Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ce wacce ta b'ata tun tana jaririya, itace Safna."

Hajiya Laila babbar Aminiyarta ce,
Itace take sayar mata da kayan sakawa tare da turarunka masu k'amshi da kayan mata,
Hajiya Laila itace ke koyamata yanda zata gyara jikinta a koda yaushe yazamana tana cikin k'amshi, da tsafta
Ita ke d'orata a kan hanyar da zata mallaki mijinta ita kad'ai batare da ya hango wata a waje ba, ko da ya hango wata d'in bazatayi tasiri a wurinsa ba."

Tirk'ashi da 'yar gidan Hajiya Laila Saudat zatayi kishi?🙆🏻 kaddai ace 'yarsu SUHAILAT wacce b'arayi suka sace itace takoma Safna."

Tirk'ashi, Ta tabbata duk abinda takeji Hajiya Laila tafita jinshi,
Ita batabin malamai da bokaye, makirci da kisisina Mai had'e da tsaftar ciki data waje shi take amfani dashi wurin tafiyar da mijinta, gaba d'aya ya rud'e akanta bayajin kunyar ko a gaban kowaye ya nuna mata tsantsar soyayya da k'auna."

Ta juya ta kalli Saudat wacce itama, ita take kallo cike da mamakin ganin jikin mommy yayi sanyi a lokaci d'aya."
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *DAN SARKI SAUBAN*




*Writing by*
*Ummu Safwan*
( _Fareeda Basheer_ )



*43*









Yana gama fad'in hakan ya juya ya koma ciki, zuciyarsa
Cike da murnar ganin abokanansa musamman Sarki Abdulraham Wanda ya dad'e basu had'uba sai dai a waya."

Yana shiga ya Tarar da Hajiya Laila ta shek'a wani irin wanka Mai firgitarwa sai k'amshi take zubawa,tsayawa yayi cak yana kallonta tare da kashe mata
Ido d'aya ya taka sannu a hankali zuwa gareta ya janyota zuwa jikinsa yashiga shisshinarta a duk inda yaci karo dashi bakinsa a kunnenta cikin wani salo yake fad'a mata,
Sarauniyar mata munyi manyan bak'i fa suna falo zaune."

Fari tayi da ido cikin wani salon, tace suwaye sukazo mana kai tsaye batare da sanarwa ba."

Dogon hancinta yaja yana murmushi yace "surunki kine Sarki Abdullah tare da Abokina, Sarki Abdulraham."

Yana murmushi yake cewa "Nasan dalilin zuwan nasu,
surinki ne
yaji tsoro, sosai wnn dalilin yasa ya janyomun sarki Abdulraham ya Kai k'arshen maganar yana dariya."

Had'e hannu biyu tayi wuri d'aya alamar rok'o👏🏻 tace "ina kuma rok'awa surukina afuwa tuba yakeyi ayi hakuri komai ya wuce a saka masa rana."

Zaro ido yayi yace "dawuri hakan?"
Ko Jan aji babu?"
Kinmanta lokacin da natura Neman aurenki sai da aka jamun aji kamar nayi kuka."

dariya tayi tace "wato ramuwa zakayi a wurin abokinka kenan,
haba Alhajina komai ya wuce mana."

Murmushi yasaki yace kada kidamu, zan amsa duk abinda sukazo dashi da hannu biyu biyu"

Ya juya yanufi toilet yayi wanka ya shirya cikin dakakkiyar shadda sai k'amshi yake zubawa yanufi babban falon saukar bak'i."

fad'in tsaruwar falon da kyansa b'ata lokaci ne
Cikin farin ciki da dariya mai cike da murna suka tarbi junansu suka gaisa tare da barkwance a tsananinsu."
Anan take aka cika masu gaba da kayan motsa baki,
wannan hikimar Hajiya Laila ce."

Bayan sun kamallah motsa baki tare da ciye ciye, suka sake sabuwar gaisuwa,
Sarki Abdulrahaman yake tambayar Alhaji Habib yaushe gamo sai dai a waya."

Murmushin farin ciki kawai Alhaji Habib yake suna tsokanar junansu,
Snn Sarki Abdulrahaman ya fara da cewa "Ina tayaka murna, ko nace muna taya junanmu murna ganin 'yarmu da akayi cikin k'oshin lafiya,
Alhmdulillah nayi farin ciki sosai danasami labarin bayyanar 'yarmu Suhailat Allah ya tsare gaba ya kauda kaddara."

"Ameen suka amsa gaba d'aya falon cike da farin ciki,
Snn Sarki Abdulraham yaci gaba da cewa,
Sai kuma naji labarin d'anmu Sauban shine ya taimaketa a lokacinda take cikin kunci da damuwa
Daga k'arshe ya fad'a cikin tsananin sonta Wanda har yakaishi da kwanciya a asibity,
Hak'ik'a nayi farin ciki da jin wannan labarin domin duka abin d'aya ne sauban da Suhailat duka 'ya'yanmu ne tuwona maina,
Wannan labarin danaji yasakani farin ciki sosai Dan hakan nace Sarki ya rakoni wurinka na nemawa sauban auren Suhailat a wurinka."

Shuru Alhaji Habib yayi yana kallonsu yana sakin murmushi, domin yarasa abinda zaice."

Sarki Abdullah ya amshe maganar da cewa,
Abokina ka manta da komai a ranka,
Ka manta da kalaman danayi a baya duk rashin sanine, Wanda nayi nadamar fad'ar hakan, tabbas nayi kuskuren banbata d'an sunnah da d'an kan titi,
a lokacin baya idona ya rufe akan son Kaina danayi,
Amma yanzun na hankalta na fahimci abinda kake fad'amun nagane d'an kan titi da d'an sunnah duk d'ayane a wurin Allah basuda wani banbanci,
Banbancinsu d'aya ne shine Wanda yafi wani jin tsoronsa."

"Alhmdulillah Alhaji Habib yace "yana murmushi domin ko d'aya bai Rik'e Sarki a ransaba dama hakan yakeso yaji a bakinsa,
Yanason yagane ko ba'a kan safna ba, ko anan gaba zai gyara kuskurenshi, ya fahimci d'a na kowa ne ba'a kyamatar d'a a duk inda yake."
Ya dafa kafad'ar Sarki yace komai ya wuce abokina Allah ya tsare gaba yana murmushi ya kallesu gaba d'aya yace Suhailat Ai 'yarkuce zaku iya zartar da hukunci akanta sauban shine nawa Dan hakan ni zan karb'ar masa aure a wurinku."

Alhaji Habib ya kalli Sarki Abdulrahaman yace "Ina nemawa d'ana auren 'yarka domin yaganta yanaso Kuma sun fahimci juna "

Sarki Abdulrahaman yace naba d'anka auren yata Suhailat,
Ka kawo sadaki a duk lokacin da ka shirya Zan d'aura masu aure."

Sarki Abdulrahaman yace "nasaka ranar aure wata uku basu zuwa shin ko hakan yayiwa d'anka?"

Alhaji Habib yace 'dana a shirye yake KO yanzun za'a d'aura bayada matsala,
Suka saki dariya gaba d'ayansu Mai cike da farin ciki,
Sarki Abdullah akan farin ciki jiyayi kamar ya zubar da hawaye,
Hakika babu abinda zai cewa wad'an nan abokanai nasa sai godiya da sanbarka Allah ya kara masu dankon Aminci da k'aunar juna."

Hakan sukayi firarsu daga k'arshe sukayi sallama,
Tare da tabbatar juna cewa an saka ranar,auren Sauban da Safna wata uku masu zuwa."

Ko wanne yana farin ciki yashiga motarsa,sunayiwa juna fatan Alheri,

Duk abinda akeyi Hajiya Laila tanaji kasancewar sautin maganar da sukeyi yana kaiwa a falon da take a zaune,
Tayi farin ciki sosai dajin duk abinda ke faruwa da hukuncin da suka zartar sanya ranar aure nan da wata uku,
Shigowar Alhaji Habib kenan fuskarsa cike da farinciki Hajiya Laila ta tarbeshi ta rungumeshi tare da zuba masa kirari Wanda kesakashi farin ciki,
Anan take kan Alhaji Habib ya juya da tsananin bukatar matarsa ya duk'a ya d'auketa yanufi bidrom da ita."
Domin yasan farin cikin da takeyi baya rasa nasaba da jin tattaunawar da sukayi da abokanansa Dan hkn bari ya kuma Sakata cikin wani farin cikin domin hakan shine burinsa."

*******************

Alhmdulillah jikin sauban yasami sauki sosai ya murmuje ba abinda yake masa ciwo saka makon Albishir da mahaifinsa ya masa na cewar an saka ranar aurensa ,wata uku masu zuwa."
Bai sauban kadai yyi farin cikiba duk wani masoyinsa saida ya tayashi farin ciki musamman Safwan da bakinsa yaki rufuwa."

Anan take likita ya bashi sallama, domin komawa gida."

Hakan itama Saudat jikin nata da sauki sosai duk da bawata matsala bace kedamunta bayan jarababben kishi dake cinta."

A ranar da akayi sallamar tunkafin sutafi gida Alhaji Habib ya iso asibity tare da Hajiya Laila,
Domin tafiya da Safna."

Sosai Sauban yashiga damuwa tafiyar da za'ayi da safna
Hajjah tashiga lallashinsa tare da tuna masa da cewa saura wata uku sukasance a cikin inuwa d'aya su zauna a tare zama na har Abada,
Sannan kafin zuwan lokacin duk lokacin da yakeson ganinta zai iya tafiya gidansu suyi zance yadawo,
Ya mutsa fuska yayi irin shifa ba abinda yake damunsa akan tafiyar da zatayi,
Dariya hajjah tasaki tana fad'in miskili kafi mahaukaci ban haushi."

Hakan suka saka safna a mota tare da yiwa sauban fatan Alheri suka tafi,

Ba sauban ba hatta da hajjah taji ba dad'i tafiyar safna
Domin a d'an za man da sukayi ta fahimci yarinyace Mai hankali da natsuwa tasami tarbiya mai kyau a wurin iyayenta,
Sosai ta kwantawa hajjah a rai Wanda take Addu'ar Allah ya nuna mata wata uku zata dawo cikin halinsu su zauna da ita zama na har Abada."

bayan tafiyar su safna,
Sauban yashiga tattara kayansa domin barin asibityn,
Hakan itama Saudat tare da mahaifiyarta wacce Sarki Abdulrahaman ya barta domin tayi jinyar yarta har zuwa lokacin da zata sami lafiya, suma suka shiga tattara kayansu dan barin asibityn."

A tare suka fito da sauban suka nufi wurin motocinsu suka shinshiga suka d'auki hanyar masarauta."

*********************

Kwanan mahaifiyar Saudat d'aya a cikin gidan sarautar ta had'a kayanta ta koma gida, cike da jimami da bak'in cikin ranar Auren da aka Sanyawa sauban da safna,
Hankalinta yakan k'ara tashi idan ta tuna da ko wacece safna 'yar Hajiya Laila ce."
Amma tasan hanyar da zatabi insha Allah idan har tana raye baza'ayi auren nan ba."

********************


Sosai hankalin gimbiya Jamila ya tashi a lokacin da labari ya sameta cewa sauban yadawo gida cikin k'oshin lafiya ya sami sauki sosai tamkar bai kwanta jinyaba,
Sosai tayi bakin ciki dajin wnn mummunan labarin domin duk a tunaninta asirin da takeyi mashine ya kwantar dashi ciwo,
Ciwon da d'ora mashi mutuwa domin daga can sai kabari injita."

bata kuma firgita da lamarin sauban ba sai da sarkin gida ya nufota a firgice ido rufe yana sheda mata cewa ansaya ranar auren sauban da yarinyar da yakeso wata uku masu zuwa."

Wani irin zabura tayi ta mik'e tsaye idonta a rufe, lokacin yayi daidai da shigowar sadeeq, ta d'aga hannu cikin tsananin b'acin rai ta d'aukeshi da mari,
Tana hucin Mai cike da takaici da bakin ciki, tana fad'in "na haifeku ne domin na d'ebe takaicin haihuwa, na haifeku ne domin kuzama jigo abin alfahari a cikin masarautar nan,
Nakan hana idona bacci na hana gaggar jikina hutawa,
Na kashe kud'i wad'anda bansan iya adadinsu ba duk dan kusami sarauta ku mallaki masarauta da duk wani Abunda ke cikin masarautar,
kaida d'an uwanka sageer, duk abinda nakeyi a banza yake tafiya saboda bakusan ciwon kankuba,
Yanzun labari yazomun cewa Sauban aure zaiyi zai auri Mata ta biyu,
Tunda ta farko bata haihu ba ya zama dole ta biyu ta haihu,
Idan matarsa ta haifi d'a namiji shikenan yayi zarrah a cikin gidan nan,
kuna nan zaune, ko da wasa bantab'ajin d'ayanku ya furta cewa zaiyi aureba bare ya haihu."

Ta nuna masa hanyar fita tace "kafita kabani wuri,
Kafad'awa d'an uwanka cewa sati biyu kacal nabaku kafin d'aurin auren sauban Ku tabbatarmun da cewa kunfitar da matar da zaku aura."
Idan ba hakan ba kowa zaiga b'acin raina a cikin gidan nan."
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *DAN SARKI SAUBAN*




*Writing by*
*Ummu Safwan*
( _Fareeda Basheer_ )



*42*






"A d'akinsu Sauban Safna tana gefen gadonsa akan kujera zaune,
Idon sauban yana kanta duk wani motsi nata akan gadonsa takeyinsa,
Jiyakeyi babu abinda yake masa ciwo a jikinsa a sallamesa ya koma gida kawai yake buk'ata."

Hajjah ta turo k'ofa tashigo tare da sallama tafito daga wurin ganin saudat,

Amsa Mata sallamar sukayi suna kallonta,
Itama kallonsu tayi tasaki murmushi mai cike da tsokana tana kallon sauban tana fad'in "oh ni hajjah yanzun shikenan yaron nan yadawo daga duniyar mutuwa,
Ashe haka ciwon soyayyah yake."

Had'e fuska sauban yayi bayason hajjah da Safwan suna masa wannan maganar a gaban Safna salon ta raina shi."

Hajjah ta mere baki tace miskilin mutum Mai ban haushi,
Ba had'e fuska zakayiba, idan katashi kasaka kuka, amma baka isa ka rufemun bakiba, saina fad'i abinda ke raina."
Lokacin da ciwon soyayya ya kamaka har kuka kakeyimun Anna itace shaidata."

Guntse baki safna tayi tanaso tayi dariya ba fuska, sauban ya tsare gida."

katse hajjah yayi daga maganar da zatayi dan bai san abinda zata fad'aba a nan gaba, yace Yaya jikin Saudat taji sauk'i kuwa?"

Kuma mere baki hajjah tayi, tace tasami sauk'i tana can tare da uwarta,tana sak'a Mata,

murmushi sauban yayi yace "me likita yace dangane da abunda yake damunta?"

Hajjah mere baki tace "kafi kowa sanin halin matarka tare da dalilin fad'uwar da tayi,
Idan kana iya tafiya ka tafi ga ganewa idonka halin da take ciki DaGa nan saika tambayeta bayanin da likita yayi

Murmushi yayi yace yanzun kuwa Zan tafi tinda ke bazaki fad'amun ba ."
Ya kalli safna wacce ta daina murmushin da takeyi fuskarta ba yabo ba ballasa yace "Mutafi mugano Antynki."

"to tace "tare da mik'ewa tsaye,
tsaye tayi tana kallon yanda zai sakko daga kan gadon,
Sannu a hankali ya zuro kyakkyawar k'afarsa izuwa saitin silifas d'insa Wanda safna ta saita masa su wuri d'aya,
Zura k'afarsa yayi yasaka ya cije leb'onsa na k'asa sannu a hankali ya mik'e tsaye jiki ba kwari"

Murmushi farin ciki hajjah tayi ganin ya tashi da kansa,
Ido biyu sukayi dashi ta mere baki,
Tace sannu kinji safna kinceci rayuwar wani daga mutuwa."

Murmushi kawai safna tayi tashige gaba sauban yabi bayanta, Fuska had'e yake hararar hajjah."

Sannu a hankali suke tafiya,
Inda fadawa wad'anda ke tsaronsa suka take masu baya suna zuba masu kirari,
Tafiya sukeyi cike da farin ciki,
Sauban jiyakeyi wani iska Mai dad'i yana ratsashi farin ciki yakeji yana wanzuwa a tare dashi."

D'aya daga cikin bafad'en yayi saurin zuwa ya bud'e masu k'ofar d'akin da saudat take ciki,
Hakan yanunawa sauban nan ne aka kwantar da ita."
Hannu ya d'agawa fadawan alamar su jirashi waje,
Sannan yashiga d'akin hannunsa sanye a Aljihun rigarsa safna tana biye dashi a baya."

Saudat tana kwance a kan k'afar mahaifiyarta tana kwantar mata da hankali akan tabar komai a Hannunta,
Sukaji sallamar shigowar sauban."
Zubbur Saudat tayi ta mik'e zaune tana murmushi cike da farin ciki, take kallonsa,
D'an murmusawa yayi ya kalle inda mommy take ya gaida ita,
Hakan itama safna ta duk'a ta gaida ita,

Amsawa mommy tayi fuska ba Annuri ta kafe Safna da ido tana kallonta sama da k'asa tabbas wnn 'yar Hajiya Laila ce ko ba'a, fad'aba kamanni ya nuna,
Wanda kallon yasaka safna sarguwa takame gefe d'aya."

Wurin Saudat ya nufa cikin murya k'asa k'asa yanda ba wanda zai iya jin abinda yake cewa yace "yaya jikin naki?"

Turo baki tayi alamar shagwab'a tace naji sauk'i,
Tsare gida yayi yace "meyake damunki?"

Kuma turo baki tayi tana fadin "ba Kai neba?"

"Nine danai maki me?"
Meya faru?"

Dam gaban safna ya fad'i ganin yanda Saudat take zubawa sauban shagwab'a shikuma yana kallonta yana biye mata Allah kadai yasan abinda suke cewa.
Wani abinda taji yana taso mata a zuciya tayi saurin Dannewa tare da karanto duk Addu'ar da tazo ranta."

" tsareta yayi da ido yana fad'in inajinki mena maki?"
Tayi shuru ba amsa."

Ya mere baki yace "To shikenan tunda baxaki fad'aba Allah yabaki lafiya,
Ya juya ya kalli inda safna take,
Yakira sunanta yace "Safna zo ki gaisa da Antynki kiyimata ya jiki."

Cikin natsuwa safna ta tako zuwa gadon saudat, Saudat na ganinta, sukayi ido biyu da ita gabanta ya fad'i, gani tayi duk duniya ba wanda yafita kyau wani tsantsar kyan safna ta hango a tare da ita,
Cikin sauri ta Kai kwance tare da runtse ido tamkar wacce take bacci, domin ko a lahira bata fatan ta kumayin ido biyu da safna,
Safna tace "Anty Ina wuni ya ya jiki?"

Saudat tayi banza da ita idonta a rufe hawaye suna zuba a gefen idonta a duniya babu abinda ta tsana sama da safna,
Yau itace a gabanta wata macce take tsaye da mijinta,
Kuka tasaka mai sauti tana fad'in "mommy kiyi masu magana suyi tafiyarsu bana son gaisuwar."

A harzuk'e mommy tace "Ai sai kutafi wacce kukazo gani tace bata son ganinku."

Shuru sauban yayi fuskarsa a had'e yana karantar duk abinda ke faruwa,
Sautin muryar mommy yaji tana cewa safna "malama ke ai saiki fita tunda mijinta baya iya tafiya ya barta,
Kifita Daga waje kijirashi batada bukatar ganinki."

murnushi safna tayi ta d'aga kai ta kalli sauban yana nan tsaye a inda yake ko motsawa baiyiba, alamar bayason barin wurin, kenan
jiki ba kwari ta juya zata fita,
Caraf ya rik'e hannunta yana fad'in kijira mufita a tare mana, ai a tare muka shigo,
Yaje saiti wurin fuskar Saudat ya shafi fuskarta da hannunsa wacce take jike da hawaye yace "Allah yabaki lafiya ya kawo maki sassauci akan abinda yake damunki,
Ya Juya ya fita yana janye da hannun Safna."

*****************

A gidan Alhaji Habib Naira,
Yau kwana biyu kenan ba Safna a tare dasu,
sosai Alhaji Habib yashiga damuwa, iya d'an zaman da sukayi da yarsu sunyi matuk'ar sabo a tsananinsu."

Hajiya Laila take kwantar masa da hankali cikin natsuwa tare da jansa a jiki cikin hikima irin ta 'ya mace take lurar dashi cewa "ya daina sanya damuwar rashin suhailat a kusa dasu,
Yasani cewa suhailat 'ya mace ce, aure zatayi ta tafi gidan wani, shikenan tabarsu gaba d'aya ta koma wani gidan da zama,
Meye abin damuwa na rashinta da yayi kwana biyu."

Anan taci gaba da lurar dashi akan k'arfin Amintarsu da sarki kada yabari shaid'an yashiga tsakaninsu ya raba tsakaninsu akan 'ya'ya."

Ko ba'a fad'aba yasan sarki yaji kunya tare da nadama Mai cike da danasani akan kuskuren da yayi a baya."

Sosai Alhaji Habib yaji dad'in magagganun matar tasa, ya janyota zuwa jikinsa yana shafata tare da sanya mata Albarka, dayiwa Allah godiya daya bashi Mata ta kwarai,Mai tunani da hangen nesa."

Kwakwasa k'ofar falo da akeyi yasa Hajiya Falmata ta janye daga jikin mijin nata Wanda har ya fara fita daga hayyacinsa,
Janyota ya kumayi ido rufe yashiga aika Mata da sakon ninsa,
K'arar dukan k'ofar yasa Alhaji Habib yasaki umma yafita a fusace domin ganin ko waye."

Maigadi yagani tsaye a bakin k'ofa,
Ganin fuskar Alhaji ba fara'a tunkafin Alhaji yayi magana, maigadi ya zube k'asa yana fad'in tuba nakeyi ranka ya dad'e ayi hakuri, kasan ba halina bane dukan k'ofa, bak'ine kayi,
Manyan bak'i sarakuna ne da kansu suke
nemanka.'

Ido sarki ya d'aga ya hango ta gawar motoci fadawa Acan cikin harabar gida sai jiniya akeyi,
Mamaki yashigayi yanzun duk jiniyan nan da akeyi baijiba."

_yo Abba yaza'ayi kaji ka tsunduma cikin wata duniyar_🙊

Hannu ya d'agawa maigadi akan yayi tafiyarsa,
Yakira escort nashi wad'anda suke zagaye a gidan, yace a bud'e masu babban wurin parking space dake can gefen gidan su ajiye motocinsu sannan ayo masu iso zuwa babban falon ajiye bak'i."
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *DAN SARKI SAUBAN*



BY
UMMU SAFWAN
(FAREEDA Basheer)




*44*







Tana Huci ta nunawa sarki gida k'ofa fita tace 'kaima tashi kafita saina nemeka munafuki kawai"

Jikin sarkin gida yana rawa yafita yana zarar ido,

********************

sauban sai kuma murmurewa yakeyi a kullum da tunanin safna yake kwana yake tashi a ransa,
A D'ai rana yakan yimata kiran a wayar Hajiya laila yafi ak'irga
hakan zasu sudinga fira mai cike da shaukin so da kauna,
Wani lokacin yakanyi mamakin kansa idan ya zauna yana tunaninta, ta yanda baya iya awaya daya baikirata yaji muryarta ba,
Wanda yake tunanin kodai sonta yakeyi da gaske kamar yanda Safwan yake fad'a masa cewar ya fad'a tarkon so,
Girgiza kai yayi yana fadi a ransa "ina baitab'ayin soyayyaba a rayuwarshi baisan yanda so yakeba, abinda yasani yana tsananin tausayinta ne kawai shine dalilin damuwar da yayi da ita."

*****************

Yau safwan cike yake da murna da farin ciki masoyiyarsa matarsa Safinat ta haihu anhaifa masa d'a namiji,
Inda ya d'aga waya yakira sauban Wanda yake zaune a d'akinsa ya sanya Saudat a gaba yana tambayarta saita fad'a masa abinda yake sanyata tana rama, duk tabi ta rame ta fita hayyacinta saboda tsananin kishi,
Kuka take masa tana fad'in babu abinda yake damunta ita,
Suna cikin hakan wayar Safwan tashigo wayarsa ya dauka anan yake masa Albishir cewa yazama daddy safinat ta haihu yanzun suna asibity ta haifi d'a namiji ya rad'a masa Suna SAUBAN,
Masha Allah sauban yace cike da farin ciki samun takwara da yayi yace " ganinan zuwa asibityn yanzun nan."

Ya mik'e cikin hanzari ya d'auki key din motarsa ya d'an tsaya yana kallon Saudat sannan yace "Zan tafi nadawo ki tabbatar da kin tanadi amsar da zakibani,
Inason nasan sanadin ramar da kikeyi,
Yana gama fad'in hakan ya juya ya fita."
Kai tsaye asibityn yanufa cike da farin ciki domin jiyakeyi tamkar shine akayiwa haihuwa, sauban yana tsananin son 'ya'ya Allah ne kawai baibashi bane hakan yake dannewa a ransa bazaka iya gane abinda yakesoba da Wanda bayaso."

kai tsaye d'akin da ake kwantar da wadanda suka haihu ya nufa kasancewar asibity sananniya ce sai wane da wane suke zuwa cikinta,
Yana murmushi ya tura d'akin yashiga da sallamarsa ya tarar da Safwan zaune a bakin gado yana rungume da jariri bakinsa cikin bakin safinat yana tsotsa tare da shafa mata kai da hannunsa d'aya yana jera mata sannu,

yana sane da shigowar sauban amma sai yayi kamar baisan ya shigoba,
mere baki sauban yayi yayi gyaran murya yana fad'in maye kawai hatta a cikin asibityn baza"a bar mayyatarba, d'an iska kawai."

Dariya Safwan yasaki ya Saki safinat ya taso daga kan gadon yana fad'in barka da zuwa abokina ai bansan kashigoba, Ina tayaka farin cikine samun takwara da kayi." ya mik'a masa jaririn."

Amsar yaron sauban yayi yana murmushi yana kallonsa, cike da burgewa da ban sha'awa karon farko dayaji sha'awar inama wnn yaron d'ansane ina Saudat ta haifa masashi dasai yafi kowa murna da farin ciki,
Ya ciro wayarsa a gaban Aljihu yashiga d'aukar yaron hoto,
Wanda hakan yayi matukar farantawa Safwan rai,
Domin wnn shine karon farko da abokinsa ya sanya wayarsa ya dauki hoton wani abu da kansa,
tabbas Ya tabbata bakaramun farin ciki yayi da wnn haihuwarba."

Safwan yana murmushi mai cike da tsokana yakalli sauban yace "ni nakawo rumfata saura kaima kakawo taka, koda yake ba mamaki basir ne yake d'awainiya dakai abokina Zan nema maka maganin basir."

Had'e fuska sauban yayi ya wurgawa Safwan harara,
Bai tanka masaba illah yaci gaba da d'aukar Sauban junior a waya, aka kumayi sa'a jaririn ya bud'e idonsa kwanin ban sha'awa yana kallon sauban,
_Kusan jariran yanzun da Zarar katafi barka idon biyu kake ganin jariri yana kallonka kana kallonsa_😂

Saida aka sallami safinat snn sauban ya koma gida bayan ya rakasu har gida, har yakeji a ransa inama abar masa jaririn ya tafi dashi."

a gajiye ya koma gida kai tsaye d'akinsa ya nufa, ya cire kayansa ya fad'a toilet domin ya watsa ruwa ko zai sami sassaucin gajiyar da yakeji,
Bayan yafito daga wanka yana d'aure da towel a k'ugunsa,
Hannunsa d'auke da d'an k'aramun towel din yana goge ruwan jikinsa zuwa kansa."

Saudat ta turo k'ofa tashigo hannunta d'auke da wani kyakyakkyawan tire Wanda yake jere da kulolin abinci na alfarma, tayi kwalliya sai k'amshi take zubawa,
akan dining table tanufa ta ajiye abincin snn tadawo zuwa wurinsa ta karb'i towel din hannunsa tashiga goge masa jikinsa,
Shuru yayi yana saurarenta baiyi yunkurin dakatar da itaba kamar yanda yasaba saboda a halin yanzun tausayi take bashi,
Saida ta kammala goge masa jikinsa sannan ta d'auko jallabiyarsa tare da gajeren wandonsa ta ajiye masa a gefen gado zata juya tafita domin ta bashi wuri ya sanya kayansa kamar yanda yake bata umurnin fita idan zai sanka kayanshi,
Saiji tayi ya ruk'o hannunta ya dawo da ita yana kallonta cike da tausayi,
Ya nufi kan gado da ita ya zauna ya d'orata akan k'afarsa ya juyo da fuskarta saiti fuskarsa suna kallon juna cikin murya k'asa k'asa yace "fad'amun damuwarki saudat meyake damunki?"
Ko wani abu nake maki Wanda bakijin dadinsa a gidan nan?"
ko wani yake takuraki a cikin gidan nan fad'amun naji."

kanta ta sunkuyar k'asa hawaye suna zuba a idonta har suna sauka akan k'irjinsa,
Yayi saurin runtse idonsa cike da damuwa domin a duniya idan akwai abinda ya tsana bai wuce kukan mace ba."

Cikin muryar tausayi yace fad'i naji ina saurarenki."

Zamewa tayi daga kan k'afarsa ta sakko k'asa ta tsuguna a gabansa tare da sunkuyar da Kai hawaye sukaci gaba da zuba a idonta,
Cikin muryar kuka tafara da cewa,
"Ina tsananin sonka da k'aunarka mijina,
Tunda Allah ya halliceni bansan soba sai a kanka, bansan shakuwa ba sai a kanka, duk da dai kai baka sona ni Ina tsananin Sonka Zan iya rabuwa da komai da kowa akan sonka,
Soyayyar da nake makace ta janyo nake tsananin kishinka ka taimakamun Yaya Sauban zuciyata tanada rauni akan soyayyarka Zan iya rasa rayuwata idan ka k'ara aure
Bana iya jure ganin wata macce a tare dakai a shinfida d'aya da sunan matarka ta aure
Sadaukina ka taimakeni ka taimaki rayuwata kace kafasa Auren,
Kaxauna dani ni kad'ai nayi Alk'awarin duk halina Wanda bakaso Zan daina wlh zan daina takai k'arshen maganar tare da sakin kuka mai sauti gwanin ban tausayi."

Kallonta yakeyi cike da tausayi,
Dama yasan matsalar Saudat bata wuce kishi, tsananin kishintane yake sanya take ramewa,

Hannunsa yasaka ya tallabota ya mikar da ita tsaye ya janyota zuwa jikinsa,
ya kai kwance akan gadon ya d'orata a

Please Login or Register in order to submit comment