You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
na kalle shi nayi murmushi. Zuba hannu Yayi a cikin aljuhun wandon shi yana kallona. Janye idanuna nayi daga kanshi ina kallon Malam Ansar da ya cika ya batse.
"Hammah Khalil ka tafi ka duba halin da Hammah Mohan yake ciki kaji"
"Toh babu damuwa, duk yadda kace haka zamu yi, Baba sai an jima. Kai kuma be careful" ya saka kai ya fice daga d'akin.
"Baba kin gani ko? Hidima suke mishi waye ya sani ko wani abu ne yake shiga..."
Fisge ruwan hannu na, nayi tare da sauka a gadon na shiga tura shi har kofar dakin, ina kai shi gurin na ce mishi.
"Kar na kuma ganin ka a nan idan ba haka ba hmm"
Na nuna mishi hanya tare da banke kofar..
"Mamoon,.kayi hakuri nasan babu dad'i."
"Baba kina ji yana zargina shi din waye shi? Meye na tsare mishi da yake zargina? Ina dalili zai saka Ni a gaba"
"Kayi hakuri" haka tayi ta rarrashinsa, dakyar yayi hakuri, sannan ya shiga ban daki yayi alola da wanka ya fito, tare da gabatar da sallah.
Yana idarwa ya zauna yana kallon kayan da Dan Ba'are ya kawo shi. Flast da ruwan zafi. Sai kayan ciye ciye.
Haka na zauna na ci kadan sauran na turawa baba. Tana ci tana kallona.
"Me yasa meka?"
Kasa magana nayi tare da kasa kallonta.
"Ina tambayar ka? Kasan jikinka ba karfi ne dashi ba, kai asalima baka da nau'in karfin maza, don Allah ka daina saka kanka cikin kasada kaji, ka daina cilla rayuwar ka cikin damuwa, malam Ansar yana da laifi gurin sakawa lallai sai kayi abu dole amma ka tab'a bibiyar me yasa yake maka haka? Sabida yana kaunarka gani yake baka cancanci zama a inda za a tab'a lafiyar ka ba. Don Allah karka tab'a min zuciya, wanda aka yi na shekaru sha ma bai warke ba, idan wani abu ya same ka ba zan tab'a yafewa kai na ba.[7/15, 4:04 PM] RamlatArManga: https://www.wattpad.com/1099611906?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=B2xbg56NQ%2Bj7itiadIMLq5S6mXv9S%2FsKyYdkh0H8PJKgwqgLqD%2Fo961ZM5LierkVHLwx3qEwMnG%2BOkvdE6rc9D1tbKk2fSwjLb0oWove1cVKshUkIo7LVOxrft0MhTCk
🐂🐂BOROROJI🫀🫀
~The Journey of Destiny💔~
Mai_Dambu
Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....
_*SUBSCRIBE*
_DUNIYAR LITTAFAN HAUSA TV_
https://www.youtube.com/channel/UCcAjVQ74qod9_dL0e_AqkiQ
Domin samun labarin masu kayatarwa na Hausa danna Link din nan a sha sauraro lafiya....
BABI NA SHA BAKWAI.
Kwalla ne suka cika min idanuna, na kalli Baba cikin kuka nace mata.
"Amma ko ma yayya ne dole yayi min uzuri, tunda nima mutum ne me rayuwa, taya zai dinga jifana da abinda ya fito bakin shi? Shin wannan adalci ne ko son Zuciya? Baki daya na kasa gane mishi bai da aiki sai gaya min maganar da ta fito bakin shi wallahi ki gaya mishi ya daina ko na kafta mishi rashin mutinci."
Na fada ina share kwallar da sune zubo min,
"Kayi hakuri"
Baki daya malam Ansar yaci uwar rena min hankali, dan yaga bana mishi magana ne wannan karon ya isa haka. Kuma zai ga yadda ake rashin mutunci, sai dai bai gaya min magana ba sai na rama.
Haka na share kwalla na, na cigaba da sauraron Baba, har dare yayi.
Shigowar Mohan da su Dan Ba'are ya sani mik'ewa zaune ina kallon shi, fuskar shi a sake. Kallona yake kamar me cikakken lafiya.
Murmushi nayi mishi tare da nuna mishi gurin zama. Kallona yake kamar yana son gano wani abu a tare dani, amma bai ce min kome ba, tunda ba magana ce yake ba. Sauka nayi tare da nufar shi na kawo shi bakin gadon ya zauna, zama nayi a kusa dashi ina me kallon kayan ciye ciyen da yake dakin na shiga mika mishi ina cewa.
"Ci karka damu Ayya naga ka rame da ba nan Anya Hammah Khalil kana kula dashi kuwa?" Wani kallon banza ya watsa mishi tare da cewa.
"Ba aiki Mohan ya dauke ni ba, dan haka dan banza idan ya dagama yaci abinci idan bai gadama ba ya zauna da yunwa banza dan iska Allah ya baka lafiya kace zaka fito da halin ka cin mutuncin ka zanyi"
Kallon shi nayi cikin kankace idanu nace mishi.
"Wannan cin mutuncin da me yayi kama? Ka saka mara lafiya a gaba da wulakancin meye yayi maka"
Sake hararan shi dan Ba'are yayi yana me dauke kai tare da gyara tsayuwar shi.
Abinda ya faru kuwa ba kome bane, tun suna yara suka da wata muguwar wasa da sukewa junan su, idan mutum ya duka, dai ka sake mishi dundu a baya, shine bayan ya koma gida yana ƙoƙarin su tawo asibitin, kawai Mohan ya ganshi ya duka yana saka takalmin shi ya samu gadon bayan shi ya sakar mishi dundu sai da ya kwara amai. Kuma da ya juya ya saka fuska kamar bashi ba, shine abun yake bashi haushi yake ta zagin shi tun a mota, ya kwashe mishi albarka yakai sau dari tare da jan Allah ya isa kamar zai fasa ihu, domin dai da yaji bayan ya kame kafin ya mike tsaye kai Mohan..kwafa yayi ya kuma ce mishi.
"Dan iska mugun banxa kawai"
"Amma ba na hana ka zagin nan ba?" Kallona yayi sannan yace min.
"Mamoon dundu yayi min a baya fa" .kamar zai fashe da kuka.
Kallon Hammah Mohan nayi,
"Me yasa kayi mishi haka? Kana son ka zama mugu ne dodo me ban tsoro?" Na mishi wani iri da hannuna ina gwalallo idanuna waje. Girgiza min kai yayi tare da kwantar da kanshi yana jin babu dad'i.
"Toh karka kuma kaji" na fada mishi ina kallon Hammah Khalil ina me Cigaba da bashi hakuri.
"Kayi hakuri"
"Shi kanan nazo na zauna kusa da kai?"
Matsa mishi nayi Baba bata ce min kome ba, sai bayan da suka gama suka fita, sannan tace min.
"Karka kuma haka babu kyau"
"Toh ba zan kuma ba"
***
Washi gari sai ga shugaban marasa zuciya. Shi da abokin shi suka shigo d'akin.
"Sannun ku ya masu jikin?" Inji Abokin Hammah ANSAR,
Kallon baya nayi tare da kallon su nace.
"Da sauki" na fada a takaice,
"Ashe baka ji dadi ba"
"Eh"
Yadda nace eh din a takaice Yasaka su shan jinin jikin su, tabbas na shirya musu. Fita baba tayi zata nimo goro.
Zama Mutallab yayi tare da kallon Hammah ANSAR da yake tsaye.
"Hmm! Almamoon mun zo da wani abu me girma bamu sani ba ko zaka yarda da shi?" Ya tambaye ni bayan ya kai aya.
"Ina sauraron ku?"
Gyara zama yayi tare da fara kalkalo min iyayi, ina kallon shi. Kafin yace min.
"Ansar yayi min bayanin waye kai so ina son muyi amfani da wannan damar domin nima maka lafiya?"
Kallon bayana nayi, kafin na kalli gefena, na kuma kallon saman kai na, kafin na sauka a gadon ina leka kasar gadon kafin na ce musu.
"Toh ni dai na nime lafiyar ban gan shi ba"
Na fada ina kallon su. Kafin na zauna.
"Ya kake mai da kome da wasa ne? Wannan batun lafiyar kace da? Kuma zaka mai dashi wasa? Ai ba wasa da lafiya"
"Wai ma tukun waye ya gaya maka bani da lafiya kazo ku nima min lafiya? Ku Allah ne?"
"A'a Almamoon taimako bai zama tashin hankali ba" ya faɗa yana kallona.
"Toh zakewa da shishigi ba tashin hankali bane?"
"Almamoon karka mana rashin kunya" inji Malam Ansar,
"Sai dai na muku bindin akuya, karshen rashin kunya"
"Amma kai babu manya ne a gidan ku?" Inji Mutallab,
"A'a yara ne a gidan mu irin ku."
"Kai waye ne da zaka gaya mana bakar magana?" Inji Malam Ansar,
"Toh kayi hakuri zan gaya maka farar magana yadda zaka ci ka koshi"
"Kai"
"Dalla sauke muryan ka, ba zaka min tsawa ba ana zaune lafiya dan ban cika gane seven da seventeen ba, zaku iya cigaba bujejjunku iska kar na kuma ganin ka"
Na fadawa malam Ansar a gadarance,
"Kai kasan waye kake gayawa magana?"
" Na sani mana? Waye ban da namiji a gabana, na miji ne a gabana nake gaya mishi maganar da tafi to bakina! Ko bai kai bane na gaya mishi?"
"Ka kai ka isa idanun ka ya bude ana bin bayanka ba, dole kartin maza sun lalata maka rayuwar ka, sun koya maka mugun nufinsu. Allah ya dawo da kai kan hanya domin nasan tunda suka san kai mata maza ne shi kenan sun lalata ka"
"A'a sai dai maza mata ba mata maza ba, Sharrin da kai min kuma ya kare kalau ba zan maka baki ba Allah ya shirya ka shiryar jigida"
"Almamoon kaf garin nan baka da gata sai ni" ya faɗa a fusace,
"Ayya sabida ka fado cikin mutane ni kuma na fito kalgo, ko nace na diro daga sama, masu asali." Na gaya mishi ina kallon fuskar shi.
"Ni kake wulakantawa sabida Mahaukaci wallahi sai na hana ka sukuni gaka ga mahaukacin nan"
"A'a akan me zan wulakanta ka ni din banza, kawai gani nayi rayuwar da ka dauka bai dace bane, amma kuma kato da kai na wulakanta ka, abin dubawa ne" na fada ina kallon farcena.
A fusace ya taso min, na d'ago kai ina kallon shi. Yana zuwa ya kifa min mari. Dai-dai shigowar Dan Ba'are, kura mishi ido nayi tare da jin kwalla yana cika min ido. Cikin wani irin zafin nama ya nufi malam Ansar.
"Kyale shi!" Na fada ina shiga tsakanin su.
"Ban san me yasa kake haka ba. Amma ina son wannan ya zama na farko da na karshe, Yaron nan ba bawanka bane da zaka addabi rayuwar shi."
"Ina ruwanka? Ni na kawo muku shi. Kuma Ni nake da hurumin tafiya da shi kai har ka isa ka gaya min magana akan shi, wallahi sai na dauke shi."
Dan Ba'are zai magana na hana shi, tunda nima ba maganar zanyi ba, haka ya fita a fusace. Suna fita dan Ba'are ya ce min.
"Meye alakar shi da kai?" Ya tambaye ni yana tsare Ni da ido.
"Malamina ne kuma na zauna a gidan shi"
"Shine yake maka hauka kamar shi ya haifi ka." Shima ya tadda min nashi rigimar, kamar zai dake ni har da cewa Ni na bar Malam Ansar.
***
Washi gari.
Kai malam Ansar bai da zuciya domin da asuban fari sai gashi, duk sai ya bani tausayi. Nuna mishi kusadani nayi, domin na fahimci yana cikin kad'aici. Tunda ya zauna ya kalle ni.
"Almamoon" shiru yayi tare da tagumi.
"Me yasa kake wulakantani? Almamoon duk wanda yace yana son ka ba makiyin ka bane, Almamoon ka duba girman kaunar da nake maka wallahi jiya dakyar na rintsa."
Ya fada yana kallon fuskana.
"Malam kaga"
"Ina laifin Hammah ANSAR" ya faɗa kamar zai yi kuka.
"Amma kasan dai ni din ba mace bane?"
Sauka yayi daga gadon ya rike hannuna.
"Ina masifar kaunar ka, kuma zan iya kome domin ka sami lafiya Mamoon kawai aiki za a maka akan matsalar jinsin ka a dawo da kai jinsin mata, kaga zaka haihu zaka yi rayuwa irinta mata, zaka zama."
Dariya ya bani sannan na kalle shi. Kafin na kuma kwashewa da dariya, domin kuwa mamaki yake bani.
"Na zata hauka kake ashe turu kake bukata, Allah ya shirya ka. Idan akan jinsi ne ba zan tab'a yarda a yi min aikin ba"
Matse hannuna yayi tare da kallon cikin idanuna.
"Kayi hakuri Hammah ANSAR, kai Yaya na dauke ka ba wai soyayya ba, Hammah ANSAR soyayyar nake maka ta yan uwanta ka ce, na gaya maka ba yau ba, ni ba kamar yadda kake tsammani bane"
"Na yarda zan zauna da kai haka. Don Allah ka so ni"
Tausayi ya bani, na rike hannun shi.
" Ba zan iya wannan lamanin ba"
Na gaya mishi ina me dauke kwallar da ta cika min idanuna.
Rarrashina yake amma bai tab'a sani jin ko zan iya yarda da bukatar shi, kawai dai na dai ki amsa mishi ne, haka ya gama abinda ya ga zai yi, har ya fita bayan ya tunatar dani an kusan komawa makaranta.
*** Kwana hudu a tsakanin aka sallame ni,
Muka koma tunda daga bakin kofar nake, kallon gidan kamar ka shekara ban gidan. Yana tsaye sanye da riga da wando na Adidas, kallon fuskar shi nayi naga ya kara kyau, shima kuma ni ya kura min ido. Da murmushi na isa gaban shi ina dariya kallon shi.
"Hammah Mohan"
Wani irin kallo yake min daga kasa har sama. Tare da bina da ido, sake baki nayi kawai ina kallon shi.
"Baba ga Hammah Mohan" na fada mata a sanyayye,
"Ayya Allah ya baka lafiya" riko hannun shi nayi, shima sai bina yake da idanu. Haka na kai Baba d'akina tayi sallah tare da zama ta ga gidan, bata bar gidan ba sai da Magarib.
Lokacin da na raka ta, dake ban kawo ana bin bayana ba, kawai ina juyawa nayi karo da mutum.
"Wayyooo" na tafi da baya zan fadi. Hannun shi naji a bayana zuwa k'uguna.
Kura min ido yayi yana kallon yadda nake zare idanuna.
"H...a...m..m..a..h...Mo...h...a..na" na kira sunan shi a rarrabe, ina zare idanuna, ga wani lugude da nake ji a raina, tare da rike rigar shi, kafaffuna suna dangafe da kasa.
Sake ni yayi na zube da timmmm, na kwalu da kasar.
Yayi tafiyar shi, tunda ya shiga dakin shi ya rike kanshi, yana wani irin jiri yake daukar shi kamar zai fadi,
Kwanciya yayi tare da lumshe idanun shi.
Dakin na shiga na kwanta, can na tuna dashi na shiga dakin shi, yana kwance yana juyi, ina shiga na d'ago shi da sauri ina ƙoƙarin d'aga shi. Ya tashi zaune,
"Sannun Hammah Mohan"
Mik'ewa nayi tare da tab'e goshinsa, kafin na fita na dubo mishi magani, ya sha tare da kwanciya. Zama nayi akan shi ina shafa kanshi har barci ya dauke shi.
Tashi nayi tare da fita.
***
Satin farko na koma makaranta, sai dai kuma tunda na koma makaranta bani da lokacin shi sosai. Kullum ina dawowa a gurguje zan kula da shi na.
Sai dai haka kawai nake ganin kamar akwai wani abu da yake faruwa da Hammah Mohan....
*Kuyi hakuri bani da cikakken lokacin kai na ne, kunsan sallah ya kusa ga masu yawan rai, don Allah ku min Uzuri Insha Allah sai bayan sallah. Yau ma dakyar na muku wannan.*
#Mai_Dambu......
[7/18, 8:39 AM] RamlatArManga: 🐂🐂BOROROJI🫀🫀
~The Journey of Destiny💔~
Mai_Dambu
Sadaukarwa ga
Sajidah Nijar
Samirah Nijar
OumNass
Azizah Hamza....
_*SUBSCRIBE*
_DUNIYAR LITTAFAN HAUSA TV_
https://www.youtube.com/channel/UCcAjVQ74qod9_dL0e_AqkiQ
Domin samun labarin masu kayatarwa na Hausa danna Link din nan a sha sauraro lafiya....
BABI NA SHA TAKWAS.
A sanyayye na shiga cikin dakin yana tsaye kamar ba zai shigo ba, fita nayi na shigo dashi dakin ina cewa.
"Zauna a kan na shiga ban daki na fito."
Na zaunar dashi na shiga ban dakin na gama uzurina na fito, sannan na dauko mishi maganin shi, na nutsu na tofa mishi addu'a kafin na mika mishi, wani irin duba yakewa maganin cike da kyankyame.
"Ka sha maganinka ne" na fada ina tura mishi maganin a bakin shi, dakyar ya sha yana yunkurin amai, sororo nayi ina mamakin shi. Dafa goshinsa nayi naga ya rintsa idanun shi da karfi, alamar baya son na tab'a shi. Janye hannun nayi ina kallon shi, koda na dauko wanda nake shafa mishi ma, kamar ala dole nake mishi.
Ina gama shafa mishi nace mishi.
"Kayi hakuri kaji magani ne da alamun kafara samun lafiya shi yasa baka son ina tab'a ka, amma Insha Allah idan ka samu lafiya zan tafi na koma inda na fito, sabida kai nake nan" na fada ina shafa mishi ayatul shifa a kafar shi, kwalla na zuba akan gwiwar shi, ina gamawa na mike na mai da maganin sannan na fita niman abinda zamu ci.
Ina gamawa dan Ba'are yana shigowa gidan shi da Malik. Abincin na gabatar musu, kallon Hammah Mohan suka yi da yake tsaye astep ya kura musu ido, yaki saukowa. Mik'ewa nayi cikin rawan jiki zan tafi gurin shi Dan Ba'are ya dawo dani.
"Rabu da dan iska kar yazo taci ya zauna da yunwa dan Ubanshi"
Juya nayi gurin Hammah Mohan Gandhi tsaye, kan shi a sunkuye.
Kwace hannun nayi tare da nufar shi, yana tsaye bai matsa ba, gaban shi na nufa na tsaya tare da kamo hannun shi muka tawo gurin cin abincin. Na ja mishi kujera ya zauna, sannan na zuba mishi abincin. Kallon abincin yake yana kallon nasu, kamar ba zai ci ba.
"Banza dan iska karka ci dan kaniyar ka" haka yayi ta juya abincin sai da na hakura da cin nawa na fara bashi, yana yatsina fuska.
"Ayya abincin babu dadi ko?" D'ago kai yayi yana kallona, kafin ya ture hannuna ya shiga amsa dan ya lura da yadda kwalla yake cika min idanuna, sosai yake cin abincin yana gamawa ya mika min na kara mishi, shafa kan shi nayi tare da cewa.
"A'a ba zaka ci dayawa ba, kaji sha ruwa haka ya isheka kana magani ba a son kana cin da ya fita Muslunci."
"Ai da kin bashi, tunda shi ya zama tumbi iza hana gaya rub'a."
"Auchewww" inji Dan Ba'are, yana kallon Hammah Mohan, cikin takaici da zafi.
"Lafiya?" Na tambayr shi a rud'e.
"Ban da wannan dan iskan zai karya min yatsu shege ciwo bai saka ka daina mugunta ba, Mahaukacin banza kawai" ya faɗa lokacin da ya tashi a kujeran yana dingishi.
Rike kunnen shi nayi tare da zaro mishi ido, kawai sai ji nayi ya dauke ni cak ya daura akan cinyar shi da hannu daya. Ya saka ya matse ni.
"Sake ni! Kyale Ni bana son haka" na kwace kai na ina ajiyar zuciya. Make keyar shi nayi tare da kwashe kayan da aka ci abincin. Na nufi kitchen da shi.
Haka dai yanayin shi yayi ta sauyawa har Hammah Khalil ya bar garin, ina kuma kula dashi. Wannan karon karatu yayi zafi bana iya dawowa da wuri sai Malik ya je ya dauko ni, ga Malam Ansar ya taso ni gaba. Kamar zanyi kuka haka yake disgani a gaban jama'a. Bai tab'a sani naji a raina zan mishi yadda yake so ba.
Yau ma da wuri na shigo makarantar, na nufi ajin mu. Ina shiga na same shi yana karatu, dan haka na shiga tare da sallama.
"Zoka fita min a aji"
"Malam kayi hakuri na san sai bakwai da rabi kace zaka..."
Ban idar da abinda yake bakina ba ya kifa min mari, tare da daka min tsawa.
"Fitar min a cikin ajiye, dan iskan Yaro kawai" ya turo ni waje tare da rufe min kofa, gashi ana wucewa tare da kallon mu,haka na juya na bar makarantar sabida ko ina na zaga dariya ake min, danne kuka na nake har ba samu abin hawa, na nufi Jacader. Ina isa na samu sun bude min gidan, ina shiga na taradda sabon tashin hankali. Domin Matar ranar ce ta zo, ina shiga na same shi kamar Almajiri a gabanta yana zaune.
"Sannun da zuwa Hajiya" na fada ina danne kuka na,
"Takowa tayi tare da kifa min mari." Sai da na zube kasa.
"Akan me zaka na barin shi a gida bayan kasan bai da lafiya? Toh wannan ya zama na karshe kar a kuma, ga kuma maganin nan ka tabbatar ka yi amfani dashi maza dauka ka kai daki" jikina yana rawa na kwashe kayan na nufi sama dashi,
"Kai kuma a haka zaka kare, saura kiris burin mu ya cika ba sai kana raye zaka iya taimakawa iyayen ka ba, idan ka isa ka hana mu kashe Ubanka da ita mahaukaciyar Uwarka" ba iya Ni na kad'u ba hatta shi dai da naga ya girgiza, balle ni domin a haukace yake kallon shi, ai kuwa ta shiga marin kyakyawan fuskar shi, da sauri na iso gurin tare da had'a fuskar shi da kirjina, ina bata hakuri.
Nima duka na ta shiga yi tana gaya min.
"Idan baka min aikina ba, tabbas sai na kashe ka kai ma bayan na samu ka kashe shi matsiyata."
Can kuma ta mike tare da ajiye min kudi tana faɗin.
"Kayi hakuri raina ne ya b'aci ka dauka kayi min amfani da kome zaka gan shi a rubuce,kaji yaron kirki ka kula min dashi zan maka babban kyauta."
Gyada mata kai nayi ina kallon ta, bayan ta gama ta fita. Zama nayi a gurin na fashe da kuka, sosai. Sabida yau iya maruwa na maru.
A hankali na mike tare da riko hannun shi, muka nufi sama, yana kallona, muna shiga ya ga na fidda kayan baki daya, na zazzage shi a kasa. Daidai hancina yana zubda jini.
D'ago Ni yayi yana me lakutan hancin nawa.
"Kaga babu kome kawai jini ne yake diga."
Na kwace kai na, tare da kwasar maganin kaf na nufi ban daki dashi na juye a masai na tura musu ruwa suka tafi, sai wata yar karamar mutunmutumi a kwalba, ta rubuta.
*A saka a kasan gadon shi ko a yaga rigar katifar shi a cusa maganin lafiyar shi ce*
Dauka nayi tare da nufar bayan gidan yana biye da ku, na nimo fetur na watsawa kwalbar wanda aka soka allurai a jikin abin na watsa mishi fetur na kyasa Ashana. Na jefa bayan na yi kabbara, kwalbar ce ta fashe tare da wani irin bakin hayaki ya tashi sama, ihu hayakin yayi wanda ya haifar min da wani irin ciwon kai da daukewar gani na, na tafi zan fadi yayi maza ya taro ni, daukata yayi tare da nufar cikin gidan dani, da sauri.
Yana isa dakin kasa ya kwantar dani. Yana kallon yadda gefen fuskana ya sha mari, shafawa yayi. Yana kallon yadda nake kwance. Tashi yayi ya ma rasa me zai min, kawai ya fita can sai gashi da ruwan sanyi ya samu fuskana ya juye min baki daya, a firgice na farka tare da dafe goshina, kai na yana mugun sarawa.
Zama yayi tare da riko hannuna yana kallon yadda nake ajiyar zuciya.
Tashi nayi tare da nufar ban daki na, hada ruwan wanka, sannan na cire kayana na fara, tunawa nayi ban dauko wani abu ba, na fito daure da towel a kirjina. Da sauri na nufi inda dama kayana yake na dauki yar abin da zan dauka na na koma ban d'akin.
"Karka je ko ina ganin nan fitowa"
Na gaya mishi ina turo kofar, na cigaba da abinda nake, lokacin da na fito kusa gashina me bala'in yawa ban daure shi ba, na fito haka zube a kirjina, zama nayi ina tattara su,sannan na daure su baki daya, na kuma gyara shi yadda ba zaka tab'a dauka ina da sumar a kaina ba.
Kallon inda nake bai yi ba, alola na koma nayi sannan na zo na sashi yayi.
A tare muka yi sallah, muna idarwa na fito falo da niyyar niman abin da zamu ci na rana, sai ga Malam Ansar ya shigo gidan, daidai ba fito ina gyara wandona, kallona yake cike da tashin hankali lokacin da Hammah Mohan ya fito zip din gaban wandon shi a bude. Rigar shi botir din a balle. Cikin fusata ya nufe ni tare da zare belt din wandon shi. Wani irin mugun tsoro ne ya shige ni dan ba a tab'a duka na ba, kawai ya dage ya tsulla min belt din shi a gadon bayana sai da na daka tsalle, lokaci guda ya haukata Ni da duka.
Rarrafawa nayi ina ihu tare da cewa.
"Don Allah Hammah Mohan ka taimake ni" na nufi ne shi tare da k'amk'ame kafar shi. Jikin yana rawa, tare da kerma ilahirin jikina b'ari yake kamar za a zare ruhina, sabida yau ne karon farko da aka zane ni ban san dukkan ba.
Jin bulalar bata kuma dauka a jikina ba ya sani kara k'amk'ame shi ina kuka me shiga jiki. A hankali ya janye kafar shi daga rikon da nayi mishi, ya murɗe malam Ansar da bulalar a wuyar shi kamar zai kar shi, idanun shi sun yi wasu irin jajjur, jijjiyar goshinsa sun mike rad'a rad'a, jikin shi wani irin rawa yake kamar an saka mishi mazari.
Kakarin malam Ansar ya sani, d'ago kai na, ganin yadda Hammah Mohan ya shake shi, da sauri na mike.
"Sake shi ya hakuri bar shi na yafe mishi." Na fada ina kuka.
Sake shi yayi ya fadi, sannan Hammah Mohan ya dawo bayana ya rungume ni yana kallon Malam Ansar. Tare da mishi gargadi da idanun shi da suke cike da b'acin rai.
"Wato dan na hukunta ka shine zaka saka ya kashe ni?"
Bude baki nayi zan yi magana ya juyar dani muka koma cikin dakin. Zama nayi a bakin gadon ina kuka kamar me, ban san ya aka yi ba
Book Chapters
Chapter 13
Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45