Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kuka tace "saboda bana jure ganin wata a tare da kai, Zan iya aikata komai ga duk Wanda nagani atare dakai yana rab'arka sadaukina Ina sonka."

Runtse idonsa yayi ya rasa abinda zaice Mata domin duk yanda yake tunani Saudat ta wuce nan,
Lallab'ata yashigayi har yasamu tashiga toilet domin tayi wanka,
Anan yakira bayinta suka gyara mata d'akin tare da kawo mata abinci,
Koda tafito daga wurin wankan ta tarar angyara d'akin yana zaune a inda tabarshi sai kallonta yakeyi,
Mai kawai ta shafa ta dauko doguwar rigar bacci tasaka tafesa turare,
Murmushi yasaki ya mik'amata hannu alamar tazo gareshi wurinshi tanufa tafad'a kan jikinsa, cikin dabara yasamu taci abinci snn ya kwantar da ita, tare da lullubeta da bargo, yasakar mata kiss a goshi yana mata saida safe,
Idonta yacika da hawaye tayi saurin runtse idonta tana fad'in "karik'emun Amanata kada ka kwanta da ita,
Murmushi yasaki yace "kada kidamu my luv kiyi bacci kawai saida safe, yana kaiwa nan ya juya ya fita."

Sunanda yakirata dashi my luv yafi komai Sanyaya mata rai,KO bKomai tanada wani matsayi Mai mahimmaci a rayuwarsa."

********************

Tafiya yakeyi zuciyarsa tana Mai tsananin tausayin Saudat, domin Saudat tana sonshi sosai soyayyar da baya iya fassarata,bare misaltata
Kai tsaye part d'insa yanufa, tin a bakin k'ofar shiga yaji wani irin kamshi mai dadi ya dakar masa hannci, murmushi yasaki domin ko ba'a fad'a masaba Safna ta iso gareshi tana ciki,

Kai tsaye d'akinsa yanufa ya sanya k'afarsa cikin d'akin yaji wani kalar k'amshi na daban ya kuma ratsashi lumshe ido yayi yana furta "Alhmdulillah."

Motsin shigowarsa da kuyangi sukaji cikin sauri suka mik'e tare da yimata sallama suka fita."

Cigaba da tafiya yayi har yazo bidrom ya sanya k'afa yashiga tare da sallama,
A bakin gado ya hangota zaune ta rufe fuskarta da Alkyabba,
Ajiyar zuciya ya sauke wacce baisan lokacin da yasauketaba ya k'afe
Idonsa akanta yana hango kwalliyar fuskarta wacce ta k'awata Mata. fuska idan bai mantaba rabonda ya Sanyata a ido tun ana sauran sati biyu bikinsu."




_kuyi sorry banida chagi ya sin_🤒🤒
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *DAN SARKI SAUBAN*



*BY*
*UMMU SAFWAN*
( FAREEDA BASHEER)




*49*





A Cikin ruwan zafi yasakata ya gasa Mata jikinta sosai yanda zata sami sassauci daga rad'ad'in zafin da takeji, snn sukayi wankan tsarki a tare ya d'aukota suka fito."

Akan kujera ya ajiyeta ya d'auko jallabiyarsa a cikin wedrup ya saka mata,
Snn yaje kan gadon ya cire zanen gadon da suka b'ata ya canza wani, ya d'auketa ya kwatar da ita akan gadon shima ya kwanta a bayanta ya janyo bargo ya rufesu tare da Janyota zuwa jikinsa ya rungumeta cike da so da k'auna yana shafa kanta tare da bayanta alamar lallashi yana sakar Mata kiss a duk inda bakinsa ya kai,
Jiyakeyi kamar ya mayar da ita ciki akan so da k'auna."

Suna hakan har bacci mai dad'i ya d'aukesu sune basu farkaba sai ana kiran sallar Asuba, shine ya fara tashi yayi yashiga toilet yayo arwala,
Snn yaje ya tayar da ita jikinta yaji ya d'auki zafi sosai, ya zaro ido waje tare da furta ya salam ya kai zaune a gefen gado dafe da goshi,
Yarasa taimakon da zaimata zazzab'in jikinta ya sauka wanda dashi ta kwana gashi ta tashi dashi,
Wayarsa ya d'auka ya dauka ya kira family doctor dinsu ya shaida masa yana nemansa yanzu a part dinsa."

Docter ya shaida masa cewa gashi nan zuwa insha Allah
Snn ya kashe wayar ya d'auko sallaya ya shinfid'a ya tayar da sallah domin baya iya fita zuwa masallaci ya bar Safna a cikin wnn halin na tsananin zazzab'i ba."

Bayan ya kammala yin sallar ne
ya taimaka mata itama tayo arwala ya dorata akan sallaya yaje ya zauna yana kallonta har ta kammala yin sallar snn ya d'auketa cak ya d'orata akan gado yabi bayanta, suka kwanta tare da cire Mata duka kayan jikinta shima ya cire nashi ya had'e jikinsu wuri d'aya yana gogamata jikisa a nata yanda zata sami sassauci daga zafin da jikinta yayi."

Matseta yayi gam a jikinsa yana sauke nishi idonsa a rufe domin ya Fara fita hayyacinsa jijiyarsa ta mik'e tana neman agaji,
Gaba d'aya laushin jikin safna da k'amshinta uwa uba dukiyar fulaninta dake tsaye wacce ta tokare masa k'irjinsa yanajin laushinta da taushinta a kirjinsa, anan take wasa ta canza salo ya Fara shafarta yana sumbatarta a duk inda yaci Karo a jikinta."

K'arar kwankwasa kofar dayaji itace tadawo dashi a cikin hayyacinsa,
Ajiyar zuciya ya sauke da k'arfi,
ya Lallab'ata sannu a hankali ya sauketa Daga jikinsa ya janyo bargo ya rufeta,
Snn ya sauko daga kan gadon tare da janyo jallabiyarsa yasaka ya yafita domin ganin ko waye."

Kuyangin Safna ya gani a tsaye, tsaye
Suna ganinsa ya fito da kansa fuskar nan a had'e ba Fara'a a tare dashi domin baiga dalilin kwankwasa masa kofaba da sanyin safiyar nan yana tsaka dajin dadinsa,

Saurin zubewa k'asa sukayi suna gaidashi cike da girmamawa, hannu ya d'aga masu bai tanka masu ba, Wanda hakan ba halinshi bane, cikin dasanshiyar murya Mai cike da jarumta da sarauta yake tambayarsu "meyafaru ne?"

Had'a baki sukayi sukace "ranka ya dad'e munzo ne zamu tafi da Gimbiya Safna domin mu shiryata lokacin yin wankanta yayi."

Idan kuma anan takeso muna Neman izini a wurinka zamu shiga mu shiryata domin tafe muke da duk wani abin bukatarta."

Kallonsu yayi d'aya bayan d'aya
D'aya daga cikinsu yagani rumgume da wani d'an k'aramun kwati Wanda baya rasa nasaba kayan Safna ne a cikinsa,
Hannu ya mik'a mata alamar tabashi kwatin,
Jiki na rawa ta mik'a masa,
Ya kuma had'e fuska ya kallesu yace kuna iya tafiyarku domin baxaku gantaba,
Yana kaiwa nan ya juya yashige ciki tare da rufo k'ofa."

Kallon juna sukashigayi suna mamakin wani sabon salo Wanda yarima ya fito dashi a wnn karon,
Sukashiga tsegumin lokacin da aka kawo Saudat washe gari shine ya Fara nemansu domin sufita da saudat daga dakinsa sutafi da ita sugyarata."
D'aya daga cikinsu tace "tafd'ijam hali ba d'ayaba."

wurinta ya nufa wacce take kwance a inda ya barta, ya d'auketa cak yanufi toilet da ita dama ba komai a jikinta,
Wanka ya mata ya kuma gasa Mata jiki da ruwan zafi snn ya d'aura mata towel yafito da ita ya d'orata akan kujera ya shafa Mata Mai snn ya d'auko a kwatin kayanta ya bud'e ya dauko kayanta ya shiga saka Mata cike da tausayinta, tsaf ya shiryata cikin atamfarta riga da zane Wanda lunkin ya Mata kyau a jikinta, sai kallonta yakeyi yanaji kamar ya had'iyeta akan so,
Wanda ita kuma zazzab'in jikinta yafi komai damunta,
a cikin zuciyarta kuma tanajin dadin kulawar da Sauban yake bata musamman idan ya d'orata akan jikinsa, tanajin dad'i da sanyin lallausar fatan jikinsa tare da k'amshinsa Mai dad'i."

akan kujera ya ajiyeta yana murmushi tare da yimata kiss a goshi yana fad'in baby kinyi kyau zauna akan kujera kwanciyar ta isa hakan tare da kashe Mata ido d'aya, Wanda baisan lokacin da ya iya hakan ba,
Yace kid'an kijirani minti goma Ina zuwa,
Ya fad'a toilet yayi wanka yafito,
Koda yafito har angyara d'akin anjera masu break fast a kan dining, Wanda aikin hajjah ne ta turo a kawo masu."
Yasaki murmushi yashiga shirya kansa."

Manyan kaya yasaka kaftani Wanda yaji d'inki irin na masarauta,
Yayi kyau sosai Wanda safna takasa d'auke idonta akansa sai kallonsa takeyi tana murmushi a fuskarta."

Bayan ya kammala shiryawa ne, yaji ana kwankwasa k'ofa,
Cikin sauri yaje ya bud'e, likita yagani a tsaye,
Murmushi yayi ya bashi hannu suka gaisa sannan yayi masa izinin shigowa
da sallama likita yashiga yana bin bayan sauban,
a falo sauban ya tsayar dashi tare da nuna masa kan kujera alamar ya zauna yajirashi yana zuwa,

Saida ya sakawa safna hijabi snn ya Rik'ita ta mik'e tsaye sannu a hankali take tafiya tana d'an runtse ido domin zafin da takeji ak'asanta ba kad'an bane,

A Kan kujera ya ajiyeta shima ya zauna a kusa da ita snn yashiga fad'awa likita abinda yake damunta,
Ya d'ora da cewa amaryace jiya aka kawota."

'Yar dariya likita yasaki domin ya fahimci abinda yake damun safna tun daga yanayin tafiyarta da yagani,
Snn ya shiga rubuta magani a cikin yar takarda, ya mik'awa sauban yana fad'in asawo mata wnn insha Allah zata sami lfy,
snn ta dinga shiga cikin ruwan zafi komai zai dai daita Allah ya bata lafiya,
Sauban ya amsa da Ameen."
Snn likita ya mik'e yafita."

Yana ganin fitar likita ya duk'a ya d'auki safna kamar jaririya yana fad'in mutafi muyi break fast nasan kinajin yunwa tun jiya bakici komai ba,
Murmushi tasaki tare da kallon fuskarsa ta kuma lafewa akan faffad'an kirjinsa,
Shima fuskarta yake kallo har zuwa d'an karamun bakinta,
yana sakar mata murmushi,
Rufe idonta tayi cike dajin kunya, Wanda hakan yasakashi sunkuyar da kansa ya cafko bakinta yashiga tsotsa yana d'auke da ita a tsaye."

Sautin k'ara mai cike da ihu yaji,
A firgice yayi saurin cire bakinsa a cikin na safna ya juya da sauri domin ganin KO meye,
Saudat ya gani dafe da zuciya tana nunasu tare da zaro ido tana sauke shed'a sama sama kamar wacce tayi wasan gudu."

K'ok'arin sauke safna yakeyi ya tafi gareta safna tasanya hannu biyu ta lank'ameshi gam alamar bazata saukaba,
Hakan yatafi da ita gaban Saudat wacce tayi saurin runtse idonta domin batason ganin wata macce dauke a jikin mijinta tana addu'a Allah yasa mafarki takeyi,
sautin muryarsa taji yana kiran sunanta da sauri ta bud"e ido ta tabbatarwa da kanta sadaukinta ne dauke da wata macce Wacce ba itaba, a iya zaman da sukayi dashi bai tab'a d'aukarta hakan ba,
Da gudu ta juya tafita tana kuka."

Ajiyar zuciya sauban ya sauke snn yajuya yanufi bidrom da safna,
Yashiga zuba masu break fast,
Bayan sun kammala karyawa ya kwantar da ita akan gado, tare da lullub'eta yanafad'in kiyi bacci beauty bara natafi nasawo maki magani tare da shafa gefen fuskarta ya juya fita."

A bakin k'ofa yaci Karo da Safwan, yana k'ok'arin shigowa,
sauban kuma yana k'OK'arin fita,
Tare Safwan yayi ya hanashi shiga d'akin tare da jifarsa da wani wani irin kallo na bakada hankali,
Ya had'e fuska tam ba alamun wasa a tare dashi ya cewa safwan"malam lafiya kake k'ok'arin shiga d'akin mutane Kai tsaye batare da neman iziniba."

Dariya Safwan yasaki yana fad'in "Allah yabaka hakuri, so kake kafad'amun Daga yau idan zanshiga d'akinka na tsaya a waje sai kabani izini snn zanshiga?",

Harara sauban ya wurga masa bai tanka masaba,

Safwan ya kuma sakin dariya yana fad'in "haba abokina ai na fahimceka fitowa fili zakayi kafadamun cewa jiya ka gane hanya shiyasa naga kana wani zuru zuru da ido kamar Wanda yayi k'arya,
Nidai Addu'ata D'ayace Allah yasa bakayiwa yar mutane I'llah ba,

hannunsa ya Kai ya karb'i takardar maganin dake hannun sauban yana fad'in takardar meye a hannunka,
Banza sauban yayi dashi bai tanka masaba,
Wata irin dariya Safwan yasaki yana fad'in jarumin maza kace kayi yak'i jiya,
A'a koma ka kwanta ka huta bara natafi nasawo maka maganin."
Baijira amsar da sauban zaibashiba yayi gaba yana dariyar mugunta."

Harara sauban yabishi dashi tare da mere baki ya ja dogon tsaki yana fad'in "ayi mutum da shegen saka idon tsiya, ga surutu bakinsa KO gajiya bayayi, ya ja dogon tsaki yanufi part din Saudat."

Kuka takeyi sosai hankalinta a tashe yake, musamman wayar da tagamayi da mahaifiyarta yanzun take shaida mata cewa itama mahaifinta yayi aure maganar da take fad'amata a halin yanzun har Amaryar ta fara laulayi Dan hakan yanda tayi hakuri ta zauna da kishiya itama dole tayi hakuri ta zauna da ta ta kishiyar,
Kuka sosai Saudat takeyi tana cewa ita batasan wani abu wai shi hakuriba,
Abinda tasani d'aya ne duk abinda takeso a duniyar nan sai anyi mata shi, komeye shi, komai kudinsa komai muninsa komai Kyansa don hakan Dolene mommy kisan yanda zakiyi da kishiyata."

Dogon tsaki mommyn taja ta tsinke wayar cike dajin haushin Saudat, idan kura na maganin zawo da tafara yiwa kanta mana."

Kuka takeyi sosai zuciyarta tana k'una jitakeyi kamar ta cinnawa kanta wuta akan tsananin kishi,.sauban ya bud'e k'ofa yashigo,
Ido biyu sukayi da ita, karon farko da taji batason maganinsa, taji ta tsaneshi,
Cikin sauri ta d'aga masa hannu Cikin muryar kuka da bak'in ciki take fad'in kada kazo gareni kayi tafiyarka banason ganinka."

Zaro ido waje yayi cike da mamaki yana fad'in nine bakyason gani Saudat?'

Eh banason ganinka macuci azzalumi me kazo kafad'amun bayan abinda idona ya ganemun kafita nace."

Ya girgiza Kai cike da b'acin rai yafita zuciyarsa na k'ona."

*********************

Bayan sati d'aya,
Sati d'ayanda sauban yaci amarcinsa ya gane inda gabas take, ya tabbatar da ko a cikin mata suna suka tara akwai mace akwai muna mace,.
Wato mata daban daban ne akwai mace Mai dad'i akwai macce marar dad'i, snn akwai mace Mai wari akwai marar wari, shidai cikin satin nan ya shaida hakan,
domin a kullum sai yayi suman dad'i yatafi wata duniyar mai cike da abubuwan dad'i ya kuma dawowa, tabbas ya tabbatar da duk abunda safwan yake fad'a akan macce gaskiya yake fad'a."
Baiga lafin Safwan ba, domin shima zai iyafad'in fiye da abinda Safwan yake fad'a akan macce."

Yau girkin safna ya k'arewa kuyanginta sukazo suka tattara kayanta sukayi Mata rakiya zuwa d'akinta tana Mai cike da kewar mijinta abin sonta,"

Yau ranar girkin Saudat ne,
Tana sane da yau itakeda sauban amma tayi biris dashi taki zuwa dakinsa bare tabashi abinci ta kula dashi,
Shima yana kwance akan gadonsa Safna kawai yake tunani domin tana kuladashi tana riritashi k'aramar yarinya Mai hankalin manya,
Shuru har 11 ba Saudat ba alamunta ya tashi yafita yanufi part dinta,
Kwance take cikin kayan bacci masu d'aga hankali tana chat a wayarta,
Ganinta cikin kayan baccin anan take yajisa a cikin wani yanayi na buk'atuwa gaba d'aya safna ta sauyasa ya daina ka waici akan macce ya zama mutum wanda baya iya awa uku batare da macce ba,

Sannu a hankali Ya tako zuwa wurinta,
Wayar hannunta ya fisge yana jifarta da wani irin kallo Mai cike da shauk'in bukatuwa,

kyalesa tayi ta juya kwanciyarta tare da turo masa mazaunenta,
Kuma firgucewa yayi domin sak Safna yake ganinta idonsa a rufe suke,
Kai tsaye kan gadon ya fad'a ya rarumota yashiga aika Mata da sakonninsa masu wuyar fassara
Saudat abin nema yasamu domin bata iya fushi da sauban a wurin kwanciya ita kad'ai tasan sirrin abun
A nan take tashiga mayar masa da martani,
Tafiya tayi tafiya kamar yanda yasaba jinta yauma a hakan take, ya mutsa fuska yayi ya sauka a kanta bayan ya tabbatar da tasami gamsuwa,
Toilet yanufa ya wanke jikinsa yafito ya kwanta akan gado yana tunani aransa,
Tabbas akwai banbanci Ashe duk iya zaman da yakeyi da saudat yana cutuwa sosai bai saniba mararsa yaji ta kulle masa wuri d'aya ruwan da baifitar bane sune suke neman illatashi,
Yaja dogon tsaki ya tashi yafita yanufi d'akinsa yana neman ruwan Lipton domin ya sha, rabon da yasha lipton da lemun tsami tun zuwan safna gidansa
Dafe Kai yayi yana fad'in "akwai matsala Saudat batada lafiya ya zama dole na d'auketa mutafi asibity inason nasan abinda yake damunta, inaso likita yadibata ya gano meye matsalar."

A hakan Saudat ta kammala kwananta biyu a d'akin sauban, KO sau d'aya bata ga giftawar safna ba,
Wanda hakan ya Mata dad'i domin bata son ganinta Sam a rayuwarta,
Hakn itama Safna Saudat bata gabanta burinta d'aya ne tayaya zata farantawa mijinta yaji dad'i a rayuwarsa,
Ita har ga Allah bata d'auki Saudat a matsayin kishiyaba,
dai dai da rana d'aya bata tab'ajin wani Abu na kishinta ba a ranta, tadaisan mijinta yana sonta Dan hakan ya aureta ya kawota gidansa Dan hkn batada wani buri a ranta wanda ya wuce ta faranta masa a koda yaushe."
Sai dai ta d'auki Alwashin baxata shiga hurumin Saudat ba,
Amma muddun ita tashiga nata hurumin saita koya Mata hankali, domin abinda tasaka akayi masu a k'auye yana nan a ranta bata mantaba,

yau kwanan safna ya zagayo
Bayan ta kammala girkinta Mai dadi da d'and'ano Wanda tasan mijinta zaiyi farin ciki idan yaci,
Tashiga toilet ta shek'a wanka,
Kuyangi zuka shiga shiryata cikin shiga irinta sarauta wnn umurni ne daga yarima domin yaune zasu tafi zagayen cikin gida, tunda aka kawota basu tafiba har hajjah tasoma magana,
Shi kuma abinda yasa bai zagaya da itaba saboda yanda yaga yanayin jikin nata musamman washe garin kawota ba lafiya ce da itaba."

Shima shiri yayi cikin kayan sarauta yanufi d'akin nata ya rika hannunta suka fito kuyangi suka take masu baya suna zuba masu kirari,
fada suka fara zuwa suka Kai gaisuwa wurin Sarki yayi farinciki tare da yi masu nasiha da zaman Lafiya mai d'orewa
Ya kumayiwa sauban Albishir cewa ya zama cikin shiri banda gobe akwai wasan dawakai a can filin wasan doki domin tayashi murnar aurensa ya tabbatar d ya zama cikin shiri snn yafito tare da matansa da duk wasu masoyansa domin ayi kallo,
Godiya sukayiwa Sarki snn sukafito daga fada suka nufi wurin hajjah."
Sosai hajjah tayi farin cikin ganinsu,
Ta d'ora da tata nasihar akan Sauban yayi adalci a tsakanin matansa kada ya nuna yafison wnn da wnn,
Nan ma godiya sukayiwa hajjah suka fito suka nufi sashen matan Sarki,
K'annen sauban da iyayensu sunyi farin cikin ganinsu,
Sun karb'i safna hannu biyu domin safna yarinyace Mai girmama na gaba da ita anan take tashiga ran matan Sarki sukacikata da kyautuntuka na ban girma, snn sukafito suka nufi part din gimbiya jamila wacce tacika tayi fam akan jin haushin sauban Dan me ya Fara shiga part din kishiyoyinta, Bayan yasan itace gaba dasu, yaranta ne a gabanta sageer da Sadeeq sai fad'a take masu akan sunki fitar da matar aure duk Lokacin da ta sanya masu lokaci akan sufitar da matar aure har lokacin yazo ya wuce ba wani bayani,
Me suke nufine, KO so sukeyi sukasheta da sauran ranta,
Shigowar sauban da safna yasa tayi shuru daga fad'an da takeyi, ta tsura masu ido tana kallonsu d'aya bayan d'aya,
Ba laifi sundace da juna wnn karon bafulatana ya auro yarinyar akwai tsantsan kyau da kuriciya tashiga fad'i a ranta,
Wayancewa tayi tasaki murmushin yake tana fad'in "Ashe za'axo gareni"

Murmushin gefen baki sauban yasaki Wanda shi kadai yasan fanufarsa,
Safna ta durkusa a gabanta ta gaida ita cike da girmamawa gimbiya Jamila tasaki murmushin kasaita ta amsa Mata domin taji dadin durkusawar da safna tayi a gabanta,
Sauban kuma akan kujera ya zauna kamar yanda yaga saqeer da sadeeq a kai ya gaida ita yana fad'in "barka da gida gimbiya."

Dam gabanta ya fad'i dajin yakirata da gimbiya da yayi sab'anin Mama dayake kiranta dashi,
Murmushi tasaki tana fad'in yawwa barka d'ana baxaka duk'a kamar yanda Amaryarka tayiba."

Murmushin gefen baki yasaki ya kalli sageer da sadeeq yace "layi d'aya muke da k'annena,
Ta fahimci maganace yasakar mata wato baiga yaranta duk'e a gabantaba bareshi."

"Hakan yana da kyau tace,
Snn ta mayar da hankalinta akan safna tana k'are Mata kallo Wanda shima sageer safna yake kallo sama da k'asa a duniya bai tab'a ganin maccen da ta burgeshi kamartaba, bai tab'a ganin macce kyakkyawa kamartaba lallai ya zama dole sauban yasakar masa ita ya aura,
Itama gimbiya Jamila tunanin da takeyi kenan safna tayi matukar burgeta tabata sha'awa sai take tunanin inama a cikin yaranta suka sameta."

Sauban kallon yanayin ko wannensu yakeyi musamman sageer dayaga ya k'ure Safna da ido yana kallonta yana had'iyar miyau,
Yasaki murmushi tare da cije leb'onsa na k'asa ya mayar da idonsa a wurin gimbiya Jamila wacce itama safnar take kallo
Katseta yayi da cewa zamu wuce tunda baxakice komai akanmu ba."

Murmushin yak'e tasaki Wanda yafi kuka ciwo ta furta "Matarka tanada kyau kadace."

"Murmushi yasaki yace "nagode tare da mik'ar da safna tsaye ya rungumeta suka fara tafiya a hakan yana fad'in nabarku lafiya yafita yana murmushin mugunta,

Wani irin bakin ciki sageer yaji a lokacin da yaga sauban ya rungeme safna sunfita a hakan,
Ya mik'e tsaye a fusace yazo gaban mahaifiyarsa yana huci yana fad'in "mama kince na fitar da matar aure ko wacece ko yar wacece zaki auramun ita,
Yau naga yarinyar da nakeso har nakeji idan bansametaba Zan iya kashe kaina,

Gimbiya Jamila tace "wacece ita yar waye?

Sageer yace "wnn yarinyar da sauban yashigo da ita a yanzun har yake Kiran matarsa ce, k'arya yakeyi bata dace dashiba,
Bata dace dakowaba sai dani, nine ya kamata na auri kyakkyawar yarinya irinta nidai asan yanda za'ayi tadawo gareni idan ba hakan ba kowa zai rasa dagani har shi."
[3/30, 9:56 PM] Hayat: *DAN SARKI SAUBAN*



BY
UMMU SAFWAN
(FAREEDA BASHEER)




*48*





*******Taku yakeyi sannu a hankali cike da mulki da k'asaita yanufi wurin da take zaube a gefen gado,
idonsa akanta yana kallon kyakkyawar fuskarta, wacce ya tsinci kansa da kasa d'auke ido daga kallon nata sai murmushi yake saki a fuskarsa."
A kusa da ita yanufa ya zauna a gefen gado tare da sauke ajiyar zuciya Mai tattare da nishi, kamar Wanda yayi aikin wahala."

Safna tana ganin ya zauna, tayi saurin zamewa daga kan gadon ta durkusa a gabansa kanta a sunkuye tana fad'in "Yaya sauban Ina wuni cike da biyayya da girmamawa."

Murmushi yasaki cike da farin ciki ko ba komai safna tana girmamashi idan bai manta ba saudat bata tab'a sanya gwaiwoyinta zuwa k'asa domin ba, domin ta gaida shi,
saidai ta gaida shi a tsaye kamar zata fad'a kansa,
hannu biyu yasa ya d'agota zuwa kusa dashi yayi Mata maxauni a gefensa har cinyoyinsu gogar juna,
Yana fad'in "lafiya k'alau safnar baba yau gaki a cikin gidan mu, a cikin a halina,
Wanda nayi maki Alk'awarin Zan d'aukoki na kawoki cikin zuri'ata muzauna tare dake mutuwa kad'ai zata rabamu."

Ya sanya hannu ya bud'e rufar da tayi da fuskarta tare da gyara mata lullub'en Alkyabbar, anan take kyakkyawar fuskarta ta bayyana,
Ido ta d'aga ta kalleshi Wanda shima ita yake kallo,
Kallon juna sukeyi ido cikin ido cike da wani shauk'i Wanda baisan lokacin da ya fad'a a cikinsaba."

lumshe idonsa yayi tare da sanya hannu ya shafa gefen fuskarta yace "Amarya kinyi kyau, dole Umma ta hanani ganinki har na tsawon sati biyu."

Murmushi tayi Mai k'ayatarwa, ta janye idonta daga kallonsa ta sunkuyar da kai k'asa tana wasa da ya tsun hannunta cike dajin kunyarsa."

Shima murmushin yakeyi ya mik'e tsaye yanufi dining ya d'auko ledar kaxa ya zube a plate tare da fresh milk Mai sanyi ya dauko cup ya nufo wurinta dashi,
Tana ganinsa dauke da plate d'in a hannunsa tayi saurin tashi ta tarboshi ta karb'i plate din daga hannunsa yana murmushi ya mik'a mata,
A tsakiya center cafet Wanda yake a shinfide a gefen gado d'an matsakaici mai kyan gaske, a nan ta ajiye plate din, tayi saurin karbar cup din hannunsa tare da robar fresh milk din ta ajiye a kusa da plate din kazar,
Ta juya zata koma kan gado ta zauna yayi saurin Rik'o lallausan hannunta ta juyo tana kallonsa, shima ita din yake kallo ido cikin ido ya kasa furta kalmar komai a bakinsa sakamakon
Tsikar jikinsa dayaji ta tashi lokaci d'aya ya tsinci kansa cikin wani irin shauki na buk'atuwa Wanda baitab'a jin irin saba,
Hakan itama safna laushin hannun sauban ba karamun ta yar mata da hankali yayiba dama tunda Umma tabata wasu ruwa da tasha a lokacin da za'a kawota takejin kanta cikin wani yanayi na daban."

Da kyar ya fisgo magana a bakinsa tare da sakin hannunta yana fad'in Ina zakije zo nan ki zauna abinci zakici domin nasan yunwa kikeji ya kai k'arshen maganar yana sakar Mata murmushi tare da nuna mata kusadashi."

Sunkuyar da kai k'asa tayi tashiga takowa zuwa wurinsa ta zauna a inda ya nuna mata daf dashi har kafad'arsu tana gogar juna ta sunkuyar da kai k'asa alamar kunya takeji."

Plate d'in ya janyo ya matso dashi gabanta ya sanya hannu ya ciro cinyar kaza ya nufi saitin bakinta da ita,
Nok'e kafad'a tayi alamar bataci,
Ta furta na k'oshi cikin sanyin murya."

"Kin k'oshi mekikaci?

shuru tayi ba amsa."

Shurun da tayi ya tabbatar masa da bataci abinci ba tana tare da yunwa
Ya furta "bana son musu bare gaddama, ni mutum ne Wanda banason k'arya nafison a fad'amun gaskiya komai d'acinta."
Ya mik'a mata kaxar a bakinta yace karb'i kici."

D'an k'aramun bakinta ta bud'e ta faracin kazar yana bata milk tana kurb'awa,
A hakan saida ya ciyar da ita ya tabbatar da tak'oshi snn ya barta hakan
Snn shi ya faraci,
kad'an yaci ya

Please Login or Register in order to submit comment