Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Da jidda tai mata da sauri ta fito ta hangota tai b'angaren dakin khaleel, kishi mai xafi ya taso mata ta dawo kitchen ta kashe gas jikinta asanyaye ta hau sama ta zauna tana sak'e sak'e aranta, me jidda tajeyi dakin ya khaleel mik'ewa tayi ta fara safa da marwa, ta tuno da duk lokacin daxa shiga dakin shi sai ta tadda jiddan kusan ajikinshi gabanta ya fadi jikinta ya fara karkarwa


Kai tsaye dakinsa ta nufa tura kofar dakin tayi ba sallama ya dago ya daka mata tsawa, baki iya sallama ba ? Juya wa tai tayi sallama ya amsa ta shigo yana xaune kan 3 sitter yana kallon labaran BBC ta xauna akasa kusa da kafarshi tana murmushi ya khaleel naga baka ci abincinka ba shine na xuvo na kawo maka, idonshi akan tv yace ok, tashi tayi ta xauna kusa dashi sosai kanta tasa akafadarshi, matsa ! Yace mata da mmk ta dago kai taki matsawa ya waiwayo fuskarshi adaure kafin ya kuma mgn ta sauka ta koma inda take ajiyar xuciya tayi ranta ya baci sosai, ya khaleel nai maka laifine ? Meyasa baka kula dani ? Kodayaushe cikin gwasaleni, plx aure fa xamuyi kasani ina sonka banason narasa, idan nai mk laifi kayi hkr tunda nabar gidan nan nake cikin tunaninka kwatsam naji lbrn aurenka da Jennifer, nasan ba tsarinka bace sbd bakason k'aramar yarinya sannan gata Mara asali duk da naji ance ta musulunta ko kadan bata dace da kai ba waya sanima ko shegiyace, tsawa ya kwatsa mata ke ! Idan cin mutuncin matata xakiyi tashi kibar min daki, wani irin kallo tai masa da nanata mgnr shi "matarka ?
"Tana da asali kada ki kuma sheganta ta ki girmamata tunda ni take aure, kamar ta fashe da kuka Dan takaici haka ta daure ta janyo wata hirar ta daban

Kasa jurewa tayi
afusace ta fito daga dakinta tai b'angaren ya khaleel xuciyarta na tunxirata cak ta tsaya da sauri ta koma daki silent makeup taiwa fuskarta ta nufi kitchen ta hada mass coffee ta nufo b'angarenshi sallama tayi ya amsa tashigo jidda na kusa da kafarshi, taji dadin ganinsu a haka dan sun yi nesa da juna, ta ajjiye coffee din ta cire hijab dinta kai tsaye bed room dinshi ta wuce ya bita da kallo yana mmk dan baiyi tunanin xata kawo masa coffee ba, jidda xuciyar ta kamar tayi bindiga ganin ya khaleel yana kallon jannat yasa ta k'ara jin haushi fitowa tayi hannunta rik'e da rigarsa sbd farar singlet ce ajikinshi ta k'araso kusa dashi tana k'ok'arin saka masa yaji dadin kulawar ta shiyasa ya tayata Sa rigar taxauna kusa dashi ta xuba masa coffee din ta miko masa ya amsa yana sha, ta dauki remote, ta canza channel ta kaishi zee tv akwai series din da suke yi mai kyau, mmk ta bashi yanda yaga tasaki jiki sosai yau adakin shi sab'anin da datake a d'arare, wani mugun kallo jidda take binta dashi, tsam jannat ta mike dan tagaji da Harar da jidda take mata hawa kan kujerar tayi tasa kanta akan cinyarshi tana kallon tv lumshe ido yayi ya ajjiye coffee din hannunsa kamshin turaren mai dadi ya shaka yasa hannu yana shafa kashin kanta tayi matuk'ar birgesa yanda ta nuna msa kulawa, jidda kasa jure kallonsu tayi ahaka tayi mmkin yanda k'aramar yarinya ta d'auke hnklinsa da sauri ta mik'e xata fita, shi sam ya manta da ita futa tayi afusace, ya tabe baki


By
*Ummee Garkuwa*
[2/28, 6:42 PM] Nana Zee: ✍✍✍JENNIFER✍✍✍





59&60

Shiru sukayi kowacce da abinda take sak'awa aranta,
Abin ya matuk'ar d'aure musu kai,
Sulthana ce tak'atse shirun,
Y'an uwa menene abinyi ? Abin nan ya bani mmk ni sam ban yadda da maganar wannan mai k'asumbar ba,
Hindu ta kalleta nasan osasa abokin mariki nane na yadda da abinda yace sosai sbd nasan wanene shi,
Ajiyar xuciya, tayi kudin daya nema ne bamu dasu ko Rabin su ma ni banda shi,
Ni abin ya isheni wllh, takarasa maganar da hawaye,
Gyda kai sulthana tayi kiyi hkr sis hindu ko mai yayi xafi maganinshi Allah ni kaina narasa me yake min dadi nakuma rasa mafita,
Sukayi shiru dukansu xuciyar kowacce tana kuna hade da sakawa da warware wa basu da mafita basu da yadda xasuyi,
Jannat ce ta katse shirun da sukayi,
Mudage da addu,a mu cigaba da fadawa ubangiji Allah yana kallon kowa yana kallon xuciyar kowa Allah ya kawo mana dauki Allah ya baiyanar mana da iayayenmu, dukansu suka amsa da amin,
Hindu tace plx sulthana kada ki fadwa kowa xancen nan, koda kuwa dady ne ko Momy
Da sauri ta kalleta sbd me ?girgixa kai tayi muyi tunani plx, bayin Allah nan suna iya bakin kokarinsu wajan taimakon mu da kyautata mana kada mu k'uresu, kud'in da osasa yafada sunyi yawa, mubar abin iyakarmu tunda mu ya shafa,
Sulthana tace gaskiya sunyi mana taimako sosai sun maida mu yayansu sun d'auki damuwarmu sun maida ita tasu wannan kam dole mu b'oye,
Jannat tace hakane sis idan suka san zancen d'aga hnklinsu xasuyi, akan xasu bashi kud'in kuma sunyi yawa, addau itace mafita Allah yaka womana k'arshen wanann masifar,
Ku tashi mu shirya kada dare yai mana asanyaye suka mik'e kowacce tana jin d'aci aranta ta na kuma d'okin sanin suwaye iyayensu haka suka gama kwashe kayan babu wacce taiwa wata mgn acikinsu akan haryarsu ta komawa ma haka sukayi xugum babu hirar kirki sai sak'e sak'en xuciya,


Gab da magruba suka dawo gida jikinsu asanyaye alwala suka dauro sukayi sallah jannat ta dad'e tana xuba addu,a akan Allah ya kawo musu mafita, bayan ta idar da sallah tayi jigum ad'aki tana tune tunane har akayi isha'i ta mik'e ta yi sallah had'e da yin adduar data saba tana idarwa ta kishingida bacci ya fara daukanta k'arar wayanta ne ya tasheta, tana dubawa taga Mr coffee ne tasan abinci yake jira takai masa kafin ta daga wayar ta katse da ta tashi ta tashi kitchen ta d'eba masa abiincin Sa ta had'a masa coffee ta nufu b'angarensa,
Sallama tayi ta shiga yana kishingide jikin kujera yana sanye da 3quater jikinshi ba riga yana kallon labarai kallo daya tai mishi ta kauda kai,
Ajjiye kayan tayi tana kokarin xuba masa coffee,
Ke" ta kalleshi,
Ki cire hijabin,
tarasa meyasa kullum taxo sai ya ce ta cire hijab dinta, ba yadda taso haka ta cire hijab din kanta ba dankwali sai fakin din gashinta da tayi ta xauna, ta dauko cup ta xuba masa ya amsa yana sha tana xuba masa abinci karar wayarshi sukaji da take a bed room dinsa,
Ya kalleta kadan,
" tashi ki dauko min, a hnkl ta mike ta nufi bed room dinshi ya bi bayanta da kallo yana mmkin kyawun dire datake dashi,
Lumshe ido yayi a hnkl ya furta jannah kina da tsari da halitta me Kyau ngd wa Allah daya mallaka min ke,
Ta dawo hannunta rik'e da wayr ta mik'a masa ya xiro hannu xai amsa hannunsu sukayi karo da juna yaji hannun laushi kamar auduga ya amsa ya duba, Jidda ce d'an k'aramin tsaki yaja ya ajjiye wayar,
Mikewa tayi xata sa hijab, ya dago kai yana kallonta,
Muryarshi asanyaye,
"Ina xaki ?? Ta kalleshi suka hada ido,
" daki zan koma,
Xauna muyi mgn,
Xama tayi tana kallon kafet din dakin,
"Daxu ina kikaje ??
Da mmk ta kalleshi,
Hotoro mukaje ban ma je gidan Maman David ba,
" da ixinin wa ?
Xaro ido tayi tana mmk, da ixininka mana, na tambayeka kuma ka mince,
Girgixa kai yayi,
Bana son yawo tafiyar bata da amfani, ni ban San kin tmby niba,
Ranta ya baci ta bata rai, idonshi akan tv yana shan coffee yace baki fadamin xakije hotoro ba, daga yau ma babu inda xaki k'ara xuwa, kina ji ?
Turo baki tayi batare da ta amsa ba,
Waiwayowa yayi yana kallonta ta hada rai ta turo karamin lip dinta, ya tsurawa lip din ido yanda sukai Kyau,
Ajiye cup din yayi ya janyo ta kusa dashi,
"Bakiji abinda nace ba ?
Asanyaye tace,
Naji " sbd ya tsura ta da manyan idanuwansa sannan yana gab da ita hannunta cikin nashi yana murxasu a hankali, ta marairarice tana k'ok'arin fusge hannun, daya hannun nasa yasa yashafa karamin lip dinta,
Ta matsa tana kokarin tashi, ya kalleta,
Ina zaki ?
Turo baki ta kuma yi, daki xani bacci nakeji,
Da hannunshi ya dawo da ita kasa, kamar xatai kuka tace plx ya khaleel ka sakeni.....kafin takai karshe taji bakin ta cikin nashi yana shansu da sauri sauri kamar yana shan alewa, tayi tayi ta kwce kanta ta kasa sbd ya rike ta gam ajikinshi, ya Dade yana shan lip dinta sannan yasaketa hade da tsura mata idanuwa, yana mata kallon yarinya amma tsarin dirinta yana Sa yana jin feeling dinta, ganin ya saketa yasa ta mike da sauri xata fice sam ta manta hijab dinta,
Daukar hijab din yayi hade da mikewa yabita bakin kofa dashi dakyar
Yace, "karbi hijab dinki, ta miko hannu xata amsa ya rike hannun gam tana kokarin fisgewa ya janyo ta jikinshi da karfi kamar xai tura ta cikin cikinshi jinta ajikinshi yasa yai ajiyar xuciya yana jin tamkar ana kara masa soyayyr ta, ahnkl ya xamota daga jikinshi, itakam duk ta rude jikinta sai rawa yakeyi ya kalleta ta sunkuyar da kanta kasa ya dago da fuskar suka kalli juna,
Asanyaye yace mata,
" kifad'i abinda ke ranki?
Da mmk ta kalleshi ta kasa kauda idonta sai da tace masa "me kakeso nace?
Hannunshi biyu yasa ya tallbo fuskarta,
Abinda kike boyewa arnki, ya kalli kirjinta yanda yaga yana bugawa yai ajiyar xuciya baiyi tunanin ta kai haka ba,
Tureshi tayi, sbd jin haushin mgnrsa, da fada tace masa, wanne àbu nake boyewa ?
Cikin ko inkula yace yace, Wanda kikeso,
Runtse ido tayi mgnr ta mata zafi har yanxu yana nan da wannan tunanin ? Dole kam ta sauya Dan taga abin xai wuce gona da iri,
Rike kugu tayi tana kallonshi, ni babu Wanda nakeso babu kuma abinda nake b'oyewa,
Aurenka kuma bani na xab'a ba kusan dolenshi ma akaimin, ta juya ta bude kofa ta fice hade da yi masa Harar sama da k'asa
Wani mugun mmk ne ya kamashi ya xauna yana nanata xancen,
" kusan dole akai mata ?
Gaba daya yaji kanshi wani iri ta bashi mmk baiyi tunanin ta iya tsiwa hakaba,

Da matukar jin haushi ta nufi bangarenta ta kwanta tana mmkin halin khaleel haushin sa sosai ya kamata ta gaji da wannan rainin wayon, kallonta kawai yake bai sonta ba,
Tsaki taja xaka sha mmk na, ta kwanta ranta abace cike da jin haushin shi,



*****************
Washegari da rana suna dakinta inda suka saba zama suwaiba ta shigo sbd tana koyawa jannat karatu, bayan sun gaisa, sulthana ta kalli hannunta da mmk tace suwaiba ina son henna waye yai miki ?
Zama suwaiban tayi tana murmushi ni nayi sulthana, wow ina so kiyi mana nida Anty jannat banda waccen ta nuna hindu Dan ko kin mata ba Kyau zaiyi ba, kin ganta cen duk itace mummunar mu,
Dariya sukayi banda hindu datake hararar sulthana, da dariya suwaiba tace haba duk kamarku daya ni kaina da yanayin shigarku nake tantance ku, Baku da banbanci, bari naje na hado kayan kunshin in dawo,
Bata dade ba ta dawo tai wa sulthana me Kyau sannan ta fara yiwa jannat ana gama mata na hannu wayarta tai kara hindu ta dauka ganin Mr coffee yasa tace jannat waye kuma Mr coffee? lokaci daya sukayi dariya da suwaiba, kar ta katse fa " ajjiye kwai hindu tunda lalle ne a hannuna haka wayar tai ta kara har ta tsinke sai wajan 4:00 tagama musu lallan mai Kyau dake gwana ce suwaiban ta kware sosai yayi Kyau


Toilet tashiga tai wanka kafin ta fito suma sun tafi wankan ta dakko kayan daxata Sa ka English wears ne murmushi tayi da ta kalli kayan yayanta Emanuel ne dayaje jos ya siyo mata su atsaraba satin da xasu shiga wannan wahalar rayuwar bata taba Sa kayanba body hock ce pink me karamin hannu da siket dinta bai karasa sauka kasa ba sun mata Kyau sosai ta tsaya gaban mudubi tana taje kanta bude kofa akayi ta xaci su sulthana ne ganin shi tayi cikin madubin ta hade rai tai kamar bata ganshi ba ya xuba mata ido Hannunshi sanye cikin aljihu,
"Bakiga miscalled dina ba ?
Banxa tayi dashi kamar bata jiba,
Mmkinta yake, bakyaji ina mgn ? Ya fada da fad'a,
Ya b'una fuska tayi mgnr takace bata da amsa,
Kadan yarage yasaki baki sbd mmk,
Mikewa tayi tana gyara xaman siket dinta, ya karewa shigar ta kallo tai mata Kyau ya kalli kirjina gabanshi sai da ya fadi,
Adake yace meyasa baki daga ba ??
Far tayi da ido "sbd bani da abinda zance,
Ta gama kaishi karshe a mmk tambayar kansa ya fara yi dama haka ta iya tsiwa ?
Har ya juya xai fita sai kuma ya dawo hade da fincikota, jikinta na gogan nashi idonta kir akanshi, ki kawo min coffee dakina ina jiranki, fincike jikinta tayi ta kasa sbd bakaramin riko yai mata ba, shiru tayi tana kallonsa, da tsawa yace ko bakiji ba murguda baki tayi, da mmk ya saketa lallai yarinyar nan ta shammaceshi, ta koma nesa dashi, ya fice daga dakin, tayi dariya ta cigaba da taje gashinta, mutun sai kafiya da riqak'k'en ra'ayi taja karamin tsaki



******
Ya kalli agogan hannunsa 11:30 ya furxar da huci me yarinyar nan take nufi ? Kodan taga yana hada jikinshi da nata ? Tun kafin magrub yace ta kawo masa coffee har yanxu bai ganta ba ? Dalilin daya Sa baison yarinya kenan dafe kanshi yayi idanfa yayi sake rainashi xatai shi mutun ne da baya son raini shiyasa ko k'annan sa baya wasa dasu xabura yai ya mike ya fice daga dakinshi kai tsaye bangarensu yayi yashiga dakinta tana kwance ta na bacci ya kalli beauty face dinta tayi kyau da baccin, tsura mata idanuwansa yayi yana kallonta, a hnkl ya xame bargon jikinta ya kalli hannunta dayasha lallai mai kyau yashafa hannun sbd yana matukar son lalle motsi tayi ya cire hannunsa ta juya daga kwanciyar ya kalli gashin kanta cikin sha'awa yakai hannu ya shfa kan, xabura tayi ta mike idonta taf cike da bacci ta galla masa harara menene haka ? Hada rai yayi ban sani ba ya mike tsaye, daxu nace ki kawomin coffee meyasa baki kawo ba ? Ya b'una fuska tayi "mantawa nayi ta fada tana gyara kwanciya, jannah ! Ya kira sunanta da tsawa har sai da ta tsorata,me kike nufi ne amarairaice tace kayi hkr plx bacci nakeji,
Mantawa nayi,
" kinga bana son musu ko gardama kina jina ya fada hade da xare ido, na kyaleki sbd yau kika fara kada ki kuskura ki kara maimaitawa, ya fice daga dakin ajiyar xuciya tayi hade da hararan bayansa, idan baxaka canxa ba ya khaleel nima yanxu na fara ta juya ta cigaba da baccinta,

Da safe bayan sunyi breakfast suna hira ga al'adarsu, muryar Jidda taji tayi sallama suka shigo ita da mamanta da gudu zahra ta rungumesu gaban jannat ya fadi tasan wannan xuwan ba alherine ya kawosu ba

By
*Ummee Garkuwa*
[2/28, 6:42 PM] Nana Zee: ✍✍✍JENNIFER✍✍✍



63&64

tabe baki yayi yana jin dadin fitar tata tana ganin ta fice ranta ab'ace taji dadi sosai dama tayi hakanne dan ta bata mata rai ta dago kai suka hda ido ita da shi ta b'ata rai ta sauke kanta a hnkl ta xame kanta daga cinyarsa ta mike ta dauki hijab dinta ta fice kallonta kawai yayi hade da lumshe ido yau kam tabashi mmk yanda ta nuna ta damu dashi

cikin jin dadi ta kai flast din kitcean ta nubo bangaren su afalo ta sameta, ganinta yasa jida ta mike taxo gaf da ita xata wuce ta fisgo hijab dinta, fisge hijab din jannat tayi tana kallonta, hararta tayi mara asali wacce aka watsar da ita a bola, kina gadarar cewa khaleel mijinki ne ? auren na kaddara har aurene baya sonki ba kuma xai taba sonki ba dan ya khaleel yafi karfin ki yar matsiyata mara
asali waya sanima ko shegiya ce, tafiyar ta tayi ta kyaleta tana jifan ta da maganganu na cin xarafi daki ta shige xama tayi akan gado xuciyar ta na kunan maganganun da jidda ta yaba mata hawaye masu daci suka xubo mata cikin kuka take magana, dan kawai Allah ya jarabcemu shine muka xama abin gori ,meyasa mutane basa gane kaddara? sun manta Allah shiyake tsarawa bawa rayuwa ba ba bawane yake tsarawa kansa ba ?? hannu ta daga ya Allah ya ubangiji ka kawo mana agaji Allah kanuna mana iyayenmu kuka sosai takeyi, nagaji da wannan cin mutuncin jidda dole na dau mataki baxan iya jurewa ba ko ada ina kyalekune saboda aiki nake muku yanxu kam yayanki nake aure bazan iya ba dole na dau mataki

*********
washegari da safe ta fito daga wanka hindu ta shigo da breakfast dinsu sulthana na biye a bayanta, ta kallesu anan zakuyi breakfast din ? kai sulthana ta daga mata waccen masifaffiyar matar ta hakimce a dining area tana ta muxurai shine momy ta kawo min tace muje sama muyi breakfast din,zama jannat tayi hade da tagumi,sulthana ta kwashe da dariya anty jannat ki kwantar da hnklinki wllh duk da tana takamar ita kanwar dadyce gidan dan'uwanta ne idan ta kuskura tace zata kara takamu nima sai na takata dan bata da girma a idona bazan iya jure cin mutunci ba dan ma nayi sauki sai na nuna mata kuskurenta, hindu ta katseta, haba sulthana matar nan fa ba sa'arki bace kodan darajar dady ki kyaleta plx dan Allah muna xaune lfy kada kija mana tashin hnkl duk masifarta nasan ba dadewa xatai a gidan nan ba, hararar hindu tayi idan xaki iya jurewa ki jure nikan wllh bazan iya ba ita tasan ba sa'ata bace take janmu da masifa ta xubar da mutuncinta nasa kafa na take, jannat ta kalli sulthana any'a kuwa kina shan mgninki sulthana ? ina sha sosai naga canji bakuyi mmkin jiya ban rama abinda matar nan tai mana ba ?? plx anty jannat sauko miyi breakfast a hnkl ta sauko tana tausayawa kansu na rashin sanin iyayensu,
bayan sun gama breakfast hindu tace jannat dama jidda budurwa ya khaleel ce ? kai jannat ta daga mata,sulthana tace jiya ruby take bamu lbr wai har ansa musu rana,tsaki tayi hanji dadi ba ko kadan, anty jannat naso ace ke kadaice matar khaleel banso kiyi kishi da tsohuwar guxuma irin jidda, murmushi jannat tayi dole ne sulthana sbd an dade da sa musu rana,addu'a xaki mana Allah ya bamu zaman lfy,test ya shigo wayarta tana dubawa taga ya khaleel ne...... ki kawo min breakfast..... ajjiye wayar tayi ta kyaleshi


*********
karfe 3:00 na rana suna xaune a falo jannat tana cikin daki haisam ya shigo, sulthana ta bata rai tai kamar bata ganshi ba xama yayi yana kallon tv da suke kallo, ya kalli sulthana ya ga ta bata rai, ya fuskanci kwana biyun nan ta daina kulashi, sulthana ba gaisuwa ? bata kalleshi ba tace ya kk ? murmushi yayi lafiya lau nake naga kin canza ko wani abun akai miki, murguda baki tayi wai kai ya kk so nayi in yi mgn kace bani da kunya sannan nayi shiru kana tmbyr me akaimin ina ruwanka da shiruna ? murmushi yayi ya mik'e bai ce mata komai ba ya fice, ta harari bayansa hade da yin kwafa, yana fita ya khaleel ya shigo dai dai lokacin da jidda take saukowa da ga upstairs ganinshi yasa ta karaso da sauri, gab dashi taxo sannu da xuwa ya khaleel, yawwa sannu, rubayya ki kawo min lunch dina daki, da sauri jidda tace ta bash shi zan kawo maka, ok yace ya fita kitcean ta wuce, sulthana ta tabe baki ta hau sama ta tadda jannat na karatun kur'ani, ta ajjiye kur'anin ta mike tana kallon sulthana, wani kallo takewa jannat din wai meya sameki ? ga shi cen waccen muciyar ta tafi kaiwa mijinki abinci tana matsayin budurwar shi idan kika tsaya sanya xata fiki daraja ni banga amfaninki ba keda mijinki ki xauna wata cen budurwar shi ta dinka yi masa hidima ? ki nemi dabara dan wannan ba ta dace da ke ba, ta fice daga dakin jannat tabita ta kallo hade dayin ajiyar xuciya, sulthana bakisan halin ya khaleel bane canza kaya tayi tai makeup ta fesa turarenta mai kamshi ta nufi kitcean ta hada masa coffee tai bangarensa sallama tayi ya amsa hade da galla mata harara, yarasa gane ina yarinyar nan ta dosa kusa dashi ta anjiye coffee din ta cire hijab dinta kamshin turarenta dayake so ya shaka ta xauna kusa da shi jidda na cen gefen ranta amatukar bace, ta gaishe da ya khaleel ya amsa yana danne dannen wayarshi miko masa coffee din tayi duk da yana fushi da ita haka ya amsa dan baya iya yin xuciya dashi, sannu ya khaleel ka gaji ko ? gama shan coffee din kaci abinci in maka tausa, araxane jidda ta kalleta shima mmk ne yasa ya kalleta yarinya sai kace mai aljanu kullum da salon daxata bullo dashi shi sam bai gane dan jidda takeyi ba,
ya harareta kadan dauko waccen ledar ya nuna mata leda nesa dasu da sauri ta mike tana tafiya a hnkl ya bi ta da kallo ya lumshe ido, jannat kina da tsari da xubi mai kyau hawaye ya saukowa jidda ganin irin kallon daya kewa jannat da sauri da goge hawayen, ledar ta dauko ta dawo kusa da shi ta ajjiye xama tayi ta bude ledar English wears ne masu kyau, da murna tace ngd sosai Allah yakara budi rufe mata baki yayi da hannunsa bana son gdy hannunta tasa ta riko hannunsa gam tana dariyar farin ciki Allah ya saka da alkairi ya tsareka da ga sharrin mutane da aljanuma, yaji dadin adduar ta hade da mmkin tulin yarintar ta, sakin hannunshi tayi, jidda ta mike tamkar xata fadi kasa da kyar ta fice daga dakin murmushin jin dadi jannat tayi aranta tace kadan kika gani idan baxaki daina shigowa dakin ya khaleel ba tana futa tafara tattare kayan ta xuba su a leda ta mike xata fita ya fisgota jikinshi, meyasa daxu baki kawo min breakfast ba ?hade rai tayi tace, sbd banyi niyya ba kara matseta yayi ajikinsa ni kike fadawa mgn son ranki matsar taji tayi yawa, a a ya hakuri plx dan Allah kasakeni, banza yai da ita yana jinta cikin jikinshi yana jin dadin kamshin turarenta dayake shak'a kuka tasaka sannan ya saketa ta dauki hijab dinta tasa dai dai bakin kofarshi ta tsaya bazan kara xuwa dakin kaba, yanayin yanda tai mgn cike da yarinta murmushi yayi har hkrnsa suka fito yanxu kam yarintar ta birgeshi takeyi tana kokarin fita ya riko ta kwabe fuska, "me kikace ? shiru tayi tana kallon gefen shi kamar xata fashe da kuka, baxaki kara xuwa dakina ba ko ? to babu inda xaki nan xakiyi ta zama, zaro ido tayi hade da kwabe fuska, kayi hkr ya khaleel, lip dinta ya kalla ganin yana kallonta yasa ta bata rai plx zan tafi daki ka cikani, kafin ta karasa taji bakin ta acikin nashi ya riketa gam yadda baxata iya motsawa daga rikon da yai mata ba sai da yagaji dan kansa ya saketa ta juya aguje ta fice ya bi bayanta dariya ta subuce masa cikin jin dadi ya xauna shi kam da baya son yarinta yamxu kam yarintar jannat birgesa take tana kuma sashi nishad'i



***********
da sauri ta nufo bangaren su jidda ta hango idonta sunyi jaa tana kara sowa hijab dinta ta kuma fincika, tsaki jannat tayi

Please Login or Register in order to submit comment