Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira)
Copied by Umar Dalha


[5/22, 07:52] Umar Dalha: 🌸👩🏻'Ya Mace Kyautar Allah🌸👩🏻

A true life *love* story.

By *Aaashmad*

Page 1....

Ban kade kofar da'akayi da karfi ne yasa su saurin juyawa don ganin ko waye hka, *Afeefah* ce ta shigo tana zum6ure zun6ure hawaye cike idonta ba tare da ta bi ta Kansu ba ta nufi hanyar daki da sauri, A fusaace ya daka mata mugun tsawa yace "ke xo nan" a sanyaye ta dawo hawayen da ke cike idonta ya shiga gangarowa fuskarta, *Adnaan* dake xaune gefen babban yayan nasu yyi tsaki yace "kedai gabaki daya rayuwarki ba ki da aikin yi sa na kuka koh? A hka nake ga xa ki qare koda yake ma banga laifin ki ba samun waje kika yi wllh, wawiya kawae" muryar *Ma'mee* su ka ji a falon ashe har ta shigo basu sa ni ba, a fusace take cewa " ke wllh idan baki dinga kama kanki a gidan nn ba sae kin dinga shan mamaki na, hka kawae xa ki sa mutane gaba da kuka a gida, ke yarinya ce ko uwarki ce ta mutu ko uban ki?" Adnaan yace "tambayeta dae Ma'mi, shegantaka kawae don ta ga ba a dukanta, ni da ma xa ki ban izini in saita mata xama a gidan nn" Aliyu kam shiru yyi don kwata kwata bayaso yaji ana wa yar kanwartasa fada shima bada son ranshi yai mata ba, bai ankara ba yaga ma'mee ta daga hannu xata kaiwa Afeefah da ke tsaye gun tana kuka har da shessheka duka, aikam yai xumbur ya miqe yana fadin "ma'mee don Allah kiyi haquri karki daketa kibarni da ita kawai," Adnaan da ransa bae masa ddi ba yace "haba yaya aida ka bari ta kai mata koda daya ne xata maida hankalinta," A tsawa ce Aliyu yace "shut up" ba'shiri kam ya maida sauran maganganunshi ciki yana hararan Afeefah, Aliyu na juyawa yaga babu ma'mee a gurin, janyota yayi ya shiga lallashinta dakyar ya samu ta haqura snn yace ta wuce daki, adnaan kam banda ta6e baki babu abinda yake, miqewa tai tanufi sama tana share hawayenta tashiga dakinta ta kwanta tana maida ajiyar xuciya tana tunanin abinda xata yi ma yayyin nata don rama abinda suka mata taji ddi, bude kofarta da akayi ne yasa ta dago kai don ganin ko waye *jiddah* ce tashigo tana dariya tana fadin "yar lelen yayan mu yau de mun ganku a raana muna labe mun ga duk abinda ya faru, aikam charaf afeefah ta dauka " to sai me? Bai isa yamin fadan bane? kuma ai gwara ni koda munyi fadan a ranar xamu shirya ku fa?, kuma kan ya doke ni ko ya min fada sau daya ku ya maku sau hamsin, xa ki xo kina wani gaya min maganar bnxa sae kace ba ku ku ka ma janyo min ba, kuma wllh sae na rama kmr xata yi kuka ta kare maganar, Daga mata hannu jiddah tai alamar ya isheta "ya isheni haka futsararra dama indai gurin fitsara ne ke gwanace," anyi fitsarar cewar *afeefah* ai ban gayyaceki dakina ba daxa kixo kidinga gaya man magana.A fusace jiddah ta bude qofar tabar dakin, tana fita Afeefah tabi bayanta don ta san inda xa ta, dakin Mami suka nufa gaba daya, Jiddah tace "Mami kina ganin Afeefah daga na mata mgna sae ta kama yi min rashin kunya ko" Mami ta daga kai tana kallon Afeefah, Afeefah ta fashe da kuka tace "Mami wllh su suka fara tsokana na daga mutum yyi min fada a hanya sae su kama min dariya dukansa" Jiddah tace "to Mami tafiya fa take bata kallon hanya saura kadan machine ya bugeta shine wani mutumi ya fara mata fada....." Tsawa Mami ta daka masu tace "duk ku bar min daki na" suka juya suka fita har lkcn Afeefah na hawaye.
Afeefah 'ya mace ce ta biyar ga Hajiya Zuwaira snn kaninta uku su ma duk matan, Alhaji Umar mai gidanta dan kasuwa ne da ke xaune Kano da iyalan nasa, mutum ne shi mai rufin Asiri sosae tunda ya wadata 'ya yansa da komae bbu abinda suka rasa na rayuwa, Hajiya Zuwaira da suke ce ma Mami ita ce matarsa ta biyu, bayan rasuwar Uwargidansa kuma uwar 'ya yansa Maza wato Aliyu da Adnaan, a lkcn Mami na amarya bata fi watanni biyu a gidan ba don da cikin Adnaan ta xo ta sami uwar gidan tasa, Aliyu kuwa na da shekaru biyar a lkcn, tunda ta shigo gidan bata taba samun matsala da matarsa ta farko ba Hajiya fateema har xuwa lkcn da Allah ya karbi ranta bayan ta haifi Faisal da ake ce ma Adnaan da kwana biyu, ssae mutuwar Hajiya fateema ya girgixa Alhaji Umar da amaryarsa Mami, Mami ce ta yi rainon Adnaan da madara har yyi wayo ya fara cin abinci, sae dae har lkcn ko bari bata taba yi ba, dai dai da rana daya bata taba cutan 'ya yan mijin nata ba ta rike su da amana tamkar uwarsu, bata taba barin sun yi rashin uwa ba a duniya don Mami mace ta gari ce, kowa yaba halayenta yake barin mai gidan nata, sae da tayi shekara dai dai har takwas kafin ta samu cikin 'yar ta ta fari wato Nusaiba sae sauran 'ya yan nata shidda duk mata suka biyo baya, Alhaji umar mutum ne me tsattsauran ra'ayi da ya rike policyn cewar sae 'ya yansa sun yi karatu me xurfi kafin su yi aure, don 'yar sa ta fari Nusaiba sae da ta gama karatun ta na Mass com tayi service snn ya aurar da ita ynxu hka tana xaune gidan mijinta a Katsina, hka ma 'yar sa ta biyu Safiya sae da ta kare karatun ta na Microbiology snn ya aurar da ita, ynxu su shidda mata suka rage, Sadiya, Jiddah, Rahma snn Afeefah, sae Fadila da Sumayya. Jiddah na shekara ta biyu a Jami'a ita da Sadiya suna karanta Biology, Afeefah kuma shigarta Jami'a knn tana karanta Bio Chem, Sumayya Fadila da Rahma basu kare secondary ba, Afeefah yarinya ce kyakkyawa don duk tafi 'yan gidan kyau da komae ma ka rantse kace ba gida daya suka fito ba idan suka jera da 'yan uwan nata, ga haskenta me daukan ido ga ta doguwa, komae nata daban ne daga na yan gidan nasu, Duk gidan Abbansu ya fi ji da ita, ka rantse kace ita ce auta, komae take so shi yake mata, ga son Duniya da babban yayansu ya Aliyu ya dauka ya dora mata sae dae hkn bae hanasa bata mata ba idan tayi ba dai dai ba hkn yasa take abun da ta ga dama a gidan, sae dae Mami bata daukan shagwaba da kukan da take addabar mutane da shi a gidan.

Eeshatullah Goni😘😘

🌸👩🏻 'Ya *mace* Kyautar Allah'🌸

A true life *love* Story

By Ashmaad

2.... Washegari da safe Afeefah da sauran yayyinta suka gama shirin tafiya makaranta don duk Bayero suke, suka sauko kasa gaba daya don yi breakfast, su Sumayya dama bakwae da rabi suke barin gidan, tea kawae Afeefah ta hada, ita a dole fushi take tun kan abinda ya faru jiya, bbu Wanda ya kalli inda take, Adnaan sae watsa mata harara yake ganin bata gaishesa ba ta kuma ki gaishesan, ya gama shan tean sa ya mike don shima yyi shirin xuwa aiki ne da yake Banker ne shi, Kudi ya ciro a aljihunsa dubu biyu ya mika ma jiddah yace "ga wnn ke da sadiya ku kara a kudin break yau" Afeefah ta shiga mitstsika ido murya can kasa tace "ina kwana yaya" harara ya galla mata yace "wnn kuma da wa take" mikewa tayi da sauri tana kkrin boye dariyarta ta kamo hannunsa tace "wllh ni ma sae ka bani yaya" ya fixge hannunsa yace "da'alla" su Sadiya suka dinga dariya ta fashe da kukan karya ta rungumesa tace "ni wllh yaya kana ganinsu ko" murmushi yyi ya ciro duba daya ya mika mata ta washe hakora tace "ngdd yayana" yace "ayi karatu da kyau snn ya fice rike da briefcase dinsa don ya sallami Mami, Abba bae yrda sun sa gyale su fita ba don hka dukkansu da Hijab suke xuwa sch, Afeefah ta nufi dakin Aliyu ganin bata gansa ba tun da ta sauko ta gansa kwance yana bacci har lkcn, ta isa kusa da gadon ta dan yi kara ya bude ido da sauri tace "yayanmu xa mu tafi" harara ya galla mata yace "nace ki daina tashi na idan ina bacci" ta turo baki ta juya ta fice daga dakin, Driver na ajiyesu makaranta duk suka kama hanyar Faculty dinsu, Afeefah da ko sati biyu bata yi da fara Bayero ba taji duk makarantar ya isheta, lecture Hall dinsu ta nufa tayi mmkin ganin har an soma lecture, ta karasa gun kofar shiga lecture hall din ta tsaya kmr munafuka don bata manta me Aunty Safiya tace mata ba wae idan ka xo ka tarar lecturer ya shiga class to kadda ma ka sa ran shiga lecturen ranan don koro ka xae yi, lecturan da baxae wuce shekaru talatin da biyu ba ya daga kai yana kallon ta, ta dauke kai da sauri ya ci gaba da lecturing dinsa, har aka kai karshen lecture din Afeefah na tsaye inda take, ya bada assignment snn ya kwashi takardunsa ya fito ta basa hanya da sauri, yana kallonta yace "me yasa ba ki shiga lecture ba?" Kmr xata yi kuka tace "idan na shiga xa ka Kore ni" Murmushi yyi kawae ya wuce, ta nufi wani karkashin bishiya a sanyaye tana tunanin shknn bata samu lecturen safe ba, wata yarinya ce ta xauna gefenta tace "Baki shigo lecture ba kika tsaya bakin kofa, ae wnn lecturan baya kora da kin shigo" Afeefah tace "haba" yarinyar tace "wllh kuwa, ga handout din da ya bada sae kiyi photo copy, ya sunan ki" Afeefah tace "sunana Afeefah" yarinyar tace "ni sunana Maryam Sadis" Afeefah tayi murmushi tace "nyc name" Maryam ta mike tace mu je kiyi photocopyn," Afeefah ta mike ta bi bayanta suka nufi shagunan da ake photocopy. Karfe uku da minti sha biyar suka fito daga lecturen su na karshe ranan, Maryam tace "mu je mu dan sha drinks kafin lkcn sllh yyi" wani cafeteria suka nufa suka karbi drinks biyu suka xauna suna sha suna hira kmr da can sun saba, Afeefah tace "to dan koya min lecture din da ku ka yi da safe mana idan kin gane" Maryam ta bude handout din tace "nima fa ba wae na gama ganewa ne ssae ba don ni course din wahala yake min, amma bari in maki bayani iya in da na gane" bayani Maryam ta shiga yi mata da farkon handout din kmr ynda lecturen yyi masu, murya suka ji daga gefensu duk suka juya suka juya gaba daya, lecturan course din suka gani xaune shima da drink a gabansa, yana kallon Maryam yace "idan lecturer yyi maku lecture ba ku gane ba, tun a ajin ya kamata kuyi tambaya ya ganar da ku" Maryam tayi murmushi cike da jin kunya bata ce komae ba, Afeefah ma ta sunkuyar da kai, mikewa yyi ya dawo spare kujerar dake kusa da su ya xauna, ya karbi handout din ya shiga masu bayani gaba daya har sae da ya tabbatar sun gane, godiya ssae suka yi masa barin Maryam, ya sakar masu murmushi yace "yhu re all welcm" yana kallon Maryam yace "ya sunanki?" Tace "sunana Maryam," ya gyada kai yace "nyc name, ke fa me tsoron shiga lecture" ya fadi hka yana kallon Afeefah, ta sunkuyar da kai da sauri cike da jin kunya tace "Afeefah" ya wara nanyany idonsa yace "Afeefah kuma, sunan gskyan ki xa ki fada min" murmushi tayi har lkcn bata dago ba tace "Zainab" yyi murmushi shi ma yace "Nyc name, next tym ki dinga xuwa sch da wuri don kadda ki dinga missin lecture daga farawan ki" ta gyada masa kai tace "nagode" mikewa yyi, yyi excusing kansa ya fita daga cafterian.

Eeshatullah Goni😘😘

🌸👩🏻'Ya *Mace* Kyautar Allah🌸👩🏻

A true life *love* story

By *Ashmaad*

3.....

Kallon juna sukai snnan maryam tace "saiki ki kkri nxt class dinshi kixo dawuri sabida course din mutuminnan naada wahala, tana fadin hka ta miqe tashi muje masallaci muyi sallah mutafi gda, masallaci suka shiga sukai sallah suna idar wa ta dauki wayanta sabida tunda take sallah taji yna vibrating, missed call din Sadiya tagani saita dubi maryam tana cewa " kinga drivern mu yaxo saimun hadu gobe, har ta wece sae ta kuma dawowa" what tym Muke da lectures Cox bbu tym table a gurina" 8:30am ki kkri kixo dae da wuri don matar itama da xarar tashiga to bbu wanda xai shiga, godiya tae Mata sukai sallama, tana fita sukaci Karo da jiddah "dallah mallama kixo mutafi tuntuni muke jiranki sallah kamar kina hadawa tun daga subhi, harararta afeefah tayi tai wucewarta ta shige motar,

Basu fita daga motar ba har sae da drivern ya ijye motar a parking space snnan suka fita, afeefah ce karshen fita koda ta fito saita nemi su jiddah tarasa wanda suna fitowa da sauri sukai cikin gida, ta6e baki tae tana tafiyarta a hankali kamar wadda kwae ya fashe mawa, tana stepping qafarta cikin gidan taji an fuxgota da sauri ta juya tana fadin yaya adnaan me kuma nae? "kewae yaushe xaki wayo? Sisters dinki kowacce saida ta gaidaani kafin suka shiga gida, amma kina ganina kika dauke Kai wlh saina saisai ta maki tunani a cikin gidannan, tuni hawayen dake idonta suka soma bin kuncinta daidai lokacin Aliyu yashigo da sauri ya rungumeta "Adnaan! Adnaan!! Adnaan!!! Kaji na kiraka sau uku, wlh idan baka fita harkar afeefah ba ranka xae baaci, Akan wani dalili xaka tasata gaba tuntuni na lura kap cikin yarn gdannan kafi sa mata ido matsawar ka cigaba da takurata wlh ranka baxai kyauba" am telling u this, shikam mamakin duniya duk suka isheshi ya rasa dalilin dayasa Aliyu ke haka bbu dama yaji anamata fada, Amma idan shi yatashi mata bbu mai cewa don me

Tana shiga daki ta nufi bathroom tae wanka, kaya mara nauyi tasaka jikinta ganin yamma tayi dakin ma'mi tashiga ta gaidata "ya makarantar afeefah? Cewar ma'mi,... Hmm!! Ai ma'mi yaukam ban samu lecture din safe ba, ina xuwa na tarar da lecturer a cikin lecture hall din duk a tunanina shima mutumin bai bari a shiga idan ya shiga ashe shi baya Koro, ma'mi tace to baki samu wasu sun nuna miki ba? Nasamu handout din nai photocopy cikin ikon Allah sai muka hadu da lecturen ya koya mana har muka gane "masha Allah" gobe ma kya kara Komawa baccin asbah, don ya koya maku yau bashi xaisa nxt tym ma ya koya makuba, gara kudinga hakura da baccin asbah a'ah tou

Washe gari da wuri suka shirya don basu jira yin breakfst da yan gida ba, har ta nufi kofar Aliyu saita tuna Jan kunnen daya mata akan tashinshi bacci Sai tajuya tama su ma'mi sallama suka fita, duk da irin sammakon da tayi saida ta tararda lecturer din harta shiga, duk da tasan baxata barta ta shiga ba kuma koda tashigan ma sai ta korota hakan baisa taqi shiga ba, bin ta da kallo lecturer tayi har ta xauna snn a nutse tace "Get out" mikewa Afeefah tayi lkci daya hawaye ya cika idonta ta fice da sauri daga class din, karkashin wani bishiya ta samu ta xauna ta dinga hawaye, ta kusa minti goma a gun tana kuka ta ji murya a gefenta ta juya da sauri tana kallonsa, wani matashin saurayi ne da baxae wuce shekaru ashirin da shidda ba, da damuwa yace "me ya faru kike kuka" share hawayenta ta shiga yi da sauri ta mike ta bar wajen kmr munafuka, ta fara tafiya da sauri da sauri don ma kar ya biyota wae, sae da ta dan yi tafiya me nisa snn ta soma waige waige ko xata ga ya biyota, karo ta kusan ci da mutum ta koma baya a tsorace, a dan fusace yace "watch were yhu re goin" shiru tayi tana kallonsa shi ma kallonta ya tsaya yi, "me yasa baki shiga lecture ba?" Tambayar da yyi mata knn, ta sunkuyar da kai ta gaishesa da ladabi ganin lecturansu na jiya ne, bae amsa ba ya kuma jefo mata tambayar da yyi mata, lkci daya hawaye ya soma cika idonta tace "matar ta Kore ni" strictly yace "wat did I tell yhu yesterday?" Kmr xata yi kuka tace "wllh da wuri na xo fa" hawaye ne ya shiga sintiri a fuskarta, yace "mu je," ba musu ta shiga bin sa da alamar yana da lecture da wani class ne, wani lecture hall ya shiga duk 300 level student din dake ciki suka yi tsit, front seat ya nuna mata ta xauna kmr munafuka, class rep din ajin ya mika masa Marker ya soma lecture, ssae take ganewa, awa daya da qtr yyi yana lecture daga bisanni ya ba class rep handout suyi photocopy, yana kallon Afeefah dake bin manyan matan ajin da kallo, ko kadan bata lura ita yake jira ba har sae da yace "Zainab!" Firgit ta mike ya juya ya fita ta bi bayansa da sauri, duk yan ajin suka bi ta da kallo barin matan.

Eeshatullah Goni😘

🌸👩🏻 'ya *Mace* kyautar Allah🌸👩🏻
A true life *love* story

By Ashmaad

4.....

"Why are yhu late yau ma? ina ne gidan ku?" Tambayoyin da ya jefo mata knn suna cikin tafiya, A hnkli tace "jan bulo" ya juya yana kallonta yace "nan nn jan bulo shine baki xuwa da wuri" shiru tayi bata ce komae ba, ya ci gaba da tafiya yace "me kuke da next ynxu?" Ta ce "ni bani da timetable" ya juya ya kalleta yace "to tafi class ki duba" ta gyada masa kai snn ta nufi lecture Hall dinsu, bakin hall din suka hadu da Maryam, da damuwa Maryam tace "yau ma baki xo da wuri ba" Afeefah kmr xata yi kuka tace "kuma fa wllh da wuri na tashi" Maryam tace "to ki dae dinga daurewa seven xuwa seven thirty ki shigo sch, kinsan wasu lectures basu da mutunci" Afeefah tace "to" Maryam tace "muje kiyi photo copyn handout" bin ta Afeefah tayi suka nufi wani shigo suka gama photo copyn, Maryam ta shiga gwada mata abinda aka koya masu, sha daya saura minti goma Maryam tace "kin ga tashi mu je cafeteria yunwa nake ji, kinsan bana breakfast kafin in fito" Cafeteria suka nufa Maryam tayi masu orderin jollof rice da nama plate biyu sae soft drink, Afeefah tace "ynxu cikin mutanen nn xa mu ci abinci, ni dae kunya nake ji" Maryam tayi dariya tace "lallai, hala baki yi boarding bne" Afeefah tace "kallon mu fa xa ayi" Maryam tace "kin ji ki wa xae kalle ki, kowa na ta cikinsa" Da kyar Afeefah ta ta ci abincin tana duka kai wae ita kunya, Maryam sae dariya take tace "Xa ki daina ne yarinya"

Sae da suka yi sllhn Azahar snn suka shiga next lecture dinsu, ssae ta maida hnkli a lecture din har suka gama wajajen uku da rabi, Maryam tace su jira ayi la'asar snn su tafi, a masallaci suka hadu da su Sadiya da Jiddah, Afeefah tayi introducin yayyin nata wa kawarta Maryam, suka gaisa. Karfe hudu da minti goma drivern gidansu ya xo, Afeefah ta tilasta Maryam su je a rage mata hanya tunda hanyar daya ne, da kyar ta yrda shi ma sae da su jiddah suka sa baki, sun kusa inda motarsu ke Parke driver na jiransu ta hango lecturan su, da alama shi ma gida xae wuce, rasa sunan da xata kirasa da shi tayi don bae ganta ba, can tace "Sir" juyawa yyi suna hada ido ta sakar masa murmushi hade da daga masa hannu tace "sae gobe" murmushi yyi shi ma ya gyada mata kai, snn ya karasa gun motarsa ya shiga, su ma suka shiga ta su motar suka bar makarantar, a hanya Maryam tace gun nn xata sauka, drivern yyi parkin ta fita snn tayi ma yayyin Afeefah sallama, Afeefah ta daga mata hannu snn drivern ya ja motar suka nufi gida.

Da daddare suna xaune falo suna kallo da Mami, Abba ya shigo gidan, duk suka yi masa sannu da xuwa, hnklinsa duk na kan Afeefah da ta hade rae, ya karaso falon yace "ya aka yi dota, me aka maki" cikin shagwaba tace "ba kai ne ba baka tambayeni ya karatu ba" dariya yyi yace "to ae bacci kike kafin in dawo, in xa ki tafi kuma baki shigowa sallamata" Mami ta tabe baki, Adnaan ya mike ya bar falon, su Sumayya kam dariya suka soma yi, Abba yace to tashi mu je ki gaya min ya karatun, ta mike da sauri ta bi bayansa suka nufi sama xuwa falonsa. Karfe goma saura Afeefah ta fito daga falon Abba, dakin Aliyu ta nufa, ta samesa xaune yana danna laptop, ta hade rae tace "yayanmu baka tambayeni
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment