Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yaji sunabin fuskarsa, cikin yanayin tausayi yace "yanzun shikenan safna ta mutu?"
Safna marainiyace bata da iyaye hakan rayuwarta ta k'are cikin wahala daga k'arshe tayi mutuwar wulak'anci a cikin Daji,
Ya juya ya rik'o hannun dattijiyar yace " Inna "bansan so ba, bansan KO meye so ba, amma abokina Safwan yana yawan fad'amun cewar son safna nakeyi nakanji duk wani bugun zuciyata safna ce duk wani numfashi na safna ce inna hakan shine so?
A yanda nakeji a cikin zuciyata tunda safna ta mutu nima mutuwa zanyi."

Girgiza kai dattijiwar tayi tace "baxaka mutuba d'ana, Safna tana raye bata mutuba,

Cikin sauri sauban ya kalleta cike da mamaki tace "nice na taimaki safna a cikin wnn dajin kamar yanda na taimakeka a yanzun, safna tana raye tana zaune a cikin garin adamawa sai dai tana tare da farin cikinta, kashiga gari ka nemeta dan kuwa ba'a samun macce kamar safna mai tsananin baiwa a kyauta, batare da ansha wahala ba."
Akwai farin ciki a tsakaninku akwai wani haske a tsakaninku itace komai naka itace majinginin rayuwarka kamar yanda mahaifiyarka ta fad'a Dan haka ya zama dole kashiga gari ka nemo safna a duk inda take."

Cike da mamaki yake kallo dattijiwar yace "Inna dama kinsan mahaifiyata ne?"

Murmushi ta saki tace "yanzun ba lokacin wnn tambayar bane katafi kaje kayi abinda nace,

Cikin sauri ya mik'e tsaye batare da yamata musuba, ta mik'a masa key din motarsa ya bud'e yashiga ya tayar ya dauki hanyar gida."

Hankalin Sarki idan yayi dubu to ya tashi, a lokacin da labari yazo masa cewar sauban yafita da mota shikad'ai snn koda yafita baya cikin natsuwar shi, hankalinsa bakaramun tashi yayi ba sai zufa yake gogewa a kai akai, yana kiran wayar sauban din kashe take."

hankalin kowa a tashe har magariba sauban baidawoba,
Saudat sai kuka takeyi tana fadin tabani ta lalace, sadaukinta ya b'ata

Sarauniya Jamila sai murna takeyi domin duk a tunaninta asirin da tamasa ne ya fara aiki a kansa sai fad'i takeyi daga can sai bangon duniya."

Ana kiran sallar insha'i sauban yana shigowa gidan,
anan take labari yasami Sarki cikin gaggawa yatura a Kira masa shi,

tun kafin yashiga b'angarensa umurnin kiran mahaifinsa ya sameshi,
Ya juya ya fasa shiga part din nasa yanufi wurin mahaifinsa."

Fad'a sosai Sarki yake masa akan fitar da yayi batare da izininsa ba, snn Ina yatafi?"
Sunkuyar da kai k'asa sauban yayi yace "Abba kayi hakuri kauyen gidan gona natafi domin na duba safna, saboda tun lokacin da kacemun ta mutu hankalina ya tashi nakasa samun natsuwa har sai da natafi k'auyen da kaina."

Mari Sarki ya tsinkawa yarima abinda baitab'a yimasa ba tinda aka haifesa, cikin fushi yace "wato ni k'arya nafad'a maka kenan KO?
Wanda har yasaka sai da katafi da kanka kayi bincike, akan shegiya marar asali."

Sauban yana Rik'e da kunci kansa sunkuye a k'asa,
Yace "Abba kayi hakuri na tuba baxan sakeba, amma tafiyar da nayi nasamo labarin Safna tana raye bata mutuba tana cikin garin nan na adamawa."

Sarki ya kuma har zuk'a yace "wallah tallahi na rantse da Allah bazaka auri shegiya marar asaliba kana matsayin d'an gidan sarauta, kai ko bayan raina ban yafe ka aureta ba, Kai koda mutuwa zakayi a kan sonta gara ka mutu na d'auki gawarka na binne a cikin cikin k'asa, da hannuna *TIRK'ASHI* zaro ido sauban yayi idonsa yana fitar da hawaye abinda Sarki baitab'a ganiba akan idon d'ansa cikin sakan d'aya sauban ya zube a wurin bakinsa yana zubar da jini da hancinsa,

Cikin dakewar zuciya Sarki yakira fadawa yace ku d'aukeshi kuyi asibity dashi gani nan zuwa yanzun."

*************************

Alhmdulillah jikin safna tasami lafiya sosai inda take samun kulawa a wurin Hajiya falmata, da Alhaji Habib naira inda suke janta a jiki suke jikinta tamkar yarsu wacce suka haifa da cikinsu,

Ganin tasami lafiya likita yabasu sallama Hajiya falmata ta Rik'a safna suka nufi gidanta da ita dake cikin garin na adamawa,
Sosai Hajiya falmata ta gyara safna da kanta ta zuba mata ruwan wanka tare da turarunka masu k'amshi ta, tanuna mata duk yanda zatayi amfani da duk abinda ke cikin toilet din,
Bayan safna tayi Wanda tayi brush hajiya falmata tashiga wanke mata kanta da mayunkan wankin kai, anan take gashin safna ya fara haske da gyalli, yazubo mata har a gadon bayanta,

Masha Allah Hajiya falmata tace tana kallon safna cike da sha'awa da burgewa, ta rungumota zuwa jikinta suka fito daga toilet din,
Da kanta ta gyara mata gashin ta saka ribon ta daure matashi, snn Tashafa mata Mai ajikinta tayi mata kwalliya ba mai yawaba, ta d'auko wata doguwar rigar abaya bak'a cikin wad'anda akayi mata odarsu daga Dubai kasancewar itace sa'arta, tasakawa safna tare da d'aura mata d'ankwalin, Masha Allah kuzo kuga yanda safna tafito tayi kyau gaba d'aya Annurin fuskarta da kyawonta da kwarjinita duk sun bayyana,
Babu abinda Hajiya falmata kecewa sai Masha Allah,
Kunya ta kama safna tasaki murmushi ta rik'a hannun Hajiya falmata wacce take Kira da umma, tace "umma nagode Allah ya faranta maki kamar yanda kike k'ok'arin farantamun yanda kika taimakeni kema Allah zai taimaki ya k'ara d'aukakaki"

Dam gaban Hajiya falmata ya fad'i, yanda taga safna tana murmushi tamkar Alhaji Habib ne mijinta yake murmushi a gabanta, yanda safna take magana tana rausayar Kai hakan Alhaji Habib yake magana wani lokacin har kwaikwayonsa takeyi, kuma kallon fuskar safna tayi sai gani tayi ta koma Mata sak mijinta Abin k'aunarta Alhaji Habib, wani murmushin safna ta kuma Saki Wanda yasaka har k'oranta suka bayyana, a k'asan leb'onta Hajiya falmata taci Karo da wani tabo Wanda harta mutu baxata manta da wnn tabonba a bakin sulaihat 'yarta, Wanda tabon na gadone gadarsa tayi a wurin mahaifiyarta."

Da sauri Hajiya falmata ta mik'e tsaye cike da firgici





[3/30, 9:56 PM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 35*






A kan gadon Alhaji Habib Naira ya nufa ya nemi wuri ya zauna a gefen gado, ya Rik'o hannun safna yana kallo,
tabbas komai nata irin nasane yace zonan 'yata ya janyota zuwa jikinsa ya d'ura kanta akan kafad'arsa yana fad'in "hak'ik'a ke 'yatace ke jina nace na tabbata hakan tun ranar da nafara ganinki a asibity jikina yabani ke jinina ce.",

Ya kalli Hajiya falmata yace "Hajiya kinga yanda Allah yake nasa iko, 'yarmu tadawo garemu cikin ruwan sanyi, bayan munshare shekaru muna nemanta, ya d'aga hannu sama yana fad'in Kai Alhamdulillah Allah mungode maka."

Kuka Safna ta fashe dashi, ta tashi daga kan jikin mahaifin nata tace "Abba umma meyasa kuka jefar dani a lokacin da nake neman taimakonku? Menamaku kuka watsar da rayuwata a gefen hanya, bakuyi tunanin halin da Zan shigaba na tsakanin mutuwata da rayuwata."

Janyo ta Hajiya falmata tayi tana lallashinta tace "Suhailat shine ainahin sunanki Wanda mahaifinki ya nad'a maki, a ranar sunanki kasan cewar ke kad'ai muka mahaifa a duniya kuma tin daga kanki bamu kuma samun wata haihuwar ba ."

Mahaifinki yanada Mata biyu nice Amaryarsa uwargidansa Allah ya Mata rasuwa a sanadin ciwon hawan jini Wanda baya rasa nasaba da rashin haihuwar da Allah bai bata ba."

Ranar juma'a aka haifeki a babbar asibityn kud'i dake garin nan na Adamawa,
ranar da aka haifeki a ranar mahaifinki da duk wasu masoyinsa sai da suka tayashi murnar samun haihuwa da akayi masa a gidansa, Wanda sun san ita kad'aice Allah bai bashiba amma duk wani jin dadi na duniya mahaifinki yana dashi."

Anan take haihuwarki ta zagaye garin Adamawa dama wajenta domin mahaifinki babban mutum ne ya tara dukan komai a rayuwa uwa uba ga taimakon talakawansa."

Ranar sunanki, a ranar munga duban jama"a wadan baki bazai iya fad'ar iya adadin mutanen da suka halarci bikin sunanki ba,
Kafafen yad'a labarai kuwa ko ta ina watsa hotunanki akeyi ana sambarka."

washe garin sunanki misalin k'arfe uku na dare kina tare da mahaifinki akan gado d'aya,
kasancewar dake yake kwana akan kirjinsa sai dai idan kikayi kuka na farka nabaki nono kisha ya kuma karb'arki ya d'ora akan k'irjinsa, yana matuk'ar ji dake Wanda yakai baya iya b'oye soyayyarki a duk inda yake."

Kwatsam na kammala baki nono kenan na mik'awa mahaifinki ke ya rungumeki,
sai ganin mutane mukayi a gabanmu Rik'e da bindigogi dukansu fuskarsu a rufe take basa da kyan gani saboda girman halittarsu,
Hannu suka mik'awa mahaifinki suna fad'in kabamu ita,
Ita kad'ai mukeso, bamason komai naku."
Idan ba hakan ba zamu kasheku dukanku mu d'auketa mutafi da ita."

Babu irin magiyar da mahaifinki baiyi masuba akan suyi hakuri zaibasu duka abinda ya mallaka a duniya, amma sukace sam basaso ke sukeso sutafi dake,
Narasa dalilinsu nayin hakan,
Anan mahaifinki yaga da gaske tafiya zasuyi dake ya rungumeki yana fad'in sai dai sukashe shi amma baxai bayar dakeba,

Babban cikinsu ya saita bindiga ya harbi mahaifinki a k'afa Wanda idan kika lura da tafiyarsa baya tafiya dai dai kamar yanda kowa yakeyi,
Tunda naga sun harbi mahaifinki jini yana fita a k'afarsa na fad'i wurin na suma ban kuma sanin abinda yafaru ba,

ashe mahaifinki anan shima ya fad'i ya suma yana rungume dake gam a k'irjinsa."

Bamu kuma sanin abinda yake faruwa ba sai dai muka farka muka ganmu kwance akan gadon asibity babu ke babu labarinki suntafi dake."

Tafiya dake da sukayi bak'aramun tashin hankali ya janyoba domin duk wani a halinmu da masoyanmu sai da suka shiga cikin tashin hankalin b'atanki."

Bayan komai ya lafa aka barwa jami'an tsaro aikinsu sukaci gaba da bincike lungu da sak'o shuru ba wani labari mai Kama da ansan inda kike."

A kullum inaji a jikina baki mutuba zaki dawo garemu dan hakan duk abinda na mallaka da sunanki a cikinsa hakan mahaifinki."

Bayan shekara biyar da b'atanki kishiyata hajiya Nana na kwanta ciwo anan take ta shiga tonawa kanta asirin cewa "itace tasaka yan fashi suka saceki suka jefar dake a can nesa da gari, saboda batason ta bud'e ido ta ganki saboda irin son da mahaifinki yake nunamaki tasan duka dukiyarsa kice zaki mallaki rabinta, bayan ita Allah baibata haihuwarba,

Anan Tafara neman yafiya a wurinmu dani da mahaifinki muka dinga kuka,
Domin mahaifinki yana tsananin son hajiya Nana da tausayinta musamman rashin haihuwar da batayiba, sosai yake nuna Mata k'auna da tausayi wani lokacin har tunani nakeyi yafi sonta a kaina,
Amma da irin wannan sakamakon zata saka mashi,
Kuka mukeyi sosai a wurin muna tunanin wanne irin girman laifine muka mata Wanda yakai zata saka a k'arb'e mana tilon yarmu."
muna wurin Allah ya k'arb'i rayuwar Hajiya Nana, tana neman yafiya a wurinmu."

Suhailat Kinji dalilin rabuwarmu dake, Suka rungume juna gaba d'ayansu cike da k'auna da farin ciki juna"

Bayan komai ya lafa Safna tabasu labarin duka rayuwar da tayi tun tashinta har zuwa girmanta har kawowa lokacin da umma ta bugeta a mota,
bata b'oye masu komai ba har irin taimakon da sauban ya mata da fagen shad'in da yashiga ya taimaketa bata auri barde ba."

Sosai suka tausaya mata sukaji dad'in taimakon da sauban ya mata anan take Alhaji Habib yaji sauban ya shiga ransa koda baisan kowaye shiba."
Sunyi jimamin mutuwar Baba Wanda ya rik'eta hannu biyu, inda Alhaji Habib ya d'auki Arwashin zaiyi bincike akan mutuwar Baba yaji yana raye ko ya mutu."

Bayan kwana biyu gidan yacika da farin cikin bayyanar Suhailat inda yan uwa da abokanan arziki sai zuwa sukeyi suna masu barka da arziki inda duk Wanda ya kalli safna yasan jinin Hajiya Laila ce da Alhaji Habib."

Waya Alhaji Habib ya d'auka ya danna lambar sarki domin ya shaida masa bayyanar 'yarsa Suhailat."

Sosai sarki yayi murna dajin hakan daga nan yake shaida masa cewar shima d'ansa sauban yana asibity akwance rai a hannun Allah yana tsakanin mutuwa da rayuwa."

Subahanallahi Alhaji Habib yace tare da cewa "meyake damunsa?"

Sarki ya sauke ajiyar zuciya yace "ciwon soyayya yakeyi, soyayyar ma ta wata yarinya shegiya marar asalima, kaduba ka gani Alhaji Habib ina matsayin Sarki Wanda ya tashi a gidan sarauta gidan asali mai cike da tarihi Mai kyau ace d'ana Wanda nafi k'auna,
yakeso ya ruguzamana komai namu yashigo mana wata al'ada Wanda tinda aka haifeni tun zamanin kakan ni da iyaye bantab'a ganin d'an Sarki ya auri shegiya marar asaliba."

Alhaji habib yace "kayi hakuri ranka ya dade kasan yaran yanzun ka haifesu baka haifi halinsuba, ni dai shawarata anan itace kabashi abinda yakeso domin wnn al'adar masarauta ce ba Addiniba,
kasani marayuma ya'yane ba laifin yarinyar bane laifin iyayenta ne da suka haifata bata hanyar sun nah ba,

Kabawa sauban abinda yakeson hakan shine kwanciyar hankalinka da nasa,

Sarki dake tsaye a gefen gadon sauban Wanda aka sanyawa oxygen domin janyo numfashinsa Wanda gaba d'aya baya motsi, ko hannunsa baya motsawa tamkar matacce hakan yake."

Yake cewa Alhaji Habib nariga da na rantse sauban baxai auri shegiyaba marar asali, sai dai ya mutu na binnesa da hannuna, akan na zubar da 'yancin masarautata da asalinta."

Wani irin tari sauban yayi Wanda jini ya fara zuba a bakinsa,
Wani k'oton gudan jini sare ya fad'o a cikin bakinsa, yasaka Sarki yin jifa da wayar hannunsa cikin tashin hankali yanufi wurinsa yanakiran likita."
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 34*






A firgice itama Safna take kallon hajiya falmata ganin yanda take jifarta da wani irin kallo mai cike da tuhuma tare da firgici,
Kuma matsowa tayi ta rik'o hannun hajiya falmata tace "umma kiyi hakuri idan maganar danayi itace ta firgitaki bazan sakeba ki gafarce ni."

Kasa magana Hajiya falmata tayi illah taci gaba da kallon safna d'aya bayan d'aya,
Tabbas wannan Suhailat d'in tace tadawo gareta ashe bata mutuba Ashe tana da rabon sake rayuwa tare da tilon 'yar ta,
Wani irin kuka ta fashe dashi ta rungume safna suka fad'a kan gado a tare Wanda safna sai zarar ido takeyi hankalinta a tashe tarasa dalilin yin hakan."

Sosai ta rungume safna kamar wacce zata sub'uce mata sai shinshinarta takeyi tana share hawayen dake zuba a fuskarta,
Zaro ido kawai safna takeyi domin gaba d'aya kanta a d'aure yake tarasa dalilin wnn rungumar da umma take mata uwa uba ga hawaye da take gani suna fita a idonta."

Kalaman da taji umma tana fad'a tana kuka sune suka d'aure Mata kai tare da girgizata, suka sakata a rud'ani

"dama nasan zaki dawo garemu dama nasan baki mutuba na dad'e inaji a jikina baki mutuba "yata zaki dawo garemu nida mahaifinki muna matuk'ar kewarki tare da shaukinki, sulaihat ke yar muce naga alamomi da yawa a tare dake Wanda yake nuni da hakan,

Hawaye suke zuba a idon safna tana girgiza kai tace "umma kada kucutar dani dan kunganni banida gata, ku taimaki rayuwa kubarni nayi tafiyata k'auyenmu amma kada kuce ni 'yarkuce,
saboda a k'auye na tashi bansan kowa nawaba, Inna marikiyata ta fad'amun cewa iyayena cikin shege sukayi suka haifeni suka jefar dani a gefen hanya,
Sannan baba Wanda ya taimakeni yanuna son tamkar yarsa ya fad'amun cewa a gefen gari ya tsinceni anjefar dani ta yaya zakice ni yarkuce." Ku daina danganta kanku dani, kubarni nayi rayuwata batare kamar yanda kuke da nayar taimakona."
Wlh zanyi maku biyayya tamkar yarda kuka mahaifa amma ni ba 'yar kubace."

cikin d'aga murya hajiya falmata tace "suhailat ke yarmuce ke ba shigiya bace ta hanyar sunna aka haifeki,

Turo k'ofa akayi Alhaji Habib naira yashigo tare da sallama da gudu Hajiya falmata tasaki safna ta nufeshi ta rungumeshi tana fad'in Alhaji farin cikinmu yadawo garemu 'yarmu tadawo garemu, Suhailat dinmu tadawo itace muka taimaka,
hannu biyu yasaka ya rungume matarsa ya d'ora kanta asaman kirjinsa yana bubbugar bayanta yana fad'in daina kuka hajiya ki natsu kiyimun bayani ina Suhailat din take ne?"

Safna da tuni ta sulale tabar d'akin tin lokacin da taga umma ta fad'a akan jikin Abba ya kuma mayar da hannu ya rungumeta duk sai taji kunya ta kamata, anan take tana sharar hawaye ta sulale tafita tanufi d'akinta wanda umma tanuna mata acewar shine d'akin nata a nan zata dinga kwana."

Kai tsaye kan gado ta fad'a tasaki kuka mai sauti, kuka kawai takeyi tana sharar hawaye tarasa kukan da takeyi na farin ciki ne ko a kasin hakan,
Tabbas tinda Allah ya had'ata da wad'an nan mutanen takejin k'aunarsu irin ta iyaye ta shegeta, a lokaci d'aya tasamu kanta a cikin farin ciki marar misaltuwa,
Tasaka bayan Hannunta tashare hawayen fuskarta tana fad'in wanne dalili yasa suka d'aukeni sukabar garin nan dani suka jefar dani a k'auye a gefen hanya?'
Mena masu? Menatare masu suka jefar dani a dai dai lokacin da nake Neman kulawarsu?"

Sauban ya fad'o Mata a rai, ta fashe da kuka Mai sauti tana fad'in kazo gareni katafi dani, nasan kafi kowa sona da tausayi,
Mijina ko a wanne hali zaka shiga idan kaji nabar k'auye na b'ata ba'asan inda nakeba."
zamewa tayi ta kwanta tana kuka ta janyo fillow ta rungume tana tunanin fuskar sauban yanda yake murmushi mai nuna tsantsar tausayinta da k'aunarta,
Wasu daga cikin kalamansa ta tuna da yake cewa "Safna ki kwantar da hankalinki ki daina kuka ni Zan taimakekii zan zama gatanki zan d'aukeki a cikin k'auyen nan natafi dake cikin birnin Adamawa a cikin gidanmu na sarauta Zan baki farin ciki zan mantar dake rashin iyaye da kikayi.

hannu biyu tasaka ta damk'e fillow tare da runtse ido tana fad'in gani a kusa dakai a cikin garinku mijina ta yaya zanganka kacikamun Alk'awarin da kayimun, domin na tabbata kafi iyaye na tausayina da k'aunata." Tabbas dolene na bar gidan nan na shiga cikin gari lungu da sak'o domin na nemoka na zauna tare dakai na rayu dakai rayuwa ta har Abada."

Tana hakan wani irin bacci mai k'arfi ya Figeta Wanda bata shirya yinsaba."
Dattijiyar nan tagani bafulana wacce ta taimaketa a cikin daji, Wacce tasaba gani a duk lokacin da take cikin damuwa tana share mata hawayenta,a cikin baccinta
tsaye take a gabanta ta had'e fuska Sab'anin duk zuwan da take mata cikin murmushi take ganinta,wnn karon daga ganinta ranta a b'ace yake tsaye take a gaban Safna tana kallonta, wanda itama Safna ita take kallo,
cikin b'acin rai tace "meyasa zakiyi butulci ga iyayenki bayan kece farin cikinsu,
Iyayenki basuda laifi a sanadin b'atanki,
Kin bani mmki safna a maimakon kiyi farin cikin had'uwarki da iyayenki sai akasin hakan,
To kisani muddun Kika bar gidan nan da sunan guduwa zancire hannuna ga duk kan lamarinki Zan sakamaki ido, ina mai tabbatar maki mundun Kika gudu kikabar gidan nan zakiyi rayuwa Mai tsanani Wanda zaki gwammace gara zaman k'auye da ita.'


Hannu biyu safna ta had'e wuri d'aya alamar ban hakuri tana fad'in kiyi hakuri Inna bazan gudu ba,
Kifad'amun gaskiya Da gaske sune mahaifana?" Sune suka haifini?"

"Kwarai kuwa sune mahaifanki sune farin cikinki
Kema kece farin cikinsu."

Ta mik'a mata towel Mai had'e DA kayan sanyi masu shegen kyau tare da zanen da aka tsinceta dasu sanye a jikinta,

Kayan da ita dai safna tasan tabarosu a gida a cikin d'akinta,
Wad'anda ta rigada ta sadak'ar da sunriga da sun b'ata, saigasu a hannun wnn dattijiyar kirki Tana mik'o mata,
tace ga kayanki kirikesu a wurinki sune zasu kuma tabbatarwa iyayenki ke 'yarsu ce jininsu ce."

Karb'ar kayan safna tayi ta rungume a jikinta tana murmushin jin dadi domin taji dadin ganin kayanta wad'anda take ajiya da b'oyo tamkar kud'i."
d'aga kan da zatayi domin tayi Mata godiya sai gani tayi ta b'ace mata bako alamunta,

A firgice ta farka daga baccin da ya d'auketa abin mamaki ta ganta rungume da kayan jarintarta a jikinta.
Zaro ido tayi cike da mamaki ta rungume kayan tana zubar da hawaye."

A d'akinsu Hajiya falmata.
"Alhaji na rantse da Allah wnn yarinyar 'yatace Suhailat wacce tab'ata naga shaidu da alamomi wad'anda baxan tab'a mantawa a jikin 'yataba."

Shuru Alhaji habib yayi yana naxarin maganar matar tashi wacce take rungume a jikinshi, domin shima tun lokacin da yayi ido biyu da yarinyar yaji yana k'aunarta anan take yaji wani irin yanayi a tare dashi tamkar yana tare da jininsa yakeji."

Meye shedar taki wacce take nuni da 'yarki ce Hajiya?"
Ta tashi daga jikinsa ta zauna a gefen gado tace "Suhailat 'yata tun fad'owarta duniya na d'aga Kai na kalleta a lokacin da take tsala kuka a nan kalli bakinta har zuwa lebbonta naganta da tabo a leb'onta Wanda a lokacin sai da nanumaka kasancewar tabon gadon mahaifiyarmu ne, Wanda duk wata zuri'a tamu saika sameta da wnn tabon a gefen leb'o,
Suhailat 'yata tin tana jariri babu abinda ya banbataka da ita hatta 'yan yatsun hannunta dana k'afa duka nakane Kai ta d'ebo, musamman idan tayi mafarki tana dariya tamkar Kaine kake murmushi,
Yau naga duk abinda nake lissafa maka shi a tare da 'yata Wanda kaima kasan da hakan, Dan hakan katashi mutafi mugabatar mata da kanmu a matsayin mahaifanta domin 'yarmuce ba yar kowa bace."

Baiyi musuba hakan ya mik'e yabi bayan Hajiya falmata suka nufi d'akin safna,
Tura k'ofa sukayi suka shiga gaba d'ayansu tare da sallama."

Amsa masu safna tayi tana zaune a tsakkiyar gado rungume da kayan jarintarta."

Karaf idon su Hajiya falmata da Alhaji Habib ya sauka akan kayan wad'anda har su mutu bazasu manta dasuba a jikin yarsu wad'anda tana sanye dasu a jikinta a b'ata,
Kayan da Alhaji Habib yasayo da hannunsa a lokacin da ya tafi dubai, ganinsu yayi a jikin wata jaririyar balaraba suka bashi sha'awa sai da yashiga kasuwa ya nemosu yasaya a lokacin Hajiya falmata tana da tsohon ciki d'an wata tara."

A tare suka zaro ido suka had'a baki sukace Suhailat,
Hajiya falmata ta ruga ta rungume Safna tana fad'in wlh 'yar muce tadawo garemu Alhaji kaga zahiri KO."

Alhaji Habib murmushi farin ciki yakeyi y d'aga hannu sama yana hamdala a wurin ubangijinsa."
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *REAL PURE MOMENT OF LIFE WRITER'S*✍



🤴 *D'AN SARKI SAUBAN*🤴



Writing by
*UMMU SAFWAN*
( _Fareeda Basheer_)




*Page 36*






Shigowar Hajjah kenan a d'akin taga yanda gudan jini yake fita a bakin sauban Sarki yana kansa yana girgiza shi cikin tashin hankali yana fad'in "katashi sauban kada.mutu kabar mahaifinka,
Bintu ta mutu ta barni bana so kaima katafi ka barni."

Hankalin Hajjah a tashe tanufi ofice d'in likita cikin tashin hankali ta tura k'ofa tashiga tana fad'in likita sauban ya mutu yakazo ka taimakemu."

cikin hanzari likita ya ajiye biron hannunsa ya biyo bayan hajjah domin yatafi yaga halin da sauban yake ciki."

Sarki akan gadon sauban yana share masa jinin dake fita a bakinsa cike da tashin hankali yake cewa kada kamutu kabarni sauban katashi Zan baka dukkan abinda kake so."

Turo k'ofar da likita yayi, yayi dai dai da kuma turo wani gudan jini a cikin bakin sauba,
Cikin hanzari likita yanufeshi yashiga bashi taimakon gaggawa, ganin abin ya citura yakasa dawowa da numfashinsa gashi ga dukkan alama zuciyarsa ta kusan bugawa gaba d'aya ta daina aiki."

Ya juya ya kalli Sarki da hajjjah tare da safwan Wanda shigowarsa kenan, sai sharar hawaye yakeyi ganin mawuyacin halin da abokinsa yake ciki,
Likita ya bada umurnin duk sufita waje zaiyi aikinsa."

Hakan suka fita jiki ba kwari,
Hajjah ta kalli Sarki tace "umurni nabaka ba shawara ba, abawa sauban abinda yakeso idan ba hakan ba mudun sauban ya mutu bazan b'ata yafe makaba,
Dafe kai sarki yayi ya kalli mahaifiyar tasa hajjah yace "umma kiyi hakuri tun farko nayi kuskure danak'i goyon bayan sa akan abinda yakeso,
Da ace na Amince masaba da ba'a kawo hakan ba,
Nima nayi Alk'awarin duk inda safna take a cikin garin nan sai na sanya annemowa sauban ita ya aureta in har hakan shine samun lafiyarsa da kwanciyar hankalinsa."
Ya juya ya kalli Safwan yace
"Safwan kanada hoton ita budurwar abokin naka?"

d'aga Kai Safwan yayi alamar eh cikin yanayin rashin k'arfin jiki,
Yaciro wayarsa a Aljihunsa ya shiga ma'ajiyin hotuna yashiga kamo hotunan safna Wanda ya d'aukeso tareda sauban suna cikin farin ciki a k'auye,
Ya nunawa Sarki, Sarki ya karb'a yana kallo ya fahimci yanayin da suke ciki a lokacin da akayi masu hoton ya tabbatar da bak'aramar shakuwa bace tashiga tsakanin sauban da yarinyar dibon yanda yake murmushinsa Mai tsada Wanda bakoda yaushe yakeyin irinsa ba sai idan yana cikin farin ciki, ya girgiza kai ya mik'awa Safwan wayarsa,
Snn ya juya yakira bafadensa na hunnun damarsa yace kaje Safwan yatura maka duka hotunan sauban da yarinyar da

Please Login or Register in order to submit comment