah dake daure da towel yafito daga sama yace "Ya Marwan menene kasa naji tsoro wanka nake saisa ban amsaba yanzunan nadawo daga sport ya Omari tun dazu yafice" yay maganan yana saukowa daga benen, muryan shi har rawa yake yace "w..where..have you seen my wife?" girgiza mai kai yayi yace "yanzun nan nadawo wah happen?" hanyar waje yayi da sauri yace "I can't find her go and get dress" da sauri Abdallah yace "wat?" amma harya fita sama yakoma da sauri ya sako riga da wando yafito shima saida ya zagaye gidan sanan yabiyoshi waje amma harya hau kan bike dinshi yay gaba azuciye.


Lashe mata kafa dataji anayi yasa ta farka a firgice, raguna tagani kusan guda hudu da yaransu sun zagaye ta suna lashe inda ke jini a kafarta kaman tadawo abinci, wani irin ihu tayi ta ja kafar nata a tsorace tana komawa baya tana kallon su yanda suke mata "emeeee" aka, mikewa tsaye tayi da kyar tana dafa bishiyar ta arce da gudu tana kallon raguna data firgita su suma sun kwasa da gudu tasake fasa ihu, sosai take gudu da duka karfinta tana juyawa tana kara kallon saman dajin gabaki daya batasan inda zataba, karan motoci dataji yasa tawani irin kara karfin gudunta tana numfashi, bigewa tayi da bishiya taji kanta na juyawa da kyar ta koma baya sanan ta cigaba da gudu kaman tababba, yanka dajin kawai take jin karan motoci yasa tawani irin fashe da kuka takara karfin gudunta tai hanyar da kyar ta iya fita taganta akan titi mai kyau davatasan kona ina bane, fashewa tasakeyi da kuka sosai titin ma daidai motoci ke wucewa da gudun gaske, gudu tacigaba dayi duk motan dayazo tana kokarin tsayar dashi amma basa tsayawa, sosai tai gudu na kusan minti shida, hango wani Fulani man mai kiwo tayi yana kada shanun shi da raguna hakan yasa tai wajen da gudu ta ta tsaya kusa dashi cikin kuka tace "malam dan Allah ka aramin wayanka nakira mamana wani zai saceni ne" yanda take kuka yasa yace "assha yarinya garin yaya? Aiko saidai kiyi fulashin wayanta a kwadala tai aggareta" gyadamai kai tayi tana share hawayen ta da bayan hijabin ta, ya ciro wayarshi rakani toilet daga aljihu ya mika mata yana gyara rokon sandar kada shanun hanunshi, tsugunnawa tayi a gefenshi har lokacin jikinta baibar rawa ba tasaka number Mum tai dailing akashe, fashewa da kuka tayi tasaka na Ya Muhsin shima akashe sosai tafashe da kuka har dan Fulani na tambaya lafiya ta girgixa mai kai, number Ya Ahmad ta saka saida yakusa katsewa sanan aka dauka kafin ma yay magana tafashe da kuka tace "Ya Ahmad come and pick me kafin ya kamani am scared" daga tachan bangaren ya Ahmad dake tiki zaije siyo wani allura awani babban pharmacy daza ama ya Muhsin ya kalli wayar sanan ya maida a kunenshi, kukan ta dayaji yasa yace "Princess, Nadeera kece" gyadamai kai tayi bakinta narawa tace "kazo ka daukeni Ya Ahmad nine, zai kamani nagudo ne ina bakin hanya wani Fulani na ari wayanshi nakiraki Ya Ahmad kazo please baida kati call me" katse kiran yayi yakirata da sauri ta amsa yace "calm down princess yimin magana anatse, yanzu kikace kina ina kinsan wani bakin titi kike? Inane wurin?" girgiza mai kai tayi ahankali tace "I don't know" da sauri yace "bame wayan to" mikama dan filon tayi tace "gashi yayana" karba yayi tana share hawaye tana Kalle Kallen titin daga tsugunnon miko mata wayan dan filon yayi yace "gashi zai miki magana" karba tayi takara a kunne Ya Ahmad yace "kina jina princess zaisaki a mota dazai taho dake cikin Abuja zan jiraki a zuba" gyadamai kai tayi daidai nan dan filon harya tare mata mota ya kalleta yace "zokije Allah tsare gaba, sai akula akuma kiyaye" tashi tayi arude tana kallon hanya kafin taje ta shiga motar bama tamai godiya ba tsabagen rufewa, dama mutum daya ya rage a motan yacika direba yarufe motan yakoma gaba yatada yaja, sosai take kuka tajuya tana kallon baya daidai lokacin taga boyayyen mutum sanye da hoddie dinshi da face mask akan machine ya tsaya daidai bakin hanya yana waige waige, da gudu ta juyar dakai ta dukar dakai kasa tana kuka ahankali, kafe motan yayi da ido saikace yasan tana ciki yabi motan da kallo harta bacemai jikinshi na fadamai tanaciki.

Daidai lokacin Abdallah ya iso akan bike dinshi yace "kaganta kodai mukoma cikin dajin ne Ya Marwan muduba da kyau?" girgiza mai kai kawai yayi batare dayay magana ba tsabagen yanda zuciyarshi ke tafarfasa, wani irin tada machine din yayi a zuciye yadau hamlet ya kafa yajuya yakoma cikin dajin shima Abdallah yabi bayanshi.

Saida suka kai zuba aka sauketa driver yace " kawo kudinki" waige waige tafara ko zataga Ya Ahmad daidai lokacin ya sauko daga motar shi idanunshi boye cikin bakin glass yazo wajen wani irin fashewa tai da kuka tace "ya Ahmaddd" kafin tafada jikinshi ta kankameshi tana kuka, wani irin murmushi yayi mai ciwo ya ciro kudi da baima san yawan su ba ya mikama direban daya tsaya yana kallon su, karba yayi yay godiya yakoma cikin mota yatada yabar wajen ahankali Ya Ahmad ya dago fuskarta yana wani irin kallonta kafin yasa hannu ya share mata hawayen yace "stop crying" gyadamai kai tayi ya rike hanunta sukai inda yay parking, agaba ya sata yarufe kofan sanan yakoma ta mazaunin direba ya zauna yatada motar tana kallon titi dukansu sunyi shiru yana tafiya, ahankali tace "am hungry Ya Ahmad" gyadamai mata kai yayi yay parking agaban wani eatry nakan hanya ya kalleta yace "am coming" fita yayi ya shiga eatry bai
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment