Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

YAKANAH!-1
Agogon ‘alarm’ da ke gefen makeken gadon ya buga karfe shidda dai-dai na safe, Dr. Hadizah wadda ke kwance a gadon doguwa ce ba can ba, irin tsayin nan gare ta mai tsari da ban sha'awa. Tana sanye cikin rigar barci mai santsi fara sol. Ta yi mika a hankali tare da koro addu'ar (Alhamdulillahil lazee ahyana, ba'ada ma amatana wa ilaihin nushour). Ta mika hannu side din da maigidanta ke kwance, wayam! Tayi hanzarin mikewa daga kwanciyar don a zatonta, ta makara.
Daga can kitchen ta jiyo motsin mai aikinsu Goggo Alti tana karakaina da kwanuka. Tana shirin mikewa ta ji motsin maigidanta Sulayman a shower, don haka ta yi ajiyar zuciya mai sanyi, a kalla ko ta makara kadan ne. Ita ma ta fada bandakin don ta taimaka mishi wajen wanka kamar yadda yake a al’adarsu.
Wasu ma’aurata ne wadanda samun masoyan da suka shaqu da juna suka kuma yarda da juna, suka aminta da juna, suke matukar kaunar junansu kamarsu a wannan zamanin zai yi wuya.
Suka fito kowane daure da towell, shi iya kugun shi ita iya cinyoyin ta. Jiki ne da ita lukui-lukui kamar atafa. Jiki ne da shi na MANYA, kuma kasaitattun maza, wadanda suka dama, suka kutsa cikin manyan ilimummuka daban-daban.
Yana da duhu, amma duhun mazan Marocco ne. Dogo ne sosai ma'abocin karfi da kyawun sura ta ko’ina. Idan baka san asalin shi ba, za ka yi tsammanin ya fito ne daga Sirreleone, amma a zahiri Bakatsine ne dan asalin garin Bakori. Wanda Bakorin ta bi sunan shi, ta boye Sulayman-Sulayman din, ake kiran shi Dr. Bakori.
Ta bude wardrove ta dauko mishi bakaken Spanish-Suit mai hade da farin tie mai santsi. Ita kuma ta fiddo wata atamfa super shudiya mai ratsin rowan hoda da hasken sararin samaniya, riga, zane da kallabin su, ta dora da farar rigar su ta likitoci. Tuni ta fito a Dr. Hadizarta. Tana tsuke mishi tie ya ja zankalelen dogon karan hancinta in appreciation din (cike da jin dadin) irin kulawar da take mishi. Ya ce
"Allah ya bar min ke Dr. D.Z". Ta ce
"….Ya bar min kai nima, likitan zuciyata…..". Ta manna mishi kyakkyawar sumba a kirji, kasancewar ya kere ta a tsaho, ita iya kirjin shi ce. Ta dauko tashi rigar likitocin ta zagaya ta bayan shi ta rufa mishi, ya zura hannun shi kana a hankali ya janyo ta ya rungume ta. Sun dau tsawon lokaci a hakan, suna sakin ajiyar zuciya mai sanyi cike da matsananciyar kauna wadda biro ba zai iya rubutawa ba, kamin su saki juna ba don sun so ba, sai don tunanin dimbin al'umma masu larura da suka yi sammako suke jiran su.
Sai da suka gama kammalawa tsaf sannan suka fito, tana rike da gilashin idonta a hannu, yayin da shi yake rike da jakarta da brief case din shi. Kai tsaye dakin yaransu suka nufa, inda suka tarar tuni Alti ta shirya su tsaf, kasancewar yau garin an tashi da lullumin sanyi mai tsanani ya sanya ta sanya musu rigar sanyi mai kauri a ciki, ta sanya musu fararen socks ta rufe musu kafafu cikin farin cambas.
Yaran su biyu ne mace da namiji, namijin dan kimanin shekaru hudu, macen 'yar kimanin shekaru biyu da kadan. Dole in ka gansu sai ka sake marmarin kallon su, sun kuma baka sha'awa.
Munib sak Babansa, yayin da Muniba komi nata na Dr, Hadiza ne. To ba Mamin ba, ba Daddyn ba, kowanne ji yake da kyau tamkar shi ya yi kansa. Akwai shakuwa, fahimta da soyayya mai yawa a tsakanin wannan family.
Hadiza ta rage tsawo ta russuna ta rungume diyarta Muniba,
"Gud morning my dear......."
"Morning Mummy….".
Munib ma ya ce
"Gud morning Daddy…..".
Ya amsa da
"Morning my Munib, an tashi lafiya?"
Su dukka suka nufi tebir domin yin kalaci.

Goggo Alti ta fito daga kitchen za ta wuce bangaren ta, daga Hadiza har Sulayman suka gaishe ta, kamin ita ta gaida su. Wannan dabi'arsu ce da ke karawa dattijuwar jin dadin zama dasu, saboda yadda suke ba ta girma kamar ba a karkashin su take ci ba. Hakan ne yake kara mata himmar kula musu da yaransu saboda Allah.
Hadiza ta bude ma'adanan abincin ta soma serving kowannen su da abinda yake so. Sinasir ne da miyar ganye, sai farfesun kayan ciki, sai kuma soyayyen dankali da kwai domin su Munib da bazasu iya cin mai nauyin ba.
Ga al'adarsu sun fi cin abinci mai nauyi da safe, don ba za su kara ci ba sai dare in sun dawo aiki, sai 'yan ciye-ciye da ba a rasa ba a office.
Hankalin Dr. Sulaiman yana kan 'ya'yan shi, sai da ya tabbatar sun koshi sannan ya ci nasa. Zuwa bakwai da rabi sun gama komai sun fito, suka yiwa Goggo Alti sallama suka wuce rumfar adana motocin su.
Akwai motoci har guda uku, daya ta Sulaiman, daya ta Hadiza, daya ta amfanin gida. Sai da suka aje yaran a makarantar su (Maitama Sule) da ke dab da asibitin da suke, wato (AKTH) sannan suka karasa cikin asibiti, kowanne ya nufi bangaren sa.

Dr. SULAIMAN-SULAIMAN BAKORI shi ne consultant na (cardiology), yayin da Dr. Hadiza Ja'afar Mai-Yadi take likitar mata wato (gynaec) a labour ward take. Sai da ya fara sauke ta sannan ya wuce ofishinsa, ya soma attending dimbin cases din da ke gabansa.
Karfe sha biyu na rana ya zame ya je ya debo yara ya kai ma Goggo Alti, sannan ya dawo. Wannan shi ne tsarin rayuwar su a kullum.
***







Shekarun su biyar kenan da aure, amma har zuwa inda yau ke motsi, babu abinda ya canza na daga soyayyar da suke yiwa juna, sai ma abin da ya karu.
Hadiza dalibar shi ce irin yaran likitocin nan da ake koyarwa a (teaching hospital). Ya fahimce ta yarinya ce mai matukar kwazo a tsakanin tsararrakin ta. Wani abin mamaki da ya fara bincike a kanta 'yar talakawa ce likis, amma iyayenta sun tsaya tsayin daka wajen daukar nauyin karatun ta, duk da tsadar shi kuwa, da dukkan iyawarsu.
Soyayya ce mai tsabta irin ta wadanda suka wadata da ilimi suka gudanar kamin aure. Ga Hadizah ba karamar sa'a ba ce, kuma ba karamin abin alfahari bane samun mutun kaman Sulayman (as a husband). To haka shi ma.
Hadiza ta tara duk wasu qualities da yake nema ga diya mace, ga dai kyau ga kyan hali, ga addini da kyakkyawar zuciya, sannan uwa uba ta samu ingantacciyar tarbiyya daga iyayen kwarai.
Iyayenta suna nan a unguwar Karkasara dake cikin birnin Kano, sana'ar mahaifinta shi ne yadiddika yake sayarwa, yana da shago a nan kantin Kwari.
Hadiza ita ce ta biyu a cikin 'ya'yan gidansu, akwai Yayanta Mukhtar wanda ke aiki da (Zenith Bank) a Kaduna, kusan da tallafin shi ne Hadiza ta samu ta kammala karatun ta.
Duk da haka shi ma mahaifinsu a tsaye yake a kan karatun su, don yaga amfanin da karatun yayiwa Mukhtar. Sai kanwar ta Fati, budurwa ce 'yar kimanin shekaru sha bakwai, a bana ne ta kammala karatun sakandire. Sai Hamza da Yusuf, da dan autan su Abdulyassar.
Duk cikin kannenta Hadiza ta fi son Fati, wata irin yarinya ce mai sanyin hali, sanyin kyau da sassanyar zuciya. Akwai wata irin shakuwa ta musamman tsakanin Hadiza da 'yar uwarta Fati. Jininsu ya hadu sosai ta yadda Hadiza ba ta iya shawara da kowa kan al'amuranta kamar Fati saboda hankalin ta.
Fati yarinya ce mai tsananin son addini da nutsuwa, ba ta da rawar kai ko kadan irin na 'yammatan zamanin nan, komi nata cikin hankali da nutsuwa yake. Ita da Hadiza kamar an tsaga kara, sai dai Hadiza fara ce sol, yayin da Fati ta kasance wankan tarwada. Amma hatta yanayin tafiyar su da murmushin su iri daya ne.

****


Sulaiman – Sulayman Bakori, mutumin garin Bakori ne ta jihar Katsina, daga kallo na farko mawuyaci ne ka bambance daga kabilar da ya fito, wani mutum ma'abocin cikar zati da kamala da duk wani nau'in daidaito na rayuwa, ga dimbin ilimi a cikin fannonin kiwon lafiya daban-daban. Ya ci sunan mahaifinshi ne don haka a gidan su ake kiran shi mai sunan Malam.
Mahaifin shi Malam Sulaiman, Malami ne mai karantarwa, yana baiwa magidanta anguwar su karatun buzu. Duk wani da ya kwana ya tashi a garin Bakori ya san Malam Sulaiman Mai-Gafaka. Mutum ne da al'ummarsa ke matukar ganin girman sa, kuma ya yi fice a garin Bakori baki daya saboda ilimin da Allah ya ba shi, kowa yana daraja shi.
Shi ne da na biyu a gidansu, yayar shi Jummai ta rasu wajen haihuwar fari, sai kannen shi Ramatu, Saude da Ruma, duk suna gidan aure. Sai Khalid wanda ke karatun sakandire a halin yanzu.
Sulaiman ya yi dukkan karatun shi ne da taimakon gwamnati da mahaifiyar shi Inna Halima, wadda duk lokacin da hidimar karatun ta tashi take fitar da kadararta ta siyar ta yi masa. In dan ta Malam ne sakandire ma kawai ta isa. Burinsa Sulayman ya zauna a gida ya tallafa mishi kasuwancin shi na fata, ya yi aure ya haifa mishi jikoki shi kuma zai yi masa komai.
Amma Sulaiman ya ki, ya dage ga son cimma burinsa na son zama likita. Ba abin da yake so a rayuwar shi irin yau a ce ya zama likita yana yiwa mutane allura.
Irin yaran nan ne gifted tun suna kanana, wato 'yan baiwa. Wata irin kwakwalwa gare shi da ba duk mutane Allah yake baiwa ba, duk inda yayi karatu malaman shi sai sun san shi, sun kuma ja shi a jiki, sun so shi saboda hazakar shi.
Ya yi gaba dayan karatun shi daga jami'ar Najeriya (NSUKKA). Bayan ya kammala MBBS din shi ya yi nasarar samun scholarship zuwa jami'ar (Manchester) inda ya yi specializing a kan zuciya da duk abin da ya shafe ta. Bayan kammalawar shi da dawowar shi ya soma aiki da federal Government, hakan ne ya sa ake yawan canza mishi wajen aiki. Daga wannan gari zuwa wancan cikin jihohin Najeriya.
Ya fara ne da aiki a babbn asibitin koyarwa na Ibadan, daga baya suka mai da shi ABU Teaching Hospital. Nan din bai dade ba suka dawo da shi nan AKTH na Kano, inda Allah ya hada shi da Hadizah.


HADUWAR SULAIMAN DA HADIZA
Haduwar su haduwa ce special kuma haduwa ba ta dadi ba. Yana tare da patient da ya yiwa aiki satin da ya wuce, Hadizah Ja'afar, da wasu abokan karatun ta suka shigo domin daukar lacca kamar yadda suka saba. A matsayinsa na consultant dinsu, basu samu kallo daga gareshi ba, balle ya tantance kamannin su, kasancewar Allah bai dora mishi lalurar yiwa mata kallon kurilla ba. Tsakanin shi da kowacce diya mace, kallo daya ne, da kau da kai. Wannan a jinin Sulaiman yake.
Suka samu kujeru suka zauna, kowacce da jotter din ta da biro a hannu. Yana ta yi musu bayani cikin lafiyayyen turancinshi na Birtaniya mara surki, wani zubin ya yiwa mara lafiyar tambaya ta ba shi amsa.
Wata amsa da patient din ta bayar ta sanya su murmushi dukkanin su (ban da Hadiza), cikin kalaman ta za ka fahimci kwakwalwarta ta tabu sakamakon bacin zuciya da damuwa.
Ta ce,
"Likita nifa 'yar sarauta ce ba mara lafiya ba!".
(Wannan ne ya sanya su yin murmushi). Ya ce,
"Wacce sarauta gare ki don mu fara girmama ki?"
Gaba daya daliban suka yi dariya don yadda yake biye ma shirmen matar dole ya baka dariya. Ta ce,
"Sarautar Kano gare ni".
Ya ce, "Wacce ke nan?" Ta ce,
"Nice 'yar ruwatan Kano".
Gaba daya suka yi murmushi, wannan karon ma ban da Hadizah, wadda a lokacin hankalinta baya tare dasu, yana ga halin da ta baro Mamansu a ciki na rashin lafiya mai tsanani.
Ba zato Dr. Bakori ya jefo tambaya, "Mene ne delusion?" Ya kuma nuna Hadiza da ya lura hankalinta ba ya tare da shi matsayin wadda za ta amsa mishi tambayar shi.
Ya yi mata magana ya kai sau uku ba ta san yana yi ba. Hadiza ta damu da Mamanta sosai, kasancewar ta jarumar Uwa mai hidimtawa rayuwar su, tun daga yarinta har a girman su. Yaya, (Sa'adatu), ba ta huta da dawainiyar su ba. Don haka jin ciwon ta suke tamkar a gangar jikin su.
Duka kawayen ta babu wadda ta zungure ta, don sun san da ta ji za ta ba da amsa a yabe ta kamar yadda manyan likitoci suke yabon ta a kullum saboda kokarin ta.
Ya buga tebir din gaban shi da karfi har ta razana, ya nuna mata hanyar waje ya ce, 'You can go out..... in kin gama tunanin kya dawo".
Ta mike sumi-sumi ta fita, murna gun su Hafsat kamar su yi yaya, yau Allah ya nuna musu likitan da ya yi maganin 'yar gaban goshin likitoci. Ya yi (referring patient) din zuwa psychiatric, su kuma ya sallame su.

Ya koma gida a wannan ranar, bayan ya gama duk abubuwan da ya saba na al'adar rayuwar shi kamin ya kwanta, kamar shan fruits da exercise saboda shi da daddare yake exercise din sa kasancewar da safe ba shi da lokaci.
Amma abin mamaki ya kasa runtsa idonsa, tunanin fuskar dalibar da ya kora a yau ke gilma mishi, ya hana shi sakat, ya hana shi sukuni, ya yi duk kokarin da zai yi don ya samu barci amma hakan ya faskara. Ya ko kasa runtsa idon sa, wani bakon al'amari ne mai takura zuciya da bai taba tsintar kansa a ciki ba.
Hadiza ba wata muguwar kyakkyawa ba ce cancan, tana da kyau dai-dai nata, sai dai kuma yarinya ce mai aji na karshe. Fuskarta zagayayya mai dauke da dara-daran fararen idanu masu sheki da walainiya, hancinta kamar an sanya ruler an ja shi an daidaita shi a kan (oval -shaped) fuskarta. Bakinta dan karami kamar cokali baya shige ba. A kan tsinin hancinta tawwadar Allah ce da aka haife ta da ita, fara ce sol! Irin farin nan da wadataccen ilimin boko ke taimakawa wajen zahharar sa.
Bai taba ganin yarinyar da (lab-coat) ta yi ma kyau kamar Hadizah ba. Ba sai ya tsaya wahalar da kanshi wajen tunanin abin da ke faruwa da shi ba, ya tabbata son Hadiza ne ke ratsa kowanne sako a jikinsa.
Abin haushin ko sunan ta bai sani ba, zuciya ta kwashe shi ya yi abin da ya zo ya dame shi. Bai taba tsintar kansa a kwatankwacin irin wannan yanayin ba, a kan diya mace.
Sai dai shi a ce ana son sa yana hura hanci, kada hakan ya janyo raini, baya fatan hakan ya kasance sakayya ce Allah ya yiwa dimbin matan da ke binsa agindi-agindi don ya so su yana yakice su. Tare da yi musu wulakancin da ko a hanya suka ganshi bazasu yi fatan ace sun san shi ba.
Ya fahimci dalibar (obstetric and gynaecology) ce, daga (ID Card) din ta. Yadda ya ga rana haka ya ga dare, ko na second daya bai runtsa ba. So da kaunar student (daliba) Hadiza na narkar mai da zuciya.
Abin kamar sihiri, daga ranar bai kara ganin Hadiza ba, bai kuma san ya zai yi ya tambaya ba, tunda ko sunanta bai sani ba. A matsayinsa na babban likita, mai juya sauran likitocin bangaren su, ba karamin zub da kima bane a ji shi yana tambayar wata yarinya cikin masu daukar darasi a wurin su. Duk da haka bai fidda rai ba, yana da yakinin watarana Allah zai sake hada shi da yarinyar ko da a mafarki ne.

Ita kuwa Hadiza ba ta dawo TH ba sai bayan sati uku, tana gida tana jinyar Maman su da suke kira Yaya, da ke fama da ciwon hanta. Tana ganin likita a Murtala, har suka kwantar da ita sati guda.
Kawarta Surayya ke daukar musu lacca tana kuma sanar da ita duk abin da ke faruwa ta waya. Ranar monday Maman su ta ji sauki sosai, don haka ta shirya ta dawo.
Ba zato babu tsammanin shi, yana ganawa da wata patient din suka shigo ita da Surayyah, ya zare gilashin idonsa a hankali, ya saki wata sassanyar ajiyar zuciya irin ta wanda ke neman abu, ya wahala ya dade, kamin ya samu. Duk hankalin sa da attention din sa sai ya koma kanta, ya manta abin da ke gabansa, ya samu kansa da rudewa. Abin da bai taba yi ba a kan diya mace, akwai wani sassanyan kallo cikin kwayar idon Hadizah, da ba duk mata Allah ya mallakawa ba.
Suka gaishe shi cike da girmamawa, sannan suka samu kujeru suka zauna. Hadiza dai a darare take, ko kanta ba ta dago ba. Daga gefe-gefen idon ta take satar kallon likitan da ya hargitsa mata tunani 'yan kwanakin nan. Tunda ya kore ta ba ta kara samun nutsuwar zuciyarta ba, har zuwa yau da ta sake tozali da shi a karo na biyu.
Ta tambayi kanta, shin ko mutane nawa ne a duniya masu ilhamomin Dr. Bakori? Yana da wasu ilhamomi na musamman a tare da shi da ba ta taba ganin su a da namiji ba, ko yadda yake duban mutane daban ne da na sauran likitocin da ta sani. Tsarin maganar sa cikin seriousness shi ne babban abinda ke burge ta da shi, ga kamun kai da sanin mutuncin kai, hadi da rashin son wasa ta ko’ina. Dr. Sulayman Bakori, ya shiga cikin rukunin wasu mutane da take ganin matukar kima da mutuncin su, sannan kuma ya bi ya manne a zuciyarta, ta yadda dai-dai da minti daya ta kasa manta shi cikin satittikan da ta yi tana jinyar Mamanta.
A gurguje ya basu laccar ya kuma sallami mara lafiyar da suke tare da ita. Suka mike da nufin su tafi, baya fatan wannan damar da kubuce masa, don haka bai yi kwauron baki ba, ya yi ta maza (in ji mata) ya ce da Hadiza cikin wata irin lallausar murya da ya kasa yarda cewa tashi ce.

"Wato fushi kika yi? Kika daina halartar karatun ki sabida na kore ki a kan kin yi min laifi?"

Ta yi ajiyar zuciya a hankali ba tare da ta juyo ba, ta ce,
"A haba Doctor! Wane ni in yi fushi? Mum dina aka kwantar a asibiti kuma ni nake jinyar ta sai jiya aka sallame mu".
Ya nuna tausayi tsantsa a kan kyakkyawar fuskarsa, a fili kuma ya ce,
" Am sorry….!"
Ta juyo don ta yi mishi murmushi, suka yi ido hudu da dan Inna Halima, wani chemistry yayi aiki cikin 'yan dakikai, ya kimsa wani al'amari mai GIRMA a zuciyoyinsu mai wuyar bayyanawa.

Gwiwoyinta suka yi sanyi, zuciyarta ta karye, duk wata soyayya da Allah ya halitta a zuciyarta ta hadu ta tattare ta dunkule a waje daya. To haka shi ma. Jikin shi ya ba shi wannan ita ce matar auren shi, wadda za ta samar mishi da 'ya'yan da zai yi alfaharin fitowar su daga tsatson ta. Ya ce.

"A bani address zan zo in duba Mamar mu".
Muryar Dr. Sulaiman har tsakar kan Hadiza.
Daga ita har Surayyah sai suka yi mutuwar tsaye, domin abune da ko da wasa basu taba kawowa ba. Kowa ya san shi da halin ko in kula da yake nunawa a kan mata, musamman dalibansa, wanda ke burge kowa. Don haka sun sha mamaki.
Ita Hadiza ta kasa magana, sai Surayyah ce ta rairayo mishi adireshin Hadiza. Ya ce,
"Idan na zo wa zan ce?"
Ta ce,
"Hadizah!".
Ya ce,
"Hadizahh, am I welcome?"
Ta yi murmushi ta ce, "
You are welcome, our humble consultant!!".


(The beginning of everything kenan ).

Tun daga wannan ranar kakkarfar soyayya ta kullu tsakanin Malamin da dalibarsa, kullum suna tare, a gida ne ko a ofis. Abin ya soma bayyana ga abokan aikin shi da abokan karatun ta, da manyan likitoci mata na bangarensa da ke yi mishi asirtacciyar soyayya.
Wannan ya janyo ma Hadiza hassada karara a wajen mafi yawan abokan karatun ta, to ita ma sai ta share su, saboda ta san Surayyah kadai ke kaunar ta saboda Allah.

***Auren su, wani abu ne da ya bar dimbin tarihi a asibitin Malam Aminu Kano, domin mafi akasarin likitocin cardiology department kabilu da Hausawa sun halarta. Ba a taba ganin daurin auren da ya tara 'yan boko tsantsa, manyan likitoci ziryan a unguwar Karkasara irin na Hadiza ba. Suka tare a gidan Sulaiman da ke cikin asibiti, cikin wata irin soyayya mai wuyar fassarawa.
Aure ne auren soyayya mai tsabta, wanda babu ha'inci, yaudara ko karya a cikin ta. Kar-ta-san kar, kowa ya san asalin kowa. Dr. Sulaiman ya sha mamakin samun Hadizah a cikakkiyar mace (virgin) wani abu da bai taba zuwa cikin hasashen sa ba, musamman in aka yi la'akari da matakin karatun ta. Ba gaskiya bane zargin da ake yiwa da yawan 'yammatan (medicine), kawai dan iska dan iskan kansa ne, amma da yawa abin da ya kai su shi ne a gabansu.

Cikin shekaru uku da auren su ta yi mishi tukuicin kauna da Munib da Muniba, wannan ya kara sayowa Hadiza matsiyaciyar kauna a zuciyar Sulaiman. Daga baya ne da ya kammala ginin da yake yi a Janbulo suka bar cikin asibiti suka koma, daga nan ne likitocin aka rufe bakin mahaifa ruf, aka fuskanci cigaba. Hadiza ta kare karatun ta cikin nasara, da taimakon mijinta. Ita ce (overall) a year din su. Da gudu aka rike ta a (labour room) wato dakin haihuwa. Sannan ba ta tsaya a nan ba, ta ci gaba da halartar kwasai-kwasai a kan bangaren ta. Har kawo matakin da ta ke kai a yau, na cikakkiyar likitar mata.

****
Karfe hudu na yammacin ranar litinin aiki ya tsagaitawa Dr. Hadiza, babu yawan marasa lafiya, don haka ta soma hada 'yan komatsanta don barin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

2 Comments On YAKANAH
avatar
rabiatu-2

8 months ago

Reply

Thanks

avatar
fatima-2-7-5

6 months ago

Reply

very nice book

Please Login or Register in order to submit comment