Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta lallasheta,

Wayam tagani ba Saudat ba fadawanta ba alamarta,
Alamar tayi zuciya kenan tabar asibityn."

********************

Sai wurin k'arfe goma na dare dakaru suka Dura k'auyen su safna,

Rarraba k'afa sukayi gaba d'aya suka zagaye k'auyen,
Fetur suka fito dashi da ashana karon farko suka shiga kunnawa runbun hatsin da duk sukaci karo dashi,
Anan take garin ya d'auki hasken wuta, tanaci bal bal,
Tin shigowarsu hankalin mutanen k'auyen ya tashi domin yanda sukaji shigowar motocin suka tabbatarwa da kansu ba lafiya,
duk Wanda yake bacci aka tayar dashi yara k'anana iyayensu suka goyasu a bayansu sukayi tsaitsaye suna jiran mutuwa ko rayuwa."

Hakan gidansu safna Wanda yake zagaye da dakaru,
Idon safna biyu domin batayi bacci ba gabanta kawai takeji yana fad'uwa yarima take gani yana mata gizo a idonta, anan take ta tabbatarwa da kanta yana cikin mawuyacin hali."

Sautin maganar mutane taji a bayan d'akinta suna fad'in mu cinawa gidan wuta kawai kowa ya k'one,
Wani Mai kakkausar murya yace "gimbiya Saudat tace "na haye yarinyar na moreta son raina, snn daga k'arshe mukasheta."

Idonta ya cika da hawayen tausayin kanta domin, ta tab'ajin sunan matar yarima Saudat a bakin Safwan,
Wani lokacin suna tare da yarima safwan yakira wayar sa,
Yake shaida masa da cewa ya ina ne,
GIMBIYA SAUDAT takira wayarsa tace tajita a kashe,
tace ya kirata tanason zatayi magana dashi,
A lokacin dogon tsaki taga sauban yaja bai bawa Safwan amsaba illah ya kashe wayar gaba d'aya ya ajiye,
anan ta fahimci matarsa ake nufi
Cikin ranta tashiga fad'in Ashe sunanta Saudat, tin daga lokacin sunan Saudat ya tsaya mata a rai,
Duk lokacin da taji an anbaci sunanta takanji gabanta ya fad'i ta rasa dalili hakan da takeji,
hannu tasaka tashare wayen fuskarta ta mik'e tsaye, tanufi k'ofar fita,
Tana fad'in wato itace ta turo a kasheni kenan burinta ayi mun illah a rayuwa mai natare mata?" Hasalima bata sanniba ban santaba."

Tanajin muryar su a waje suna shawar yanda zasu shigo cikin gidan,
Cikin sand'a tabud'e k'ofar d'akin tafita tanufi d'akin baba Wanda suke tare da inna idonsu biyu sunajin duk abinda ake fad'a a waje ko wanne sai zarar ido yakeyi cike da tsoro,
Ganinta da sukayi Baba ya taso ya rungumeta yasaki kuka itama safna kuka takeyi domin sun rigada sun sadakar lokacin mutuwarsu ne yazo,
Inna sai fad'I takeyi muna zaman zamanmu lafiya muka d'aukarwa kanmu bala'i da masifa Safna ke annoba ce a rayuwarmu."

Jin anfara durowa cikin gidan, yasaka inna yin shuru, bakinta kawai ke rawa."
Hannu Baba safna ta Rik'e cike da zafin rai tace "baba mugudu bana son rabuwa da Kai."

Girgiza kai Baba yayi yace "Safna ta ina zamu gudu bayan gasu nan suna shigowa cikin gidan da Zarar munfita kashemu zasuyi."

Safna tace "baba idan bamu fita a gidan nan ba cinnawa gidan wuta zasuyi duk muk'une a cikinsa,

Baba zaiyi magana wani k'arfi yazowa Safna ta fisgo hannun Baba suka bud'e k'ofa suka fito inna tana biye dasu a baya,
K'atti majiya k'arfi hud'u suka gani a cikin gidan sun juya baya sunajiran shigowar Sauran,
Cikin sand'a safna take Rik'e da hannun Baba sukabi ta bayansu suka nufi k'ofar baya sukafita, Wani irin ihu inna tasaki a lokacin da ta taka k'usa a k'afa, Wanda ya hankaltar da dakarun inda suke."
Suka nufo wurin inna tana kwance rik'e da k'afa,
Safna tana rik'e da hannun Baba sai gudu suke shek'awa."

Ai kuwa dakarun sukace gata can ta gudu,
Suka dafawa safna,
Gudu kawai sukeyi dakaru suna biye dasu a baya da makamai a hannu,
Baba ya fisge hannunsa daga na Safna sakamakon gajiyar da yayi da gudu ji yakeyi kamar numfashinsa zai d'auke,
Ya kalli safna hawaye suna zuba a idonsa yace "safna kiyi tafiyarki Allah zai taimakeki zai tsiratar dake a duk inda kika tsinci rayuwarki, kibarni su kasheni domin baxan iya kub'utar DA kaina daga garesuba, bazan iya aikata komai ba, Allah yayi maki Albarka,
Ki mik'e kada ki karya kwana a kan hanya kike, zatayi magana kenan ta hango dakaru sun kusan zuwa wurinsu, a lokacin Baba ya zube ya d'auke numfashi,
tanaji tana gani tabar Baba a wurin ta keci daji da gudu,
Gudu takeyi suna biye da ita a baya jefa k'afa kawai takeyi a cikin daji batasan inda takeba ga duhun daji."


*Wayyo safna*😭😤







*Mrs Ana's Bawa*✍
[9/9, 7:43 AM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 28*






****** " Gudu take shek'awa Idon rufe jefa k'afa kawai takeyi a duk inda tasamu hanya, Wanda takejin zugin zafi k'afarta kasancewar ba talkami a tare da ita,
Wani irin k'aton macije tagani ya tashi tsaye a gabanta Wanda girmansa baya misaltuwa,
Wani irin ihu tasaki ta zube wurin a some."

Sautin ihunta yayi dai dai da farkawar Sauban a kan gadon Asibity, babu abinda yakeji a kunnensa sai sautin kukan safna tare da ihunta da ya farkar dashi."
Waige waige yakeyi akan gadon asibityn domin yakasa barin jin sautin a kunnensa,
Hajjah ta taso tanufoshi tana fad'in "Sauban ka farka me kakeso?"
Girgiza Kai yayi alamar baya son komai, ya lumshe idonsa hawaye suna zuba a gefen idonsa."

Kallonsa takeyi cike da mamakin ganin hawaye suna zuba a idonsa, yaushe rabon da taga hawayen sauban tin yana k'arami, KO a lokacin ba komai yake sakashi zubar da hawayeba,
Sai gashi yanzun da girmansa yana zubar da hawaye."

Matsawa ta kumayi a gefen gadonsa tana share masa hawaye tana fad'in "magaji meyake damunka?"
Me kakeso?"
Kukan me kakeyi?"
Girgiza mata kai yayi alamar ba komai hawaye sukaci gaba da zuba a idonsa."

Babu Neman da dakaru basuwa safna ba a cikin dajin amma basu ganta ba wata alamarta."

ai kuwa Sai k'ara kutsa Kai sukeyi cikin dajin, da manyan fito masu hasken gaske a hannunsu,
D'aya daga cikinsu yaji wani abin ya sareshi a k'afa, wani irin Ashar yasaki ya juya domin ganin Ko meye wani irin k'aton maciji yagani ya nad'e wuri d'aya,
ya kuma kai masa Sara a cinya,
Ihu yasaki ya d'aga murya yana fad'in ku gudu kada ku karaso maciji,
ai kuwa anan take kumfa yashiga zuba a bakinsa ya fad'i wurin a macce,
Sauran dakarun sunajin hakan suka juya a guje, macijin yabi bayansu shima suna gudu yana gudu yana biye dasu a baya yana masu rakiya sai da yayi nasarar kashe mutum biyu a cikinsu snn saura suka tsira."

Koda suka shiga cikin k'auyen suka shiga cinawa gidaje wuta k'urumus suka k'one gidansu safna tare da makotansu snn suka shiga mota sukabar k'auyen cike da bakin cikin mutuwar yan uwansu."

Mutan gari sunajin tafiyar tasu suka firfito suna kuka domin ba k'aramar b'arna akayi masu ba,
Ank'ona masu rumbun abinci ankashe masu shanu wasu sun rasa rayukansu me sukayi masu?
Suwaye suka aikata masu hakan?"
Daren ranar gaba d'aya garin basuyi bacci ba, babban tashin hankalinsu gidajen da aka k'ona daga ciki har da gidansu Safna Wanda a yanzun ya zama fili,
Kuka suka fashe dashi domin sunada ya k'inin har mutanen dake cikin gidan an k'onasu sun mutu."

Yanda sukaga dare hakan sukaga safiya,
Koda safiya ta waye duka garin ya cika da jama'a ana masu jaje tare da amsar gaisuwa,
Acan bayan gari aka hango inna tafe tana jan k'afa fuskarta duk tab'aci da jini ba hijabi bare d'an gwali akanta,
Ai kuwa da sauri aka nufota aka rik'ata aka zaunar da ita,
Ruwa aka bata tasha jama'ar gari suna fad'in Alhmdulillahi Allah ya kub'utar DA lnno ta tsira, cikin muryar kuka tace "dukanmu mun tsira harda malam da Safna domin kuwa su guduwa sukayi,
Ta kuma fashewa da Kuka tana fad'in Safna Annobace a garin nan ranka ya dad'e duk ita ta Janyo mana wnn bala'in."

Maigari yace "subahanallahi Allah ya kyauta, ba Wanda ya janyo mana duk abinda yasamemu daga Allah ne bama d'orawa kowa laifi,
Alhmdulillah tinda sun tsiratar da rayuwarsu Allah ya tsaresu a duk inda suke Mun san zasu dawo garemu komai daren dad'ewa."

Anan sukaci gaba da amsar gaisuwar wad'anda suka mutu tare da jajen shanun da aka kashe."

***************

Cikin wata bunka ta farka ta tsinci kanta a cikinta, gefenta akushine Wanda yake d'auke da waina da miya da manshanu,
Wata mata tagani 'yar fillo irinta sanye da kayan fulani irin nata zaune a gefenta Tana kallonta tana murmushi,
a k'allah matar zatayi shekara 40."

Murmushi safna tasakarwa matar tare da k'ara waigawa domin ganin inda take,
Matar tace "sannu Safna har kin farka."

Zaro ido safna tayi tana mamakin a Ina take? Wacece wnn?" Ya akayi tasan sunanta?"
Anan take komai yadawo mata sabo cikin razana ta motsa tana neman ta firgita, tare da kallon hannunta tana fad'in macijin ya sareni ko?"

Murmushi matar tasaki tace "bai sarekiba ki kwantar da hankali,
Ta mik'a mata Akushin dake d'auke da waina tace 'ga abinci kici."

K'amshin abincin ya daki hancin safna a nan take cikinta ya k'ulle akan yunwa ta tina da rabon ta da abinci har ta manta, ta karbi abincin ta Faraci, citakeyi tana lumshe ido domin ba kad'an takejin dadin abincin ba,
Sai da ta cinye wainar gaba d'aya snn tasha ruwan pure water dake ajiye a gabanta,

Murmushin matar takeyi tana kallon safna cike da tausayi,
Itama safna kallon matar takeyi, tana tinanin a ina tasan wnn fuskar tabbas ko a inane tab'a ganin wnn matar kuma tasanta sosai."
A mafarki wata zuciyar ta fad'a Mata,
Tabbas a mafarki kika santa anan kike ganinta, da zarar kinshiga damuwa ita ke zuwa tana lallashinki tare da kwantar maki da hankali."

D'aga kai tayi ta kuma kallon matar wacce take sakar mata murmushi tace "Safna kin tinani?" Kin tina inda Kika sanni?"

hawaye suka soma gangarowa safna ta taso tazo gabanta ta durkusa tace "Inna bazan tab'a mantakiba domin kina taimakona a duk lokacin da nafad'a cikin k'unci da damuwa,
Ke wacece?"

Murmushi matar tayi ta dafa kan Safna tace "zakisan KO ni wacece idan lokacin sanin yayi, kafin nan kitashi kitafi domin akwai sauran k'alubale a rayuwarki,
Ta nuna Mata wata hanya tace "kibi nan kiyitafiyarki domin tsiratar da rayuwarki,
Snn kiya wai ta Addu'a a a duk halin da kika tsinci kanki a cikinsa sai wata Rana."

Share hawayen fuskarta safna tayi, tayi matar godiya,
Matar ta bata silifas tasaka Wanda tanemi zugin zafin da takeji a k'afarta ta rasa,
Snn ta nufi hanyar da aka nuna Mata tafara tafiya."

Tafiya takeyi sosai tanayi tana hutawa saboda gajiya har yamma ta Mata a kan hanya,
Hakan take tafiya cikin daji, batare da wani tsoro ko fargaba a tare da itaba,
Kwatsam ta ganta a tsakiyar hanya akan wani babban titi wanda motoci suke wucewa da k'arfi ba batare da sun tsayaba,
Wani Mai sayar da abinci ta hanga a can tsallaken titi taji cikinta yayi kuka alamar yunwa takeji ga kuma kishirwa,
Hawaye ta share a idonta tana "fad'in Allah Sarki Baba Allah ya jik'anka ya gafarta maka.

Ta mik'e tsaye tanufi wurin Mai sayar da abincin,
Tanaso ta k'etara titi tsoro takeji saboda yanda taga motoci suna wucewa da gudu, sai tazo ketarawa sai kuma ta dawo baya tana sharar hawaye,

A can tajiyo jiniya tajuya ta hango motocine tafe wad'an da basa da iyaka, cikin zafin nama ta nufi kan titin da gudu tana fad'in kafin ku k'araso na k'etara,
Ai kuwa sai dai taji a d'auketa da mota ta fad'i a tsakiyar titi jini yana fita a hancinta da bakinta."

Da sauri motocin suka taka burki suka tsaya,

Wata kyakkyawar macce wacce hutu ya zauna a jikinta 'yar birni 'yar gayu tana sanye da glass a fuskarta sai k'amshi take zubawa wacce shekarunta bazasu wuce 37 ba, tabud'e mota tafito ranta a b'ace take kallon direbanta tana "fad'in yahuza baka ganine ko idonka a makance yake kadiba kagani aikin da akayi d'an Adam ba dabba bane."

A nan take Tabawa escort d'inta masu take mata,baya umurni tace "ku dauketa kusakata a mota mutafi asibity da ita."

Cikin sauri aka tallabi safna aka sakata a mota suka d'auki hanyar babbar asibity dake zaman kanta a cikin garin Adamawa."




*REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 29*






******* A lokacin da aka nufi asibity da Safna ba rai bare numfashi a tare da ita,
Kai tsaye Emergency aka nufa da ita cikin gaggawa likitoci suka k'arb'eta suka duk'ufa a kanta domin ceto rayuwarta da tsayar da jinin dake fita a hanci da bakinta."

Sosai hajiya LAILA ta girgiza da ganin yanayin da yarinyar tashiga, danko fuskarta bata tsaya ganiba hankalinta a tashe yake matuk'a."

Hajiya laila mace ce mai mai tausayi mai son 'ya'ya,
haihuwarta d'aya a duniya 'yarta d'aya macce mai suna *SUHAILAT* wacce ta b'ata tin lokacin da ta haifeta bikin sunanta kawai akayi washe gari aka wayi gari babu ta ba alamarta tab'ata."

B'acewar da har yanzun ba labarinta bare a san dalilin b'atan nata,
wacce a kullum hajiya laila take kukan rashin 'yarta kwaya d'aya tilo wacce take tunanin itace kwanta a duniya, tun daga gareta KO b'atan wata bata kumayi ba, amma sai dai tanaji a jikinta Suhailat d'inta bata mutuba, tana raye domin tana yawan mafarkin 'yarta ta girma tana cikin mawuyacin hali."
A kullum Addu'a takeyi Allah ya bayyanar mata da tilon yarta cikin k'oshin lafiya"
Cire glass din idonta tayi ta share hawayen dake zuba a idonta,
snn ta mayar da glass din a fuskarta,
takoma cikin mota ta zauna tare da jinginawa akan kujera,
Wayarta ta d'auka kira mijinta Alhaji *HABIB SANI NAIRA*,

*RINGING* d'aya zuwa biyu Alhaji Habib ya d'auka, a lokacin yana office suna mitting tare da yaransa akan cigaban da aka samu a kanfaninsa,
Yana ganin kiran nata Saida yasaki murmushi ya kalli wayar,
Snn ya tsayar da maganar da yakeyi,
Snn Ya d'auki wayar , Cikin so da k'aunar matarsa, kuma Amaryarsa yake fad'in "Amarya bakya laifi koda kin kashe d'an masu gida, da fatan kin isa lafiya."

Murmushi tasaki tana fad'in "Alhajina akwaika da tsokana shekara goma shatakwas kake kirana da Amarya,
Da ace Suhailat tana raye aida munfara shiga sahun iyaye dan kuwa kasan kamar yanzun mun sami suriki."
Murmushi yasaki domin shi kansa ta tayar masa da dafin b'atan 'yarsa wacce tafi soyuwa a ransa,
Itama yanzon yasan tashiga cikin damuwar domin yasan da zarar akayi zancen suhailat sai ta zubar da hawayenta,
Gyaran murya yayi yace "Amarya kamar yanda yake kiranta meyafaru dake ne?" domin najiya a jikina kina tare da matsala."

Share hawayen dake zuba a idonta tayi, cikin da sanshinyar murya tace "Alhajina muna kan hanyar tafiya,
munzo gaf da fita cikin gari muka samu matsala,
Yahuza direba ya bige wata yarinya 'yar fulani tana sanye da kayan fulanin a jikinta , a lokacin tana k'ok'arin k'e tara titin, yanzun hakan muna Asibity."

"Subahanallahi Alhaji Habib Naira yace,
Tare da mik'ewa tsaye a firgice,
yayiwa yaransa Alama da hannu akan sutafi sai ya k'ara nemansu,
Cikin Sauri yanufi hanyar fita , Da waya a kunnensa yana fad'in wacce asibityn kuke a halin yanzun?"
Hajiya laila ta fad'a masa sunan asibityn."

OK gani nan zuwa yace "yanufi wurin motarsa escort dinsa suka bud'e masa yashiga,
Suma suka shinshiga cikin nasu motocin suka nufi Asibityn."

***************

Kwance yake akan gadon Asibityn Sauk'i yasamu garesa Dan kuwa ba abinda yakeji yana masa ciwo a jikinsa,
Likita kawai yake jira yashigo ya sallame shi,

Gabansa yakeji yana fad'uwa akai akai,
Da zarar yaji hakan ba wacce take fad'o masa a rai sai Safna,
Tabbas yasan tana cikin mawuyacin hali,
Musamman rashin ganinsa da batayi ba, bataga yatura wurin maigariba domin a tsayar da ranar aurensu, dolene tashiga cikin damuwa."

Runtse idonsa yayi yanajin wani abin yana bugar masa zuciya wanda yarasa ko meye shi,
Babu abinda yake gani sai Fuskar safna yake kallo a idonsa,
a lokacin da take ce masa , "Yarima inasonka zanyi biyayya a gareka, zan zama tamkar baiwa a gareka,
Kada kajuyamun baya idan katina DA ni shigeyace bana da iyaye."

Hawaye suka shiga zuba a gefen idonsa,jikinsa yasoma rawa,
ji yakeyi kamar ya tashi ya tafi k'auyen a d'aura masu aure da ita ya d'aukota ya taho da ita domin yabata gata tabbatar da cewa *MARAYU MA 'YA'YA* ne kamar kowa.,

Hajjah tana ganin zubar hawayensa wanda har tagaji da ganin suna fita a idonsa,
tin Tana Tausayinsa tana tambayarsa damuwarsa har ya Kai ta zuba masa ido tana kallonsa,
Dan tasan halin sauban sarai akwaishi da zurfin ciki, idan zai shekara dubu da abu a ransa yana damunsa baxai tab'a furtawa ba, hakan zai barshi a ransa yayita damunsa, yana ramewa sai dai idan kai ka fahimta da kanka snn ka magance masa matsalar cikin salama."
Hakan yayi a lokacin Auren Saudat bai furta baya sonta ba,
Sai da akayi bikin yashiga cikin damuwa yana ramewa,
Tambayar duniya ba wacce ba'ayi masaba akan ramar da yakeyi kodai auren da akayi masa ne baya so,
Hakan zai girgiza kai alamar yanaso shi ba abinda yake damunsa,
Sai daga baya da hajjah ta saka masa ido anan ta fahimci baya son Saudat shine dalilin ramar tasa,
Hakan tayita kwantar masa da hankali akan ya rik'e matarsa hannu biyu tinda anriga da and'aura auren har ankawota gidansa,
Dole ne Ya koyawa zuciyarsa soyayyarta illaso daga baya idan yasami wacce yakeso sai ya aure ta."

sai gashi shigowar Saudat gidan lokaci d'aya tashiga ran hajjah saboda tsananin son da takeyiwa sauban wanda bata iya b'oyeshi a duk inda take ko a gaban waye,
Snn shigowar saudat cikin gidan lokacin sauban yasami kwanciyar hankali da zama a lafiya a cikin masarautar dan kuwa gimbiya jamila tsoron mahaifiyar saudat takeyi."

Maimartaba ya turo k'ofa yashigo da sallama,
Ganin hawaye suna zuba a idon yarima ya dakatar da fadawa akan kada sushigo su dakata waje ya mayar da k'ofa ya rufe."

Cikin takon mulki yake takowa ya isa gaban gadon sauban ya sanya hannu ya dangwalo hawayen dake fita a gefen idonsa,
ya dubesu da kyau cike da mamaki ya tabbatar da tabbas hawaye ne ke zuba a idon magajin sarki,
Cikin gid'ima sarki yake kallonsa bakinsa yana rawa yace "magajin Sarki hawaye a idonka?" Ina raye a duniya?"
Meyafaru?"
Ina yake maka ciwo?"
Sam ba girma bane hawaye su dinga fita a idon gwarzon namiji kuma magajin Sarki, tashi zaune muyi magana."

Jiki a sanyaye sauban ya tashi zaune yana kallon mahaifin nasa,
Hannu Sarki yasaka ya shafe masa hawayen fuskar tasa,
Yana kallonsa yace "bani labarin abinda yake damunka Wanda inada raina da lafiyata magajina yake zubar da hawayena akansa."

Kallon mahaifinsa sauban yayi ya sunkuyar da kai yace "Abba damuwata safna ce."

Sarki yasaki wani murmushin irin nasu na manya,
Hajjah taja dogon tsaki ta juyar da kai gefe, domin ita wlh ta d'auka wani abin can daban yake damunsa ko yake masa ciwo wanda yake sakashi yana zubar da hawaye.
Ita tarasa ko yaushe sauban ya susuce yazama raggo hakan DA. har yake zubar da hawayensa Mai tsada a kan macce."

Sarki ya juya ya kalli hajjah yasaki murmushi snn ya nemi wuri ya zauna a gefen gado a kusa da sauban ya kallesa yana murmushi yace "fad'amun meyasami safna d'in?"

Kallonsa sauban yayi ya sunkuyar da Kai k'asa yace "inaji a jikina akwai wani mummunan abu da yasameta,
Abba Safna abar tausayice bata da iyaye bata da kowa sai Allah saini dana d'auki Alk'awari Zan taimaketa,
Abba bawai son safna nakeyiba kawai ina tausayin halin da take cikine,
DA kuma Wanda zata shiga idan tarasani,"
Abba Ina neman Alfarma a Karo na farko a wurinka itace katura fadawa yanzun nan sutafi k'auyen domin a tsayar da ranar aure na da Safna,
domin gudun kada asami Matsala a cikin Al'adarsu."

Murmushi Sarki yasaki Wanda har sai da hakoransa suka fito,
Yana kallon sauban cike da wauta wai ba sonta yakeyi ba, bayan ga soyayyarta nan ya gani k'arara a cikin idonsa,
Murmushi Sarki ya kuma saki yana kallon sauban Yace "hakan kakeso a aiwatar yanzun magajin sarki?"

D'aga kai sauban yayi alamar eh."

Sarki yace to "idan maigari yace a lokacin yake so d'aura
auren naku a tsaya a amso maka aurenta ko kuwa abarshi rana kawai kakeso asaka maka?"

Shuru sauban yayi ba amsa.
Sarki yasaki dariya wacce yasaka sauban shima ya d'an murmusa cike dajin kunya,
Sarki yace kabani amsa kai nake saurare domin da kaina zantafi ba aikeba "

Cikin jin kunya sauban ya sunkuyar da kai yace "duk yanda kace ranka ya dade a aiwatar da hakan."

Sarki ya kuma sakin dariya yace "wnn amsar kai zaka bani ita,
Saboda a lokacin da kake zubar da hawayen k'auna baka nemi shawara daniba."

Cike da jin kunya sauban ya kuma sunkuyar da kai sarki yana ganin hkn ya had'e fuska cike da zulaya yace "to shikenan Zan fasa tafiyar zan tura fadawa Zan ce masu da zarar suntafi akace za'a d'aura aure a lokacin zance kabada umurnin "kada a d'aura kai baka ra'ayin hakan, rana kawai kakeso asaka maka,
Idan sukace ba hakan sukeyiba,
Zance kace kabarwa duk Wanda yake sonta a d'aura dashi."

Da sauri sauban ya d'aga Kai ya kalli Sarki yaga da gaske yake ba wani alamar wasa a tare dashi yace "ranka ya dad'e ba hakan nake nufiba, a d'aura auren dani, sutaho tare da ita."

Dariya ta sub'ucewa sarki wacce tasaka sauban jin kunya,
Yayi saurin kwanciya tare da juya baya yana murmushi cike da jin kunya."

Hajjah tana jin duk abinda sukeyi bata tanka masuba domin ta dade da sanin Sarkin Abdullah shi yake sakanta sauban yake yin duk abinda yaga dama."

Sarki ya mik'e tsaye yana murmushi ya kalli hajjah yace "umma zamutafi karb'owa jikanki Aure a k'auyen gidan gonarsa, saiki shirya tarbon kishiya ta biyu."

Mere baki hajjah tayi tace kafin a d'aura ayi binciken asalinta da abinda ya kashe iyayenta domin naji yana fad'in bata da iyaye,
Snn a tabbatar da asalinsu mai kyau ne tafito a cikin gidan asali, da daraja basa da wani abin fad'a,
kodan samun zuri'a mai tsafta,
Snn kada ka manta a cikin gidan sarauta zata shigo shi kuma gidan sarauta duk Wanda kagansa yashigo cikinsa a matsin matar Sarki KO d'an Sarki KO jikan Sarki dolene ya zamana yana da asuli Mai kyau.
Idan babu wnn to tabbas bata cancanta da zama matar saba dole ne ya barta duk son da yake mata."

Gaban sauban ya fad'i dajin furuncin hajjah."

Sarki yace "tabbas hakan ne umma,
Sai dai inaji a jikina kamar farin cikin da mahaifiyarsa take fad'ar masa zai samu a cikin gidan gonar sa,
Ina hasashen shine ya fara bayyana a garesa." Domin samun macce ta gari babban farin cikin d'a namiji, yasami rabin duniyarsa domin kullum cikin farin ciki zaiyi ta zama har k'arshen rayuwarsa

Yanufi k'ofar fita yace "muntafi,
Hajjah tace "adawo lafiya."

Snn Sarki yafita ya bawa fadawa umurnin sushiga mota,
ya fad'a masu inda za'a tafi,
Suka d'auki hanyar k'auyen Lassa."

Suna fita daga asibityn Anawa Sarki jiniya,
Alhaji Habib Naira shima yashigo da tawagarsa sarki yabada umurni a tsaya,
hakan shima Alhaji Habib yaba da umurni a tsaya, anan suka fito daga motar suna dariya suka shiga gaisawa da juma cike da farin ciki da kewar juna,
Tare da tambayar yaushe rabo,
Domin Alhaji Habib business dinsa baya barinsa zama yau yana wannan k'asa gobe yana wancan k'asa jibi yana wancan k'asa."

Anan Alhaji Habib yake tambayar Yaya Sauban?" Ai yanzun
Yasan yaron ya girma sosai."
.dariya sarki yasaki yana fad'in sosai kuwa har yayi aure,
Yanzun hakan k'arb'o masa auren mata ta biyu zamu tafi muyi."

Kuma tab'awa sukayi suna dariya Alhaji Habib yace "yaro yayi gadon ajiye mata da yawa,
kaine baya ko ni."

Sarki yasaki dariya yana fad'in lafiyar kenan, ai duk Wanda ya ganmu yasan ba rangwanci a tare damu."

Suna dariya tare da zolayar juna sukayi sallama ko wanne yashiga motarsa Alhaji Habib yana fad'in abokina kafin natafi zan shigo fada domin asakamun Albarka,

Sarki yana dariya yace "badamuwa sai ka shigo,
Sukaja mota suka tafi cike da farin cikin ganin juna domin abokanaine sosai kasuwanci ne yarabasu da junansu."

Sarki yana fita daga asibityn likita yashigo ya k'ara duba jikin sauban yaga yasami lafiya,
Anan take ya sallamesu direba tare da fadawa suka d'aukesu a mota suka nufi gida su."

****************

Dawowar dakaru da labarin da sukaje dashi na tarwatsa k'auyen su safna ba k'aramun farin ciki yasaka Saudat da mahaifiyar taba,
Musamman dasukaji cewar Safna ta mutu domin,
Sunce dajin da tabi da gudu anan ne maciji ya kashe biyu daga cikin mutanensu, suma dakyar suka sha,
Suna da yak'inin ko gaggar jikin safna baza'a gani bare gawarta shikenan ta mutu sai dai wata ba itaba"

Wayyo dad'i a ranar

Please Login or Register in order to submit comment