Join Our WhatsApp Group

TSOHON ALKAWARI Complete Hausa Novel Document by TSOHON ALKAWARI


TSOHON ALKAWARI

Cover Design Copyright and attribute to Marus Graphics

Uploaded by @Taskar

Total Words: 33061



TSOHON ALKAWARI

Reading Time: 2 Hours

Added On: 28, Sep 2023

Author: Nazir Adam Salih ,

Ebook Compiler : Admin

Author Group : Unknown group

Author Phone : Not Inserted

Book License : Free

Category: Action Novels

File Size: 171.67 kb

File Type: txt

Views: 503+

Download: 190+

Last download: 6 days ago

Description/Story: TSOHON ALKAWARI 1
.
Nazir Adam Salih (Nas)
.
A ranar ashirin da takwas ga
watan Afrilu na shekarar
Milladiyya ta dubu biyu da guda
hudu wacce ta yi daidai da ranar
Laraba na tashi a rude,
kwakwalwata a cunkushe domin
sama ko kasa na nemi sabuwar
basirar da zan yi rubutu na rasa.
Tun misalin karfe goma nake
zaune na sa littafin a gaba ina
kallo har zuwa karfe goma sha
biyu na rana kwakwalwata ba ta
zo min da komai ba sai tunane-
tunane marasa amfani. Ina nan
dai zaune cikin akurkin dakina ni
kadai da biro a hannu sai
jujjuyashi nake yi kamar sigari
daga karshe dai na tabbata ta
kare min dan haka sai na ajiye
biron na mike tsaye gami da
mika kuma cikin damuwa.
"Me ke damuna ne?" Na tambayi
kaina ko da idanuna suka kai ga
shafin littafi na ga ko alif ban
rubuta ba sai na yiwa kaina
murmushi, maganar
makaranta littattafaina ta fado min sa'ar
da suke cewa wai ta qare min,
lokacin da na kasa fito musu da
cigaban
ALJANI YA TAKA WUTA
da kuma
BINDIGAR KWALI NA BIYU
lallai ga dukkan alamu suma da
gaskiyarsu tabbas ta kare min
tunda dai gashi na sa littafi a
gaba na kasa rubuta komai
tsawon sa'o'i biyu.
.
Na gama hakura, na fito kofar
gida kenan sai na hango wata
yarinya dauke da fanteka da
kwanuka a samanta abin
tsautsayi ta zo tsallaka kwata
kenan sai kafarta ta zame,
fantekar a cike take da danwake,
wannan shi ne ya yi sanadiyyar
barkowar wani zazzafan gumi a
kan goshina, zuciyata ta fara
harbawa, sakamakon abin da na
tuna, tabbas na san inda zan je
na samo labari. Na sake duban
dunkule-dunkulen dan wake
burjuk a kasa sai ta tuno min da TUBANI
ina tuno da tubani sai na tuno da dattijo
SIDI MAI JAKA A
cikin sauri na nufi gidan wata
kakata, na yi sa'a kuwa na
sameta a gida. Bayan mun gaisa
sai na ce da ita.
"Tubani nake son ki yi min." Ta
dubeni cikin dariya ta ce "Ka ci
gidanku ja'iri dan nema, kai a
zamaninku ana yin tubani ne? Sai
dai jefi-jefi." Na dubeta gami da
sa alamun nutsuwa a fuskata na
ce. "Dan Allah ki yi min wallahi da
gaske na ke yi, fada min duk
abubuwan da za a saya sai na
baki kudin..."
.
Bata sami damar suturta tubanin
nan ba sai bayan karfe biyu.
Bayan na gama sallar Azuhur sai
na ga ta bade tubanin da yaji
sosai, domin na riga na san Sidi
Mai Jaka zai yi matukar farin ciki
da hakan, na sa ta dada kwarara
masa mai, sannan aka zuba min
shi a cikin kwano.
Karfe biyu da kwata na isa gidan
Sidi Mai Jaka dake bakin kasuwa.
Abin da ya fi damuna shi ne tun
sa'ar da muka rabu da shi
shekara biyu da suka wuce ban
kara zuwa wurinsa ba.
.
Ina isa kofar gidan sai na leka
zauren cikin doki, gabana na ta
faduwa domin kada na yi zuwan
banza ko baya nan. Ga mamakina
Sidi Mai Jaka na nan zaune akan
kujerar katakonsa, carbi a
hannunsa, haka nan akwai lofe a
gefensa a ajiye bisa wani farin
buzu. Sidi Mai Jaka ya dago kai
muka yi ido biyu, ko dakika biyu
ba a yi ba ya shaida ni.
.
"A'aha, yaushe a gari inji ma ki
bako Nas, ashe daman kuna
duniya?" Na dubeshi da dariya.
"Baba Sidi kuma tsofaffi ba ku
bar duniya ba ballantana mu."
Sidi Mai jaka ya fashe da wata
shakakkiyar dariya.
Na dubi Sidi Mai jaka kallon tsaf,
kana idanuna suka yo nazarin
zauren. Ko kusa ko alama babu
wani canji a kamannin Sidi Mai
jaka ko kuma zauren gidan. Wani
abin dadin mamaki kuma shi ne,
tsohuwar rigar nan dake jikinsa
mai kamar rariya, ita ce dai har
yanzu bai sake wata ba, na yi
mamakin karfin hali irin na
wannan rigar, domin sa'ar da na
fara ganinta shekaru biyu da
suka wuce ban taba tsammanin
zata sake wata guda a duniya ba
ta fatattake ba. Har yanzu katon
farin tabaron nan nasa na nan
daraf akan hancinsa.
.
Jikinsa kuwa sa'ar da na dubeshi sai na
fara tunanin me yiwuwa tun
bayan rabuwata dashi a shekara
biyu wankansa bai fi sau uku ba,
me yiwuwa ma sai dai ko alwala.
Amma fa duk da wannan
al'amari na Sidi Mai jaka ina
matukar girmamashi. Shekaru
biyu da suka wuce, wannan
tsoho Sidi mai jaka dogo fari
yankwanannen tsoho, kansa fari
fat, da furfura, farin gemu da
fuska ma'abociyar fadin goshi ya
taba bani labarin wata malamar
asibiti TANI da wasu yan fashi.
.
Sidi mai jaka ya dubi kwanon
dake hannuna cikin farin ciki yace.
"Ko shakka ba na yi wannan
alkawarina ne na TUBANI ko?" Na
ajiye kwanon a gabansa lokaci
guda kuma na matsar da lofen
dake kan farin buzun na zauna
na dubeshi cikin murmushi.
"Tabbas ka canka tubaninka ne."
.
Fuskar Sidi Mai jaka ta washe,
cikin nutsuwa ya mika hannu ya
dauko wata butar roba, ya guntsi
ruwa a bakinsa ya kuskure
bakinsa ya fesar a jikin bango.
Kana ya janyo kwanon tubanin
nan ya bude ya fara kallonsa
cikin nutsuwa.
"Nas, ina me yi maka albishir da
cewa wannan kyauta ta tubani
da ka kawo mini tamkar wani
dan mukullin labari ne da na
dade ina son na baka to sai dai
kuma shekaru biyu kenan yau
rabonka da nan sai yau Allah a
kawoka."
"Haka ne." Na ce dashi, sannan
na dada gyara zama domin na
san sabon labari ya riga ya zo....
.TSOHON ALKAWARI--> 2
.
Shekaru biyu kenan yau rabonka
da nan sai yau Allah a kawoka."
"Haka ne." Na ce dashi, sannan
na dada gyara zama domin na
san sabon labari ya riga ya zo....
Sidi Mai jaka ya birkita manya-
manyan tubanin, sannan ya
dauki tsinke, ya tsiraki wani kato
ya tura a baki, nan da nan
idanunsa suka fara zubar da
hawaye saboda yaji.Ko wace ce
ta yi ma tubanin nan, ba karamin
kwarewa ta yi ba Nas." Sidi mai
jaka ya ce dani. Na gyada kai. Sidi
mai jaka ya cire farin tabaron
dake idanunsa ya sa hannun
rigarsa ya goge idanunsa sannan
ya dubeni ya ce."Nas kune samari
yanzu idan aka ce ka yi auren jari
za ka yi?" Na dubeshi cikin
mamaki na girgiza kai na ce."Ya
danganta da irin macen...koda
yake dai ni a gaskiya baya bani
sha'awa, ni na fi son auren da
muke kaunar juna don Allah." Sidi
mai jaka ya dubeni ya kyalkyale
da dariya ya ce.Abin da Anas
mijin Mabaruka gurguwa kenan
ya kasa fahimta." Na dubeshi a
karo na biyu "Wa yekuma Anas
mijin Mabaruka gurguwa?" Sidi
mai jaka ya tsikari katon tubani
ya jefa a bakinsa."Shi ne labarin
da nake son na baka Nas ban
saniba ko kana da sha'awar irin
wadannan labarai na irin
wadannan mata masu matukar
son kansu a duniya fiye da
kowa?" Na yi shiru na dan lokaci
ina juya, abin da ya ce cikin
zuciyata. A gaskiya ni a son
zuciyata na fi son a bani labarin
yan ta'adda irin wanda ya bani
shekaru biyu da suka wuce, to
amma da yake ni yanzu ta riga ta
kare min dole ne na saurari
komai domin bani da zabi. Wa ya
sani ma ko wannan ma ya fi
wancan labarin dadi."Zan so
kuwa na ji labarin wannan
gurguwa, wace ce ita'" Na
tambayeshi, Sidi mai jaka ya yi
dariya ce."Bi ni a hankali Nas
dadina da kai gaggawa sannu a
hankali zan fara saka ma
zararrukan labarin ina kulla maka
su kamar yanda gizo-gizo ke
sakar gidansa" Sidi mai jaka ya
dan yi shiru sannan ya ci
gaba."Ita wannan gurguwa mai
suna Mabaruka ba a taba samun
wata mace a zamanin ta mai
arzikinta ba, miloniya ce a fagen
kudi, to sai dai kuma wani ragin
jin dadi da ta samu shi ne
gurguwa aka haife ta" Sidi mai
jaka ya juyo ya dubeni."Nas,
domin ka fahimci zaren labarin
nan da kyau, dole ne na ajiyar
zaren labarin gurguwa
mabaruka, na koma na dauko ma
hoton Anas" Na dago kai a
kagauce na kalle shi."Ka ce kuma
da labarin gurguwa za ka ba ni."
Sidi Mai jaka ya gyara tabaronsa
kana ya tsikari tubani guda ya
jefa a bakin salatinsa."Dole ne
mu fara da zaren labarin Anas, in
kuwaba haka ba Nas, ba za ka
taba fahimtar labarin nan ba" Na
gyada kai cikin fahimta."Yauwa
Nas, ina son ka dauki zuciyarka
ka mayarda ita cikin wata
mashahuriyar otal." Na dubi Sidi
mai jaka cikin kaguwa na ce
dashi "Na mayar""Yauwa" Ya ce
dani sannan ya fara.****
"To Nas ga Anas nan a cikin
dakin karbar
baki na otal din yana zagayawa
cikin farin ciki da annashuwa
domin aljihunsa a cike yake da
albashinsa na wannan
watan"Sidi mai jaka ya yi yar
atishawa sannan ya ce."Kafin na
ci gaba bari na baka hoton Anas.
Ka ga Nas Anas dogo ne wankan
tarwada mai kyawun fuska na
ban mamaki. Domin an ce ba
mata kawai ba hatta maza idan
Anas ya zo wucewa sai sun
kalleshi sun yaba da halittar
Ubangiji. Wani karin abin
burgewa kuma gareshi shi ne
duk irinsuturar da ya sa sai ta
karbeshi cif-cif kamar daman da
ita aka haifeshi. Wannan da
kuma iya zancensa da tarairaya
shi ya sa dimbin mata suke
kaunar Anas kamar su hadiyeshi.
Wani abu da zai baka mamaki
Nas, shi ne Anan ba wai yan mata
bane kawai ke son sa, hatta
dattijan mata ma suna kaunarsa
sau da yawa masu budurwar
zuciya daga cikinsu kan yi
kokarin su kaiwa Anas cafka
musamman ma dattijan
zawarawa attajirai. Wani sa'in
Anas ya kan kula su ba don
komai ba kuwa sai don dan abin
hasafin da sukan bashi.Daya
daga cikin abin da Anas ya fi
kauna a rayuwarsa shi ne hira da
kyawawan mata, sau dayawa
Anas ya kan tsinewa talauci sau
daruruwa cikin zuciyarsa, domin
a cewarsa shi ne ya shiga
tsakaninsa da kyawawan mata
masu aji. Duk da yake dai
kyawunsa kan janyo ra'ayin
kyawawan mata, to amma Anas
bai taba gamsuwa ba domin shi
ya riga ya sani, akwai irin
kyawawan matan da kyawunsa
bai isa ya janyo su ba. Wannan
ita ta sa Anas ya yi kurda-kurda
ya sami aiki a Lagwada Hotel. Duk
da yake dai shi ba kowan kowa
bane a otal din domin aikinsa ya
fi karfi a rabon abinci, wani sa'in
kuma ya kan nunawa baki
dakunansu su ta hanyar daukar
dakon yan jakunkunansu, to
amma wannan bata dami Anas
ba domin shi burinsa ya cika. Dan
wannan ita ce hanya daya jal da
zai yi ta ganin kyawawan mata
iri-iri, yanda yake so duk kuwa
da cewa bashi da ko kwabo.
Babban abin farin cikin Anas shi
ne ya ga ana liyafa a otal din,
musamman ma ta bakin aure,
domin tana bashi damar gani
kyawawan mata wani sa'in ma
har yazanta da su. Anas yana
daya daga cikin irin samarin nan
marasa zuciyar nema, wadanda
harkullum kwanan duniya
burinsu su ci BULUS ba tare da
sun sha wahala ba. Dan haka......
.TSOHON ALKAWARI--> 3
.
Wadanda harkullum kwanan
duniya
burinsu su ci bulus ba tare da
sun sha wahala ba.
.
Dan haka Naira dubu takwas din da ake
biyan Anas a wata sun isa su
sashi farin ciki, tun da dai ba zai
iya kokarin samun abin da ya fi
haka ba.Anan, sai Sidi mai jaka ya
yi shiru ya dago kai ya dube
ni."Nas, ina fatan kana fahimtar
hoton Anas da nake ta kokarin
zana ma" Na gyada kai na ce."Ina
fahimta" Sidi mai jaka ya gyara
zama sannansai ya ce."Bari to in
koma da kai can baya kadan inda
nake cewa Anas yana zagaya wa
a otal din cikin farin ciki, lokaci-
lokaci ya kan shafi aljihunsa a
fakaice domin baya son mutane
su fahimci cewar dan albashin
Naira dubu takwas din aljihunsa
yake tabawa. Haka nan shi kuma
bashi da imanin da zai iya jurewa
daidai da minti gudabai taba
aljihunsa ba domin ji yake yi
kamar kudin za su zube.Anas ya
ci gaba da zagaya wa a dakin
karbar bakina otal din ya gaisa
da wancan ya yiwa wannan
wasa har dai ya kawo daidai kan
kanta inda Balaraba mai bada
dan mukullan dakuna ke zaune.
Anas ya matsa kusa da kantar ya
dora hannunsa sannan ya dubi
Balaraba da kyakkyawar fuskarsa
ya hasketa da murmushi fararen
hakoransa suka fito fili."Hajiya
Balaraba ya ya garin
ne?"Balaraba ta dubeshi da
murmushi sannan ta turo biron
dake hannunta cikin kunne ta
fara juya shi, tana kanne
ido."Lafiya lau Anas. Har ka tashi
ne?"Anas ya dubi agogo sannan
ya dube ta."Da saura dai
Balaraba." ya dan yi shiru sannan
sai ya ce."Balaraba ba ki ga
motsin Halima ba ne?" Balaraba
ta girgiza kai."Ban ganta ba,
rabona da ita tun jiya da yamma
kamar ya yanzu da ta zo neman
ka." Balaraba ta ci gaba da susa
da biron cikin kunnenta."Anas,
wai don Allah yaushe za ka daina
yaudarar yayan mutane ne?"
Anas ya dubeta da murmushi ya
ce."Sai kin shirya Balaraba."
Balaraba ta harareshi."Me kake
nufi da sai na shirya?"Anas ya
shafi kyakkyawar fuskarsa."In
har kin yarda za ki aure ni, me zai
sa na ci gaba da yaudara? Daman
ke ce ai ki ka ki da tuntuni kin
amince dani da tuni na yi aure na
huta." Balaraba ta kyalkyale da
dariya."Oh! Anas Allah ya rufa
asiri wallahi wadda bata san ka
ba ka cuce ta." Ta dan yi shiru ta
sunkuyarda kai.Balaraba
bazawara ce, sau uku tana aure
tana fitowa. Da yake tana da
sakamakon diflomarta a hannu
kuma basira ta bace mata
maimakon ta yizamanta a dakin
miji sai ta nemi aiki a otal, a
lokacin watanta takwas kenan da
fara aiki. Tun sa'ar da ta fara
dora idanu akan Anas ta ji duk
duniya babu wanda take kauna
sai shi. Balaraba kyakkyawa ce
daidai misali, to sai dai kuma
bata cikin irin tsarin matan da
Anas ke so, domin a cewar Anas
duk macen da ta fiye gajarta bata
cika kyakkyawa ba ko da kuwa
tana da kyawun fuska. Balaraba
ta so ta cusa kanta a wurin
Anas,to amma irin jeri-jerin
matan da kan zo neman Anas tun
daga cikin gari har otal din, shi
ya gargadi Balaraba ta hadiye
maitarta ta yi shiru. To sai gashi
kuma yanzu Anas da kansa yana
zolayarta da zancen soyayya. Duk
da yake Balaraba ta tabbata
karya yake sai da kalaman nasa
ya faranta mata rai."Balaraba."
Anas ya kira sunanta. Balaraba ta
juyo frgigit."Tunani n me ki ke
yi?" Balaraba ta dago kai ta
dubeshi na dan tsawon lokaci
sannan sai ta ce."Kana da labarin
kayatacciyar liyafar da za a yi yau
a otal din nan?" Anas ya dubeta
cikin mamaki."Tun jiya na sami
labari a wurin Sabi'u amma ni bai
ce dani ta hadu ba." Balaraba ta
dube shi."Ai kuwa tun..."
Kalamanta suka makale a fatar
bakinta ba ta karasa ba. Anas ya
dubeta cikin mamaki sai ya ga
bashi take kallo ba bayansa take
kallo. Can wajen kofar shigowa.
Anas ya yi mamaki domin duk
kusan lokaci guda jama'ar dake
cikin dakin tarbar bakin suna
surutai suka yi shiru na dan
lokaci. Anas ya juyo sosai domin
ya ga abin da ke faruwa. A daidai
lokacin ne to ya hangesu.Wasu
kyawawan mata ne suka shigo
kowaccen suta ci kwalliya ta gani
ta fada. Anas ya ji yawun bakinsa
ya kafe, sannan sai ya lura daya
daga cikin yan matan tana tura
kujerar guragu ta farinkarfe akan
kujerar a zaune sanye da kayan
alfarma masu tsadar gaske, wata
budurwa ce gurguwa, za ta yi
kimanin shekaru ashirin da
bakwai.Koda Anas ya ci gaba da
kallon gurguwar da yan matan
ke turawa, sai ya yi ajiyar
zuciya."Kai amma fa an yi asarar
kayan kwalliya." Balaraba ta
dubeshi da dan murmushi ta
ce."Me ya sa ka ce haka?" Anas ya
dan yi shiru sannan ya dada
waigawa a karo na biyu ya kalli
gurguwar, sannan ya juya ga
Balaraba."Kin san ni ban cika
shiri da munanan mata ba.Dube
ta fa gurguwa mummuna amma
kayan jikinta sun fi na kowa
tsada, ai dole in ce an yi asarar
kayan kwalliya." Balaraba ta fashe
da dariya."Kai dai Anas wallahi ba
ka da kaico, me ya sa kake son
muzanta munana? Suma fa Allah
ne ya haliccesu kamar yadda ya
halicceka kyakkyawa kuma idan
ya so yana iya sa wa ka aure ta......TSOHON ALKAWARI-4
.
Me ya sa kake son
muzanta munana? Suma fa Allah
ne ya haliccesu kamar yadda ya
halicceka kyakkyawa, kuma idan
ya so yana iya sa wa
KA AURE TA."
Anasya harare ta."Allah sawwake,
kin ga Balaraba ni fa bana son
mugun fata, tun da abin na ki
haka ne ma ni kin ga tafiya ta."
Anas ya juya cikin sauri ya nufi
cikin otal din a daidai lokacin ne
to ya hango Sabi'u cikin sauri ya
matsa gareshi."Sabi'u ka ga
wata mummuna da alamun
kudi." Sabi'u ya dubi Anas ido da
ido, akwai wani yanayi a irin
kallon da yake yi da ya sa Anas ya
jigwiwarsa ta yi sanyi."Ya ya na
ga kana yi min wani kallon uku
ahu?" Sabi'u dan lukuti, gajere
ma'aboin son sa kayan turawa
duk kuwa da cewa ba wani kyau
suke yi masa ba, ya gyara
tsayuwa sannan ya dubi Anas "Ka
san
inda kake wage bakinka, in kuwa
ba hakaba wata ran za ka kwana
a ciki. Shin ka san waccan
gurguwa ko wace ce kuwa?"
Anas ya girgiza kai ya
ce."Fahimtar dani." Sabi'u ya
gyara wandonsa wanda ke
kokarin sullubewa ya fado."Ni na
san ba ka santa ba shi yasa kake
kokarin muzantata. To bari in
fada ma, ka ga duk munin nan
nata, wallahi ba muni bane...


Read / Download TSOHON ALKAWARI

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .

START READING

OR

Login Register

Please Login or Register in order to submit comment

Releted Novels

Releted Album