Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Mum da tuntuni Muhsin take kallo ganin Abba zai fara hali ga danta ya farfado yasa ta kalli Nadeera tace "Princess tashi kutafi" "ta tafi? Ta tafi ina Hajara?" Abba yafada cikin ihu, saikuma yay tsaki yace "nasamu Princess ta dawo wayan nan yan arzikin irin albarka masu kama da larabawa da banmasan a ina suka ganta ba, sun dawo min da ita shine zakice ta tashi ta tafi ta tafi ina? Eh, nace ta tafi ina yar bakin ciki?" da sauri Ahmad yatashi ya kalli Abba dawani irin jan ido yace "Alhaji Naseer please don't start with this your trash, kamana shiru anan inbadai so kake ka kara kai danka lahira ba, kamana shiru and respect your self" wani irin matsiyacin kallo Abba yama Ahmad yace "Ahmadu ni agidana, gidan dana gina da kudina ne kake cewa namaka shiru? To kaci gidanku, dan uwatata anki ayi shirun, anyways ina cikin tsananin farin ciki banison bacin rai, am so happy my baby girl is back" yay maganan yana kallon Nadeera da ta rirrike hanun Ya Muhsin daya lumshe ido yanajin tsanar mahaifinshi aranshi, karasowa wajen Abba yayi ya mikoma Nadeera hannu yace "zomu tafi Princess, yauwa yar albarka zomu tafi" make mai kafada tayi a tsorace tasake kankame Ya Muhsin wani irin tsoron Abba yake bata yanzu, tsugunnawa Abba yayi agabanta yana washe mata baki yace "haba my baby girl, my one and only princess, yarinyar Abban ta, yarinyar kirki, princess din babanta, zo kinji kidena tsorona, iyye kamota kamota, yar duma duma taaa, my chubby chubby gurl, sangandaliya gandaliya ta, haba princess din Abban ta, kinga ko namiki order Lamborghini tama kusa isowa Nigeria ta jirgin ruwa za'a kawo, Kinga yanzu yanda kika dawon nan kotun zamu shiga za'a raba auren ki da danta shegiyar nan saimuyi auren mu musha amarci ko princess mubar musu garin muje Spain honeymoon abunmu" wani irin kuka tafashe dashi da kyar ta juyo kai tadan kalli Abban tace "Abba na wai mena mane? Kataba ganin inda akai aure tsakanin uba da y'a, Mummy, Ya Ahmad, Ya Muhsin" ta kalli Ya Muhsin daya dan bude idanu kadan ya kalleta, girgiza kai tayi tana goge idanunta da bayan hanunta tace "Abba natamin abinda yaga dama kunki mai magana ko, bakaji meyake cewa ba uhm? Tayaya zan auri babana an taba hakane? Is Abba okay? Kaman baida lafiya mu kaishi asibiti please Mummy na" ta karashe maganan tana kallon Mum da idanunta sunyi jajir, cikin tsananin fushi Abba ya nuna kanshi yace "ke dan uwatata ni kike cema banda lpy akaini asibiti? Kin dauka hauka nake kome iye? To bari kiji nafada miki lafiyata kalau, bani na haifeki ba Princess" da sauri Nadeera ta dago kai ta kalleshi, yace "eh bani na haifeki ba, Mummy dakike gani nan ba ita ta haifeki ba, Muh..." da sauri Ahmad yawani irin kirashi yace "Naseeru!" dakuwa Abba yamai yace "uwataru ne ba Naseeru ba, shegen yaro mai kama da sangami" ya kalli Nadeera da idanunta ke kyam akanshi yace "Muhsin dakike gani ba wanki bane, Ahmad ma haka, a gidan marayu muka dauko ki a eygpt tun kina yar wata uku muka dinga rainanki, da kudina namiki suna na rada miki Nadeera, na kaiki asibiti, na raineki nai kewonki har kikai girma haka, kikai kyau, bakutu dake, shine kuma zan barma wani ke ya more aikina?" wani irin kallon Abba take kirjinta nawani irin bugawa, ahankali ta saki hanun Ya Muhsin ta juya ta kalli Mum da ke kallonta zatai magana Mum ta rigata tace "yes princess hakane we are not your biological parents, adopting dinki mukayi daga motherless home, and Abdallah da Omari" tamata pointing su Abdallah dake zaune kusa da Marwan da kanshi ke kasa tace "are your biological siblings, sanan Marwan your husband is your cousin, munso mufada miki mijinki yace ki warke tukunna, all I know shine u will always be my daughter, my baby girl my princess okay, tashi kibi mijinki kutafi" wani irin gangarangan maganan yamata akai gabaki daya zuciyarta yakasa containing d shocking revelation she just heard, na Abba bata yarda ba amma na Mum kam ta yarda, maganan Abba ne yadawo da ita daidai yawani irin tsalle ya tsaya agaban su Abdallah yana kallon Mum yana cewa "waye Marwan din cikin su, au dama kune? Ina masks din dakuke sawan? Har gidana kuka shigo sabida kun isa, Hajara nunamin ina Marwan din wlh saina zubar mai da hakori yanda ya zubar da nawa, saina mai lilis na rantse and saiya saki princess kafin yabar gidan nan nahada shi da hukuma" yay maganan yana wani irin tattare hanun riga sama, wani irin smirking Mum tayi Muhsin yabude idanunshi tass yana kallon mahaifin nashi, Nadeera ma kallon Abba take daya gama tattare hanun riga yawani irin wage kafa yana nuna musu power yana kallon su ukun yana huci, wani irin fashewa da dariya Ahmad yayi, dariyan da rabonshi da yinta tun jiya yace "dan girman Allah koma waye Marwan cikin ku dan ya rasulullahi kuma wanan tsohon shegen duka, wlh kaji kunya Naseeru" juyowa Abba yayi ya kalleshi ya nuna shi da yatsa yace "banga laifinka ba Ahmadu, dama chan tsinanne ne kai, tsinuwar kesaka yin haka mai kama da uwatata" ya kalli su Abdallah yace "waye Marwan cikin ku nace, wlh kodai yatashi mubama hammata iska kokuma zanyi rushing dukan ku uku, and saikun sakin mini y'ata yau" yawani irin gyara tsayuwa yana gyara kafa yana shirin yin gusha gusha kaman irin dan Chinese dinan yay wani irin ihu yace "dan uwatata nace Marwan yafito muyi fito nafito dan wlh saina rama dukana dakuma asiri dayamin yasa nabashi auren princess bana hayyacina, dan uwatata da ubatata Marwan ka mike tsaye kazo mubama hammata iska" ya juyo ya kalli Nadeera dake wani irin kallonshi yace "don't worry princess I can take them down, ina mugun sonki princess da I can do anything for you, I love you so much my baby girl, don't worry kinji" yajuyo yana wani irin gyara tsayuwa yana kallon su yace "Marwan ka mike mu fafata nabaka kashi wlh, sai kasan ka tabani, uban wayace ka auremin y'a? Wlh saina zubar ma da hakora, ka mike kona hadaku ukun na rushing dinku".


*masu posting novel waje, kuda Allah*
*karki karanta in baki biyaba*
*in kinason littafin nan Zaki tura 300 3107021073 first bank aisha Muhammad, saikimin magana a watsapp 07012181461*




*BOYAYYEN MUTUN*

Wani irin bubbuga kafa Marwan yafara akasa kirjinshi na tafarfasa, yanamai suya kaman an hura wuta aciki, cikin fushi Abba yace "au bazaka kuyi magana ba ko, nace Marwan yamike tsaye mu bama hammata iska" cikin fushi Mum da batai niyyan magana ba tace "Alhaji!" afusace Abba yawani irin juyo ya kalleta yana nunata da hannu, yace "karki sake ki kira sunana makirar mata, annamimiya, wato kinyi iyakan bakin kokarin ki ki rabani da Princess kicire sonta a raina, amma kikaga sonta kainuwa ne araina dashin Allah, kikaga son princess zanen dutse ne araina, shine zaki sirfafo wanan karyan ki narka, kika bullo ta wanan hanyan kicemin wayanan yan daban yayyin princess dina ne? Yan uwanta ne bla bla bla, to sannu makira, kinji ko nace sannu makirar, mai bakin hali me princess ta tsare miki dakike kishi da ita? To bari kiji Allah ubangiji daya dauramin son Princess araina shi kadai ne zai ciremin shi daga raina, kuma wlh yau koma uban waye Marwan cikin su saiya sakin mini y'a, saiya saki baby girl dita, bazan kiwanci yarinya kimanin shekara ashirin da biyu babu wata uku ba, tai lumu lumu haka da ita, yarinya yar duddurma pakutu kaman kataba jini yafito wani yazo ya auremin ba, ai abunda bazata sabu bane wai taba nonon sirika, ya mori kiwona, kiwon danayi? Ina! " wani irin tashi Omari yayi cikin fushi ya kalli Abdallah yace "Abdallah get the check book from d car" ya kalli Abba dayawani gyara tsayuwa yana tale kafa yace "name your price Malam nawa ka kashe arainon kanwata? 100 million? 200 million? 500 million? How much just name it?" wani irin tashi Marwan da idanunshi sunyi jajir, jijiyoyin kanshi sunfito yayi ya kalli Abba yace "zan baka 50billion naira for rainonta, inma yafi haka name your price zan biyaka instantly" cikin fushi Abdallah ma yamike yarike hanun Ya Marwan dan yaga yanda hanunshi ke rawa and inhar yarike Abba zai iya kasheshi cikin fushi yace "Ya Marwan please mutafi, wlh baza'aba tsohon nan kosisi ba" wani irin ihu Abba yayi yawani irin kaima Marwan naushi a kirji amma ko gezau, yace "dama kaine Marwan? Dama kaine matsiyacin dibabbe wanda aka haifeshi babu cibiya shaidani, zo dan uwatata mubama hammata iska" wani irin jumping Ahmad yayi daga kan kujera yay wani irin ihu. "tirrrrrrr, yauwa Marwan dan Allah give him d beating of his life, karkai sparing tsohon nan, go Marwan" wani irin tunzura Abba maganan Ahmad yayi yay wani irin tsalle yadane jikin Marwan da zuciyarshi kewani irin zafi tsabagen fushi kanshi har wani irin rawa rawa yake, Abba yawani irin gannamai cizo a kirji yana nushin shi a ko'ina kafin ya dira kasa kuma yana nishi, fashewa da kuka sosai Nadeera tayi ta kalli Ya Muhsin da idanunshi kekan Abba da a yanzu jiya ke kaman yatashi ya kasheshi dan bakin ciki da tsanan halinshi, cikin kuka taja hanun Ya Muhsin tace "Ya Muhsin Abba yana dukanshi" ahankali Ya Muhsin ya kalleta yama kasa magana baida karfi ko kadan, da rarrafe taje wajen Mum tarike hanun Mum tace "Mum say something, Abba is beating him" kallon kwayar idonta Mum tayi tai shiru danhar cikin ranta sotake su uku suma Abba shegen duka dako tashi bazai iyayi ba, karan saukan Mari yasa da sauri suka daga kai, Abba ne ya kwashe Marwan dawani irin shegiyan mari, kawad dakai gefe Marwan yayi jikinshi nawani irin rawa ahankali yafara wani irin dunkule hannu da sauri Omari ya rike hanun koba komi darajan yayan shi da suma basa murna dahalin baban nasu, da kuma Mum dake son Nadeera tsakani ga Allah bai kamata ya daki Abba agabansu ba, wani irin shako kwalanshi Abba yayi cikin fushi yana jijjiga shi yana nishi yace "nace ka sakin min Y'ata, ka saketa, fight me now, tsoro na kakeji, fight me back Marwan, look me in d eyes, ka kasa kallona, ka kalleni muhada ido and fight me back like a Man, mu dambata, princess tasan wayafi chanchanta da ita, ka sakenmin yarinya ta inkana neman zaman lafiya" yakara marinshi tawani side din, da sauri Nadeera ta saki hannun Mum tazo wajen da gudu tana kuka, juyowa Abba yayi ya kalleta ya washe mata baki yana nishi kaman wanda yaje yaki yace "matsa baya my princess karna sameki garin dukanshi, kije ki zauna basai kin shigan min ba, I can take them down wlh, bakiga yanda natsuwa yasoma shigan shi ba, stop crying my baby girl, bazai iya dukan Abban kiba, he's to small for me, don't be scared okay" wani irin gyara tsayuwa yayi yana ware kafa ya daddage ya hambari Marwan akafa saida kafan Abba yay kara yay baya kaman zai fadi yay kara tareda yin baya da sauri ya kalli fuskan Nadeera dake kuka sosai ya daddage ya tsaya yana nishi sosai yace "am fine, am fine princess, stop crying, zan bashi kashine yau" yakara komawa yanadan dingishi dan kafan dayay hambari dashi tamai tsami, chakumo wuyan Marwan din da idanunshi ke kasa har lokacin yawani irin yi ya jijjiga shi yace "nace ka sakenmin my princess, ka saketa nace, bata saki" ya kaimai mari, fashewa da kuka Nadeera tayi tazo wajen da gudu tana kuka sosai tana wani irin yarfe hannu, tasa hannu ta janye hanun Abba daga kwalan Ya Marwan da idanunshi ke kasa har lokacin tace "stop beating him Abba, Abba mesa kake haka, ni I don't like you, bazan taba auren ka ba, koma abinda sukace gaskiya ne koma ba gaskiya bane u will always be my Abba, and ni babu aure tsakanina da Abba na, kaine wanda nasani amatsayin uba and u will always be dat, Abba please stop all dis, wlh bazan taba auren kaba, koka raba auren mu bazan taba auren kaba, tayaya ma zan auri babana? I don't like you Abba, I don't like you, I don't like yo... " wani irin wawan Mari Abba ya dauketa dashi yana huci, da sauri Marwan yadago jajayen idanunshi ya kalli Abban dawani irin idanu masu firgita mutum, da sauri Ya Muhsin da baida karfi ko daya yaji wani irin karfi yazomai ya mike tsaye yana dan dingishi yazo wajen ya tsaya a gefen Nadeera Marwan na dayan gefenta suna ma Abba wani irin kallon, wani kallo Abba yabisu dashi kirjinshi namai zafi kaman zai tarwatse kafin ya maida idanunshi kan Nadeera data fashe da kuka hanunta akan inda yamara ya nunata da yatsa yana dafa kirjinshi sabida yanda maganganun ta yamai wani irin shegen ciwo yace "P...Pr..Princess ni kika gayama magana haka? Ni Abban ki? Ni kike cema baki sona? Princess ni? Wat is my fault in loving you? Kinsan tun yaushe nake sonki? Princess ni" hawaye ya zubo daga idanunshi tsabagen yanda abin kemai ciwo, da sauri Nadeera ta ware ido gabanta na faduwa ganin Abba na kuka akanta, ahankali tace "Abbaa" hannu Abba yadaga mata yana girgiza mata yace "karki ce min komi, baniso naji komi, baniso naji me zakice, princess I fought the whole World for you, I stood by you through thick and thin, am always there to keep you company lokacin da maman ki ke abandoning naki tayi tafiyar ta kasashe, Princess I adopting you wen u were 3months old, u were this small" yanuna dan karamin yatsanshi yana share hawayen dayake yi, yace "I took you to the hospital aka miki check up, nakawo ki gidana nahadaki da family na, namiki suna, every sort of baby toy dat u could think of aduniyan nan nasai miki shi dakudina dakina yarinya, nasaki a one of the best schools da Nigeria keji dashi, I clothed you, hired one of the best nani, na kaiki Montessori kika fara tun daga creche har zuwa primary school, where turawa oyinbo ke koyar dake, kikai girma you told me bakison BSc Nursing normal school of nursing kikeso I took you there, d best damuke dashi agarin nan, St. Edward school of nursing and midwifery, nasai miki laptop, nai fentin dakin ki to your dream color baby pink, Princess I've always given you wat you wanted kafin na tai coughing dinshi out, I've always been there for you my baby girl, I know nai couple of mistakes but am human Ain't I?" yasake goge kwalla yana jan majina yace "and human make mistake, I wanted to wait for you kigama school of nursing dinki nafada miki everything sai muyi auren mu mutafi spain, but rashin Mum dinki shiya kaini namiki nai pushing dina har nai abinda nayi but it was never my intention" yafashe da kuka sosai yana goge idanunshi da hanun rigan shaddan jikinshi, yace "takan ki an zubarmin da hakora, wanan mutumin hit me badly, he injured me, he kidnapped you from me ya auremin ki, walls din stomach dina as am talking to you right now is very very weak princess, but dudda haka bantaba giving up ba on u, I've suffered alot because of you amma ko kadan sonki bai ragu a..a..rai..na..ba" yafashe da kuka sosai da sauri Nadeera data fashe da kuka dan maganganun Abba sun mugun tabata ta matsa zata kama hanunshi cikin wani irin kuka da tausayi Marwan yawani irin fizgota yace "let's go" yajata dawani irin force yay hanyar fita daga dakin da ita, wani irin ihu Abba yayi cikin kuka yarike Marwan gamgam yana kuka yana kallon Nadeera dake kuka sosai tana kallon shi ya mika mata hannu yana kuka harda majina yace "Princess don't leave me, don't leave me dan Allah, zan wulakanta, zan tozarta, My Princess karki bari yaraba ki da Abban ki, wayyo Allah princess kinaso Abban ki yamutu?" wani irin runtse ido Marwan yayi dan Abba yafara kaishi karshe zai kasheshi faa, ihu Ahmad yayi ya rike hanun Ya Muhsin da hawaye ya gangaro mai yace "na rantse da Allah Abba ya haukace, ko kaffara bazan yiba, kalli Abba fa yanda ya makalkale Marwan kaman dan biri alalo alalo, wlh Abba deserve to be examine and admitted in the asylum kai! The old Man head don loose noti fa" Nadeera kuka Abba kuka ya makalkale Marwan gam gam, ahankali Marwan yamika ma Omari Nadeera da hannu yace "take her away" wani irin ihu Abba yayi yay wani irin jumping ya rungume Nadeera tsam tsam yace "Princess karki bari arabani dake I will just die, I will die wlh, Princess dan kaunar dakike ma Manzo sallalahu alaihi wa sallama karki bari arabani dake, Nadeera! My baby girl, I need you, my princess, karki bari arabani dake" wani irin fizgo Abba Marwan yayi yawani irin bankare shi mercilessly kaman roba kafin yawani irin murde wutsiyar hanun Abba a zuciye jijiyoyin kanshi kaman zasu bullo tsabagen fushi jikake kakar kakar kasssas ya balle ma Abba wutsiyar hanunshi duka biyun Abba yay wani irin ihun azaba, wani irin ture Abba yayi yafada a tsakiyar dakin ya nuna shi da yatsa yace "never in your come close to my wife or touch my wife mugaffal" yawani irin ja hanun Nadeera dake kuka kaman zata mutu tana kallon yanda Abba ke kallon hanunshi da tana iya ganin yanda fatane kawai yarage tsakanin wutsiyar hanunshi da tsintsiyar hanun dan Marwan yakarya kashin tass, Abba nawani irin kuka yana kallon hanun yafita da ita daga gidan su Omari biye dashi yawani irin jefata cikin mota ya karbi key a hanun Omari suka shiga yawani irin ja motan da mugun gudu.



Ahankali Mum ta mike tsaye ta tsallake Abban tafice abinta da sauri Abba yakirata. "Hajara, Hajara bazaki taimakamin ki kaini asibiti a dauremin hannu ba" ko kallonshi Mum batayi ba, Muhsin ma yajuya yafice, Abba yafashe da kuka sosai gwanin ban tausayi, Ahmad yazo gabanshi ya tsugunna ya matso da fuskarshi kusa dana Abba yawani irin fito da harshe ya nunama Abba yamai gwalo kafin yace "Allah yaaaa kaaaraaaa" cikin kuka Abba yace "ja'iri mai kama da uwatata sai kaga sakayya" gwalo Ahmad yakara mai ya murguda mai duwaiwai yace "gobema ka sake taba matar wani" yamai bye bye yawuce yafice. Cikin wani irin kuka Abba yace "Ahmadu ni? Ni ubanka kakema haka? Wat is my crime for loving princesses? Menene laifina na son y'ar da na Haifa?" yafashe dawani irin kuka.



__Jama'a soyayya wata irin abace da bata iya kama mutum ba, only wayanda sukai soyayya sukasan kan so, sune wayanda zasu iya relating da wat Abba is going through right now. Couple with the fact that Abba tsoho ne shin kun taba ganin yanda tsoho yake behaving idan yanason yar yarinya?._

_Zanso inji veiw dinku kan situation din Abba, Abba deserve Nadeera yes or no??? Ko wanne ka zaba back up your reasons please, I will be reading your comments.__

*karki karanta in baki biyaba, kisani idan kin karanta ina binki bashi*

*Zaki iya samin access to karanta labarin nan akan kudi naira Dari 300 kacal*

*3107021073 first bank aisha Muhammad*
*07012181461 watsapp min tanan for any enquiry*


*BOYAYYEN MUTUN*


Da kyar Abba ya mike tsaye yana dan dingishi yana nishin azaba sosai dan wani irin tafarfasa kwanyarshi takemai yana wani irin kallon hanun nashi yace "wayyo Allah na shiga uku ya kashe ni, Princess please ki dawo gareni" da kyar ya iya yafita daga dakin yana kwalama Adamu driver kira awahale. "Adamu, Adamu, wayyo Allah na Adamu zoka kaini asibiti hakika yau bakar rana ce agareni" arude Adamu yafito daga dakinsu yana salati ganin yanda hanun Abba yayi kafin yay magana ma Abba yace "kaini asibiti kai, kaini asibiti kafin narasa hannuna" jan kafadar Abba yayi yabude mota ya sakashi ya shiga gaba da gudu ya rufe yaja da sauri suka fita daga gidan, private asibitin daya bari dazu ya koma yana zuwa suka karbeshi da gudu.


Direct bedroom dinta Mum ta shiga tana share kwalla tabude wardrobe taciro manyan manyan akwatinan ta tana kwaso kayanta tana hadawa ciki tana hawaye sosai, wani irin bakin ciki takeji sama dana kullun, ahankali Muhsin yatura kofan dakin ya shigo Ahmad biye dashi duk suka tsaya suna kallon yanda Mum ke kuka tana hada kaya inka ganta saika tausaya mata kaman wacce take fama da wata cuta, ahankali Muhsin yataka yakaraso gaban wardrobe inda take yasa hannu ya karbi kayan dake hanunta ya ijiye akan gado kafin yabata wani irin hug yana bubbuga bayanta, fashewa tai da wani irin kuka da tuntuni takeso tayi irinshi takasa, sosai take kukan tana shesheka tace "am sorry Muhsin, am sorry, Muhsin kaya kuri okay" ahankali Ahmad ya shigo shima ya rungumeta tabaya suka sata atsakiya suka rungumeta tsamtsam, sosai take kuka tana rokon su gafara, tace "am sorry, kuyafemin, kuyafemin, komi daya faru ayau laifina ne, nice silan komi, ninaja komi, Abban ku batun yau yake nunamin bayason tafiye tafiye naba, nazauna a Nigeria nai business bazai hananiba amma bayison tafiye tafiye, nai kunen uwar shegu, nakiji, gani nake tunda ya yarda tun kafin muyi aure da business dina baida right akaina, baida right yacemin ga yanda zanyi game zanyi, gashinan yau naga illan hakan, na tarwatsa family na dakaina, nabata komi, yakuma sakeni, am sorry Muhsin and Ahmad kuyafemin dan Allah, is all my fault, am the root to all that's happening, kunsha kirana bana dauka, baban ku ma haka ya kira ya kira bazan sami time din dauka ba, princess ma haka, wlh duk laifina ne, ninaja komi, kuyafemin dan Allah" tahade hannayenta biyu tana wani irin kuka mai taba rai, ahankali Muhsin ya saketa ya sanya hannu ya saukar da hanunta kasa yasa hannu ya goge mata fuskan da hawaye yagama wankewa yace "is okay Mum, stop crying, sit" ya zaunar da ita abakin gado ahankali ya kalli Ahmad dake tsaye yana kallon Mum cikin tausayawa yace "jeka mana parking kayanmu Ahmad, lemme park Mum's own" gyadamai kai Ahmad yayi yajuya yafita daga dakin shikuma yacigaba da kwashe na Mum kayan yana zubawa a box, daurewa kawai yake daga Mum har Ahmad need him, so he has to be strong for them,
Nadeera is not his and yay accepting dis faith, yariga yaga yanda guy din yake sonta, so koma wanene shi he don't care, Alhamdulillah tunda tasamu wanda ke sonta haka, Allah ubangiji yacire min sonta araina yabani wata tagari and make me strong enough nasamu na kula da mahaifiyata da kanina, tass yahada ma Mum kayanta ya zage jakan yana dagasu tsaye yaja ya fitar dasu waje ya ijiye gaban motan shi sanan yadawo ciki yafito da Mum dake tafiya ahankali yabude bayan mota yasata yarufe daidai lokacin Ahmad yafito daga shashin su yana gunguro akwatinan su, a boot duka yahada yasa sanan yabama Ahmad key dan bazai iya driving ba ya shiga baya ya zauna kusa da Mum dahar lokacin ke kuka yana sharemata hawaye suka fita daga gidan, saida suka tsaya a hanya sukai magrib da isha'i kafin suje wani babban hotel suyi lodging, yabiya musu kudin komi suka kai Mum dakinta suka zauna a wurin dan suyi keeping dinta company sai wuraren 12 sanan suka fito suka tafi nasu dakin dan bacci dan gobe da safe sukeso subar garin.


**
Dawani irin gudu Marwan ke tuki har kaman mahaukaci har saida ta kankame kanta cikin tsananin tsoro tana kuka sosai, tsayawa dataji anyi yasa tadago kai ahankali tasa hannu tana share kwalla dake zubo mata daga ido, wani irin kashe motan yayi yabude kofa yafita batare daya kallesu ba, fashewa tayi da kuka sosai tana goge kwallan da bayan hijabi, ahankali Omari da Abdallah suka bude kofa suka fito zagayo wa ta bangaren ta Abdallah yayi yabude side dinta ahankali ya mika mata hannu cike da tausayin ta dan yanda take kuka na mugun tabashi yace "come" gyadamai kai tayi cikin kuka kafin ta mikamai hanunta dake rawa sosai ya rike, da taimakon shi tafito daga motar dan kafafunta sun mata wani irin sanyi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment